17/09/2025
                                            A ci gaba da shirye-shiryen zaɓen shugabancin matasa na Najeriya, ɗan takara Umar Lauya ya ƙara samun yabo da goyon bayan jama’a musamman daga matasa, sakamakon tsare-tsaren da ya fito da su domin bunƙasa rayuwar su.
A yayin yakin neman zaɓen nasa, Umar Lauya ya bayyana cewa manufarsa ita ce ganin an samu ingantaccen shugabanci na matasa wanda zai ƙarfafa haɗin kai, ya samar da damammakin aiki da horo, tare da kare muradun matasa a dukkanin matakan tafiyar da al’amuran al’umma.
Ya jaddada cewa ba zai yi wannan tseren don kansa ba, illa domin ci gaban matasa da kuma tabbatar da cewa an ba su dama wajen taka muhimmiyar rawa a harkokin rayuwa da shugabanci.
Jama’a da dama da s**a halarci gangamin yakin neman zaɓen Umar Lauya sun bayyana gamsuwarsu da irin shirin da ya gabatar, inda s**a tabbatar da cewa shi mutum ne mai gaskiya, kishin al’umma da kuma jajircewa wajen ganin an samu cigaba.
Daga cikin muhimman tsare-tsaren da yake gabatarwa akwai:
(1) Samar da sana’o’i da horo ga matasa.
(2) Ƙarfafa ilimi da wayar da kan matasa.
(3) Inganta haɗin kai da zaman lafiya.
(4) Kare muradun matasa a wuraren da ya kamata a ji muryarsu.
Yakin neman zaɓen Umar Lauya ya kasance abin sha’awa da jan hankali, tare da samun karɓuwa daga sassa daban-daban na al’umma.
A cewar wasu matasa da s**a halarci taron, sun bayyana cewa "Umar Lauya shi ne jagoran da muke buƙata domin tabbatar da makomar mu matasa.