Yaqini Media Hausa

Yaqini Media Hausa "Tsantsar gaskiya" shi ne takenmu. Domin samun sahihan labarai da ƙwarewa daidai da ta zamani da ba ku damar bayyana ra'ayoyinku.

𝐀𝐧 𝐆𝐮𝐝𝐚𝐧𝐚𝐫 𝐝𝐚 𝐭𝐚𝐫𝐨𝐧 𝐰𝐚𝐲𝐚𝐫 𝐝𝐚 𝐤𝐚𝐢 𝐤𝐚𝐧 𝐚𝐦𝐞 𝐦𝐮𝐡𝐢𝐦𝐦𝐚𝐧𝐜𝐢𝐧 𝐲𝐢 𝐰𝐚 𝐲𝐚𝐫𝐚 𝐏𝐨𝐥𝐢𝐨 𝐀 𝐣𝐢𝐡𝐚𝐫 𝐆𝐨𝐦𝐛𝐞-----------Daga: Aliyu Bala GerengiWa...
30/04/2026

𝐀𝐧 𝐆𝐮𝐝𝐚𝐧𝐚𝐫 𝐝𝐚 𝐭𝐚𝐫𝐨𝐧 𝐰𝐚𝐲𝐚𝐫 𝐝𝐚 𝐤𝐚𝐢 𝐤𝐚𝐧 𝐚𝐦𝐞 𝐦𝐮𝐡𝐢𝐦𝐦𝐚𝐧𝐜𝐢𝐧 𝐲𝐢 𝐰𝐚 𝐲𝐚𝐫𝐚 𝐏𝐨𝐥𝐢𝐨 𝐀 𝐣𝐢𝐡𝐚𝐫 𝐆𝐨𝐦𝐛𝐞
-----------
Daga: Aliyu Bala Gerengi

Wani gangamin wayar da kan jama’a kan yaki da cutar shan inna ya hada ‘yan jarida daga gidajen rediyo, talabijin da sauran kafafen yada labarai daban-daban a fadin jihar Gombe, domin karfafa yada sahihan bayanai da kuma wayar da kan al’umma.

Taron Wanda ya gudana a Dakin taro da Hotel don Laylah dake hanyar Kano, ya jaddada muhimmancin bai wa yara allurar rigakafin cutar shan inna sau biyu a kowane zagayen rigakafi, musamman yara masu shekaru daga haihuwa zuwa watanni 59.

Jami’an lafiya sun ce rawar da kafafen yada labarai ke takawa na da matukar muhimmanci wajen isar da sahihan bayanai ga jama’a tare da karfafa iyaye da masu kula da yara su rika kai yaransu wuraren rigakafi.

Sun kuma bayyana cewa allurar rigakafin cutar shan inna na da inganci kuma tana da matukar tasiri wajen kare yara daga kamuwa da cutar, wadda kan haddasa nakasa har abada.

Abokan hulda irin su World Health Organization da UNICEF na ci gaba da tallafa wa wannan shiri ta fuskar wayar da kai, kudi da kuma bayar da shawarwari na fasaha.

Wadanda s**a halarci taron sun bayyana aniyarsu ta kara kaimi wajen yada sakonnin da ke karfafa rigakafi da kuma kawar da jita-jita a cikin al’umma.

Gangamin ya jaddada cewa hadin kai tsakanin ma’aikatan lafiya, kafafen yada labarai da kuma al’umma baki daya na da muhimmanci wajen kawar da cutar shan inna gaba daya.

Farfesa Abdulla Uba Adamu ya sanar da yin ritaya daga Jami’ar Bayero Kano yana da shekaru saba’in, inda ya kawo ƙarshen ...
25/04/2026

Farfesa Abdulla Uba Adamu ya sanar da yin ritaya daga Jami’ar Bayero Kano yana da shekaru saba’in, inda ya kawo ƙarshen doguwar rayuwar hidima da kuma gagarumar tafiya ta ilimi da ta shafe kusan shekaru arba’in da shida yana yi.

Ya ce: “Tafiyar ta kasance mai wahala, amma cike da gamsuwa — saboda yadda na koyi yadda zan rungume shi.”

Ya ƙara da cewa: “Jami’ar Bayero ta kasance gidana na kusan shekaru arba’in da shida ba tare da hutu ba. Na shiga tsarin a ranar 24 ga Yuli, 1980 a matsayin malamin jami'a a mataki na farko (Graduate Assistant) a sashen Ilimi.”

Ya kuma riƙe matakai daban-daban har ya zama ɗaya daga cikin manyan malamai da ake girmamawa, inda daga baya ya taka muhimmiyar rawa wajen ƙirƙira Sashen sadarwa da yaɗa labarai a shekarar 2014.

Ya ce: “Na fuskanci ƙalubale, na yi tuntuɓe a wasu lokuta, amma a koyaushe ina sake ƙoƙarin tsayawa kan ƙafafuna don in ci gaba (da tafiya)”

Farfesa Adamu ya bambanta kansa a matsayin mai bincike, mai ba da shawara ga ɗalibai, kuma murya mai tasiri a fagen ilimi. Ayyukansa sun haɗa ilimi, nazarin kafofin yaɗa labarai, da al’adun zamani na dijital, lamarin da ya sa aka san shi a Najeriya da ma ƙasashen waje.

An san shi da zurfin bincike da hangen nesa mai faɗi.

Farfesan ya ba da gudunmawa sosai wajen bunƙasa nazarin sadarwa da kafofin yaɗa labarai a Arewacin Najeriya, inda ya zaburar da ɗalibai da malamai da dama.

Ya ce: “Ba na nadama kan hanyar da na zaɓa; domin tasa na zama nagartaccen mutum.”

Duk da cewa a farko ana sa ran zai karanci likitanci, sai dai Farfesan ya tsaya tsayin daka kan abin da zuciyarsa ke so.

Ya rubuta: “Na yi tunanin zan zama mai bincike a abin da yanzu ake kira kimiyyar dakin gwaje-gwajen lafiya (medical laboratory science), amma hakan bai tabbata ba. Duk da haka, yayin da ritaya ta gabato, sai na fahimci wani abu mai zurfi: cewa ina yin abin da daɗe ina fatan zama tun da farko— wato mai bincike.”

Ya ƙara da cewa: “Sau da yawa nakan tuna wata tattaunawa da na yi da mahaifina a shekarar 1972. Ya so na karanci likitanci. Ban yi hakan ba—ba don na raina shawarar ba, amma domin na san hanyar da zan ɗauka ba a nan take ba.”

Ya yi godiya sosai ga iyalansa, abokan aikinsa, da al’umma baki ɗaya kan goyon bayan da s**a ba shi na tsawon shekaru.

Ya kuma yaba wa matarsa, “wacce ta jure da irin mai da hankalina da nake kan kwamfutata, intanet, da yin bincikena.”

Sai dai Farfesan ya nuna ƙudirin ci gaba da aikinsa na ilimi, inda ya bayyana cewa kamfanin wallafa littattafai na Bloomsbury ya nuna sha’awa kan wasu littattafansa.

Ya ce: “Sha’awar bincike tana nan daram kamar da. Ina da ayyukan littattafai da dama da nake kan yi, kuma Bloomsbury ta nuna sha’awa a kansu.”
Ya ƙara da cewa: “Na yi ritaya ne ba don na gaji ba.”

Game da Farfesa Abdulla Uba Adamu:

Abdulla Uba Adamu farfesa ne a Najeriya, fitaccen masani kuma mai sharhi kan al’amuran jama’a, wanda aka san shi da gagarumar gudunmawarsa a fagen nazarin sadarwa, musamman a kan kafofin yaɗa labarai na Afirka, al’adun jama’a, da masana’antar finafinai ta Hausa (Kannywood).

An haife shi a jihar Kano a ranar 25 ga Satumba, 1954, kuma ya gina doguwar sana’ar ilimi mai tasiri a jami’ar Bayero Kano, inda ya yi aiki a mukamai daban-daban ciki har da zama mataimakin shugaban jami’a (Vice-Chancellor).

Haka kuma ya yi aiki a matsayin mataimakin shugaban jami’ar koyo daga gida (National Open University of Nigeria – NOUN) daga 2016 zuwa 2021.

Baya ga harkokin jami’a, ya kasance mai shiga cikin tattaunawar jama’a, yana ba da haske kan ilimi, tsokaci kan fasahar sadarwa da sauransu.

Bayan kusan shekaru 46 na hidima ba tare da yankewa ba a jami’ar Bayero Kano, ya yi ritaya bayan ya cika shekaru 70, inda ya bar gado na ilimi, jagoranci, da bunƙasa cibiyoyin ilimi wanda ke ci gaba da tasiri ga ɗalibai, malamai, da masu harkar kafofin yaɗa labarai a Najeriya da ma ƙasashen waje.

Babbar Kotun Jihar Kogi da ke Lokoja ta umarci Natasha Akpoti-Uduaghan da ta biya tsohon gwamnan jihar, Yahaya Bello, di...
24/04/2026

Babbar Kotun Jihar Kogi da ke Lokoja ta umarci Natasha Akpoti-Uduaghan da ta biya tsohon gwamnan jihar, Yahaya Bello, diyyar Naira biliyan 1 kan ɓata masa suna.

Hukuncin, wanda Mai shari’a A. S. Ibrahim ya yanke a ranar 23 ga Afrilu, ya biyo bayan kalaman da Natasha ta yi a shirin “The Morning Show” na Arise TV a ranar 4 ga Nuwamba, 2022. Kotun ta ce kalaman sun zargi Bello da aikata munanan laifuka ba tare da hujja ba, wanda ya ɓata masa suna.

Kotun ta kuma hana Natasha sake yin irin waɗannan kalamai a kafafen yaɗa labarai. Tun farko, Bello ne ya shigar da ƙarar, yayin da lauyan Natasha ya ƙalubalanci hurumin kotun.

Daga baya, Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yi watsi da ƙarar Natasha, tare da tabbatar da cewa Babbar Kotun Jihar Kogi na da ikon sauraron shari’ar.

Sakataren jam’iyyar ADC na ƙasa, Rauf Aregbesola, ya soki shirin “sabunta fata” na Shugaba Bola Tinubu, yana mai cewa ba...
14/04/2026

Sakataren jam’iyyar ADC na ƙasa, Rauf Aregbesola, ya soki shirin “sabunta fata” na Shugaba Bola Tinubu, yana mai cewa ba zai haifar wa ‘yan Najeriya wani ci gaba mai ma’ana ba.

Ya bayyana hakan ne yayin gangamin taron jam’iyyar ADC na ƙasa a Abuja, wanda tsagin shugabanci ƙarƙashin David Mark ke jagoranta.

A cewarsa, shirin “sabunta fata” yaudara ce, yana tambayar lokacin da al’umma za su fara ganin sakamako a zahiri.

Ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya su yi taka-tsantsan tare da gujewa sake zaɓen gwamnati a shekarar 2027, bisa zargin gazawar cika alƙawuran da aka ɗauka a yaƙin neman zaɓen 2023 ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Aregbesola ya yi nuni da muhimman fannoni da ya ce gwamnati ta gaza cikawa, musamman batun samar da ingantacciyar wutar lantarki.

Ya ce duk da alkawarin samar da tsayayyen wuta, har yanzu matsalar tana nan daram ba tare da gagarumin ci gaba ba.

Haka kuma, jam’iyyar ADC ta nuna damuwa kan matsalar ilimi, musamman yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, wanda ta danganta da gazawar gwamnati wajen inganta tsarin ilimi a ƙasa.

A bangaren siyasa, Aregbesola ya yaba wa shugabancin David Mark, yana mai cewa cikin watanni tara kacal jam’iyyar ADC ta samu ci gaba sosai har ta zama babbar jam’iyyar adawa a Najeriya.

Bugu da ƙari, ya soki hukumar INEC bisa rashin sa ido kan gangamin taron jam’iyyar, yana mai cewa ba ta bayar da hujja mai gamsarwa ba.

Ya kuma zargi hukumar da nuna son kai ga jam’iyyar APC, zargin da ke ƙara tayar da kura kan sahihancin ayyukanta.

Hukumar SSS a Kano ta tsare wasu mataimakan gwamnan jihar Kano, Abba K. Yusuf, bisa zargin amfani da dandalin sada zumun...
12/04/2026

Hukumar SSS a Kano ta tsare wasu mataimakan gwamnan jihar Kano, Abba K. Yusuf, bisa zargin amfani da dandalin sada zumunta wajen cin cuzguna wa tsohon gwamnan Kano, Rabi’u Kwankwaso, da wasu ‘yan siyasa na adawa.

Ƙarar ta fito ne daga hannun Musa Danzaki, shugaban ƙungiyar Kwankwasiyya a Kano, wanda ya zargi Sanusi Bature, Ibrahim Adam da Salisu Yahaya Hotoro da yawan cuzguna wa jagororin Kwankwasiyya a dandalin sada zumunta.

An shigar da ƙarar ce a ranar 9 ga Afrilu inda ta isa hannun SSS a ranar 10 ga Afrilu.

Kungiyar Kwankwasiyya na zargin jami’an gwamnatin Kano da cin zarafin manyan ‘yan siyasar jam'iyyar adawa ciki har da tsohon mataimakin gwamnan Kano, Aminu Abdussalam da Sanata Rufa’i Hanga.

Sanusi Bature ya tabbatar wa PREMIUM TIMES da amsa gayyatar hukumar inda aka tsare shi na tsawon sa’o’i huɗu kafin a sake shi.

Rikicin tsakanin 'yan siyasar ya samo asali ne tun bayan sauya sheƙar gwamna Abba daga NNPP zuwa APC a watan Janairu, matakin da ya jawo zarge-zargen cin amana daga magoya bayan Kwankwaso, yayin da ɓangaren gwamna ke cewa ya yi hakan ne domin ci gaban Kano ne.

Fitaccen malamin addinin Musulunci a Kano, Abduljabbar Kabara, ya shigar da koke ga Kudirat Kekere-Ekun yana zargin rash...
30/03/2026

Fitaccen malamin addinin Musulunci a Kano, Abduljabbar Kabara, ya shigar da koke ga Kudirat Kekere-Ekun yana zargin rashin adalci a hukuncin kisa da aka yanke masa kan zargin ɓatanci ga Annabi Muhammad (SAW).

A cikin koken mai shafi 14 da ya aika wa kotun ƙoli a ranar 26 ga Maris, ya ce shari’ar cike take da siyasa da kuma ƙoƙarin rufe masa baki.

Kabara ya bayyana cewa an hana shi damar ɗaukaka ƙara yadda ya kamata tun daga shekarar 2022, har zuwa wani yunƙuri da ya sake yi a 2024.

Ya kuma zargi wasu alƙalai da sauya bayanai da ranaku domin biyan buƙatun gwamnatin Kano. A cewarsa, shari’ar ta saɓa da sashe na 38(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya wanda ke ba da ‘yancin addini da tunani.

Sai dai mai magana da yawun ma’aikatar shari’a ta Kano, Baba Jibo, ya musanta zarge-zargen, yana mai cewa an ba Kabara dama sosai ta bin hanyoyin shari’a, kuma duk matakan da aka ɗauka sun kasance da saninsa.

A koken, Kabara ya kuma yi zargin akwai yunƙurin shigar da shi cikin wata tafiyar juyin-juya-hali mai alaƙa da wasu ƙasashen waje, wanda ya ƙi amincewa da shi.

A halin yanzu, an mayar da shi gidan yarin Kuje a Abuja saboda dalilan tsaro, yayin da yake roƙon a sake duba hukuncin da aka yanke masa.

𝐌𝐨𝐣𝐭𝐚𝐛𝐚 𝐊𝐡𝐚𝐦𝐞𝐧𝐞𝐢 𝐲𝐚 𝐳𝐚𝐦𝐚 𝐒𝐚𝐛𝐨𝐧 𝐉𝐚𝐠𝐨𝐫𝐚𝐧 Juyin Juya-hali na 𝐈𝐫𝐚𝐧Mojtaba Khamenei ya zama sabon Shugaban Jagoran Addini na ...
08/03/2026

𝐌𝐨𝐣𝐭𝐚𝐛𝐚 𝐊𝐡𝐚𝐦𝐞𝐧𝐞𝐢 𝐲𝐚 𝐳𝐚𝐦𝐚 𝐒𝐚𝐛𝐨𝐧 𝐉𝐚𝐠𝐨𝐫𝐚𝐧 Juyin Juya-hali na 𝐈𝐫𝐚𝐧

Mojtaba Khamenei ya zama sabon Shugaban Jagoran Addini na Iran (Supreme Leader), shi ne na uku tun bayan Juyin Juya-hali na Iran a shekarar 1979. Ya gaji mahaifinsa, Ali Khamenei, wanda ya jagoranci ƙasar sama da shekaru 37 kafin kashe shi a gidansa da ke Tehran sakamakon harin haɗin gwuiwar Amurka da Isra’ila.

Rahotanni sun nuna cewa Mojtaba ba ya gidan a lokacin harin, amma ya rasa mahaifiyarsa, matarsa da kuma ‘yarsa a wannan hari.

Majalisar Malami mai mambobi 88 masu biyayya ga tsarin Jamhuriyar Musulunci, ita ce ke da alhakin zaɓen sabon jagora.

An ruwaito cewa ginin da majalisar ke yin taro a ciki ya lalace sakamakon hari ta sama da aka kai, amma babu wani mamba da abin ya shafa a lokacin.

Ba wanda ya san abubuwa da yawa game da Mojtaba ba. Kuma shi ne ɗa na biyu ga Ali Khamenei. Rayuwarsa a killace take kuma ba ya yawan bayyana a bainar jama’a ko yin hudubar sallah.

Sai dai ana ganin yana daga cikin masu tsattsauran ra’ayin mazan jiya. Ya taba yin aiki tare da rundunar juyin juya-hali a rundunar a cikin bataliyar Habib a lokacin yaƙin Iran–Iraq a shekarun 1980, inda ya samu kusanci da manyan jami’an tsaro.

Duk da bai taba rike wani mukamin gwamnati ko tsayawa zaɓe ba, dangantakarsa ta kusa da rundunar tsaron ya fito da tasirinsa. Ana ganin kuma hakan zai iya shafar yunkurin kawo ƙarshen yakin da ake yi tsakanin Iran da Amurka da Isra’ila.

A yau Asabar aka gudanar da zaɓen cike gurbi a jihohin Kano da Ribas da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli ...
21/02/2026

A yau Asabar aka gudanar da zaɓen cike gurbi a jihohin Kano da Ribas da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli a birnin tarayya Abuja.

Sai dai kafafen yaɗa labarai a jihar Kano, sun rawaito ƙarancin fitowar al’umma domin kaɗa ƙuri’a a rumfunan zaɓe da dama da ke ƙaramar hukumar birnin Kano da Ungogo.

Shugaban hukumar zaɓe ta Kano, Abdu A. Zango, ya alaƙanta rashin fitowar mutane da rashin shigar jam’iyyun siyasa da yawa.

“A gaskiya ƙila saboda zaɓe ƙarami ne. Duka local government biyu ne. Kuma jam’iyyu guda 9. Ban da wannan gaskiya ba za mu iya cewa komai ba,” ya faɗa.

A yayin da yake amsa tambaya game da rashin shigar jam’iyyun PDP da NNPP zaɓen cike gurbin duk da cewa su ake wa kallon manyan jam’iyyun siyasa a Kano, Zango ya ce, ya nuna cewa ba hukumar zaɓe ya kamata ta ba da wannan amsa ba.

“Su (jam’iyyun) ya kamata su ba da wannan amsa. Mu INEC, party ɗinmu ita ce jama’ar Kano,” ya bayyana, inda yake ƙara da cewa, “Mu aikinmu mu shirya zaɓe, mu bai wa kowa dama ya zo ya kaɗa ƙuri’ar shi.”

Game da zaɓe cikin lumana:

Sannan shugaban hukumar zaɓen ta Kano ya yaba da yadda irin gudunmowar da jami’an tsaro s**a bayar wajen wanzar da zaman lafiya.
“Ko’ina ga ‘yan sanda sun kawo mana gudunmowa. Kuma muna godiya ƙwarai,” in ji shugaban zaɓen.

“Kun gani da idanku mun zagaya,” Zango ya faɗa wa manema labarai, inda ya ci gaba da cewa, “ana zaɓe cikin zaman lafiya. Ba tarzoma ba. Kamar yadda muka jawo hankalin jama’a, sun ba da haɗin kai kuma mun ji daɗi. Kano ba kasafai take haka (cikin zaman lafiya a yayin zaɓe), amma yau dai an nuna (zaman lafiya).”

“Muna fata wannan abun zai ɗore,” in ji Zango.

Sai dai rahotanni sun nuna yadda al’umma s**a ƙaurace wa fitowa zaɓe a Kano duk da ƙoƙarin rabon Naira 1000 da wasu ‘yan siyasa s**a yi a cikin ƙwaryar birnin Kano.

Wannan dai na nuna irin yadda al’umma s**a gaji da gafara sa ba su ga ƙaho ba game da alƙawuran ‘yan siyasa da ke shafe shekaru 4, wasu har 8 ba tare da tsinana wa mazaɓunsu da al’umma komai ba.

Muna yi muku barka da shigowa watan azumin Ramadan. Allah ya karɓi ibadunmu.
19/02/2026

Muna yi muku barka da shigowa watan azumin Ramadan. Allah ya karɓi ibadunmu.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yaqini Media Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share