Najeriya Hausa

Najeriya Hausa Najeriya Hausa Jarida ce mai inganci zaku iya bibiyarta a ko da yaushe domin samun ingantattun labarai
(1)

Mun maida Kano ta zama cibiyar kasuwanci ta yankin Sahel — Gwamna YusufGwamna Abba Yusuf na Jihar Kano ya bayyana cewa c...
16/10/2025

Mun maida Kano ta zama cibiyar kasuwanci ta yankin Sahel — Gwamna Yusuf

Gwamna Abba Yusuf na Jihar Kano ya bayyana cewa cikin sauri jihar Kano na zama babbar cibiyar kasuwanci ta yankin Sahel, sak**akon sauye-sauyen da aka aiwatar tare da janyo masu zuba hannun jari.

Gwamnan, wanda mai ba shi shawara kan harkokin jiha, Alhaji Usman Bala, ya wakilta a wajen kaddamar da littattafai biyu a Abuja, ya jaddada cewa gwamnatin sa na amfani da tarihin kasuwancin Kano tare da rungumar sabbin hanyoyin kasuwanci na zamani.

Ya ce gwamnatinsa ta dauki matakan farfado da tattalin arziki ta hanyar inganta tsaro, i'ababen more rayuwa, da bunkasa wutar lantarki.

Haka kuma, ya bayyana cewa an fara aikin sauya tsarin karbar kudaden shiga zuwa na zamani da kuma toshe hanyoyin salwantar kudade.

16/10/2025
16/10/2025

An sace wayar kwamishinan tsaro a wurin taro kan matsalar tsaro a Kaduna Ana zargin sace wayar hannu ta Kwamishinan Tsar...
16/10/2025

An sace wayar kwamishinan tsaro a wurin taro kan matsalar tsaro a Kaduna

Ana zargin sace wayar hannu ta Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar Kaduna, Barista Sule Shu’aibu (SAN).

Lamarin ya faru ne a lokacin wani taron da ya shafi harkokin tsaro da aka gudanar a Kaduna a yai Alhamis.

Jaridar LEADERSHIP ta rawaito cewa satar ta faru ne a bainar jama’a, abin da ya haifar da tambayoyi kan yadda mai laifin ya samu damar aikata hakan a wurin da ke cike da jami’an tsaro.

Jaridar ta rawaito cewa har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a k**a wanda ake zargi da laifin ba, kuma hukumomin jihar Kaduna ba su fitar da wata sanarwa ta hukuma game da lamarin ba.

16/10/2025

Ƙasar Inĝilã Ita Ta Ƙirƙiri Wãbiŷãɲci, An Yi Amfani Da Lawrēɲcē of Arabiã Wajen Yin Hakan. Ku Je Ku Karanta Tarihi Ku Dawo Ku Ce Mana Ba Haka Ba Ne, In ji Shêikh Muhammad Nuru Khalid

Me zaku ce?

🟢DA DUMI DUMI- Gamayyar Malamañ Musùlunci Na Yankin Arewa Sun Gudanar Da Taro A Jihar Kaduna, Inda Taron Ya Samu Halarta...
15/10/2025

🟢DA DUMI DUMI- Gamayyar Malamañ Musùlunci Na Yankin Arewa Sun Gudanar Da Taro A Jihar Kaduna, Inda Taron Ya Samu Halartar Wasu Jiga-Jigan 'Ýàn Siyasa

15/10/2025

Dangane Da Canzawa Abduljabbar Muhalli.- Brr

🟢YANZU YANZU- Hukumar Gidan Gyaran Hali ta Najeriya Ta Bayyana Dalilin Sauyawa Sheikh Abduljabbar Wurin Tsare Shi Daga K...
15/10/2025

🟢YANZU YANZU- Hukumar Gidan Gyaran Hali ta Najeriya Ta Bayyana Dalilin Sauyawa Sheikh Abduljabbar Wurin Tsare Shi Daga Kurmawa Zuwa Kuje, Abuja

Hukumar Gidan Gyaran Hali ta Najeriya (NCoS) a Jihar Kano ta bayyana cewa sauya Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara daga gidan yarin Kurmawa na jihar zuwa wata wani ɓangare ne na tsarin aiki da doka ta tanada.

Mai magana da yawun hukumar a Kano, CSC Musbahu Lawan-Kofar Nassarawa, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Laraba.

Ya ce sauya ɗan fursuna daga wata bursin zuwa wata na daga cikin haƙƙin hukumar, bisa ga la’akari da yanayin tsaro da kuma tanadin da ake da shi a gidan gyaran halin.

“A cewar dokar Hukumar Gidan Gyaran Hali ta Najeriya ta shekarar 2019, hukumar na da ikon tafiyar da fursunoni a dukkan gidajen gyara hali a faɗin ƙasar nan,” in ji shi.

Lawan-Kofar Nassarawa ya ƙara da cewa sauyin wurin ba zai shafi shari’a da ake wa Abduljabbar ba, ko kuma ‘yancin daukaka ƙara da samun lauya.

Ya kuma jaddada cewa walwalar Sheikh Abduljabbar da ‘yancinsa za su kasance a ƙarƙashin kariya ta doka.

A nasa bangaren, Kwamandan hukumar a Kano, Ado Inuwa, ya nanata cewa hukumar za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta na tsarewa, gyara hali, da kuma sake haɗa fursunoni da al’umma don tabbatar da tsaron ƙasa.

In ba a manta ba, wata babbar kotun Shari’a a jihar Kano ƙarƙashin mai shari’a Ibrahim Sarki-Yola ta yanke wa Abduljabbar hukuncin kisa ta hanyar rataya a ranar 15 ga Disamba, 2022, bisa zargin yin kalaman ɓatanci ga Annabi Muhammadu (SAW).

Gwamnatin Jihar Kano ta gurfanar da shi a ranar 10 ga Agusta, 25 ga Oktoba, da kuma 20 ga Disamba, 2019 bisa tuhume-tuhumen da s**a shafi batanci.

15/10/2025

Laifuka uku da ake zargin DCP Abba Kyari da su - Bulama Bukarti.

Address

Area 1
Abuja

Telephone

+2348061549604

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Najeriya Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Najeriya Hausa:

Share