Al-Haqqu TV

Al-Haqqu TV Wannan gida an gina shi ne dan tattaunawa da nemo mafita a kan matsalolin Arewacin Nigeria

25/09/2025

Kamar yadda magoya bayan Sheikh Lawan Triumph ke ikirarin korewa Annabi yake, to haka shima Sheikh Abduljabbar korewa yake.

Gara ma Sheikh Abduljabbar yana kore zantukan da a yadda ya fassara su munana ne, shi kuwa Sheikh Triumph maganganun girmama ga Annabi yake wa izgili.

Breaking News 💥 Wani Matashi Mai Suna Abdulazeez Maddock Anti-Propagandist  Ɗan Auta Dake Kofar Kibo Zariya Ya Cinnawa T...
20/09/2025

Breaking News 💥
Wani Matashi Mai Suna Abdulazeez Maddock Anti-Propagandist Ɗan Auta Dake Kofar Kibo Zariya Ya Cinnawa Takardun Degree Dinsa Wuta Sabo da Acewar sa Yau Shekarar Sa 3 Da Gama Degree Bai Samu Aiki Ba, Amma Sai Ga Mawaki Rarara Wai Yagama Degree Harda Shaidar Girmamawa,Yace Gara Ya Kona Takardun Yakoma Kasuwanci

Zindiqi
11/09/2025

Zindiqi

"Muna kira da a canja hafsoshin tsaro"---Sen. Ali Ndume.Me za ku ce?
11/09/2025

"Muna kira da a canja hafsoshin tsaro"---Sen. Ali Ndume.

Me za ku ce?

Kwankwaso, Ganduje da Abba Kwankwaso ya yi sama da fadi da 2.5 biliyan daga asusun yan fansho na jihar Kano. EFCC ta ton...
10/09/2025

Kwankwaso, Ganduje da Abba

Kwankwaso ya yi sama da fadi da 2.5 biliyan daga asusun yan fansho na jihar Kano. EFCC ta tono badakalar bayan yan fansho sun kai kokensu. An nemo shi, kuma ya yi fashin baki. Bincike ya tabbatar da ya yi wasa da dukiyar al’ummar jihar Kano da ya kai 41 biliyan da sunan gina gidaje.

Bayan an gina gidajen Kwankwaso ya rabawa yan uwa, abokai, da kuma masu masa hidimar siyasa kusan 324. Yan fansho an barsu a rana. Gwamnatin Kwankwaso ba a harkar fansho kadai ta rika wasa da kudi ba, har da kwangila da tallafin karatu da ake cirewa dalibai da sunan fita kasashen waje karatu.

Kwankwaso ne ya fara kashe ilimin firamare da sakandire bayan Shekarau ya sauka. Da yana son ilimin a hakika da ba cire dalibai kasashen waje kadai zai yi ba, hadawa zai yi da ilimin kasakasa. Bukatar ita ce, a cire matasa masu digiri su je su karo karatu su dawo, daga karshe su saka jar hula su rika kare Kwankwaso. Yau daidaiku ne masu kare kasar Kano da talakawan Kano, amma duk sun zama yan bangar siyasa.

Ganduje ya gaji lalacewar ilimin firamare da sakandire ne a hannun Kwankwaso, amma da yake su yaran da aka dauka zuwa kasashen waje basu da adalci, sai su ka ce shi ya kashe ilimi. Bayan kuma hatta satar kudin al’umma ta hanyar kashe mu raba da sunan Kwangila a hannun Kwankwaso ya koya, da kuma hada yan daba su sassari abokan hamayya.

Ganduje ya fi kowa cire kudade masu nauyi dan zuwa karatu a kasashen ketare. Ya kashe biliyan 20, Kwankwaso kuma biliyan 12, Abba kuma biliyan 5.3. Amma da yake su matasa basu da wayo da ilimi sai suke gani Kwankwaso ne jagora. Idan ana maganar raya jihar Kano da ayyukan cigaba dan saukaka sufuri babu kamar Ganduje. Ya tafka satarsa cikin ilimi, domin shi ya kware a saka hannun jari a samu riba kowa ya samu.

Ba abin mamaki bane dan Abba ya yi sata, gado ya yi a wajen Kwankwaso. Daman barewa ba za tayi gudu danta ya yi rarrafe ba, tayaya za ka saka hannu Audu Rogo ya saci 6.5 biliyan daga ofishinka kuma ka ce ai Ganduje ma barawo ne! Kenan tun asali burinka cin amana ne da gangan, wacce irin magana ce wannan! Yanzu shi Ja’Afar Ja’Afar bashi da hankali ne da ya binciko badakalar? Haba Abba, da wayonka amma ka ba da mu!

Babban takaicina ma shi ne; masu ganin wai Abba ba barawo bane, bayan a gwamnatinsa aka yi satar kwangilar maganin marasa lafiya. Amma da yake ya iya ashana haka ya fito yana nuna bacin ransa. Ga harkar shinkafa dss. Ga barna barjak ta ko ina, ga kuma badakalar Namadi da Danwawu mankas! Duk fa ana sane, kawai an rainawa al’umma hankali ne. Wani kwallo ne ba shege ba! Kar mu ke kallonku. Kwankwasiyya cin amana!

Na tafi fada nemo bayanai!

Tebo

Jarumin Kannywood Lawan Ahmad wanda aka fi sani da Umar Hadin, a cikin shirin Izzar So, kuma mashiryin Izzar So ya sake ...
02/09/2025

Jarumin Kannywood Lawan Ahmad wanda aka fi sani da Umar Hadin, a cikin shirin Izzar So, kuma mashiryin Izzar So ya sake shirya wani fim mai suna "Matashiya", kuma ya kusa zuwa kasuwa.

Wane fata za ku mishi?

"Ni ban yiwa Adam Zango butulci ba domin bai taimake ni ba nine na taimake shi.A lokacin da muke tare dashi duk abinda z...
02/09/2025

"Ni ban yiwa Adam Zango butulci ba domin bai taimake ni ba nine na taimake shi.

A lokacin da muke tare dashi duk abinda zanyi na waka bashi yake min ba da kaina nake yi kuma A lokacin bai taimake ni ba.

Da ina Kaduna a kwararo nake kwana yau na kwana can gobe na kwana nan, duk cikin masu cewa sun taimake ni babu wanda ya taba tambaya ta ina nake ina iyaye na suke.

Maganar daukaka kuma Allah ne ya bani koshi da mukai waka Allah ne ya hadamu dan haka babu wanda ya taimake ni sai Allah

~ Cewar Mr Bangis tsohon yaron jarumi Adam A Zango

01/09/2025

"Na zabi M+M ne saboda Muslunci"---AshSheikh Muhammad Sani Alhaji Yahaya Jingir.

Ku duba da kyau, kamar Gwamnan jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ne a wannan tsohon hoton ko? Allah mai jujjuya lamura, a...
31/08/2025

Ku duba da kyau, kamar Gwamnan jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ne a wannan tsohon hoton ko?

Allah mai jujjuya lamura, a lokacin ba lallai yayi tsammanin za'a wayi gari shine shugaban duk wa 'yanda yake daukan su hoton nan ba.

Malam ka tsoraci duniya, wata ran na baya ya koma gaba, na gaba kuma ya koma baya.

Da Dumi-DumiJam‘iyyar Tinubu ta APC ta lashe kujeru 20 cikin 23 a zaben kananan hukumomin jihar Rivers
31/08/2025

Da Dumi-Dumi

Jam‘iyyar Tinubu ta APC ta lashe kujeru 20 cikin 23 a zaben kananan hukumomin jihar Rivers

Bansan ya akayi na shiga film ba, saboda mu a gidan mu ko tv babu inji jarumar kannywood Basarakiya.Kamar yadda zaku gan...
31/08/2025

Bansan ya akayi na shiga film ba, saboda mu a gidan mu ko tv babu inji jarumar kannywood Basarakiya.

Kamar yadda zaku gani acikin wannan bidiyon: https://onlineamazingfact.blogspot.com/2025/08/bansan-ya-akayi-na-shiga-film-ba-saboda.html

Wani sabon labari ko ince wani sabon abun ban mamaki daga daya daga cikin jaruman kannywood wacce akafi sani da basarakiya, cikin wani hira da akayi da ita ta bayyanawa duniya cewa ita sam bata san taya akayi ta shiga harkar film ba saboda ita kwata kwata bata da raayin yin film amma sai ta tsinci kanta tsamo tsamo acikin harkar kamar yadda zaku gani anan: https://onlineamazingfact.blogspot.com/2025/08/bansan-ya-akayi-na-shiga-film-ba-saboda.html

Jarumar ta bayyanawa duniya cewa koda ta taso a gidan su, su basa kallon film saboda ko tv babu a gidan su har ta taso bata ganin film sannan babanta malami ne duk da cewa ba irin malamai dake hawa mimbari suna waazi bane, Amma dai daidai gwargwado yasan addini sosai.

Kuma yadda ta tsinci kanta a harkar film, bai wuce ta hanyar aikin da takeyi ba, kasancewar ta maaikaciyar asibiti ma'ana ita nurse ce, wasu lokutan yan film suna yawan zuwa asibitin su, suna daukan film a haka har s**a saba, har s**a fara sakata a film jefi jefi.

Shin me zaku iya cewa.

Rahoto: Farashin kwallon man kaɗanya ya faɗi da kashi 33% bayan Najeriya ta dakatar da fitar da shiFarashin kwallon man ...
31/08/2025

Rahoto: Farashin kwallon man kaɗanya ya faɗi da kashi 33% bayan Najeriya ta dakatar da fitar da shi

Farashin kwallon man kadai, wadda ake amfani da shi a wajen yin kayan kwalliya da kayan zaki, ya yi mummunan raguwa a Najeriya bayan gwamnatin kasar ta yanke shawarar hada kai da wasu kasashen Yammacin Afirka wajen dakatar da fitar da ita, in ji mujjallar Bloomberg.

A karshen ciniki ranar Alhamis, farashin ya tsaya a Naira 800,000 ($521) a kowace ton, wanda ya ragu da kashi 33 cikin dari daga kwanaki kadan da s**a gabata, in ji Bloomberg, inda aka ambato Rildwan Bello, babban darakta na Vestance, wata cibiyar bada shawara a Legas da ke bibiyar kasuwar noma na faɗin haka.

A ranar 26 ga watan Agusta, Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin dakatar da fitar da kwallon tsawon watanni shida na wucin gadi.

Ministan noma da tsaron abinci, Abubakar Kyari, ya bayyana cewa dakatarwar ta yi nufin “tabbatar da wadatar kayan masarufi ga masana’antun cikin gida, samar da ayyukan yi, da kare darajar kayayyaki".

Kyari ya kara da cewa haramcin zai taimaka wajen gyara gibin kasuwa, inda Najeriya ke samar da kusan kashi 40 cikin dari na kwallon a duniya, amma tana samun kasa da kashi 1 cikin dari na kasuwar da darajarta ta kai dala biliyan 6.5.

Da yake magana da Bloomberg, Bello ya ce duk da cewa an yi wannan mataki da kyakkyawan nufi, sakamakon kudi nan take zai iya zama mai tsanani ga ‘yan kasuwar da za su iya gaza cika kwangilolinsu.

“Fitar da ita waje ne ke sanya kasuwa ta yi armashi. Bukatar cikin gida ba ta kai samarwa ba,” in ji shi.

Address

Northern
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al-Haqqu TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category