WAYYO AREWA

WAYYO AREWA Domin Kawo muku A bubuwan da ke faruwa a Arewacin Nijeriya

A ci gaba da shirye-shiryen zaɓen shugabancin matasa na Najeriya, ɗan takara Umar Lauya ya ƙara samun yabo da goyon baya...
17/09/2025

A ci gaba da shirye-shiryen zaɓen shugabancin matasa na Najeriya, ɗan takara Umar Lauya ya ƙara samun yabo da goyon bayan jama’a musamman daga matasa, sakamakon tsare-tsaren da ya fito da su domin bunƙasa rayuwar su.

A yayin yakin neman zaɓen nasa, Umar Lauya ya bayyana cewa manufarsa ita ce ganin an samu ingantaccen shugabanci na matasa wanda zai ƙarfafa haɗin kai, ya samar da damammakin aiki da horo, tare da kare muradun matasa a dukkanin matakan tafiyar da al’amuran al’umma.

Ya jaddada cewa ba zai yi wannan tseren don kansa ba, illa domin ci gaban matasa da kuma tabbatar da cewa an ba su dama wajen taka muhimmiyar rawa a harkokin rayuwa da shugabanci.

Jama’a da dama da s**a halarci gangamin yakin neman zaɓen Umar Lauya sun bayyana gamsuwarsu da irin shirin da ya gabatar, inda s**a tabbatar da cewa shi mutum ne mai gaskiya, kishin al’umma da kuma jajircewa wajen ganin an samu cigaba.

Daga cikin muhimman tsare-tsaren da yake gabatarwa akwai:

(1) Samar da sana’o’i da horo ga matasa.

(2) Ƙarfafa ilimi da wayar da kan matasa.

(3) Inganta haɗin kai da zaman lafiya.

(4) Kare muradun matasa a wuraren da ya kamata a ji muryarsu.

Yakin neman zaɓen Umar Lauya ya kasance abin sha’awa da jan hankali, tare da samun karɓuwa daga sassa daban-daban na al’umma.

A cewar wasu matasa da s**a halarci taron, sun bayyana cewa "Umar Lauya shi ne jagoran da muke buƙata domin tabbatar da makomar mu matasa.

Marigayi Firimiyan jihar Arewa, sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato tare da marigayi Sarkin Kano Muhammadu Sunusi a bir...
10/09/2025

Marigayi Firimiyan jihar Arewa, sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato tare da marigayi Sarkin Kano Muhammadu Sunusi a birnin Venice na kasar Italiya cikin shekarar 1960.

Allah ya jiƙan Magabatanmu

Dubban Jama’a Sun Halarci Babban Taron Mauludi Na Sheikh Dahiru Bauchi Da Aka Gudanar A Jihar BauchiAn gudanar da babban...
05/09/2025

Dubban Jama’a Sun Halarci Babban Taron Mauludi Na Sheikh Dahiru Bauchi Da Aka Gudanar A Jihar Bauchi

An gudanar da babban taron Mauludi a jihar Bauchi ƙarƙashin jagorancin fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi. Taron ya gudana ne a babban filin wasa na Sir Abubakar Tafawa Balewa Stadium da ke cikin garin Bauchi.

Dubban mabiya daga sassa daban-daban na Najeriya da ma ƙasashen waje sun halarci wannan gagarumin biki na tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW), wanda Sheikh Dahiru ke jagoranta a duk shekara.

Taron ya haɗa manyan malamai, shugabanni, da mabiya na Darikar Tijjaniyya, inda aka gabatar da karatun Alƙur'ani, salawata, da jawaban wa’azi masu ƙayatarwa.

Sheikh Dahiru Bauchi ya jaddada muhimmancin bin koyarwar Annabi Muhammad (SAW), yana mai kira da a zauna lafiya da juna tare da inganta zamantakewa da ƙaunar juna a matsayin Musulmi.

Daga Bashir Abubakar, Bauchi.

Kungiyar Prof. Pate Free Medical Outreach Team a karkashin jagorancin Comr Yusuf Aliyu Fada tare da hadin gwiwa da Ibrah...
31/08/2025

Kungiyar Prof. Pate Free Medical Outreach Team a karkashin jagorancin Comr Yusuf Aliyu Fada tare da hadin gwiwa da Ibrahim Ali Usman Foundation sun gudanar da aikin gwaje-gwaje da jinya kyauta kamar haka;
• Gwajin ciwon hanta (Hepatitis B)
• Gwajin hawan jini (BP)
• Bada magani kyauta
• Wayar da kai kan yadda za'a kaucewa kamuwa da ciwon hanta.

Comrade Fada yace zasu cigaba dayin irin wannan aiki a sauran kananan hukumomi 20 na jihar Bauchi dan tallafawa al'umma kan kiwon lafiya da manufar tallata Prof. Ali Pate a matsayin Gwamnar jihar Bauchi da Dr. Ibrahim Ali Usman a matsayin Sanatan Bauchi ta kudu a shekarar 2025 dake tafe.

Shugaban central market Bauchi ya bayyana jin dadin sa kan wannan kokari da kungiya tayi na kai musu tallafi kan kiwon lafiya har kasuwa yayi fatan Allah saka da alheri ga wadda s**a dauki nauyin wannan jinya kyauta.

Su ma wadda s**aci gajiyar shirin Alh. Danlami, Ibrahim Mai-anguwa da Amira Usman sun bayyana jin dadin su kan wannan shiri tare da addu'ar Allah ya sakawa wadda s**a dauki nauyin wannan jinya da alheri ya biya musu bukatun su na alheri.

Yau ce ranar dimokaraɗiyya a Najeriya, inda ƙasar ta cika shekara 26 akan tsarin mulkin dimokuraɗiyya ba tare da katsewa...
12/06/2025

Yau ce ranar dimokaraɗiyya a Najeriya, inda ƙasar ta cika shekara 26 akan tsarin mulkin dimokuraɗiyya ba tare da katsewa ba.

Menene ra'ayinku kan wannan tsarin mulki da kuma shekara 26 ana tafiya akansa?

11/06/2025

Ayau take Ranar Democracy Wani cigaba Nigeria tasamu Afannonin ko wani irin koma baya AREWA ta tsin cikan

01/12/2024

*Kun cire tallafin man fetur.
*Kun cire tallafin wutar nepa.
*Kun kulle mana boda.
*Kun kasa tsare lafiyar mu.
*Kun kasa samar da kyakkyawan tsaro.
*Kun hana mu Aikin yi.
*Kun ruguza Darajar kuɗin mu.
*Kun barmu acikin yunwa.
*Kun hana mu ilimi me kyau.
*Kun kashe mana kasuwanci.
*Kun hana mu zumunci.
*Ku fitini rayuwar mu.
*Kun maida mu mabarata.
Kun! Kun!! Kun!!!

**Yanzu kuma kun biyo cikin asusun ajiyar mu zaku fara kwashe mana Abinda muke rufawa kanmu asiri da sunan wani haraji na zalunci 🥺

Babu Abinda zamu ce sai dai muce muku Allah ya isa tsakanin daku 😭

01/12/2024

WAYYO AREWA
MUNA ALLAH WADARE DA WANNAN TSARIN HARAJIN TA GWAMNATIN TUNIBU

A YANKIN MU NA AREWA

INNALILLAH WA INNA ILAIHIN RAJI'UN CIKIN DAREN JIYA YAN UWAN MU KAHFAWA NA GARIN BAUCHI SUNKWAN CIKIN ZILLIMI SAKAMAKON ...
27/02/2024

INNALILLAH WA INNA ILAIHIN RAJI'UN

CIKIN DAREN JIYA YAN UWAN MU KAHFAWA NA GARIN BAUCHI SUNKWAN CIKIN ZILLIMI SAKAMAKON KAI HARIN YAN TA'ADDA YA YAN UWANA ALBAJIRAI

Wannan hoton wami bawan Allah ne yaji da daddare yafita Neman Abundant zai ci wato bara wasu tsinanu Allah ta'ala s**a far makesu ya kasan CE ba aganshi ba yau da safe aka fita Neman sa Akasame shi CIKIN wannan hali Anyake masa kai

Allah ubangiji ya tona Asirin WA yanda s**ayi wannan Aika aikan CIKIN gaggawa. Allah ka wargaza shirin su akan dukkakanin wani Ani mutu ka wargaza aniyn su karka basu Abundant suke nema duniya da lahira Albarkan Shugaba Annabi Muhammadu S A W

Shikuma Allah yajikan sa yayi NASA rahama

FETUR DAN JIHAR BAUCHIWannan shine Samfurin ɗanyen man fetur da aka haƙo a filin Kolamani da ke jihar Bauchi da Gombe NN...
22/11/2022

FETUR DAN JIHAR BAUCHI

Wannan shine Samfurin ɗanyen man fetur da aka haƙo a filin Kolamani da ke jihar Bauchi da Gombe NNPC.ta tabbatar da yawa da inganci sa zai kai matsayin sayarwa a kasuwa

Ko zaku iya Tina Alƙawukan da Ƴan siyasa s**a yi muka A baya Lokacin yakin neman zaɓen 2019 zuwa yanzu sun cika Al kawar...
15/11/2022

Ko zaku iya Tina Alƙawukan da Ƴan siyasa s**a yi muka A baya Lokacin yakin neman zaɓen 2019 zuwa yanzu sun cika Al kawarin da s**ayi muko ko a'a baiyana ra'ayin ka

Kuci gaba da bibiyan mu domin jin kowani Alkawarin san siyasa shin ya cika ko kasasin haka Wayyo Arewa takuce.

ME KUKA SANI GAME DA SAYAR DA KATIN ZAƁE?Daga Bashir Abubakar BauchiNayi wannan rubutun nawa ne ba dan komai ba sai dan ...
28/09/2022

ME KUKA SANI GAME DA SAYAR DA KATIN ZAƁE?

Daga Bashir Abubakar Bauchi

Nayi wannan rubutun nawa ne ba dan komai ba sai dan na jawo hankali al'umma duba da yadda naga an buɗe yakin neman kuri'a na zaɓen 2023 da muke tunkara, nan bada dadewa ba al'umma zasu fito da katin su domin yin zaɓuɓɓukan 'yan takarkarun da zasu jagorance su a kujeru daban-daban a Najeriya, hakan yasa nake jawo hankulan masu kada kuri'a da kada su bari asiye yancin su.

Duk wanda ya karbi kuɗi domin jefama wani ɗan takara kuri'a kuma yasan wannan ɗan takarar bawai ya cancanta ba, to kasani muddin kayi haka ka sayar da 'yancinka ga wannan ɗan takara, ka sani koda wata rana idan yaci zabe ka zo masa da bukatun ku na cigaba da za'a muku a yankinku wanda a karshe zai iya ce muku kudin sane ya kawo su shi kujerar da yake kai ba don Allah kuka zabe shi ba, wannan kaɗan daga cikin walakancin da shugabannin da s**a bada kuɗi aka zaɓa keyi kenan.

Daga karshe zanja hankulan masu kaɗa ƙuri'arsu dasu dinga dogon nazari a duk lokacin da 'yan takara suke neman ƙuri'un ku,domin zaɓen wanda ya cancanta kar kubari a dunga ru ɗan ku da kuɗi don hakan saida yanci ne.

Allah ya kyara mana ya bamu Shuwagabannin nagari, Ameen.

Bashir Abubakar Bauchi

Address

ABUJA
Abuja

Telephone

+2348100604750

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when WAYYO AREWA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share