09/10/2025
Shugaba Tinubu Ya Yafewa Mamman Vatsa, Herbert Macaulay Da Wasu Mutane 174
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi amfani da ikon sa na gafarar shugaban ƙasa wajen yafe wa fitattun mutane da dama ciki har da Herbert Macaulay da Manjo Janar Mamman Jiya Vatsa wanda aka kashe a 1986 bisa tuhumar yunkurin juyin mulki.
Mamman Vatsa, wanda kuma shahararren mawaƙin Zube ne, ya samu wannan gafara ne bayan amincewar Majalisar Ƙasa da ta zauna a Abuja a ranar Alhamis.
Haka kuma, shugaban ƙasa ya yafe wa Herbert Macaulay, ɗaya daga cikin jagororin neman ’yancin Najeriya da ya kafa jam’iyyar NCNC tare da Dr. Nnamdi Azikiwe. Duk da Macaulay ya rasu tun 1946, har yanzu yana ɗauke da tabon kasancewa ɗan gidan yari daga hukuncin da Turawan mulkin mallaka s**a yanke masa.
Tinubu ya kuma yafe wa wasu tsofaffin masu laifi, ciki har da tsohon ɗan majalisa Farouk Lawan, tare da Mrs Anastasia Daniel Nwaobia, Barrister Hussaini Umar, da Ayinla Saadu Alanamu. An bayyana cewa sun nuna nadama kuma ana son ba su damar sake shiga cikin al’umma.
Sauran da s**a ci gajiyar gafarar sun haɗa da Nweke Francis Chibueze, wanda akai wa daurin rai-da-rai kan laifin hodar iblis, da kuma Dr Nwogu Peters wanda ya shafe shekaru 12 cikin hukuncin shekara 17 kan zamba.
Haka zalika, shugaban ƙasa ya bai wa Ogoni Nine cikakkiyar gafara, waɗanda s**a haɗa da Ken Saro-Wiwa, Saturday Dobee, Nordu Eawo, Daniel Gbooko, Paul Levera, Felix Nuate, Baribor Bera, Barinem Kiobel da John Kpuine.
Ya kuma ba da lambar girmamawa ta ƙasa ga Ogoni Four, Chief Albert Badey, Chief Edward Kobani, Chief Samuel Orage da Theophilus Orage.
An bai wa fursunoni 82 cikakkiyar gafara, an rage wa 65 hukunci, sannan an sauya wa 7 girman hukuncin daga hukuncin kisa zuwa daurin rai-da-rai.
Shugaban ya yi wannan ne bisa shawarwarin Kwamitin Taimaka wa Shugaban Ƙasa kan Gafara (PACPM) wanda Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), ke jagoranta. Kwamitin ya kunshi mambobi 12 ciki har da wakilan hukumar ’yan sanda, hukumar gyaran hali, hukumar kare haƙƙin bil’adama, majalisar koli ta musulunci da kuma majalisar kiristoci ta Najeriya.
Rahoton kwamitin ya nuna cewa daga cikin 294 da aka tantance, mutum 175 aka amince su ci gajiyar wannan shirin bisa ƙa’idoji kamar tsufa, rashin lafiya, ƙarancin shekaru, da kyakkyawan halayya a gidan gyaran hali.