Farar Jarida News

Farar Jarida News Labarai da ɗumi_ɗuminsu, binciken ƙwaƙwaf, Nishadi,talla, faɗakarwa,sharhin jaridu. FARAR JARIDA !! FARINCIKIN AL, UMMA!!!

IDAN ZAKA GINA RAMIN MUGUNTA....!!! Ya Boye Buhunan Masara Sama Da Dubu Uku Saboda Idan Farashin Ta Ya Haura Ya Fitar Ya...
05/08/2025

IDAN ZAKA GINA RAMIN MUGUNTA....!!!

Ya Boye Buhunan Masara Sama Da Dubu Uku Saboda Idan Farashin Ta Ya Haura Ya Fitar Ya Siyar, Sai Ga Shi Masarar Ta Rubè, K**ar Yadda Jaridar Rariya Ta Ruwaito.

Me za ku ce?

Ana zargin cewa k**a ɗan gwagwarmayar nan (Anas Muhammad Game) da yan sanda s**ayi a ƙaramar hukumar Bakori domin gudana...
02/08/2025

Ana zargin cewa k**a ɗan gwagwarmayar nan (Anas Muhammad Game) da yan sanda s**ayi a ƙaramar hukumar Bakori domin gudanar da zanga-zangar matsalar rashin tsaro nada alaƙa da ƙudurin da yake dashi na tsayawa takara 2027.

DA ƊUMI-ƊUMI: Buratai ya sha da Ƙyar a Wani Hari da Ƴan Ta'adda S**a Kai Masa a BornoTsohon shugaban hafsan sojojin ƙasa...
09/06/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Buratai ya sha da Ƙyar a Wani Hari da Ƴan Ta'adda S**a Kai Masa a Borno

Tsohon shugaban hafsan sojojin ƙasa, Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya), ya kuɓuta daga harin da ake zargin 'yan Bok Hrm ne s**a kai masa a jihar Borno.

Sanata Ali Ndume ne ya bayyana hakan yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels TV a ranar Lahadi.

A cewarsa, an kai wa Buratai da ayarinsa hari ne a kusa da wani sansanin sojoji da ke gaba da inda ake fafatawa da 'yan ta'adda. Ya ce an samu musayar wuta mai ƙarfi tsakanin sojojin da ke rakiyar tsohon hafsan da kuma maharan.

“Ina tabbatar muku da cewa sun kai masa hari. Sojojinsa sun mayar da martani, amma an yi hasarar wasu kayan aiki,” in ji Ndume.

Harin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta ƙara kira da a gyara tsarin tsaro, musamman a yankin Arewa maso Gabas da ke fama da hare-haren Bok Hrma da ISWAP.

Buratai ya shugabanci rundunar sojin ƙasa daga shekarar 2015 zuwa 2021, kuma ya taka rawar gani a yaƙin da gwamnati ke yi da ta'addanci a Najeriya.

“Ina jin tausayin Tinubu, gwamnoni 22 na PDP sun mara wa Jonathan baya amma duk da haka ya fadi zabe” — Inji Sanata Ndum...
09/06/2025

“Ina jin tausayin Tinubu, gwamnoni 22 na PDP sun mara wa Jonathan baya amma duk da haka ya fadi zabe” — Inji Sanata Ndume

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ɗauki nauyin karatun Aliyu Hassan Bakori zuwa kasar waje.Aliyu Hassan Ba...
09/06/2025

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ɗauki nauyin karatun Aliyu Hassan Bakori zuwa kasar waje.

Aliyu Hassan Bakori wani matashi da Allah ya ba fasahar ƙere-ƙeren motocin zamani ta hanyar amfani da kwalaye ɗan asalin karamar hukumar Bakori.

Wannan cigaba yana zuwa ne bayan kokarin da mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Bakori Hon Musa Abubakar Barde ya yi ta karkashin ofishin maibawa gwamna shawara SA blue and digital camera economy Hon Khalil Nur Khalil

Maigirma gwamna ya yaba ma hazikin matashin sannan ya sha alwashin ɗaukar nauyin karatun shi zuwa ƙasar waje domin cigaba da karantar kere kere da nufin cigaba da cin gajiyar baiwar da Allah ya yima matashin.

Da Ɗumi-Ɗumi:- Ƴan Bindiga sun yi ajalin manoma 10 sun jikkata wasu da dama a KatsinaWasu barayin daji sun kai mummunar ...
19/05/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:- Ƴan Bindiga sun yi ajalin manoma 10 sun jikkata wasu da dama a Katsina

Wasu barayin daji sun kai mummunar hari a garin Kukar Samu da ke karamar hukumar Safana a jihar Katsina inda s**a hallaka aƙalla mutum 10 da jikkata wasu da dama wanda mafi yawansu manoma ne da s**a nufi gonakinsu a safiyar yau Litinin 19 ga watan Mayu 2025.

Rahotanni na cewa harin ya bar al’umma cikin tsoro da jimami yayin da ake ci gaba da kai dauki ga mutanen da s**a jikkata.

Da Ɗumi-Ɗumi: An K**a Ɗan Bindiga a Sansanin Alhazai!Jami’an tsaro sun yi nasarar cafke wani gagarumin ɗan bindiga da ak...
18/05/2025

Da Ɗumi-Ɗumi: An K**a Ɗan Bindiga a Sansanin Alhazai!

Jami’an tsaro sun yi nasarar cafke wani gagarumin ɗan bindiga da ake nema ruwa a jallo, mai suna Yahaya Zango, a sansanin Alhazai na Abuja.

An k**a shi ne yayin da ake ci gaba da tantance maniyyatan da za su hau jirgi domin tafiya kasa mai tsarki don sauke farali na aikin Hajjin bana.

Rahotanni sun nuna cewa Yahaya Zango ya nemi fakewa da maniyyata ne da nufin tserewa zuwa waje, sai dai tsaro mai ƙarfi da bincike na cikin gida ya tona masa asiri.

Wadannan sune masu neman kujerar Gwamna a Jihar Kano 2027Gov. Abba Kabir Yusuf (Incumbent)DSP, Barau Jibrin.Nasir Yusuf ...
18/05/2025

Wadannan sune masu neman kujerar Gwamna a Jihar Kano 2027

Gov. Abba Kabir Yusuf (Incumbent)

DSP, Barau Jibrin.

Nasir Yusuf Gawuna.

Engr. Umar Abdullahi Ganduje (Abba).

AA Zaura.

Hon. Abdulmumin Jibrin.
Mutanen Kano wa kuke so?

Ga jerin fitattun ‘yan takarar da ake sa ran za su fafata a Zaɓen Gwamnan Jihar Katsina a Zaɓen 2027:1. Gwamna Dikko Uma...
17/05/2025

Ga jerin fitattun ‘yan takarar da ake sa ran za su fafata a Zaɓen Gwamnan Jihar Katsina a Zaɓen 2027:

1. Gwamna Dikko Umar Radda (Mai Ci Yanzu)

Gwamna Radda, wanda ke kan mulki tun daga 2023 karkashin jam’iyyar APC, ana sa ran zai nemi wa’adin mulki na biyu. Ya shahara da shirye-shiryen ci gaban al’umma da kafa asusun tallafi ga matasa da ‘yan kasuwa, amma har ila yau yana fuskantar s**a daga wasu bangarorin siyasa kan yadda yake tafiyar da harkokin Gwamnati.

2. Sanata Garba Yakubu Lado Danmarke

Sanata Lado Danmarke na jam’iyyar PDP, tsohon ɗan Majalisar Dattawa kuma gagarumin ɗan takarar Gwamna a 2019 da 2023, Yana daga cikin masu fatan komawa tseren kujerar Gwamna. Ana kallonsa a matsayin gwarzon adawa mai karfi, wanda ke da karɓuwa a sassa daban-daban na Jihar musamman Talakawa

3. Sanata Ahmad Babba Kaita

Tsohon Sanata mai wakiltar Daura Zone Sanata Babba Kaita, Wanda ya sauya sheka daga APC zuwa PDP, Wanda a halin yanzu yana SDP na daga cikin matasan jiga-jigai masu tasiri a siyasar jihar. Ya jima yana bayyana damuwarsa kan yadda ake tafiyar da gwamnatin jihar, lamarin da ke nuna alamar zai iya tsayawa takarar Gwamna domin kawo sauyi.

4. Mustapha Muhammad Inuwa

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Mustapha Inuwa, wanda ya yi takarar Gwamna a zaben fidda gwani na APC a 2023 amma bai samu nasara ba, Ya fice Daga Jam'iyyar ya koma PDP. Yana Daga cikin wadanda ake hasashen za su sake shigowa tseren.

KBC Hausa

Labari na cewa: sojojin mu na cigaba da samun nasara akan yan'taadda Mu Sanya su a addu'on mu Yah Allah ka Kara Basu nas...
17/05/2025

Labari na cewa: sojojin mu na cigaba da samun nasara akan yan'taadda

Mu Sanya su a addu'on mu
Yah Allah ka Kara Basu nasara amiin 👏🙏

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Farar Jarida News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share