WAYYO AREWA

WAYYO AREWA Domin Kawo muku A bubuwan da ke faruwa a Arewacin Nijeriya

INNALILLAH WA INNA ILAIHIN RAJI'UN CIKIN DAREN JIYA YAN UWAN MU KAHFAWA NA GARIN BAUCHI SUNKWAN CIKIN ZILLIMI SAKAMAKON ...
27/02/2024

INNALILLAH WA INNA ILAIHIN RAJI'UN

CIKIN DAREN JIYA YAN UWAN MU KAHFAWA NA GARIN BAUCHI SUNKWAN CIKIN ZILLIMI SAKAMAKON KAI HARIN YAN TA'ADDA YA YAN UWANA ALBAJIRAI

Wannan hoton wami bawan Allah ne yaji da daddare yafita Neman Abundant zai ci wato bara wasu tsinanu Allah ta'ala s**a far makesu ya kasan CE ba aganshi ba yau da safe aka fita Neman sa Akasame shi CIKIN wannan hali Anyake masa kai

Allah ubangiji ya tona Asirin WA yanda s**ayi wannan Aika aikan CIKIN gaggawa. Allah ka wargaza shirin su akan dukkakanin wani Ani mutu ka wargaza aniyn su karka basu Abundant suke nema duniya da lahira Albarkan Shugaba Annabi Muhammadu S A W

Shikuma Allah yajikan sa yayi NASA rahama

FETUR DAN JIHAR BAUCHIWannan shine Samfurin ɗanyen man fetur da aka haƙo a filin Kolamani da ke jihar Bauchi da Gombe NN...
22/11/2022

FETUR DAN JIHAR BAUCHI

Wannan shine Samfurin ɗanyen man fetur da aka haƙo a filin Kolamani da ke jihar Bauchi da Gombe NNPC.ta tabbatar da yawa da inganci sa zai kai matsayin sayarwa a kasuwa

Ko zaku iya Tina Alƙawukan da Ƴan siyasa s**a yi muka A baya Lokacin yakin neman zaɓen 2019 zuwa yanzu sun cika Al kawar...
15/11/2022

Ko zaku iya Tina Alƙawukan da Ƴan siyasa s**a yi muka A baya Lokacin yakin neman zaɓen 2019 zuwa yanzu sun cika Al kawarin da s**ayi muko ko a'a baiyana ra'ayin ka

Kuci gaba da bibiyan mu domin jin kowani Alkawarin san siyasa shin ya cika ko kasasin haka Wayyo Arewa takuce.

ME KUKA SANI GAME DA SAYAR DA KATIN ZAƁE?Daga Bashir Abubakar BauchiNayi wannan rubutun nawa ne ba dan komai ba sai dan ...
28/09/2022

ME KUKA SANI GAME DA SAYAR DA KATIN ZAƁE?

Daga Bashir Abubakar Bauchi

Nayi wannan rubutun nawa ne ba dan komai ba sai dan na jawo hankali al'umma duba da yadda naga an buɗe yakin neman kuri'a na zaɓen 2023 da muke tunkara, nan bada dadewa ba al'umma zasu fito da katin su domin yin zaɓuɓɓukan 'yan takarkarun da zasu jagorance su a kujeru daban-daban a Najeriya, hakan yasa nake jawo hankulan masu kada kuri'a da kada su bari asiye yancin su.

Duk wanda ya karbi kuɗi domin jefama wani ɗan takara kuri'a kuma yasan wannan ɗan takarar bawai ya cancanta ba, to kasani muddin kayi haka ka sayar da 'yancinka ga wannan ɗan takara, ka sani koda wata rana idan yaci zabe ka zo masa da bukatun ku na cigaba da za'a muku a yankinku wanda a karshe zai iya ce muku kudin sane ya kawo su shi kujerar da yake kai ba don Allah kuka zabe shi ba, wannan kaɗan daga cikin walakancin da shugabannin da s**a bada kuɗi aka zaɓa keyi kenan.

Daga karshe zanja hankulan masu kaɗa ƙuri'arsu dasu dinga dogon nazari a duk lokacin da 'yan takara suke neman ƙuri'un ku,domin zaɓen wanda ya cancanta kar kubari a dunga ru ɗan ku da kuɗi don hakan saida yanci ne.

Allah ya kyara mana ya bamu Shuwagabannin nagari, Ameen.

Bashir Abubakar Bauchi

Shin Kun Yadda Cewa Babu Opportunity a Arewacin Nigeria ???Sun Ce Babu Opportunities a Arewacin Najeriya. Suna kallo an ...
22/08/2022

Shin Kun Yadda Cewa Babu Opportunity a Arewacin Nigeria ???

Sun Ce Babu Opportunities a Arewacin Najeriya. Suna kallo an zo Arewan an sari kilishi da arha an je Port Harcourt an yi packaging ɗin shi, an yi branding ɗin shi sannan an samar masa NAFDAC N0. An ɗauko shi an kawo shi supermarkets a Arewa suna siya da tsada wai su ƴan gayu.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. An yi packaging fura da nono daga Kudu an kawo su supermarkets a Arewa suna siya da tsada suna murna wai su wayayyu.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Ƴan Uganda da Ghana da Kenya na can suna exporting yalo da ɗata da ɗinya Dubai da China da America da daraja.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Sun rena miyar kuka kuma sun daina shan ta a yayin da babbar kasuwar da ake sai da kuka a England ta ke inda ake cinikin kuka na millions of dollars.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Basu san comparative advantage na Arewacin Najeriya ba. Zuwa ake yi ayi kashi a kan tafasa a Arewacin Najeriya a tashi a tafi a yayin da duk duniya babu tafasa mai kyau da daraja irin ta Arewacin Najeriya kuma da ita ake yin coffee. Lu'ulu'u a juji.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Ga akuyar Arewacin Najeriya mai kyau da daɗin nama ga ƙasashen Larabawa na neman ta su siya da tsada k**ar sa ci babu.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Suna kallo yanzu Yarbawa na kawo kajin gida (local chickens) tirela tirela duk sati daga Ibadan.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya amma ƴan Indiya da China da Lebanon suna tururuwa zuwa Arewacin Najeriya suna taking advantage na opportunities ɗin.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Sun kasa gane damarmakin da ke cikin manufacturing da processing da waste management bila adadin a yankin su.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Suna zaune Inyamurai sun yi dominating harkokin spare parts a yankin su.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Suna kallo Inyamurai sun mamaye harkokin Electronics a yankin Arewacin Najeriya.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Suna zaune Inyamurai sun yi dominating harkokin Satellite a yankin Arewacin Najeriya.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Suna kallo Inyamurai sun mamaye harkokin CCTV a yankin Arewacin Najeriya.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya. Suna kallo Inyamurai sun mamaye harkokin Solar a yankin su.

Sun ce babu opportunities a Arewacin Najeriya amma su opportunities a wurin su ƙyale-ƙyake ne kawai ba tunani ba kuma ba aiki ba

Allah ka ganar da wanda ke son fahimta don kai kuma don ya yi abinda ya dace.

13/08/2022

Sanarwa daga hukumar lafiya ta jahar Bauchi dangane da wata cuta da ta bullo ga mata, da kuma hanyar da zasu gujewa kamuwa daga cutar.

Daga bakin mai unguwar ƙofar wambai a cikin garin Bauchi Mallam Muhammad Bello.

13/08/2022

"yan Arewa Mu farka

Menene Dalilin Lalacewar Shugabanci A Arewa?Al-mansoor GusauAl’ummar Arewacin Nijeriya ita ce al’umma mafi kima da daraj...
11/08/2022

Menene Dalilin Lalacewar Shugabanci A Arewa?

Al-mansoor Gusau

Al’ummar Arewacin Nijeriya ita ce al’umma mafi kima da daraja a fadin Afirka, ita ce foton da daukacin al’ummar Afirka ke kallo su yi koyi a gurin gudanar da harkokin rayuwa na yau da kullum, domin ita ka dai ce al’ummar da Turawa ‘Yan-mulkin Mallaka ba su yi wa hawan ‘kawara ba, domin ko da su ka shigo Nijeriya ba su same mu al’ummar Arewa a tsirara ba, sun same mu da sutura a jikinmu tare da Ingantaccen Shugabancin mu k**a daga:

•Sarakuna.
•Limamai.
•Dattawan gari.
•Hakimai.
•Dakatai.
•Masu Unguwanni.

Saboda karfin tarbiyya da kaunar juna irin na al’ummar Arewacin Nijeriya, Turawa ba su iya shigowa Arewa su yi mana mulkin mallaka ba, dole sai da su ka hada kai da Sarakunan Lardin Arewa, daga karshe saboda Dattakon al’ummar Arewa Turawan Mulkin Mallaka ba su iya hannunta ‘Yancin wannan Kasa mai suna Nijeriya ba sai a hannun Dattawan Arewacin Nijeriya:

•Sir.Abubakar Tafawa Balewa.
•Sir.Ahmadu Bello (Sardaunan Sokoto).

Haka zalika Laraba ma da su ka shigo Arewacin Nijeriya ta hanyar kasuwanci tare da yada Addinin Musulunci sun samu al’ummar Arewacin Nijeriya da kyawawan halaye da ingantacciyar tarbiyyar da ta yi dai dai da koyarwar Addinin Musulunci, k**a daga:

•Auren Mace fiye da daya.
•Zumunci.
•Kunya.
•Kara.
•Taimakon juna.
•Tausayi.
•Gaskiya.
•Rikon amana.

Allah (SWT) ya daukaka kima da darajar al’ummar Arewa ba a Nijeriya ba, a fadin Tarayyar duniya baki dayanta, domin babu wani mutum a duniya da ake iya gano ko shi waye ta hanyar saka suturarsa sai mutumin Arewa, babu wata Kasa a duniya da ta isa ba tare da tana koyar da harshen al’ummar Arewa na (Hausa) a Jami’arta ba, haka zalika babu wata Kasa a duniya mai ji da kanta da ba ta gudanar da shirye shirye da harshen (Hausa) a gidajen Rediyo da Talabijin dinta ba.

Shugabannin Arewa na farko sun taka gagarumar rawa gurin ganin sun kare kima da martabar al’ummar Arewa, sun kafa mutanen Arewa ta hanyoyu daban daban, wanda galibin Shugabannin Nijeriya a yau dik wadan da Shugabannin farko ne su ka kafa ba tare da sun san Iyayensu ba.

TAMBAYARMU A NAN ITA CE.

• Rikon da Shugabannin Arewa na yau ke yi ma al’ummar Arewa na yau, a haka Shugabannin Arewa na farko su ka rike amanarsu?

• Me ya sa Shugabannin Arewa na farko su ka watsar da abunda za su samu na duniya su da Iyalansu, su ka zabi cigaban al’ummar Arewa, wanda hakan ya haifi Shugabannin Arewa na yanzu, amma su Shugabannin Arewa na yanzu su ka wulakantar da al’ummar Arewa na yanzu su ka zabi kudi?

Abun mamaki da takaici, a ce wai al’ummar Arewa, mutane mafi daraja a Afirka, yau an wayi gari ana k**a mutanen Arewa masu zuwa Kudancin Kasar nan domin neman abinci, ana tsare su k**ar wasu dabbobi har yau babu Shugaba a Arewa da ya ce komai..!!!

• Yau a Arewa babu murya guda daya mai magana amadadin Lardin Arewa kowa ya saurare ta ya yi da’a da biyayya.

• Yau a Arewa mun rasa makoma kullum ana kashe mana al’umma, amma bakin munafurci da son abun duniya ya sa kowa ya rufe bakinsa, babu mai iya yin magana.

• Yau a Arewa an zabi kudi an watsar da mutunci galibin al’umma, inda za su samu kudi to komai ma za a yi, to a yi idan dai an samu kudi.

• Yau a Arewa al’amurra sun lalace, babu noma, babu kiwo, kasuwanci ya yi rauni, babu aikin yi, Dan-talaka komai hazakarsa bai isa ya samu aikin Gwamnatin Tarayya ba, sai dai aikin kaki

Allah (SWT) ka ga halin da al’ummarka, mutanen Arewacin Nijeriya su ka tsinci kawunansu, Allah (SWT) ka kawo mana dauki da agaji irin na ka, Allah (SWT) ka shiryar da Shugabannin Arewa, Allah (SWT) ka kawo ma Arewacin Nijeriya mafita irin ta ka saboda Annabi Muhammad (SAW).

•Wannan rubutu ra’ayi na ne.
•Wannan rubutu tinani na ne.
•Wannan rubutu hange na ne.
•Wannan rubutu fahimta ta ce.

(Section 39 of the Nigerian Constitution)

10/08/2022
Yadda rundunar sojin sama s**a kashe fitaccen dan bindiga, matan sa biyu da kwamandojinsa 8 a Katsina...Yadda sojojin sa...
09/08/2022

Yadda rundunar sojin sama s**a kashe fitaccen dan bindiga, matan sa biyu da kwamandojinsa 8 a Katsina...

Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

A wani luguden bamabamai da sojojin saman Najeriya s**a yi a cikin makon jiya sun samu nasarar gamawa da wani fitattcen dan bindiga da ya buwayi mutane a jihar Zamfara mai suna Abdulkarimu da aka fi sanin sa da Faca-Faca, matan sa biyu da manyan kwamandojinsa 8.

Rundunar ta kai wa Faca-Faca hari a kauyen Marina dake karamar hukumar Safana jihar Katsina da misalin karfe 3 na daren Lahadi.

Majiyar da PREMIUM TIMES ta samo wadannan bayanai ‘Forward Operation Base (FOB)’ ta bayyana cewa jami’an tsaron sun kai wa Faca-Faca hari bayan samun bayanan siri game da inda yake kwana.

kakakin rundunar Ƴansandan Jihar Katsina SP Gambo Isa ya tabbatar da harin inda ya ce “Rundunar sojin sama sun kashe mutum takwas da ake zargi ‘yan bindiga ne da shugaban su Faca-Faca. Wasu daga cikin maharan sun gudu.

Dan majalisar dokokin jihar AbdulJalal R***a ya tabbatar da aukuwar wannan aiki da sojoji s**a yi.

Sannan wasu mazaunan Safana su biyu sun bayyan wa PREMIUM TIMES cewa mutane da dama sun gudu sun bar gidajen su a dalilin wannan farmaki kan yan bindiga da sojoji s**a kai.

Faca-Faca

Wani mazaunin Safana Shamsu Masud ya ce Faca-Faca ya dade yana kawo wa kauyukan dake karkashin kananan hukumomin Safana, Danmusa, Batsari da wasu bangarorin jihar Zamfara hari.

Shidai Faca faca ana zargin yana cikin Ɓarayin da s**a Jagoranci kitsa harin da aka kaiwa Motocin Jami'an tsaron fadar Shugaban ƙasa akan hanyar su ta zuwa Katsina ƙwanakin baya.

Address

ABUJA
Abuja

Telephone

+2348100604750

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when WAYYO AREWA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share


Other Media/News Companies in Abuja

Show All