AREWA MEDIA CREW

AREWA MEDIA CREW Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AREWA MEDIA CREW, Media/News Company, Abuja Street, Abuja.

Tsaron Nijeriya; Shugaban kasa Tinubu ya gana da manyan hafsoshin tsaron Nijeriya, gami da babban Sufeton yan sandan Nij...
18/03/2025

Tsaron Nijeriya; Shugaban kasa Tinubu ya gana da manyan hafsoshin tsaron Nijeriya, gami da babban Sufeton yan sandan Nijeriya, a Fadar shugaban kasa dake A*o Villa

Mi za ku so ji wannan zaman ya zartar da zai faranta ran yan Nijeriya game da halin tsaron da ake ciki?

DA DUMI DUMINSA: Tonon Asiri Shugaban Majalisar Dattawa Akpabio yaso yayi Lalata dani Naƙi Amince Masa Shiyasa yake gall...
28/02/2025

DA DUMI DUMINSA: Tonon Asiri Shugaban Majalisar Dattawa Akpabio yaso yayi Lalata dani Naƙi Amince Masa Shiyasa yake gallaza Mun, Matsalata a Majalisar Dattawa ta fara ne lokacin da na ki yarda da tayin lalata na Akpabio, in ji Natasha Akpoti, inji yar majalisa Natasha.

Natasha Akpoti-Uduaghan, Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya, ta yi zargin cewa matsalarta a Majalisar Dattawa ta fara ne bayan ta ki yarda da tayin lalata daga Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.

Akpoti-Uduaghan ta yi wannan zargin ne yayin wata hira da Arise TV a ranar Juma'a.

"Matsalata k**ar ta ɗaliba ce da ake hukunta ta saboda ta ki yarda ta kwanta da malamin ta," in ji ta.

Wannan batu ya jawo cece-kuce, inda ƙungiyar kare haƙƙin mata ta Voices for Inclusion and Equity for Women (VIEW) ta yi Allah wadai da yadda Akpabio ya yi wa Akpoti-Uduaghan. A wata sanarwa da s**a fitar, ƙungiyar ta bayyana wannan lamari a matsayin wani ɓangare na tsangwama ga mata a siyasar Najeriya da ya zama dole a bincika kuma a kalubalanta.

A gefe guda, wasu shugabannin yankin Kudu maso Kudu sun musanta rahotannin da ke cewa akwai rashin jituwa tsakanin Akpabio da Akpoti-Uduaghan, suna mai cewa dangantakar su tana nan lafiya lau. Sun bayyana zargin cin zarafi da wariya a matsayin "mugunta kuma rashin kirki."

Har zuwa yanzu, babu wata sanarwa daga ofishin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan waɗannan zarge-zargen.

GWAMNA KANO ABBA KABIR YUSUF YA  NADA UMAR FAROUK IBRAHIM A MATSAYIN SABON SAKATAREN GWAMNATIN JIHAR (SSG)Gwamnan Jihar ...
09/02/2025

GWAMNA KANO ABBA KABIR YUSUF YA NADA UMAR FAROUK IBRAHIM A MATSAYIN SABON SAKATAREN GWAMNATIN JIHAR (SSG)

Gwamnan Jihar Kano, Malam Abba Kabir Yusuf, ya amince da nadin Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Jiha (SSG), bisa la’akari da kwarewarsa da gogewarsa a fannoni daban-daban na shugabanci da harkokin mulki.

Sanarwar nadin ta fito ne daga bakin mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, a yau Asabar, inda ya bayyana cewa sabon SSG zai fara aiki daga Litinin, 10 ga Fabrairu, 2025.

Gwamnatin Kano na da yakinin cewa nadin sabon Sakataren Gwamnatin Jiha zai kara inganta tafiyar da al’amuran gwamnati, tare da tabbatar da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su kawo ci gaba ga al’ummar jihar.

Dikko House to house ta karamar huk**ar jibia taba Dantakar Shugaban karamar huk**ar surajo ado jibia gudummuwar dubu da...
04/02/2025

Dikko House to house ta karamar huk**ar jibia taba Dantakar Shugaban karamar huk**ar surajo ado jibia gudummuwar dubu dari biyar 500,000.

A ranar talata 4 ga watan janware_2025 Shugaban ƙungiyar house to house na k**ar hukumar jibia alhaji rabe ukashatu ya gabatar da gudummuwar sa ga Dantakar Shugaban karamar huk**ar jibia surajo ado domin cigaba da yakin neman zabe,taron wanda ya gudana a babban ofishin ƙungiyar na jaha da ke cikin kalilin rahman pilaza cikin garin katsina.

A lokacin da yake jawabi shugaban ƙungiyar na jibia ya jadda goyon bayan ƙungiyar ga Dantakar na karamar hukumar surajo ado wanda ya ce jibia batayi zabin tumun dare ba domin yasan sirajo ado mutum ne mai Amana mutum ne wanda yasan darajar alkawari dan haka anan sai muce alhamdulillah.

Shima da yake jawabin shugaban ƙungiyar na jaha tukur tingilin wanda shine shugaban water boad na jahar katsina yace jibia sunyi dace da samun Hon surajo ado a matsayin Dantakar shugabancin Karamar Kuma domin zaiyi ma al'ummar sa abinda ma basuyi tunanin samu ba daga gare shi.

A yayin Shima Dantakar yake jawabin godiya ga ƙungiyar da irin wannan taro da ta shirya masa ba abinda zance saide sai godiya ga Allah madaukakin sarki kuma zanyi kokari danganin na sauke nauyin da na dukar maku inshallahu.

Shugaban na jibia Alhaji rabe ukashatu jibia ya bayar da gudanmuwa naira dubu dari biyar (500,000.00) lakadan ga Dantakar karamar huk**ar wanda shima shugaban ƙungiyar na jaha tukur tingilin ya bayar da gudanmuwa naira dubu dari biyu ga Dantakar.

Taron ya samu halartar shugaban ƙungiyar na jaha tukur tingilin da ko'odinetoci na GwaGware Dr Aliyu lawal labor, Alhaji husaini,laminu bature,Danyaba,da sauran wasu daga cikin'yan Jam'iyyar apc na karamar huk**ar jibia.

Labari Cikin Hotuna Gwamna Dikko Umaru Radda na Jihar Katsina a halin yanzu yana jagorantar taron Gwamnonin Arewa maso Y...
03/02/2025

Labari Cikin Hotuna

Gwamna Dikko Umaru Radda na Jihar Katsina a halin yanzu yana jagorantar taron Gwamnonin Arewa maso Yamma a Katsina House, Abuja.

Gwamnonin da ke halartar taron sun hada da Uba Sani na Jihar Kaduna, Dauda Lawal na Jihar Zamfara, Ahmed Aliyu na Jihar Sakkwato da kuma Umar Namadi na Jihar Jigawa.

Mataimakiyar Sakatare-Janar ta Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed, da kuma Mohammed Malik Fall, Babban Jami’in Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, da kuma Maryam Uwais, mai ba Majalisar Dinkin Duniya shawara kan harkokin Arewa maso Yamma, suma suna cikin taron.

Cikakken bayani nan gaba kadan......

Masu rajin haɗa maja don kada APC na yin hakan ne don ba su samu muƙami ba - Masari Aminu Masari, tsohon gwamnan jihar K...
03/02/2025

Masu rajin haɗa maja don kada APC na yin hakan ne don ba su samu muƙami ba - Masari

Aminu Masari, tsohon gwamnan jihar Katsina, ya ce babu wata madafa a Nijeriya sama da jam’iyyar APC.

Masari ya yi wannan jawabi ne a jiya Lahadi a garin Kafur, karamar hukumar Kafur ta Katsina, yayin kaddamar da yakin neman zaben ƙananan hukumomi da aka shirya gudanarwa a ranar 15 ga watan Fabrairu.

Tsohon gwamnan ya yi watsi da labarin ‘yan siyasa masu shirin kafa jam'iyyar maja domin kawar da jam’iyyar APC mai mulki, yana mai bayyana hakan a matsayin gungun wasu fusatattu da su ka rasa muƙamai a cikin jam’iyyar.

“Labarin da ake yadawa a kafafen sada zumunta na zamani cewa wasu ‘yan siyasa na nan na hada kai don kafa maja ba komai ba ne illa taron wasu fusatattu da su ka rasa muƙamai a jam’iyyar APC,” in ji Masari.

"Yunkurin nasu na kulla kawance ba zai kawar da hankalin APC daga tunani aiwatar da ayyukan ci gaba da za su rage radadin talaka ba,".

Masari ya ce a matsayinsa na wanda da shi aka kafa jam’iyyar APC, zai ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da manufofin jam’iyyar.

Majalisar Wakilan Najeriya ta buƙaci NLC ta hakura da yajin aiki da ta shirya shiga kan ƙarin kuɗin kiran Waya da na Dat...
02/02/2025

Majalisar Wakilan Najeriya ta buƙaci NLC ta hakura da yajin aiki da ta shirya shiga kan ƙarin kuɗin kiran Waya da na Data.

Me za ku ce?

Gwamna Raɗɗa Ya Nemi Rage Kuɗin Aikin Hajjin Shekarar 2025, Inda Yace Zai JagoranciGwamnonin Arewa Maso Yamma Zuwa Wajen...
02/02/2025

Gwamna Raɗɗa Ya Nemi Rage Kuɗin Aikin Hajjin Shekarar 2025, Inda Yace Zai Jagoranci
Gwamnonin Arewa Maso Yamma Zuwa Wajen Shugaban Ƙasa Domin Duba Matsalar

A ranar Asabar 1 ga watan Fabrairun 2025, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya nemi a ƙara walwala da jin daɗin alhazai tare da neman ƙara gyara aikin haɗi da neman rage kuɗin zuwa aikin a lokacin da ya karɓi baƙuncin shugaban hukumar kula da aikin Hajji na ƙasa Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan a gidan gwamnatin jihar Katsina da ke birnin tarayya Abuja.

Gwamnan yayi bayani game da yadda aka gabatar da aikin Hajjin shekarar 2024 na jihar Katsina, inda ya bayyana wasu matsaloli da aka fuskanta musamman tsadar kuɗin zuwa aikin wanda yasa masu niyya da dama s**a gaza biyan kuɗin amma duk da haka an samu ma'aikatan aikin Hajji sama da mutum 2,700 daga jihar Katsina.

Gwamnan ya kuma ce mi zai hana a rage yawan daɗewar mahajjatan daga kwanaki sama da 40 da ake domin rage yawan kuɗin sai a mayar da shi mako Uku ko huɗu tun da naga masu zuwa ta hanyar kamfanoni masu zaman kansu da aka fi sani da jirgin yawo suna gabatar da aikin su cikin kwanaki biyar ko bakwai.

A lokacin da yake magana game da ma'aikatan lafiya masu kula da mahajjatan, gwamnan ya ce gwamnatin shi sai da ta samar da ƙarin kayan kiwon lafiya, sabo da haka akwai buƙatar a ƙara haɓɓaka ɓangaren domin kare afkuwar yawaitar ciwuka.

Ya ƙara da cewa gwamnatin shi kuma ta tallafa ma mahajjatan da kuɗi domin rage masu wahala wanda s**a haɗa da Naira miliyan 500, kuɗin hadayar ma'aikatan jihar Katsina gaba ɗaya, sai kuma ƙara alawus ɗin da gwamnatin ke badawa daga dalar Amurika 400 zuwa 4,500.

Ya kuma ce ya k**a ta gwamnati ta kawo ƙarshen zambar da ake yi wa mutanen karkara a lokacin biyan kuɗin aikin Hajjin, sannan kuma gwamnati ta rage yawan kuɗin zuwa aikin Hajjin, kuma zan nemi sauran gwamnonin arewa maso yamma domin mu kaima shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu wannan shawara.

Gwamnan ya cigaba da cewa shigo da malamai masana ilimin aikin Hajjin tare da jami'an sadarwa domin taimaka ma mahajjatan wajen samun sauƙin gudanar da ingantaccen aiki.

Tun da fari shugaban hukumar alhazan Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya bayyana yunƙurin hukumar na rage kuɗin aikin Hajjin na shekarar 2025, mun tattauna da hukumomin ƙasar Saudiyya domin samo hanyoyin da za su rage yawan kuɗin aikin da ake biya yanzu haka ma mun saka sama da Naira Biliyan 50 domin fara shirye-shiryen aikin.

Ya cigaba da cewa matsalolin da hukumar ke fuskanta akwai kaso biyu da babban bankin Najeriya ke fitarwa a duk kuɗin da aka biya, kuma shekarar da ta gabata gwamnati ta biya tallafin aikin Hajjin na Naira Biliyan 90 kuma an cire sama da Biliyan 1.7 a matsayin kuɗin k**ashon fitar da su, hakan ne yasa a wannan shekarar muke tsammanin kuɗin ajiyar aikin hajjin zai iya kaiwa kusan Biliyan 500, wanda za'a cire sama da Biliyan 20 a matsayin k**ashon.

Ya ƙara da cewa kuɗin jirgi kuma sun kai kimanin kaso 65% na kuɗin, wanda kuma yanzu haka mun yi nisa a cikin maganar yanda za'ayi a rage su, sai kuma ya yaba ma ƙoƙarin gwamnan akan gudummuwar da ya bada a lokacin aikin Hajjin da ya gabata.

Shima Kwamishinan hukumar mai kula da aikin Hajjin da kuma bada lasisi Prince Anofi Elegushi, ya bayyana irin yadda hukumar ke ta ƙoƙarin inganta aikin na shekarar 2025, ya bayyana akwai yiwuwar kuɗin su ragu duk da cewa matsalar rage kuɗin amfi samun ta daga nan cikin gida.

Kwamishinan ya cigaba da cewa munyi ƙoƙari domin tantance kamfanonin jiragen da za su yi mana jigilar mahajjatan 2025, mun tantance kamfanonin 11 amma kamfani huɗu ne s**a cika ƙa'idojin da ya sa s**a tsallake, kamfanonin su ne Flynas, MaxAir, Air Peace, da OMSA.

Maganar matsaltsalun biyan kuɗi kuma kwamishinan yace yana ganin k**ata ya yi gwamnatocin jihohi su riƙa shigewa gaba wajen cika ma mahajjata kuɗin da s**a fara zubawa domin kauce ma matsalar kasa cika kuɗin a cikin lokacin da aka tanadar, daga baya sai mahajjatan su riƙa biyan gwamnatin jihohin.

Daga ƙarshe kuma ya ce ya k**ata a riƙa wayar da kan mahajjata akan illar saka kai cikin wata hidima mai alaƙa da magani ko miyagun ƙwayoyi, wanda ake yawan samun mahajjatan Najeriya da irin waɗan nan laifuka a ƙasar Saudiyya.

Gwamnatin Jihar Kano ta ware Naira biliyan 2.5 domin gudanar da auren zawarawa daga kananan hukumomi 44 na jihar a sheka...
31/01/2025

Gwamnatin Jihar Kano ta ware Naira biliyan 2.5 domin gudanar da auren zawarawa daga kananan hukumomi 44 na jihar a shekarar 2025.

Kwamishinan Tsare-tsare da Kasafin Kudi na Jihar, Musa Shanono, ya bayyana hakan yayin da yake yi wa ‘yan jarida bayani kan yadda kasafin kudin shekarar 2025 da Majalisar Dokokin Jihar ta amince da shi ya kasu.

Ya kara da cewa daga cikin adadin kudin, an ware Naira biliyan 1 don shirin ciyar da al'umma a watan Ramadan.

Ya kuma ce Naira miliyan 955 an ware ta ne don gudanar da binciken kididdigar ma’aikata, binciken halin da gidaje ke ciki da kuma yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Bugu da kari, ya bayyana cewa an ware Naira miliyan 267.6 don samar da kayayyakin more rayuwa da kuma tallafa wa shirye-shiryen Da’awah na addinin Musulunci.

Gwamnatin Jihar Katsina ta kashe kuɗaɗe ma su yawa a fannin ilimi, inda ta kashe sama da N120 biliyan a cikin ayyukan il...
31/01/2025

Gwamnatin Jihar Katsina ta kashe kuɗaɗe ma su yawa a fannin ilimi, inda ta kashe sama da N120 biliyan a cikin ayyukan ilimi da gina kayayyakin more rayuwa.

A wani taron da Mataimakin Gwamna Malam Faruk Lawal Jobe ya gudanar, an bayyana gudummawar da gwamnati ta bayar a fannin ilimi tun lokacin da ta hau mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023.

A matakin ilimin firamare, Hukumar Ilimin Firamare ta Jihar (SUBEB) ta gina ayyuka da darajar N9.1 biliyan, ciki har da gina dakunan aji 160, rijiyoyin ruwa 81, da bayan gida 46. An kuma gyara dakunan aji 258, kuma an samar da kayan aikin malamai 612 da kujeru 14,602 ga ɗalibai. An kuma samar da littattafai, kayan koyarwa, kwamfutoci, da motoci don sa ido kan ayyukan ilimi.

A matakin sakandare, gwamnati ta kashe kusan N6.8 biliyan don gina da gyara wasu makarantu, samar da kayan kimiyya da fasaha, littattafai, da kayan koyarwa. An kuma gina makarantu na musamman guda uku a Radda, Dumurkul, da Jikamshi, tare da gyaran makarantun sakandare a Funtua, Ingawa, Zango, da Kabomo.

A cikin aikin AGILE, an gina makarantu 75 na sakandare da darajar N13.6 biliyan, tare da gina wasu makarantu 77 da darajar N36.8 biliyan. An kuma gyara makarantu 578 da samar da kayan ilimi na dijital da darajar N6.6 biliyan. Aikin ya kuma hada da ba da tallafin kuɗi ga 'yan mata 104,111 a makarantu 255.

A Jami’ar Umaru Musa Yar’adua, gwamnati ta kashe N314 miliyan don samar da wutar lantarki da hasken rana don tsaro. An kuma biya kudin shiga kwalejoji daban-daban da darajar N135.9 miliyan. Gwamnati ta kuma ba da tallafin karatu da darajar N1.9 biliyan ga ɗalibai 136,175, tare da ba da kyaututtuka ga ɗalibai masu nasara.

Ta hanyar ƙauyen ƙwararrun matasa na Katsina (KYCV), gwamnati ta ba da kayan aiki ga ɗalibai 634 da darajar N248 miliyan, tare da gina wurin gyaran motoci na gwamnati. An kuma inganta wurin gyaran motoci da darajar N31 miliyan.

Gwamnatin Jihar Katsina za tai Hadin Gwiwa da Funtua Inland Dry PortGwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya n...
31/01/2025

Gwamnatin Jihar Katsina za tai Hadin Gwiwa da Funtua Inland Dry Port

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya nemi hadin gwiwa da tashar ruwa ta kan tudu da ke a Funtua Inland Dry Port (FIDP) domin bunkasa harkokin kasuwanci a Katsina. Wannan ci gaban ya biyo bayan karbar kayanta na farko da tashar ta samu a ranar 27 ga watan Janairun 2025. Haɗin gwiwar na da nufin yin amfani da damar tashar don ci gaban tattalin arzikin yankin.

Ana sa ran haɗin gwiwar zai samar da ababen more rayuwa, manufofi, da ƙarfafawa ga ƴan kasuwa da kasuwanci na duniya, tare da yuwuwar samar da wuraren haɗin gwiwar da s**a haɗa da haɗin kai, faɗakarwa, da tallafin kuɗi. Ana sa ran tashar za ta kara yawan GDP na jihar Katsina, da samar da guraben ayyukan yi, da samar da ci gaban tattalin arziki mai dorewa a shiyyar Arewa maso Yamma, wanda zai sanya Katsina a matsayin babbar cibiyar kasuwanci a yankin.

An gudanar da bikin bude taron kasashen musulmai kan yaki da ta’addanci a birnin Niamey, na Nijar, a ranar Alhamis. Taro...
31/01/2025

An gudanar da bikin bude taron kasashen musulmai kan yaki da ta’addanci a birnin Niamey, na Nijar, a ranar Alhamis.

Taron ya hada shugabanni, kwararru kan tsaro, da masu tsara manufofi daga kasashe daban-daban na Musulmai domin tattauna dabarun yaki da ta’addanci da kuma inganta zaman lafiya a yankin.

Maharta taron sun jaddada bukatar karfafa hadin gwiwa kan bayanan sirri, hadin kan tattalin arziki, da diflomasiyya don magance tushen matsalar tsattsauran ra’ayi.

Haka kuma, an yi nuni da rawar da ilimi da ci gaban al’umma ke takawa wajen hana yaduwar gurɓataccen tunani mai tsanani.

Maharta taron sun kuduri aniyar hadin kai don samar da zaman lafiya mai dorewa a kasashen musulmai.

Address

Abuja Street
Abuja

Telephone

+2349046946443

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA MEDIA CREW posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share