15/01/2026
Minista Ya Yi Alhinin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Yakubu Mohammed
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya miƙa saƙon ta’aziyyar sa ga al’umma da gwamnatin Jihar Kogi bisa rasuwar babban ɗan jarida, ƙwararren ɗan siyasa, kuma ɗaya daga cikin waɗanda s**a kafa mujallar Newswatch, Malam Yakubu Mohammed.
A wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba, Idris ya bayyana rasuwar ɗan jaridar a matsayin babban rashi ga fannin yaɗa labarai na Nijeriya—sana’ar da ya sadaukar wa sama da shekaru hamsin na rayuwar sa.
Ya yaba wa marigayin bisa jajircewar sa wajen tabbatar da gaskiya a aikin jarida, bincike mai zurfi, da kuma ƙarfin halin gaya wa hukuma gaskiya, ko da a lokutan mulkin soja.
Ya ce: “Marigayi Yakubu Mohammed ya kasance babban jigo a fannin aikin jarida, inda ya share fagen sabon salon aiki tare da kafa harsashin bincike mai zurfi a Nijeriya, wanda ya zama ƙashin bayan sa ido kan ayyukan gwamnati da shugabanci a tsarin dimokuraɗiyyar mu.”
Ya ƙara da cewa, “Tare da abokan aikin sa da s**a kafa Newswatch, gurbin da s**a bari da kuma nasarorin da s**a cimma na ci gaba da zama abin koyi ga matasan ’yan jarida, ba kawai wajen riƙe alƙalami ba, har ma da yin amfani da shi wajen kawo sauye-sauye a zamantakewa da siyasar al’umma.”
Haka kuma, Ministan ya bayyana Yakubu Mohammed a matsayin mai kishin ƙasa na gaske wanda ya yi imani da Nijeriya, jarumi wanda ya nuna juriya a lokacin fargaba, kuma mai kawo sauyi wanda ya yi amfani da basirar sa wajen ciyar da jama’a gaba, musamman a lokacin da yake matsayin Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU).
Idris ya yi addu’ar Allah ya jiƙan marigayin, sannan ya yi kira ga iyalai da dukkan waɗanda rashin ya shafa da su yi alfahari da kuma samun natsuwa daga kyawawan ayyukan da ya bari, waɗanda aka tattara a cikin littafin tarihin rayuwar sa mai suna “Beyond Expectations,” wanda aka ƙaddamar a watan Nuwamba 2025.
Shi dai Yakubu Mohammed ya rasu ne yana da shekaru 75, kuma ya rasu ƙasa da wata biyu bayan rasuwar ɗaya daga cikin waɗanda s**a assasa Newswatch, wato Mista Dan Agbese, a ranar 17 ga Nuwamba, 2025.