Nasirul Mahdy

Nasirul Mahdy Ma aiki (S.A.W.W) Yace "Duniya Bazata Kareba Harsai Daya daga Ahalina yazo ya cikata da Adalci , Kam

26/12/2025

Shirin Amurka na mamaye Nigeria da sunan yaki da ta'adaanci , Malam Zakzaky (H) ya tona asiri.

Wannan Jawabin shekarun sa sunkai Goma Sha Daya 11.

Filin yaki mafi tsanani ba a cikin rairayi bane, kan tsauni ko falalen karfe.A'a filin yaki mafi tsanani shine yakin Kwa...
25/12/2025

Filin yaki mafi tsanani ba a cikin rairayi bane, kan tsauni ko falalen karfe.

A'a filin yaki mafi tsanani shine yakin Kwakwalwa na Tinani mahanga da nazari.

Yakine wanda ake gwabzawa tsakanin masu kokarin sarrafa tinanin mutane da masu bada kariya.

Masu kokarin sarrafa tinanin mutane, shedanun masu mulkine, gurbatattun fahimtocine ko tsarin gudanar da mulki na Zalunci da yake son sabarwa Mutane rayuwa a cikin Zalunci.
Suna amfani da mak**ai na maye gurbin gaskiya da karya, Magana daga bakin Sannanun mutane a cikin al'umma,
Yada bayanai na karya a littafai, gidajen Jaridu, fina-finai, wakoki da duk hanyar isar da sakonni ga Al'umma .

Babban Hadafin su shine samun ikon yin mulkin mallaka ga Tinanin mutane.

Su raunata alakar Tinanin mutane da qa'idojin Addini da Rayuwa, su maida mutanen masu sakaci, kuma Masu taimaka masu wajen rusa mutanen.

Suna cika Tinanin mutane da hayaniya domin su dushe sautin Sakon gaskiya daga yin tasiri.

Matsahi Dan Gwagwarmaya kuwa Aikinsa shine ya zama a fadake a Tinanin sa , mahangarsa da nazarinsa.
Makamin sa kuma ya zamo zuzzurfan dubi ga Abubuwan da suke faruwa a kewaye dashi.
Sauraren Karatun Malam (H), Tinaninsa , Da mahangar sa a cikin dukkan Al'amura.

Daga zantukan Imam Ali Karramallahu Wajahahu yana cewa.
"Nasara tana da Bukatar hangen nesa, hangen nesa kuma yana da bukatar Tinani da shiri"

Wannan ilimin Malam Zakzaky (H) ya Dade da bamu shi a karance Kuma a aikace.
kuma Wannan ilimin shine ake amfani dashi a yakin Kwakwalwa, anan ne zamu iya banbance -Gaskiya daga karya,

Anan ne zamu iya banbance Zalunci da aka boye da sunan Adalci, sanann mu iya hango nesa , ba kusa mai tsanani ba da ake bamu tsoro da ita har Zuwan nasara Kamar yadda Karbala ta Bada misali.

Dan haka sakaci da yin nazari Mai zurfi ga karatuttukan Malam (H) da Irshadinsa Kamar Mika wuyane a fagen Yakin Kwakwalwa Wanda Tinani ne Jagoran sa.

Fatanmu Allah Subhanahu Wa Ta'ala ya Bamu Nasara, ya Kuma Bamu ikon Amfani da Tinani Domin yin nasara a yakin Kwakwalwa da ake ciki.

MUQAWAMAKalmar Muƙawama a yanzu ta shahara a bakin masu kokarin kai hari a fakaice ga Harka Islamiyya da Jagorancinta, c...
19/12/2025

MUQAWAMA

Kalmar Muƙawama a yanzu ta shahara a bakin masu kokarin kai hari a fakaice ga Harka Islamiyya da Jagorancinta, cewa ana nema a mayar da Da'awar Harka Islamiyya zuwa Muƙawama, su kuma ba za su zura ido hakan ya faru ba. A maimakon hakan, za su yi sa'ayi ne wajen cigaba da Harkar, amma a salon da ba na abinda suke kira Muƙawama ba. Ina iya cewa, a salon abinda ake kira "Likimo". Ko da yake su a bayan fage suna cewa ne, suna yunkurin kawo sauyi ne a tafiyar Haraka Islamiyya.

Ma'anar Muƙawama a wajensu yana farawa ne daga dakewa da tsayuwa ƙyam wajen fuskantar zalunci da azzalumai, ko da kuwa za a kashe wanda ya tsaya din, sai (ma'anar a wajensu) ya tuƙe akan, duk wanda ke ma azzalumi barazana ko kasheji akan cewa, in har ya sake ya kai wani iyaka da zaluncinsa, to zai ɗanɗana kuɗarsa. — Wato in kace, in har azzalumi ya nufi kai hari ga waje mafi girman daraja a doron duniya a wajenka, za ka kare kanka da duk irin abinda kake iyawa, ko da kuwa hakan zai kai ka ga rasa ranka.

Ahhh! Malam da wannan furuci, ka ɗauki Da'awa daga matakin kira, ka kai shi matakin muƙawama, kuma ka yi musu laifi, kuma suna da hakki su yi maka raddi don su kubutar da mabiyansu da ke da Wilaya gare su daga zullumi da fargaban abinda ka iya faruwa sak**akon wannan dakewar.

Babban abin takaici shi ne, yadda s**a tsayu wajen kafa hujja irin wadda 'yan Commercial s**a shafe shekaru suna kafawa 'yan gwagwarmaya, na jirkita tarihin Imamai (AS), da kokarin bayar da shi a sigar kare ra'ayinsu na cewa, mafi yawan Imamai (AS) sun yi gwagwarmaya ne cikin sigar Likimo. — Wal izu billah. S**an ce, Imam wane bai rike makami ya yi yaki ba, Imam wane bai yi fito na fito da azzalumai ba, Imam wane ma ya shiga Hukuma ne, da sauransu. Wato suna kokarin nuna su mabiya wadannan Imaman ne a rayuwar da s**a zabawa kansu na yin Shi'anci mare motsi a zamanin jiran bayyanar wanda zai yi yaki ya mamaye duniya da adalci bayan ta cika da zalunci da danniya. Alhali a karshe bakinsu kan furta cewa duk Imaman nan Shahada s**a yi ta hanyar guba ko takobi, wanda wannan kawai yana tabbatar maka da irin dakewar da s**a yi, wanda ta kai ma ga Shahadantar da su ta duk hanyar da ake iyawa.

Me ya hana Imamai daukan mak**ai akan azzalumai? Amsa: Samun mabiya irin ku, masu ra'ayin cewa rayuwarku ne wanzuwar addini, in kuka sadaukar aka kashe ku saboda addini, ko kan kare alamin addini, kun yi asara ne a ganinku. Da ace duk A'imma (AS) sun samu mabiya masu sallamawa irin Sahabban Imam Hussain (AS), wato mutum kasa da 100 masu Iklasi akan bin Imami a lokacin, da tabbas dukkansu sun yaki azzaluman lokacinsu da makami.

A wasiyyar Manzon Allah (S) ga Amirulmuminin (AS), da ace Imam (AS) ya samu mutane 40 masu Iklasi tun a farkon al'amari, da ya yaki mutanen Saqifa ya karbi ikon gudanarwa, ko da kuwa hakan zai kai ga Shahadarsa da mabiyansa. Amma da ya nema ya rasa, mutane s**a zama irinku, masu jin cewa a tafi a hankali, tunda manya sun riga sun karɓi mulki, a bi su a hankali kawai a wanye lafiya. Sai Imam Ali (AS) ya koma rayuwar addini shi kadansa da Iyalansa, da tsirarun da s**a kasance tare da shi. Har sadda al'umma s**a nuna k**ar da gaske suna shirye da su bi shi, ya yanke musu uzuri, karshe s**a tabbata a mabiya ne irinku, ba masu sallamawa da sadaukarwa ba.

Imam Hasan Almujtaba (AS), har yaki ya daura damarar yi, amma fahimtar cewa mabiyan nan irinku ne, masu makyarkyata wa azzalumai, masu raba Wilaya biyu, daya ga Shi'anci a zahiri, dayan ga Shaiɗanci a baduni, dole ya kwance ɗamarar yakin, aka wayi gari yana aikata addini ne a karan kansa, da kokarin neman mabiya na gaskiya da za su dafa masa a gaba, akan haka har aka Shahadantar da shi.

Imam Hussain (AS) wanda dama k**ar haushinsa wasunku suke ji, ba ma ku cika k**a sunansa ku yi misali da tsayuwarsa da Sahabbansa ba. Amma shi kansa yana da zabi biyu a karshe, ko ya mika wuya ga azzalumai, ko ya dake kyam, da ya tabbata yana da mataimaka da s**a shirya biyayya a gare shi don baiwa addini kariya, ya baiwa ire-irenku uzuri, s**a tattafi don su je su yada addini, ko su yi sauran lamuran rayuwarsu k**ar yadda s**a ce, sai ya fuskanci mafi girman runduna tare da yana da mafi kankantar tawaga. Har Allah Ta'ala Ya bashi nasarar da a yau duk duniyar gwagwarmaya, ta Musulunci ko ta wani abu daban, suna daukarsa a matsayin abin koyi wajen fuskantar zalunci da azzalumai.

Imam Zainul Abidin (AS), ya samu mabiya ne? Imam Baqir da Imam Sadiq (AS) waye ya samu mabiya irin na Imam Husain (AS) a cikinsu? Sun samu almajirai ne kawai masu daukan karatu, wadanda da ace za su musu umurni akan jihadi, da duk za su tarwatse ne bakidayansu, k**ar yadda aka gwada wani mai nuna a shirye yake da hasa wuta aka ce ya shige ta, ya dauka Imam zai halakar da shi ne. Mabiya ne da su irinku, irin kuma wadanda kuke kokarin ginawa a yanzu, da ba amfanin da za su yi ma gwagwarmayar Imam Mahdi (AS) in ya bayyana, sai ma kokarin karyata shi da ruwayoyin cikin littafai da sunan ilimi.

Imam Kazeem (AS) ba samun mabiya irinku, irin wadanda kuke kokarin ginawa ne ya haifar da aka k**a shi aka wurga shi a Kurkuku tsawon shekaru, mabiya s**a yi shiru s**a cigaba da Shi'ancinsu da bugun kirjin an kashe Imam Hussain (AS), suna cewa, ina ma sun kasance tare da Imam Hussain a Karbala, da sun taimaka masa, da sauransu. S**a manta da cewa shi wannan da ke kurkuku s**a kasa tabuka komai akansa, bai da wata maraba da Imam Hussain din sam, har sai da aka kashe shi, aka basu gawarsa a wulakance, suna tunanin za su ga Imam (AS) ya fito salun-alun, sun sha fararen kaya, s**a sallaci gawar Imam cikin kayan farin ciki? An fada muku son Imam Kazeem (AS) ne mabiyansa s**a zama 'yan Likimo irin wannan? Da sun tashi akan taimakonsa za a kai ga hakan?

Kamar fa haka ne mutane s**a so Husainawa su kasance a lokacin da Yazidu ya nufi kashe Husainin Zamaninmu (H), Allah Ta'ala Ya kare rayuwarsa. S**a k**a shi s**a tsare a Kurkuku. Husainawa s**a tsayu kyam da gwagwarmayar nuna yatsa ga azzalumai akan su fahimci hadari ne rike abinda suke rikewa, kuma rashinsa barazana ce ga rayuwarsu. Wasu ala dole sai Husainawa sun bar wannan sadaukarwar, sun zama irin mutanen Imam Musal Kazeem (AS). Su bi azzalumai a hankali, har azzalumai su gane ba wata barazana a kansu ko sun kashe shi, su kashe shi, in an yi sa'a su bayar da gawar a masa sallah, ko su bizne shi da kansu, su barmu da bugun kirji a Markaz da Husainiyoyi, da Zikiran kashe Jagoranmu a duk shekara.😢 Kar Allah Ya nuna mana wannan kunyatan.

Suna cewa wai Imam Mahdi (AS) bai bayyana ba saboda rashin mabiyan da s**a shirya? Tambaya, Imam (AS) din in ya bayyana da masu makyarkyata wa azzalumai zai yi amfani ya yi yaki, ko kuwa da 'yan gwagwarmaya masu dakewar da suke iya fuskantar kowace irin barazana akan wanzuwar addini? Jamhuriyar Musulunci ta Iran sak**akon sadaukarwa da zubar da jinanen Shahidai ne ta tsayu, kuma sak**akon irin wannan sadaukarwa da jinanen Shahidai din ne za ta fadada a duniya, har a wayi gari Imam (AJ) yana bayyana zai zama yana da mataimaka a dukkan sassan duniya, ya yi amfani da su ya yi yaki, a samu Shahidai, karshe Allah Ta'ala Ya bashi nasara.

Harka Islamiyya, kira ne zuwa ga yunkurin tabbatar da addini, kuma cigaba ne ne da'awar Imam Khomeini (QS), wanda tsayuwa kyam din matasan Iran, da fahimtar martaban Shahada ta kai lamarin ga nasara, saboda haka irin wannan sadaukarwar ake da bukatarmu da shi a wannan lokacin. Wannan ne yasa Jagoranmu Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) wanda a makon nan aka karrama shi a matsayin mai bi tare da dabbaka tafarkin Imam Khomeini (QS), ya sha fada mana, yana cigaba da fada mana cewa, wanda duk bai shirya ba da ransa ba, ya fita daga cikin Harkar. Ko ba komai, asasi ne na tarbar Imamul Asr (AS), shi kuma ba zai yi aiki da matsorata ne ba, ko da kuwa sun kira kansu da mafiya Ilimi a duniya.

Kuma idan har jajircewa wajen yin Difa'i sunansa Muqawama, to Harka Islamiyya za ta cigaba da zama Muqawama a duk lokacin hujumin azzalumai, musamman ga Jagoranta, kuma k**ar yadda yake a Fiqihu, za mu yi Difa'i din ne da iyakan abinda muke iyawa ko da za mu rasa ranmu. Ba kisa muke ba, ba hari muke kaiwa ba, Da'awa muke yi, amma Da'awa ba yana nufin za a yi ta yinsa ba tare da kariyar kai ba ne, azzalumai da kansu za su iya kaimu kowane irin mataki, kuma idan s**a kai din, za mu yi hamdala mu karba hannu bibbiyu, Insha Allah.

Nasihar Jagora (H) da ya sha nananatawa shi ne, in karantarwa ka zaba, ka yi karantarwarka, ka yi ta koyarwa, amma ka kyale yan gwagwarmaya su yi sadaukarwarsu. Kar ka soki masu sadaukarwa, kace suna Muqawama ne, ko a kashe su bayan sun dake, su yi Shahada, kace ba Shahada s**a yi ba. Ka yi shiru da bakinka akan abinda ya shafi gwagwarmaya, ka cigaba da abinda kai kake ganin shi za ka iya ba da gudummawa a shi, ba wanda zai zarge ka. Amma duk sadda wani ya bude baki yana s**an Harka Islamiyya a fakaice, to babban Mara Kunya shi ne mai cewa warware shubuharsa rashin kunya ne.

Tafarkin addini na da santsi, a yayin da Annabi (S) ya koma ga Allah ya bar Musulmi fiye da dubu dari biyu, amma aka rasa mutum 40 masu Iklasi wajen bin wasiyinsa da gaskiya. A yayin da manyan al'ummar Annabi (S) s**A Shahadantar da ɗiyarsa ɗaya tal da ya bari, kuma sauran al'ummar s**a kalle su a matsayin manya, s**a cigaba da binsu da sunan sun rigayesu a addini, sun fi su shekaru. Abin tsoro a yayin da aka yanka Imam Husaini (AS) da mataimaka 72, a cikin al'ummar kakansa da ta mamaye duniya. Abin tsoro a yayin da aka rika daure Imamai a Kurkuku, tare da suna da masu cewa su mabiyansu ne dubbai, amma s**a kasa yi ma azzalumai bore, har s**a rika Shahadantar da su, s**a dauki ranakun Shahadarsu a matsayin ranakun kuka kawai.

Abin tsoro in ka dubi cewa wanda ya fara sauke Manzon Rahma (S) a gidansa a Madina, ya sadaukar da kansa ga addini, a karshe ya yi tsawon rayuwa, Yazidu Dan Mu'awiya ne ya masa sallar janaza. Firgici sosai a yayin da Zubair bin Awwam ya sadaukar ta hanyar baiwa Sayyida Zahra (SA) kariya da zare takobi a yayin da aka kawo mata hari a gidanta, amma a karshe ya zare takobi ya yaki Imam Ali (AS) a Jamal. Fargaba sosai idan irin su Ubaidullah, wanda ya kasance daga jaruman wannan addinin a farko, har tsanani yasa yana cikin wadanda aka tura su Hijira zuwa Habasha tare da matarsa, amma za a wayi gari ya bar Musulunci ya koma Kirista a Habasha, tare da babu takura sam a inda yake, har ya zama matarsa ta saku, sai Shugaba (S) ne ya aure ta bayan hakan.

Mamaki sosai, a yayin da Abu Zarril Gifari yake ruwaito Hadisin Manzon Rahma (S) da ke umurni da bin Ahlulbaiti (AS) a bayansa, amma aka rika azabtar da shi saboda wannan, har a karshe aka raba shi da Madina, aka mai da shi dajin Rabaza, inda ya rayu shi kadai, ya mutum shi kadai. Gaskiya tana da ɗaci da wahala, kuma tana da haɗari sosai. Amma duk wanda ya fahimce ta, ya daure ya yi iya kokari wajen tsayuwa akanta, ba tare da damuwa da zargin mai zargi ba.

Taujihi, Irshadi, Shawara, Nusarwa, Tabbatarwa da Aiwatarwar Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ne Harkar Musulunci, kuma sallama masa ne bin Harkar. Guna-guni, da zagon ƙasa, da kuma fito-na-fito da matsayarsa kuwa, da su ne ake barin Harkar. Kuma s**an matsayarsa ce fada da Harkar, yi ma Jagorancin Harkar guna-guni ko da a cikin taujihi da irshadinsa ne, alama ce ta munafunci ga wanda yake raya kansa a cikin Harkar. Saboda haka 'yan uwa mu shiga taitayinmu. Mu koma ga Jagora (H), mu fahimci Taujihinsa a gare mu, mu sallama masa. Hakan zai zame mana garkuwa daga amsa kowace irin Fikira da za a yi kokarin kunno da kanta a gare mu. Babu shakka har yanzu, har gobe Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky, da Da'awarsa suna tare da Allah Ta'ala, ba su taba barin Allah Ta'ala ba, kuma wallahi jan kafa daga gare shi ne yunkurin barin Allah Ta'ala. Allah Ta'ala Ya tsare mu.

Sabati Taufiqi ne daga Allah Ta'ala. Mu yawaita addu'ar da Jagora s**a mana Irshadi ta; “Ya Allah, Ya Rahma, Ya Raheem, Ya Muqallibal Qulubi Sabbit Qalbiy ala dinik.” Allah Ta'ala Ya bamu sabati.

— Saifullahi M. Kabir
28 Jimadal Thani 1447 (19/12/2025)

Hotuna: Wasu hotunan taron Yau Laraba 26/Jimada Ath-Thaniyah/1447 (17/12/2025) a Tehran, da aka karrama Jagora Sheikh Ib...
17/12/2025

Hotuna:

Wasu hotunan taron Yau Laraba 26/Jimada Ath-Thaniyah/1447 (17/12/2025) a Tehran, da aka karrama Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) da lambar Yabo ta "Imam Khomeini World Award" a Matsayin "Mai Girmama Al'umma da kuma hidima ga Raunana da Waɗanda ake Zalunta" sannan ɗaya daga cikin waɗanda ke yaɗa karantarwa da fikirar Imam Khomeini (R).





26/Jimada Ath-Thaniyah/1447
17/12/2025

"Mun binne mutane 347 a cikin dare": Ikirarin Gwamnatin El-Rufai mai ban takaici A cikin wani ikirari mai cike da mamaki...
14/12/2025

"Mun binne mutane 347 a cikin dare":
Ikirarin Gwamnatin El-Rufai mai ban takaici

A cikin wani ikirari mai cike da mamaki da takaici, Gwamnatin Jihar Kaduna ta amsa laifin shirya binne daruruwan wadanda aka kashe a asirce a karshen mako guda a watan Disamba na 2015. Wadanda abin ya shafa 'yan Harkar Musulunci ne a Najeriya, wadanda sojoji s**a kashe a lokacin wani farmakin soja a Zariya.

Wannan ikirari ya fito ne daga Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG), Alhaji Balarabe Abbas, yayin da yake bayar da shaida a gaban Kwamitin Bincike na Shari'a. Bayanin nasa ya saba wa musantawar da Rundunar Sojojin Najeriya ta yi cewa akwai wani kabari na gama gari daga abin da ya faru a Zariya. A gaskiya ma, wakilin Sojojin, a lokacin Kanar AK Ibrahim, ya rantse bisa rantsuwa cewa sojoji ba su kashe kowa ba.

Alhaji Balarabe, wanda aka sake nada shi a matsayin Sakataren gwamnatin, ya bayar da bayanai masu ban tsoro. Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta kula da binne akalla gawawwaki 347 a cikin kabari daya a Mando, a wajen Kaduna - kimanin kilomita 100 daga inda kisan ya faru.

An yi aikin ne cikin sama da awanni shida. An binne gawarwakin, maza da mata, ba tare da jana'izar Musulunci ba. Babu wani ƙoƙari da aka yi don gano waɗanda abin ya shafa ko kuma gano iyalansu. Sirrin da kuma gaggawar binnewar ya nuna cewa an yi ƙoƙarin ɓoye girman bala'in ne

A gaban Hukumar binciken ta JCI, Alhaji Balarabe ya bayyana matakan gwamnati a cikin kalamansa:

"An sanar da mu game da yiwuwar mace-mace bayan wani dare na rikici. Gwamna ya umarce ni da in tattara ƙungiya don tantance halin da ake ciki a Zariya. Ganin dokar jihar da ta buƙaci binne gawarwaki cikin awanni 24, dole ne mu yanke shawara kan abin da za mu yi da gawarwakin... Mun haɗu da Sojoji. An kai gawarwakin - 191 daga Depot na Sojoji da 156 daga Asibitin Koyarwa na ABU - tare da taimakon sojoji. Daraktanmu na Interfaith ya yi aiki tare da jami'an Sojoji a ƙasa. Sun ƙidaya kowace gawa a lokacin binnewar. Jimilla sun kasance su 347 ne."

Wannan shaidar ta nuna mummunan hoto na wani aiki na ɓoye don zubar da gawarwakin, wanda ya saba wa labarin hukuma da aka gabatar tsawon shekaru.

Shekaru goma bayan kisan gillar, na koma makabartar Mando. Kabarin bai-ɗayan ya kasance a bayyane a fili, wani tabo a ƙasar. Lokacin da ramin ya fara ruftawa—mai yiwuwa a ƙarƙashin nauyin gawawwaki 347 da ke ciki—sai aka cika shi da yashi ja. Yanzu, yayin da ciyawar daji ke fitowa a sauran wurin, wannan yanki na ƙasa ya ƙi yin rai; babu ko ɗaya daga cikin ruwan ciyayin da ya tsiro a kansa.

An ɗauki waɗannan hotunan ne a ranar Asabar, 13 ga Disamba, 2025. Wani shaida da ya tsaya a wurin kafin a binne gawawwakin ya jagorance ni. Mun tsaya a gaban wannan ƙasa mara ciyawa, mun yarda: dole ne a yi wa wannan kabarin bai-ɗayan alama. Ba tare da alami ba, a cikin wasu shekaru goma, baƙi za su wahala kafin su gano gaskiyar cewa wannan ƙasa tana rike da gaskiyar da ba a so ta bayyana dangane da kisan kiyashin da aka yi wa 'Yan'uwa musulmi a Zariya a Disambar 2015.

Daga Ibrahim Musa

10/12/2025

Wanda baya so A Kashe shi , Kada ya Shigo cikin mu.

05/12/2025

Taujihi ga 'yan uwa Musulmi, dangane da lura da sababbin fikirori da ake kokarin shigo da su cikin ma'abota da'awa zuwa ga komawa addini, daga waje.

— Jagora (H) a yayin rufe Mu'utamar da aka gabatar a garin Kano a shekarar 2025.

Harka Islamiyya Fikira Ce Da Ke Karkashin Marja'iyya Da Wilayatul Faqih Cikin abinda makiya s**a taso Harka Islamiyya da...
04/12/2025

Harka Islamiyya Fikira Ce Da Ke Karkashin Marja'iyya Da Wilayatul Faqih

Cikin abinda makiya s**a taso Harka Islamiyya da shi na soke-soke, akwai cewa Jagoran Harkar ba Marja'i ba ne, don haka a fahimtarsu, lazim ne motsin gwagwarmaya ya kasance a karkashin Marja'i, in ba haka ba ɓata ne.

Su sun yi da sauƙi ma, ko da yake da yiwuwar suna fata ne in s**a iya rushe Jagora (H), sai su koma kan Waliyul Faqih, wanda wasunsu ba kawai s**ansa suke ba, har ma suna la'antarsa ne. A yayin da magabatansu s**a soki motsin Ayatullah Khomaini (QS), tare da shi Marja'i ne, s**a ce yana ja ana kashe mutane a kawai, wa zai dauki alhakin jinanen da ake shekarwa a karkashinsa? Da sauran tuhume-tuhume da in mutum ya koma tarihi, zai ga duk Imam ya basu amsa.

Kullum muna tunatar da junanmu cewa, babban garkuwar Fikira ga dan uwa, shi ne lizimtar sauraron jawabai da karatuttukan Jagoran Harka, Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), domin kuwa duk wata shubuha da wani, ko wasu za su bijiro da ita a yanzu, da ma nan gaba, bakidaya Jagora (H) ya bayar da amsarta a jawabansa masu albarka.

Eh. Karatun cewa lazim ana koyi da Mujtahidi ne a wajen Ibada da Mu'amala, hatta su Jagora (H) basu boye ma 'yan uwa ba, har ma in mutum na sauraron Tafsirin Alkur'ani da s**a gabatar, da yawa in s**a kawo hukunce-hukunce daga wata Aya, s**an karkare da cewa, don samun bayani filla-filla, mutum ya koma ga Risala Amaliyya ne na Mujtahidin da ya cika sharudda. Haka ma duk shekara in an shiryawa yara masu shiga shekarun Takhlif taron tunatar da su, Jagora (H) na musu Irshadi da bin Marja'in da ya cika sharudda, har ma ya dora su a kan layin da ya k**ata su bi.

A jawabansa na baya da na yanzu, sam bai buya ga kowa ba, cewa shi Jagora (H) yana Taqalidi ne da Imamul Khomaini (QS), k**ar yadda ya sha fada, tun a shekarar 1980 ya fara bin Mazhabar Ahlulbaiti (AS), kuma yake koyi da Imam Khomaini (QS), yau kimanin shekaru 45 ko fiye kenan. Kuma ya amince cikakken amincewa da 'concept' din Wilayatul Faqih, ya bi Imam (QS) a rayuwar Imam din bisa wannan, ya dauke shi a shugaba, Jagora, abin kwaikwayo.

Bayan wafatin Imam Khomaini (QS), Jagora (H) ya cigaba da bin Magajinsa Ayatullah Sayyid Aliyul Khamenei (H) a wannan layin. Ya kalle shi a matsayin amintaccen magaji ga Imam (QS), kuma Waliyul Faqih. Kuma Sayyid Khamenei (H) bai yi ƙasa a guiwa ba wajen bibiya da tuntuba, da Irshadi ga su Jagora (H) akan wannan Kaddin da suke kai. Tun a shekarar 1992 bayan ya kafa Majma' Taqreeb Bainal Mazahib, Sayyid Zakzaky na daga mutane 12 na farko da Ayatullah Sayyid Khamenei (H) ya sanya su a matsayin masu gudanar da wannan Mas'uliyar.

Jagora (H) na da sila ta kaitsaye da Ayatullah Sayyid Khamenei (H), Sayyid Khamenei (H) na daukan Haraka Islamiyya a matsayin wata motsi da ke gudana a karkashin Kaddin Muqawamar duniya, da Manhajin Wilayatul Faqih, ko da kuwa tana marhalar da'awa ne. A duk sadda aka yi Waki'a, aka dira akan yan uwa na Harka Islamiyya, Waliyul Amril Muslimin, Ayatullah Sayyid Khamenei (H) kan kaɗu, ya tausaya, ya kuma jinjinawa 'yan uwa bisa dakewarsu. In ba a manta ba, kimanin shekaru 12 da s**a gabata, bayan Waki'ar Quds da aka kashe 'yan uwa 33 a Zaria, baya ga Ta'aziyya da Sayyid Khamenei (H) ya yi a rubuce, wanda ya ambace su da Shuhada, har da turo da wakilinsa Ayatullah Akhtari, wanda ya zo gidan Jagora (H) ya yi gaisuwa da Ta'aziyya, ya fadi kalmomin karfafawa a madadin wanda ya turo shi, wanda suna nan an taskace su. Ya kuma aiko da kudade kyauta ga iyalan Shahidan Waki'ar masu girma.

A Waki'ar Buhari din nan da yanzu ake tuna cikarta shekaru 10 da aukuwa, Allah Ta'ala kadai ya san adadin damuwa da kaduwa da Sayyid Khamenei (H) ya yi, wanda a zahiri, mun ji a karo kusan biyar yadda yake fitowa a sarari yana kalmomin yabo da jinjina ga Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), daya daga ciki shi ne, lokacin da ya ambaci Jagora (H) Sayyid Zakzaky da Shaikh, Mumini, Muslihi, wanda Video din na na har yanzu yana yawo. Ya ambaci wadanda aka kashe wajen baiwa wannan Muminin kariya da Shuhada. Watarana ma Ayatullah Khamenei (H) ke cewa, me yasa aka yi shiru ne da bayyana Mazlumiyar wannan Mujtahidin?

Shekaru biyu kacal da s**a wuce, Ayatullah Sayyid Khamenei (H) a yayin haɗuwa da Jagora Sayyid Zakzaky (H) ƙarara, mun ji kalmomi da ya ambata akansa, na nuna tsananin jindaɗin haduwar da ya yi da Sayyid Zakzaky da Iyalansa. Mun ga yadda Waliyul Amr, Ayatullah Sayyid Aliyul Khamenei (H) ya rungume Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), ya sumbace shi, sannan ya kuma ce masa:

انتم مصداق للمجاهد الحقيقي في سبيل الله، ونأمل ان تتمكنو من مواصلة“ جهادكم.”

“Ku ne ainihin misalin gwarzo mai jihadi na gaskiya a tafarkin Allah Ta'ala, muna fatan za ku cigaba da jihadinku.”

Har yanzu, ka koma shafin Ayatullah Sayyid Khamenei (H) ka ga wannan bayanin, wanda aka yi a ranar 14/10/2023. Da wane kuma baki, za ka soki Jagora Shaikh Zakzaky (H) ko Da'awarsa? Da bakin cewa shi ba Mujtahidi ba ne, alhali ga umurnin Mujtahidi din a gare shi? Anya ba rashin kunya a abubuwan da wasu mutane suke yi na s**an Haraka Islamiyya da Jagoranta Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) da sunan Shi'anci kuwa?

Ballantana kuma ƙarara Jagora (H) ya sha fada cewa, Da'awar nan cigaban Fikirar Ayatullah Imam Khomaini (QS) ne. In mutum ya koma ga jawabin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na tunawa da Imam Khomaini (QS) a shekarar 2023, Jagora (H) ya fada a fili cewa, Fikirar Imam Khomaini (QS) muke kai, kuma ita muke bi. Har ma ya jaddada k**ar yadda ya saba fada, cewa, ba ana da bukatar a samu wasu mutane a wasu yankuna da za su zama k**ar Imam Khomaini (QS) ba ne, yace Khomaini daya ne, an riga an yi shi, kuma ya bayyana Fikirorinsa, kuma lokacinsa ne har yanzu, don haka abinda duniya ke bukata a yanzu shi ne ta bi Fikirar Imam Khomaini (QS), wadda ba ta tsaya a kafa addini a iyaka Iran ba ne, Jamhuriyar Musulunci za ta cigaba da fadada ne har ta game duniya bakidaya.

Hatta batun cewa Jagora (H) ba Mujtahidi ba ne, da masu cewa shi Marja'i ne? Duk Jagora (H) ya ba da amsa kan wadannan, cewa ba lazim shi ne dole sai kowa ya zama Marja'i ba, ko sai shi ya zama Mujtahidi ba, abinda ake bukata shi ne mutum ya zama mai koyi da Marja'in. Kuma ban san mene ne ya shigarwa mutum duhu akan Harka Islamiyya ba, wanda Jagora (H) na fada cewa, ko Daula Islamiyya aka kafa, ba wata ta daban ba ce, ta Imam Khomaini (QS) ne. Don haka shi Jagora (H) ma'aikaci ne na Waliyul Faqih, aikinsa tabbatacce ne bisa hatimin Mujtahidai.

Kuma idan da gaske mutum Marja'iyya yake bi, ashe ba Marja'iyyar ce ta yi wa wasu masu Da'awar Shi'a Zallah a Nijeriya taujihi akan su komo su dafawa Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), wanda s**a kira shi da Ma'abocin Tuta ba?

Kamar yadda nace a baya, akwai wasu mutane wadanda su Shi'ancinsu na Ingila ne, wadanda hatta Marja'iyyan ma fada suke da waɗanda suke kan Fikirar Wilayatul Faqih, saboda haka Sayyid Khamenei (H) din, da ma Imam Khomaini (QS) duk ba a bakin komai suke kallonsu ba. Suna ma zaginsu ne, da aibata su, da nuna cewa su ma batattu ne masu batarwa. To kuma irin wadannan mutanen ne s**a kutso cikin 'yan uwa a tsakanin nan, suna bude shafuka su saka hotunan wasu Malaman Harka a Profile dinsu, sai kuma su rika s**an Harkar da cewa ba a bin Marja'iyya, Jagoranta ba Marja'i ba ne, da sauransu.

Yaushe ne Harkar ta saba da Marja'iyya? Ko wane aiki ne ya sauka akan Fikirar Wilayatul Faqih? Ba su iya kawowa. Ko ba komai ba su kai Waliyul Faqih din bibiya, sani, da takatsantsan ba, amma kuma tare da Taujihinsa, da fatansa ga Jagoran Harka Islamiyya na tsayuwa kyam da cigaba da abinda ya kira Jihadi, su suna s**an Jagora din a zahiri ne, har da zagi da cin mutunci. Ni ban san wane irin Shi'a mutum ke yi ba. Anya ba Shi'ar Shaidan ba ne su?

Ba matsala ba ce, koyar da yan uwa cewa lazim ana Taqalidi ne da Mujtahidi, 'yan uwa basu jahilci hakan ba, in banda kadan, wadanda yau da gobe suna fahimta ta hanyar karantarwa. Amma bayyana wajabcin Taqalidi da Mujtahidi da unwanin s**a ga Jagoran Harka Islamiyya, wanda ke gudanar da Harkarsa bisa stamfi da taujihin Waliyul Faqih, ɓarna ne da ba yadda za a yi masu lura su zura ido akansa face sun masa raddi. Kuma aiki ne da bai da nasara.

Da gaske ne, akwai wasu mutane da a cikin Waki'ar Buhari, waswasa din wasu masu irin ra'ayin Commercial a Iran s**a rude su, s**a wajjahar da Fikirarsu zuwa ga ra'ayin sassauci ga mahukunta, da nuna musu cewa Haraka Islamiyya bata da karfi, bai k**ata ta rika nuna dakewa ba, ya k**ata ne a rika bi a sannu, a yi biyayya ga mahukunta, in s**a hana wani motsin gwagwarmaya a hanu don a kiyaye jini, a maimakon tsayawa kyam a yayin hujuminsu ya k**ata ne a je a yi ta karantar da mutane Shi'ancin da ba gwagwarmaya, a yi ta da'awa zuwa ga Shi'a har a samu yan Shi'a da yawa, in s**a yi yawa, s**a riƙe manyan muƙamai a gwamnati na aiki da na siyasa, rana tsaka, in ma kafa addinin ne, sai a yi cikin ruwan sanyi.

Jagora (H) na ta mana taujihi akan wannan tunanin tun yana tsare, har ya fito ana jin bayanansa, har ma aka kai ga yanzu yana fada cewa, wannan ra'ayin an kunno shi cikin yan uwa, kuma wasu sun dauka. Amma abin mamaki, sai ka ga mutum ya rude. Ya rude da ma'anar shi Harka Islamiyya yake yi, amma kuma ya kasa fahimtar Jagoran Harkar, yana ganin akwai wani waje da ya fi samun natsuwa da gun, fiye da muhallin Jagorancin Harkar. In ka yi kokarin tunatar da shi, sai ya ɗauko jidali ya yi ta yi. Sai ya fara wasu maganganu da ke nuna zargi ne kaitsaye zuwa ga Jagora (H) a fakaice. A irin wannan halin ne kuma a kafafen sadarwa, akan sami masu irin wancan ra'ayin na s**an Jagora da sunan bin Marja'iyya alhali suna aibata Maraji'an, sai su samu bakin tsomowa, mafi yawa da 'fake accounts' din da ba sunan mutum, bare na ubansa, b***e a san wane ne shi.

Nasiha.

Idan Harka Islamiyya mutum zai bi, zai lizimci Jagoran Harka (H) ne, zai bi taujihi da irshadinsa, zai girmama shi, zai mutunta matsayoyinsa ko da kuwa bai san hikimar da ke ƙarƙashin daukarsu ba, zai sallama masa. Na'am, zai mutunta duk halitta, musamman Malamai da Iyaye, amma zai dage kai a kan kowa a cikin duk abinda ke rawa-rawa a gaban halarar Jagoransa ne.

Babu shakka duk wanda zai kasance a Kaddin Wilayatul Faqih a wannan nahiyar, wajibi ne ya bi Sayyid Zakzaky (H), domin shi ne ramzinta a wannan nahiyar a wajen ma'abotanta. Ba wata dabara, ba kuma hanya sassauka da mutum zai bi ya tsira face ita. Sai kuwa wanda bai taba sanin hanyar ba a asali saboda gazawar isar hakan gare shi.

Mu dafawa Ma'abocin Tuta, mu taimaki Jagora Sayyid Zakzaky, mu wanzu cikin biyayya ga Mujtahidi na gaskiya k**ar yadda Waliyul Faqih ya ambace shi, mu amsa kiran Waliyul Amr dinmu na kasancewa tare da Shaikh, Mumini, Muslihi, Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) wajen cigaba da dakewa akan wannan tafarkin da Mujtahidi ya kira shi da tafarkin Jihadi a tafarkin Allah Ta'ala.

Mu cika da Salati ga Annabi (S) da iyalan gidansa tsarkaka (AS) hadiyya ga Sayyida Ummu Baneen, akan Allah Ta'ala Ya kara kariya, lafiya, imani, aminci da yarda ga Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).

اللهم صل على محمد وآل محمد وعجل فرجهم ياكريم ❤️

— Saifullahi M. Kabir
13 ga Jimadal Thani 1447 (4/12/2025).

Saƙon Ta'aziyyaبِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِإنا لله وإنا إليه راجعون يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ,...
27/11/2025

Saƙon Ta'aziyya

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

إنا لله وإنا إليه راجعون

يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ, ارْجِعِي إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَرْضِيَّةً, فَادْخُلِي فِي عِبَادِي, وَادْخُلِي جَنَّتِي.

Labarin rasuwar babban Malami Sheikh Usman Ɗahiru Bauchi (R), yau Alhamis 06/Jimada Ath-Thaniyah/1447, ta sanya masoya cikin damuwa da jimami.

Marigayi ya kasance daya daga cikin fitattun malamai wanda ɗalibai da malamai s**a amfana da tarin iliminsa.

Wannan babban rashi ne ga daukacin al'ummar musulmi, Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) na mika sakon ta'aziyyarsa ga Iyalai da ɗalibansa masu daraja.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki da Ya saukar da rahamarsa ga ruhin marigayin; Ya sanya aljanna ta zama makomarsa ta har abada; sannan kuma Ya ba wa iyalansa da masoya haƙuri da juriyar wannan rashi.





06/Jimada Ath-Thaniyah/1447
27/11/2025

Address

Abuja

Telephone

+2348062756904

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nasirul Mahdy posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share