Newsday Hausa

Newsday Hausa Domin samun ingantattun labarai ilmantarwa hadi da nishaɗantarwa ku cigaba da bibiyar Jaridar Newsday Hausa.
(2)

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN: Wani Yaro Ya Ràśu A Wajen Jana'izar Sheik Dahiru BauchiRahotanni daga babban filin ...
29/11/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN: Wani Yaro Ya Ràśu A Wajen Jana'izar Sheik Dahiru Bauchi

Rahotanni daga babban filin Idi na Kofar Wambai dake cikin garin Bauchi, sun tabbatar da cewa wani yaro da ba a tantance asalinsa ba ya rasu yayin gudanar da sallar jana’izar fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi, a yau.

Lamarin ya tayar da hankalin jama’a, kasancewar babu wanda ya san daga inda yaron ya fito, ko kuma tare da wane yake kafin faruwar rasuwar. Hakan ya sa ake kira ga jama’a da su taimaka wajen yada wannan bayani domin a gano danginsa ko wanda ya san shi.

Rahoto ya nuna cewa an kai gawar yaron Asibitin Bakaro bayan Fada a cikin garin Bauchi. Ana sa ran cewa da zarar an samu danginsa, za su zo su karɓe shi.

Sai dai, idan babu wanda ya bayyana a lokaci kusa, hukumomi za su mika gawar zuwa dakin ajiye gawa na Asibitin Koyarwa na Sir Abubakar Tafawa Balewa (ATBU Teaching Hospital) domin ci gaba da adana ta bisa ƙa’ida.

Allah Ya jikansa, Ya kuma bai wa iyalansa hakurin jure wannan rashi idan aka same su.

Daga Eagle Radio

28/11/2025

🧏‍♂️

KAI TSAYE: Daga Wajen Jana'izar Marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi.
28/11/2025

KAI TSAYE: Daga Wajen Jana'izar Marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Yadda Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Jihar Bauchi Don Halartar Jana'izar Sheikh Ɗahiru Bauchi
28/11/2025

Yadda Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Jihar Bauchi Don Halartar Jana'izar Sheikh Ɗahiru Bauchi

Gwamnan Jihar Neja, Muhammad Umar Bago, Ya Isa Jihar Bauchi Domin Halartar Jana'izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
28/11/2025

Gwamnan Jihar Neja, Muhammad Umar Bago, Ya Isa Jihar Bauchi Domin Halartar Jana'izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf Ya Isa Jihar Bauchi Domin Halartar Jana'izar Marigayi Sheikh Dahiru U...
28/11/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf Ya Isa Jihar Bauchi Domin Halartar Jana'izar Marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

DA ƊUMI-ƊUMI: Sheikh Sharif Ibrahim Saleh, Wanda Zai Jagoranci Sallar Jana'izar Sheikh Dahiru Bauchi Ya Sauka A Filin Ji...
28/11/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Sheikh Sharif Ibrahim Saleh, Wanda Zai Jagoranci Sallar Jana'izar Sheikh Dahiru Bauchi Ya Sauka A Filin Jirgin Saman Bauchi.

DA ƊUMI-ƊUMI: Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar Ya Sauka Jihar Bauchi Domin Halartar Jana'izar Sheikh Dahir...
28/11/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar Ya Sauka Jihar Bauchi Domin Halartar Jana'izar Sheikh Dahiru Bauchi

28/11/2025

Sallallahu Alaihi Wasallam ❤️

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Jihar Bauchi ta ayyana gobe Jumu’a a matsayin ranar hutu domin girmama marigayi Sheikh Dahiru Us...
27/11/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Jihar Bauchi ta ayyana gobe Jumu’a a matsayin ranar hutu domin girmama marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi, tare da nuna alhini kan rasuwarsa.

Tinubu Yana Gina Ginshiƙin Mai Ƙarfi Na Makomar Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ...
27/11/2025

Tinubu Yana Gina Ginshiƙin Mai Ƙarfi Na Makomar Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu sun fara samar da ribar dimokiraɗiyya ga ‘yan ƙasa.

Ya faɗi haka ne a safiyar yau yayin tattaunawa da ƙungiyoyin goyon bayan jam’iyya mai mulki, wato APC, a ofishin sa da ke Radio House, Abuja.

Idris ya ce: “Mun cika da dama daga cikin alƙawurran kamfen ɗin mu. An kammala batun lamunin ɗalibai, mun kuma kawo ƙarshen almundahanar tallafin man fetur.

"Jihohin mu suna karɓar ƙarin kuɗi, ‘yancin ƙananan hukumomi ya zama na dindindin, kuma kowane yanki yanzu yana da hukumar cigaban sa.

"Tattalin arziƙin mu ya murmure, ajiyar kuɗin waje na ƙaruwa, hauhawar farashi tana raguwa.

"Mun fara manyan ayyukan raya ƙasa a dukkan sassa na tattalin arziki a shiyyoyin ƙasa guda shida.”

Kan batun sababbin umurnin Shugaba Tinubu game da tsaron ƙasa, Ministan ya jaddada cewa Shugaban Ƙasa ya amince da ɗaukar ƙarin jami’ai a sojoji da ‘yan sanda tare da tallafa wa sababbin rundunonin tsaro da gwamnatocin jihohi s**a kafa, yana mai cewa wannan mataki zai zama babban sauyi a yaƙin da Nijeriya ke yi da rashin tsaro.

Ya ce: “Muna fuskantar gaggawar buƙatar kawar da ta’addanci da ‘yan bindiga, mu dawo da zaman lafiya, mu kuma ba ƙasar nan zaman lafiya ga kowa da kowa, ba tare da la’akari da ƙabila ko harshe ko addinin sa ba, kamar yadda kundin tsarin mulkin mu ya tanada.”

Ministan ya sake tabbatar da ƙudirin Gwamnatin Tarayya na yin duk mai yiwuwa don tabbatar da tsaron ƙasar nan.

A ɓangaren ƙarfafa matasa, Idris ya tabbatar da cewa Tinubu zai ci gaba da kare muradun matasa, ya ƙara da cewa a wannan gwamnati, matasa da ba a taɓa yi ba sun samu muƙamai na jagorantar ma’aikatu da hukumomi.

Idris ya shawarci ƙungiyoyin da su ci gaba da shiga cikin yaɗa shirye-shiryen gwamnati da faɗaɗa haskaka nasarorin ta da tasirin ta.

Ya jaddada cewa wajibi ne a tsaya tsayin daka cikin haɗin kai, tare da bin muradun asali da s**a kafa s**a APC kuma s**a ɗore.

Shugabannin tawagar, Misis Adenike Abubakar da Dakta Abiola Moshood, a madadin ƙungiyoyin, sun sha alwashin ci gaba da bayar da goyon baya ga Ajandar Sabuwar Fata ta Shugaba Tinubu.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Newsday Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Newsday Hausa:

Share