Newsday Hausa

Newsday Hausa Domin samun ingantattun labarai ilmantarwa hadi da nishaɗantarwa ku cigaba da bibiyar Jaridar Newsday Hausa.
(3)

16/01/2026

🧏‍♂️

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Dattijon Malamin Da Ya Kubutar Da Kirìstoci Sama Da 200 Daga Farmaki, Inda Ya Boye ...
16/01/2026

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Dattijon Malamin Da Ya Kubutar Da Kirìstoci Sama Da 200 Daga Farmaki, Inda Ya Boye Su A Masallaci A Yayin Wani Rikicin Addiñi A Jihar Filato Ya Rasu

PANTAMIYYA A BALANGA: Daruruwan matasa magoya bayan Professor Isa Ali Pantami (Majidadin Daular Usmaniyya kuma Wazirin P...
15/01/2026

PANTAMIYYA A BALANGA: Daruruwan matasa magoya bayan Professor Isa Ali Pantami (Majidadin Daular Usmaniyya kuma Wazirin Pantami) sun gudanar da taro a karamar hukumar Balanga, jihar Gombe.

A yayin gudanar da taron an kara wayar da kan marubutan kan abunda ya shafi harkar rubuce-rubuce a kafafen sada zumunta da wayar da kansu.

Haka zalika matasan Balanga sun jaddada kira tare da roko ga Professor Isa Ali Pantami, da ya daure ya fito takarar Gwamnan jihar Gombe a zaben 2027.

Mutanen Balanga sunyi dan-dazo Mazansu da matansu sun fito daga kowane yanki na fadin karamar hukumar, domin nuna soyayya da kaunarsu ga Majidadin Daular Usmaniyya.

Wannan yake kara nunawa da tabbatar da cewa mutanen jihar Gombe na kowane yanki a shirye suke domin bada gudummuwarsu na ganin Professor Isa Ali Pantami, ya zama zababben Gwamnan jihar Gombe a zaben 2027.

15/01/2026

Mr Project 🤣😂

Minista Ya Yi Alhinin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Yakubu MohammedMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Id...
15/01/2026

Minista Ya Yi Alhinin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Yakubu Mohammed

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya miƙa saƙon ta’aziyyar sa ga al’umma da gwamnatin Jihar Kogi bisa rasuwar babban ɗan jarida, ƙwararren ɗan siyasa, kuma ɗaya daga cikin waɗanda s**a kafa mujallar Newswatch, Malam Yakubu Mohammed.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba, Idris ya bayyana rasuwar ɗan jaridar a matsayin babban rashi ga fannin yaɗa labarai na Nijeriya—sana’ar da ya sadaukar wa sama da shekaru hamsin na rayuwar sa.

Ya yaba wa marigayin bisa jajircewar sa wajen tabbatar da gaskiya a aikin jarida, bincike mai zurfi, da kuma ƙarfin halin gaya wa hukuma gaskiya, ko da a lokutan mulkin soja.

Ya ce: “Marigayi Yakubu Mohammed ya kasance babban jigo a fannin aikin jarida, inda ya share fagen sabon salon aiki tare da kafa harsashin bincike mai zurfi a Nijeriya, wanda ya zama ƙashin bayan sa ido kan ayyukan gwamnati da shugabanci a tsarin dimokuraɗiyyar mu.”

Ya ƙara da cewa, “Tare da abokan aikin sa da s**a kafa Newswatch, gurbin da s**a bari da kuma nasarorin da s**a cimma na ci gaba da zama abin koyi ga matasan ’yan jarida, ba kawai wajen riƙe alƙalami ba, har ma da yin amfani da shi wajen kawo sauye-sauye a zamantakewa da siyasar al’umma.”

Haka kuma, Ministan ya bayyana Yakubu Mohammed a matsayin mai kishin ƙasa na gaske wanda ya yi imani da Nijeriya, jarumi wanda ya nuna juriya a lokacin fargaba, kuma mai kawo sauyi wanda ya yi amfani da basirar sa wajen ciyar da jama’a gaba, musamman a lokacin da yake matsayin Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU).

Idris ya yi addu’ar Allah ya jiƙan marigayin, sannan ya yi kira ga iyalai da dukkan waɗanda rashin ya shafa da su yi alfahari da kuma samun natsuwa daga kyawawan ayyukan da ya bari, waɗanda aka tattara a cikin littafin tarihin rayuwar sa mai suna “Beyond Expectations,” wanda aka ƙaddamar a watan Nuwamba 2025.

Shi dai Yakubu Mohammed ya rasu ne yana da shekaru 75, kuma ya rasu ƙasa da wata biyu bayan rasuwar ɗaya daga cikin waɗanda s**a assasa Newswatch, wato Mista Dan Agbese, a ranar 17 ga Nuwamba, 2025.

Sarkin Kano Na 16, Muhammadu Sanusi II, Ya Koma Aji Biyu A Jami’a Domin Karatun Shari’a A Jihar KanoMai Martaba Sarkin K...
15/01/2026

Sarkin Kano Na 16, Muhammadu Sanusi II, Ya Koma Aji Biyu A Jami’a Domin Karatun Shari’a A Jihar Kano

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya koma dalibi a matakin aji biyu (200 Level) a Jami’ar Northwest da ke jihar Kano, inda zai yi digiri a fannin Shari’a.

Rahotanni sun nuna cewa Sarkin ya ɗauki wannan mataki ne domin ƙara faɗaɗa iliminsa a fannin dokoki da shari’a, duk da matsayinsa na masarauci.

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya karɓi baƙuncin Shugaban Hukumar Ƙidayar Jama’a ta Ƙasa (NPC), ...
15/01/2026

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya karɓi baƙuncin Shugaban Hukumar Ƙidayar Jama’a ta Ƙasa (NPC), Dokta Aminu Yusuf, tare da Darakta Janar na Hukumar, Dokta Osifo Tellson Ojogun, a ofishinsa, a jiya Laraba.

Ministan ya ba su tabbacin cikakken goyon baya domin tabbatar da nasara, yayin da suke ƙoƙarin sake farfaɗo da Hukumar domin ta zama mai tasiri da inganci wajen aiwatar da ayyukanta.

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami’an Tsaro Sun K**a Wata Mata Da Ta Yi Ƙoƙarin Shigar Da Tabar Wiwi Gidan Yarin Jihar Ondo Inda Ta Boye...
15/01/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami’an Tsaro Sun K**a Wata Mata Da Ta Yi Ƙoƙarin Shigar Da Tabar Wiwi Gidan Yarin Jihar Ondo Inda Ta Boye Ta Cikin Tumatir

TARIHI: A Ranar 15 ga Janairu 1966, Aka Gudanar Da Jùyin Mulki Na Farko A Najeriya, Kuma Ayau Tsofaffin Shugabannin Naje...
15/01/2026

TARIHI: A Ranar 15 ga Janairu 1966, Aka Gudanar Da Jùyin Mulki Na Farko A Najeriya, Kuma Ayau Tsofaffin Shugabannin Najeriya Sir Abubakar Tafawa Ɓalewa, Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto Suke Cika Shekaru 60 Da Rasuwa.

Allah ya jikansu ya gafarta musu Amin.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Newsday Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Newsday Hausa:

Share