Najeriya Hausa

Najeriya Hausa Najeriya Hausa Jarida ce mai inganci zaku iya bibiyarta a ko da yaushe domin samun ingantattun labari

27/07/2025

Yadda Ta Häɗo Shêikh Muhammad Nuru Khalid Da Wasu Daga Cikin Malaman Ƙuɲgiyar Izãla

Me zaku ce?

Yanzu Shinkafa Ta Wadaci Duk ‘Yan Nijeriya — Cewar Daniel BwalaDaniel Bwala, mai ba Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu shaw...
27/07/2025

Yanzu Shinkafa Ta Wadaci Duk ‘Yan Nijeriya — Cewar Daniel Bwala

Daniel Bwala, mai ba Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu shawara ta musamman kan harkokin sadarwa, ya bayyana cewa a yanzu shinkafa ta wadaci a fadin Najeriya, sak**akon tsare-tsaren da gwamnatin Shugaba Tinubu ta bullo da su.

A cewar Bwala, wadannan nasarori sun samo asali ne daga shirin bunkasa noman cikin gida, rage dogaro da shigo da abinci daga waje, da kuma tallafa wa manoma kai tsaye.

“Gwamnatin Tinubu ta sauya akalar abinci a kasar nan. Shinkafa yanzu tana nan, har ana ganin sauki a farashi.” — In ji Bwala.

📌 Shin Gaskiya Ne Shinkafa Ta Wadaci? Ku bayyana ra'ayinku a ƙasan Comment

🔴 YANZU YANZU- Oluremi Tinubu Ta Taya Super Falcons Murnar Nasarar Gasar WAFCON 2024Matar Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu,...
26/07/2025

🔴 YANZU YANZU- Oluremi Tinubu Ta Taya Super Falcons Murnar Nasarar Gasar WAFCON 2024

Matar Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu, ta bayyana farin cikinta tare da taya ‘yan wasan Super Falcons murna bisa nasarar da s**a samu a gasar WAFCON 2024 (Women’s Africa Cup of Nations) da aka kammala ranar Asabar.

A wata wallafa da ta yi a shafukan sadarwarta, Oluremi ta ce wannan nasara ba kawai ta ‘yan mata bane, amma ta ƙasa baki ɗaya.

“Mun taya ku murna, Super Falcons! Kun sa Nijeriya ta yi alfahari.” — in ji ta.

Kungiyar ta Super Falcons ta doke kasar Morocco a wasan karshe da aka fafata a ranar Asabar, inda s**a kafa tarihi a matsayin zakarun Afirka na mata karo na 12.

Dubban ‘yan Najeriya a soshiyal midiya na yaba da rawar da ‘yan matan s**a taka, inda suke ganin cewa a karkashin matsin tattalin arziki da ke damun kasa, wannan nasara ta zo da kwanciyar hankali da farinciki.

ILIMI KOGI: Na yarda da ƙaddara, amma ina da fahimta mai ƙarfi cewa talauci ra’ayi ne- Farfesa Almuhajir Farfesa Sheriff...
26/07/2025

ILIMI KOGI: Na yarda da ƙaddara, amma ina da fahimta mai ƙarfi cewa talauci ra’ayi ne- Farfesa Almuhajir

Farfesa Sheriff Almuhajir, fitaccen malami kuma mai sharhi a al’amuran rayuwa, ya bayyana wata magana mai daukar hankali da ke janyo tunani da muhawara. A cewarsa:

Farfesan ya bayyana hakan ne a cikin wata tattaunawa da ke yawo a kafafen sada zumunta, inda ya bayyana cewa ra’ayin mutum game da kansa da makomarsa yana da tasiri sosai wajen fuskantar rayuwa ko faduwa a cikinta.

Ya kara da cewa, “Talauci ba wai kawai rashin kudi ba ne — yana iya kasancewa tunani ne da mutum ke ɗauka cewa ba zai iya ci gaba ba. Idan mutum ya yarda da hakan, to hakan ce rayuwarsa zata zama.”

Wannan furuci ya janyo martani da ra’ayoyi mabanbanta daga jama’a a kafafen sada zumunta. Wasu na goyon bayansa, suna cewa tunani mai kyau da kwazo su ne ginshikin fita daga kunci, yayin da wasu ke ganin talauci yana da alaƙa da tsarin rayuwar kasa da rashin damarmaki.

Shin ku ma kuna ganin cewa talauci ra’ayi ne, ko kuwa ƙaddara ce da mutum ba zai iya guje mata ba?

Shehu Sani ya maida Martani Ga Masu Cewa Bzasuyi Wanke Wanke A Gidan Miji Ba.Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Sh...
26/07/2025

Shehu Sani ya maida Martani Ga Masu Cewa Bzasuyi Wanke Wanke A Gidan Miji Ba.

Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya jefa tambaya mai daukar hankali ga wasu matan zamani da ke cewa "ba lallai sai suna yin wanke-wanke ba idan sun yi aure."

A wata wallafa da ya yi a shafinsa na sada zumunta, Shehu Sani ya ce:

"Mace na cewa ba za ta rika wanke-wanke ba a gidan mijinta. To idan ta shiga banɗaki fa, tsarki ma baza ta iya ba?"

Wannan kalami na tsohon sanatan ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda wasu ke ganin cewa yana tsokaci ne akan wata sabuwar dabi’a da ke yaduwa, inda wasu 'yan mata ke kin yin ayyukan gida bayan aure, suna ganin hakan tozarci ne ko rashin wayewa.

Sai dai wasu na ganin ya k**ata a rarraba aikin gida tsakanin ma'aurata bisa fahimta da jituwa, ba sai an tilasta mace ba.

Meye ra'ayin ku?

An Shedi Buhari Da Gudun Kele-kelen Duniya — Garba ShehuTsohon mai magana da yawun shugaban ƙasa, Garba Shehu, ya bayyan...
26/07/2025

An Shedi Buhari Da Gudun Kele-kelen Duniya — Garba Shehu

Tsohon mai magana da yawun shugaban ƙasa, Garba Shehu, ya bayyana cewa marigayi Muhammadu Buhari ya ƙi karɓar kyautar jirgin sama da agogon lu’u-lu’u yayin yana mulki.

A cewarsa, wani ɗan kasuwa ya kawo agogo da sunan Buhari a jiki, amma ya ƙi karɓa, ya ce:

“Agogon lu’ulu’u? Ba zan iya saka wannan ba. Ku mayar masa.”

Haka kuma a 2016, lokacin wata ziyara a Dubai, Sarkin Abu Dhabi ya so bai wa Buhari jirgin kai tsaye, amma ya ƙi ya ce:

“Idan gwamnati za a ba zan karɓa, amma ba ni da buƙatar jirgi na kai na.”

Buhari ya mulki Najeriya daga 2015 zuwa 2023, kuma ya rasu a watan Yuli, 2025.

🔴DA DUMI DUMI- Amnesty International Ta Yi Allah-wadai Da K**a Ghali Isma’il, Ta Bukaci A Sake Shi Cikin GaggawaKungiyar...
26/07/2025

🔴DA DUMI DUMI- Amnesty International Ta Yi Allah-wadai Da K**a Ghali Isma’il, Ta Bukaci A Sake Shi Cikin Gaggawa

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta duniya, Amnesty International, ta bayyana ƙin amincewarta da k**a matashin TikToka, Ghali Isma’il, wanda aka tsare saboda wallafa bidiyo da ya yi magana kan lafiyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A cewar Amnesty, kamun da hukumar DSS ta yi ba tare da cikakken bincike ba, wata babbar alama ce ta amfani da iko ta hanyar danniya.

“K**a Ghali Isma’il ba tare da bincikar sahihancin bidiyon da ya wallafa ba, na nuna gazawa da rashin shiri daga hukumar DSS. Wannan yunkuri ne na hana matasa amfani da kafafen sada zumunta wajen fadin albarkacin bakinsu da bincike kan halin da ƙasa ke ciki,” in ji Amnesty.

“Dole ne hukumomin Najeriya su sake Ghali ba tare da sharadi ba tare da dakatar da shirin gurfanar da shi a kotu bisa karairayi da gangan.”

Amnesty ta kuma bukaci gwamnatin Najeriya da ta mutunta, tare, da inganta ‘yancin fadin albarkacin baki ga kowane ɗan ƙasa, tana mai cewa irin wannan kamun da hukunci na ƙeta dokokin dimokuraɗiyya ne kuma yana barazana ga ‘yancin walwala da amfani da kafafen sada zumunta.

Ban San Cewa Gwamnatin APC Ta Yi Watsi Da Arewa Ba Sai Da Nayi Tafiya Daga Abuja Zuwa Kano -Inji Kwankwaso Ya ce hanya b...
26/07/2025

Ban San Cewa Gwamnatin APC Ta Yi Watsi Da Arewa Ba Sai Da Nayi Tafiya Daga Abuja Zuwa Kano -Inji Kwankwaso

Ya ce hanya ba kyau, duk tsawon shekarun da APC ta mulki kasar nan amma ko hanya tsayayya an ƙasa yiwa Arewa, Kwankwaso ya kuma zargi Gwamnatin Tinubu da kwashe dukiyar ƙasa tana raya shiyyar kudu ya yinda ta yi watsi da yankin Arewa

Me zaku ce?

26/07/2025

Dalilin Da Yasa MuKe Sujjada Akan Ƙasar Karbala — Al-Abdul Faneey Alkanaweey

Malamin Shi'a, a Najeriya Al-Abdul Faneey Alkanaweey, ya bayyana dalilin da yasa mabiya Shi'a ke sujjada akan ƙasar Karbala yayin sallah, wanda hakan ke janyo cece-kuce daga wasu.

Alkanaweey ya ce wadanda ke s**ar wannan dabi’a na yin hakan ne ba tare da fahimtar cikakken dalili ko tarihi ba. Ya yi kira da a fahimci juna a cikin al’umma tare da kaucewa yanke hukunci bisa rashin sani.

🟢 | | | | | | |

Sheikh Ibrahim Inyass: Shekaru 50 Da Rasuwar Fitaccen Jagoran Darikar Tijjaniyya.A ranar 26 ga watan Yuli, 1975, da misa...
26/07/2025

Sheikh Ibrahim Inyass: Shekaru 50 Da Rasuwar Fitaccen Jagoran Darikar Tijjaniyya.

A ranar 26 ga watan Yuli, 1975, da misalin karfe 12 da mintuna 3 na rana, Allah ya karbi rayuwar Shaikh Ibrahim Inyass, fitaccen jagoran darikar Tijjaniyya daga yammacin Afirka, a asibitin St. Thomas da ke birnin London, kasar Ingila.

An bayyana cewa Shaikh Inyass ya je Ingila domin jinya, amma har yanzu ba a bayyana cikakken musabbabin rasuwarsa ba. Ya rasu yana da shekaru 75 a duniya, kuma aka sallace shi daga duniya a dakin jinya mai lamba 2632 na sashen Simeon's Ward.

Bayan rasuwarsa, an dawo da gawarsa zuwa Senegal inda aka binne shi a Madina Baye, Kaolack, kusa da babban masallacinsa, k**ar yadda darikar Tijjaniyya ke girmamawa.

A watan Juni, 1975 (daidai da watan Jumada Thani 1395 AH), Shaikhul Islam ya sanar da iyalansa cewa yana son yin tafiya "gajeriya" zuwa Landan. Duk da cewa da yawa daga cikin ’ya’yansa maza sun nemi su raka shi, ya ki yarda da hakan, yana mai cewa tafiyar ba mai tsawo ba ce.

Sheikh Inyass ya shahara a fadin duniya musamman a yammacin Afirka, inda ya haifar da juyin juya hali a ilimi da tasirin darikar Tijjaniyya. Har yanzu, miliyoyin mabiyansa na ci gaba da tunawa da shi tare da gudanar da taruka da addu’o’i domin mika godiya da rokon rahama gare shi.

🟢 | | | | | |

🟩 Ni da Abba Hikima da Sharfaddeen Bature Mun Gyara Aji a Makarantar Sakandare a Arewa – Cewar Dan BelloFitaccen ɗan faf...
26/07/2025

🟩 Ni da Abba Hikima da Sharfaddeen Bature Mun Gyara Aji a Makarantar Sakandare a Arewa – Cewar Dan Bello

Fitaccen ɗan fafutukar cigaban matasa a Arewa, Dan Bello, ya bayyana cewa shi da Abba Hikima da Sharfaddeen Bature sun hada hannu wajen gyara ɗaya daga cikin ajujuwan makarantar sakandare a wani yankin Arewacin Najeriya.

“Mun ga cewa daliban da ke wannan makaranta na karatu cikin matsanancin hali – ginin aji ya kusan rushewa. Mun yanke shawarar gyara shi da kashin kanmu,” in ji Dan Bello a wata hira da ya yi da manema labarai.

Dan Bello ya jaddada cewa aikin ba shi da alaƙa da wata jam’iyya ko siyasa, illa kawai kishin Arewa da damuwar cigaban ilimi, musamman ganin yadda dalibai da malamai ke fama da matsaloli a yankunan karkara.

👫 Abba Hikima da Sharfaddeen Bature sun tabbatar da hadin kai

Tuni dai sauran masu ruwa da tsaki s**a yaba da wannan mataki, ciki har da iyaye da shugabannin makarantar da aka gyara.

“Wannan abin koyi ne – da al’umma za su ɗauki nauyin juna ba tare da jiran gwamnati ba,” in ji wani malami daga yankin.

🟥 DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Ba Da Umurnin Bincike Kan Kwamishinan Da Ake Zargi Da Yin Belin Dillalin Kway...
26/07/2025

🟥 DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Ba Da Umurnin Bincike Kan Kwamishinan Da Ake Zargi Da Yin Belin Dillalin Kwaya.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umurnin gaggawa na gudanar da bincike kan wani Kwamishinansa, wanda ake zargi da hannu wajen fitar da wani da ake zargin dilan miyagun kwayoyi daga hannun hukuma.

Wannan umarni na zuwa ne bayan wani rahoton sirri da ke nuna cewa daya daga cikin kwamishinonin jihar ya shiga tsakani wajen ba da beli ga wani shahararren mai fataucin kwaya, wanda hukumar NDLEA ke rike da shi.

“Babu ruwan gwamnatin Kano da duk wani abu da zai cutar da matasa ko ƙasa baki ɗaya. Za mu dauki matakin da ya dace idan aka tabbatar da zargin,” in ji wata majiya daga cikin gwamnati.

Gwamna Abba ya umarci Ma'aikatar Shari'a da ta tsaro da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin. Ana kuma sa ran hukumar NDLEA da sauran hukumomi za su bayar da hadin kai.

Idan aka tabbatar da zargin, gwamna zai iya dakatar da kwamishinan ko ma korarsa gaba ɗaya.

Ana kuma iya fuskantar hukunci daga NDLEA ko EFCC, idan akwai sabawa doka.

Wannan lamarin na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Kano ke taƙaitawa da yaki da fataucin miyagun kwayoyi, da kuma farfado da rayuwar matasa.

Masana harkar tsaro da na siyasa sun bayyana cewa wannan abu na da muhimmanci sosai domin ya shafi amincin gwamnati da gaskiyar akidar Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Address

Wuse

Telephone

+2348061549604

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Najeriya Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Najeriya Hausa:

Share