Newsday Hausa

Newsday Hausa Domin samun ingantattun labarai ilmantarwa hadi da nishaɗantarwa ku cigaba da bibiyar Jaridar Newsday Hausa.

Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — MinistaMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai,...
09/07/2025

Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa tattalin arzikin Nijeriya na samun cigaba sannu a hankali, inda ya danganta hakan da sauye-sauyen da ake aiwatarwa a fannoni daban-daban ƙarƙashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a Abuja, yayin da yake karɓar baƙuncin mambobi da sababbin shugabannin Ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE) da s**a kai masa ziyarar ban-girma a ofishin sa.

Yayin da ya amince cewa har yanzu akwai ƙalubale, Ministan ya ce gwamnati na samun cigaba a hankali kuma tana samun nasarar rage tsananin matsalolin da ake fuskanta.

Ya ce: “Ba mu kai inda muke so ba a fannin tattalin arziki, amma muna iya gani cewa abubuwa suna tafiya a hankali. Shugaban Ƙasa ya faɗa sau da dama cewa mun fara fitowa daga ƙunci.

"Na san mutane da yawa za su ce ba mu kai ga cikakken cigaba da jin daɗin tattalin arziki ba tukuna. Gaskiya ne! Ni ma na yarda. Amma ba za mu ce babu cigaba ko kaɗan ba.”

Ya ƙara da cewa: “Ko hukumomin ƙididdiga na duniya suna fara ba Nijeriya kyakykyawan matsayi. Muna ganin alamu na ɗagawa a hanyar da ake tafiyar da tattalin arzikin mu.”

Idris ya ce manyan matakan sauyi kamar cire tallafin man fetur da daidaita farashin musayar kuɗi suna fara nuna tasiri mai kyau a ƙasar nan.

Haka kuma ya bayyana cewa sama da ɗalibai 300,000 ne suke cin gajiyar shirin bayar da rancen karatu na gwamnati, wanda ke ɗaukar nauyin kuɗin makaranta da kuma ciyar da su.

Ya ce: “Saboda wannan manufa da aka tsara ta gwamnati, sama da ɗalibai 300,000 na Nijeriya da a da ba za su iya zuwa makaranta ba ko kuma da s**a riga s**a bar makaranta, yanzu suna da damar komawa makaranta domin gwamnati tana biya masu kuɗin makaranta da na ciyarwa. Ba a taɓa samun irin wannan ba.”

A kan batun tsaro, Ministan ya ce gwamnati tana ɗaukar matakai masu ƙarfi don shawo kan matsalolin tsaro, inda ya ce dakarun soji na samun nasarori a yaƙi da masu laifi a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Ya roƙi kafafen yaɗa labarai da su goyi bayan ƙoƙarin da rundunonin tsaro suke yi, tare da guje wa bai wa masu laifi muhimmanci fiye da kima.

“Ina ta faɗa tun da farko cewa ba daidai ba ne mu a matsayin mu na ‘yan jarida mu riƙa ba waɗannan masu laifi, masu tayar da ƙayar baya, 'yan ta’adda ko ɓarayi ko duk yadda za a kira su, fifiko fiye da ‘yan Nijeriya nagari,” inji shi.

Ya ce ya kamata kafafen watsa labarai su riƙa bayyana nasarorin da sojoji suke samu da sadaukarwar su, maimakon maida hankali kawai a kan hare-hare da rashin nasara.

Idris ya bayyana cewa ko da yake aikin kafafen watsa labarai ne su riƙa sa ido kan gwamnati ta hanyar s**a mai amfani, wajibi ne su kuma riƙa bayyana nasarori da cigaban da ake samu.

A martanin sa kan Rahoton Gyaran Dokoki da ƙungiyar ta gabatar, Ministan ya ce zai tattauna da Ministan Shari’a kuma babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, tare da kafa kwamitin musamman a ma'aikatar sa domin nazarin rahoton.

Ya jaddada cewa manufar gwamnatin Tinubu tana daga cikin ginshiƙan dimokiraɗiyya ita ce kare ‘yancin faɗar albarkacin baki da ‘yancin kafafen yaɗa labarai.

Sai dai ya ja hankalin ‘yan jarida da su riƙa amfani da wannan ‘yanci cikin kishi da kishin ƙasa, tare da riƙon gaskiya da haɗin kai don ci gaban ƙasa.

Idris ya taya sababbin shugabannin ƙungiyar murna, tare da bayyana shirin sa na ƙarfafa dangantaka tsakanin gwamnati da kafafen watsa labarai.

Tun da farko a jawabin sa, Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Editocin Nijeriya, Dakta Sebastian Abu, ya bayyana cewa tawagar ta kai ziyara ofishin Ministan ne don gabatar da rahoton Kwamitin Sauya Dokokin Ƙungiyar a hukumance.

Ya bayyana cewa rahoton ya nuna wasu tsofaffin dokoki a kundin tsarin mulki da s**a zama ƙalubale ga ‘yancin aikin jarida a Nijeriya, waɗanda ya dace a duba ko a cire su.

09/07/2025

Tallar Shìrìñ Làbàrina 😂🤣

09/07/2025

Tattaunawar Jarumi Babasadiq Da Jaruma Hadiza Gabòn

09/07/2025

Yadda Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf Yasa A Baiwa Dattijo Mai Hoto Aikinyi, Wanda Yayi Hoto A Gwamnatin Kwankwaso Tun Shekarar 1999

09/07/2025

🤣😂

DA DUMIDUMINSA: PSG Ta Ragargaji Real Madrid Da Ci 4-0
09/07/2025

DA DUMIDUMINSA: PSG Ta Ragargaji Real Madrid Da Ci 4-0

09/07/2025

Kun Gane Wacce Jaruma Ce Kuwa?

09/07/2025

Ashe Khadija El-Rufai Ita Ce Babbar Kawar Amarya

09/07/2025

G-fresh 🤣😂

09/07/2025

❤️

09/07/2025

Nazirun Daura Ya Karrama Mawaki Dauda Kahutu Rarara

Mallam Abdulaziz Abdulaziz Kwalliya Ta Biya Kuɗin Sabulu Cikin Shekaru Biyu A Matsayin Hadimi Na Musamman Ga Shugaban Ƙa...
09/07/2025

Mallam Abdulaziz Abdulaziz Kwalliya Ta Biya Kuɗin Sabulu Cikin Shekaru Biyu A Matsayin Hadimi Na Musamman Ga Shugaban Ƙasa Tinubu

-Ya Shiga Ya Fita Ya Samar Wa Ɗumbin Matasa Ayyukan Yi Da Damammaki Cikin Gwamnati.

-Ya Riƙe Wa Shugaban Ƙasa Masoya Ya Ƙarfafa Musu Gwiwar Ci Gaba Da Kasancewa A Bayan Tafiyarsa

-Ya Riƙe Wa Shugaban Ƙasa Maƙiya Ya Hana Su S**a Da Yaƙarsa.

A yau, mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan harkokin sadarwa, Mallam Abdulaziz Abdulaziz ya cika shekaru biyu daidai a kan wannan muƙami da shugaban ƙasa ya ba shi.

Da ji ko da gani, za mu fahimci cewa ba shakka kwalliya ta biya kuɗin sabulu cikin waɗannan shekaru biyu da ya shafe a kan wannan matsayi.

Domin kuwa yayi amfani da damarsa wajen samowa ɗumbin matasa ayyukan yi da sauran damammaki na romon dimokaraɗiyya.

Ayyukan alkhairinsa ba ga iya masoya shugaban ƙasa Tinubu kaɗai s**a tsaya ba, kowa da kowa yake amfanawa. Wannan tasa hakan ya taimaka wajen riƙewa shugaban ƙasa Tinubu masoya waɗanda har yanzu suke tsaye a bayansa. Sannan kuma ya riƙe masa ƴan adawa waɗanda saboda shi suke kasa motsa adawarsu ko yaƙarsa. Irin namijin ƙoƙarin da ba kowane mai riƙe da muƙamin siyasa ne ya yi shugaban ƙasa shi ba a duk Arewa.

A matsayin Mallam Abdulaziz Abdulaziz na jajirtaccen ma’aikaci mai kula da harkokin sadarwa da ke yi wa shugaban ƙasa aiki, ya samar da kykkyawar alaƙa da fahimta mai kyau tsakaninsa da ƴan Jaridu da sauran mutanen da ke ayyukan yaɗa labarai. Wannan alama ce da ke nuni da yadda yake girmama ƴan jaridu da mutunta su gami da ba su kulawa ta musamman a matsayinsa na wanda ya fito daga cikinsu, hakan ya nuna cewa shi ɗin ɗan halak ne wanda ba ya manta mafari.

Duk da cewa Mallam Abdulaziz Abdulaziz ya yi ayyuka da dama na taimakon al’umma da gina rayuwar mutane, wasu abubuwan ma in yayi ba ya son a sani ko a ce shi ya yi. Wannan ke nuna yadda ya kasance mutum mai tsarkin Zuciya da kuma yin alheri ba dan a saka masa ba, sai don kishin ƙasa da son gina mutane.

Amma dai duk da haka, komai jimawa muna da kykkyawan fatan sai ya girbi abin da ya shuka na alheri, domin alheri ba ya faɗuwa ƙasa banza.

Mallam Abdulaziz Abdulaziz ya tona asirin mutane da dama da s**a samu irin wannan damammaki a baya ba su taimaki al’umma ba.

A cikin waɗannan shekaru biyu, ya yi abubuwan da wasu ba su yi ba a shekaru 4-8 a gwamnatocin baya. Shi ne mutum na farko da ya fara nunawa al’umma muhimmancin dama da yadda ake amfani da ita. Ya share hawayen dubban matasa sun tsaya da ƙafafunsu, ya kuma zame Garkuwa ga shugaban ƙasa Tinubu da gwamnatinsa wanda hatta ƴan adawa suke shakkar yin adawa saboda shi.

A madadin ni kaina, Bashir Abdullahi El-Bash, ina taya shi murnar cika wannan shekaru biyu a kan wannan muƙamin, yadda ya fara da Bismillah Allah Ya sa ya kammala da Hamdala. Allah Ya nunka masa dama sama da wannan a rayuwa ta gaba.

Adresse

Ogunia

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Newsday Hausa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Contacter L'entreprise

Envoyer un message à Newsday Hausa:

Partager