Newsday Hausa

Newsday Hausa Domin samun ingantattun labarai ilmantarwa hadi da nishaɗantarwa ku cigaba da bibiyar Jaridar Newsday Hausa.
(2)

09/10/2025

🧏‍♂️

09/10/2025

Yadda Super Uban Lissafi Yazo Gidansu Yake Nunawa Mahaifinshi Sabuwar Motar Da Ya Samu Kyauta Wajen Hon Dutsimari Kebbi

Shugaba Tinubu Ya Yafewa Mamman Vatsa, Herbert Macaulay Da Wasu Mutane 174Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi amfani da iko...
09/10/2025

Shugaba Tinubu Ya Yafewa Mamman Vatsa, Herbert Macaulay Da Wasu Mutane 174

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi amfani da ikon sa na gafarar shugaban ƙasa wajen yafe wa fitattun mutane da dama ciki har da Herbert Macaulay da Manjo Janar Mamman Jiya Vatsa wanda aka kashe a 1986 bisa tuhumar yunkurin juyin mulki.

Mamman Vatsa, wanda kuma shahararren mawaƙin Zube ne, ya samu wannan gafara ne bayan amincewar Majalisar Ƙasa da ta zauna a Abuja a ranar Alhamis.

Haka kuma, shugaban ƙasa ya yafe wa Herbert Macaulay, ɗaya daga cikin jagororin neman ’yancin Najeriya da ya kafa jam’iyyar NCNC tare da Dr. Nnamdi Azikiwe. Duk da Macaulay ya rasu tun 1946, har yanzu yana ɗauke da tabon kasancewa ɗan gidan yari daga hukuncin da Turawan mulkin mallaka s**a yanke masa.

Tinubu ya kuma yafe wa wasu tsofaffin masu laifi, ciki har da tsohon ɗan majalisa Farouk Lawan, tare da Mrs Anastasia Daniel Nwaobia, Barrister Hussaini Umar, da Ayinla Saadu Alanamu. An bayyana cewa sun nuna nadama kuma ana son ba su damar sake shiga cikin al’umma.

Sauran da s**a ci gajiyar gafarar sun haɗa da Nweke Francis Chibueze, wanda akai wa daurin rai-da-rai kan laifin hodar iblis, da kuma Dr Nwogu Peters wanda ya shafe shekaru 12 cikin hukuncin shekara 17 kan zamba.

Haka zalika, shugaban ƙasa ya bai wa Ogoni Nine cikakkiyar gafara, waɗanda s**a haɗa da Ken Saro-Wiwa, Saturday Dobee, Nordu Eawo, Daniel Gbooko, Paul Levera, Felix Nuate, Baribor Bera, Barinem Kiobel da John Kpuine.
Ya kuma ba da lambar girmamawa ta ƙasa ga Ogoni Four, Chief Albert Badey, Chief Edward Kobani, Chief Samuel Orage da Theophilus Orage.

An bai wa fursunoni 82 cikakkiyar gafara, an rage wa 65 hukunci, sannan an sauya wa 7 girman hukuncin daga hukuncin kisa zuwa daurin rai-da-rai.

Shugaban ya yi wannan ne bisa shawarwarin Kwamitin Taimaka wa Shugaban Ƙasa kan Gafara (PACPM) wanda Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), ke jagoranta. Kwamitin ya kunshi mambobi 12 ciki har da wakilan hukumar ’yan sanda, hukumar gyaran hali, hukumar kare haƙƙin bil’adama, majalisar koli ta musulunci da kuma majalisar kiristoci ta Najeriya.

Rahoton kwamitin ya nuna cewa daga cikin 294 da aka tantance, mutum 175 aka amince su ci gajiyar wannan shirin bisa ƙa’idoji kamar tsufa, rashin lafiya, ƙarancin shekaru, da kyakkyawan halayya a gidan gyaran hali.

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI TAJI'UN: Babban Malamin Musuĺunci A Jihar Kano, Sheik Kabiru Na Madabo Ya RasuAllah Ya gafar...
09/10/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI TAJI'UN: Babban Malamin Musuĺunci A Jihar Kano, Sheik Kabiru Na Madabo Ya Rasu

Allah Ya gafarta masa.

A cewar malamin, soyayyar Annabi a wajen ’yan darika ta zarce magana kawai, domin suna bin koyarwarsa cikin tawali’u, su...
09/10/2025

A cewar malamin, soyayyar Annabi a wajen ’yan darika ta zarce magana kawai, domin suna bin koyarwarsa cikin tawali’u, suna yawaita salati da yin koyi da halayensa a kowace rana.

Sheikh Nuru ya ƙara da cewa wannan soyayya ce da ke haifar da nutsuwa da tausayi a zukatan mabiya, tare da karfafa haɗin kai a tsakanin al’umma.

09/10/2025

Amin Amin Yaa Hayyu Yaa Qayyum

09/10/2025

😁😁

09/10/2025

Jaruma Firdausi Yahaya

YANZU-YANZU: Shugaba Tinubu Na Jagorantar Taron Majalisar ‘Yan Sanda Ta Ƙasa A AbujaShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na j...
09/10/2025

YANZU-YANZU: Shugaba Tinubu Na Jagorantar Taron Majalisar ‘Yan Sanda Ta Ƙasa A Abuja

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na jagorantar zaman Majalisar ‘Yan Sanda ta Ƙasa a zauren majalisar da ke fadar shugaban ƙasa, Abuja. Zaman ya fara ne da ƙarfe 2:39 na rana a yau Alhamis, jim kaɗan bayan Shugaban Ƙasa ya kammala taron Majalisar Ƙoli ta Ƙasa inda ya gabatar da sunan wanda zai aka zaba a matsayin sabon shugaban INEC.

Taron ya zo ne makonni biyar bayan da Shugaban Ƙasa ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya tana nazarin batun kafa rundunar ‘yan sanda na jihohi, tare da ƙarfafa sabbin jami’an tsaron daji (forest guards) da aka tura cikin dazuzzuka domin yaki da matsalar tsaro. A ranar 2 ga Satumba, 2025, yayin da ya karɓi tawagar jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dikko Radda, Shugaba Tinubu ya ce: “Ina duba dukkan fannoni na tsaro; dole ne in samar da rundunar ‘yan sanda ta jihohi.”

A yayin zaman na yau, mahalarta sun yi addu’a domin tunawa da tsohon Sufeton ‘Yan Sanda na Ƙasa, Solomon Arase, wanda ya rasu a ranar 31 ga Agusta, 2025. Majalisar ta yi nazari kan kalubalen tsaro na yanzu, cigaban da aka samu a gyaran da akai a hukumar ‘yan sanda, da kuma harkokin jin daɗi da albarkatun jami’ai a fadin ƙasar. Haka kuma, ana sa ran za a tattauna batutuwa da s**a shafi shugabanci da tsarin aiki tsakanin jihohi.

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, Sakataren Gwamnatin Ƙasa George Akume, Mai ba da shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu, da Ministan Harkokin ‘Yan Sanda Ibrahim Gaidam na cikin mahalarta zaman, tare da dukkan gwamnonin jihohi da wakilan su. Majalisar ‘Yan Sanda, wacce kundin tsarin mulki ya kafa ƙarƙashin sashe na 153, tana ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa, kuma tana ba da shawara kan tsari, gudanarwa da kula da rundunar ‘yan sanda, har ma da batun nada ko cire Sufeton ‘Yan Sanda na Ƙasa.

Majalisar Ƙoli ta Ƙasa ta amince da nadin Farfesa Joash Ojo Amupitan (SAN) daga jihar Kogi, dake yankin Arewacin Tsakiya...
09/10/2025

Majalisar Ƙoli ta Ƙasa ta amince da nadin Farfesa Joash Ojo Amupitan (SAN) daga jihar Kogi, dake yankin Arewacin Tsakiya, a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne ya gabatar da sunansa domin maye gurbin Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya kammala wa’adinsa a watan Oktoba 2025 bayan shafe shekaru goma yana jagorantar hukumar.

Shugaba Tinubu ya bayyana Farfesa Amupitan a matsayin ɗan jihar Kogi na farko da aka gabatar don wannan muhimmin mukami, tare da jaddada cewa shi mutum ne da aka sani da gaskiya, riƙon amana, da rashin tsangwama irin ta siyasa.

Mambobin majalisar sun amince da wannan nadin ba tare da wani sabani ba, inda Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya bayyana sabon shugaban a matsayin mutum mai nagarta da amincewar jama’a.

Bayan wannan mataki, za a tura sunansa gaban Majalisar Dattawa domin tantancewa da amincewa, kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Newsday Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Newsday Hausa:

Share