Jaridar Aku

Jaridar Aku Media/ News Company

YADDA HAIHUWAR JARIRIN WATAN SALLAH ( SHAWWAL ) DA BAYYANARSA A SARARIN SAMANIYA DA IZININ ALLAH, 29/03/2025. FANIS /NS/...
29/03/2025

YADDA HAIHUWAR JARIRIN WATAN SALLAH ( SHAWWAL ) DA BAYYANARSA A SARARIN SAMANIYA DA IZININ ALLAH, 29/03/2025.

FANIS /NS/KD/001/1446 - 2025/00031

KUNGIYAR MALAMAI MASANA ILIMIN TAURARI-NAJERIYA
(FALAKI NETWORK)

Bismillahir-Rahmanirr-Raheem was salatu was-salamu ala Atimmanil-Akmalaniy Sayyidna Muhammadur RasulilLah wa Ahali baitihil Dayyibinal Dahireen : Kamar kullum shi ilimin Falaki ilimine Qa'imi da aka gada tun iyaye da Kakanni amma kullum qara fadada yake musamman yanzu da ake ta samun cigaba duk bayan lokaci , to zamu bi lamarin ganin Jinjiri Watan Sallah bisa lura da yadda Malamnanmu na zaure da ma Turawa suke yin nasu a zamanin ce (Westrrn Astrology) .

Insha Allahu za a haifi jinjirin watan sallah (Shawwal) na shekarar 1446H (wato haduwar wata a tsakiyar rana) a Yau din nan Asabar, 29 ga watan Maris, 2025 dai dai 29 ga Watan Ramadhan 1446 bayan hijrar Shugaba (S.A.W) daga Makkah zuwa Madinah da ƙarfe 11:58 na rana amma bisa daidaitaccen lokaci na duniya (UTC) za'a samu ragin sa'a guda wato (-1 hour) sabanin Agogon GMT da akan qara sa'a daya (+1 hour) Agogon Najeriya , Qasar Kamaru da kuma Chadi .

Kamar yadda taswirar da ke qasa ta nuna, ana iya ganin jinjirin watan Sallah (Shawwal) da ido qarara a yammacin Arewacin (Northwestern) Amurka (Kanada) a daren Asabar (daren shiga Lahadi), sannan ana iya ganin sa da na’urar hangen nesa a mafi yawan yankunan Arewacin da Tsakiyar Amurka.

A yammacin Lahadi (daren shiga Litinin), ana iya ganin jaririn watan da ido qarara cikin sauƙi a mafi yawan sassan duniya irinsu Arctic, Kanada da wasu Qasashenmu na nan Nahiyar Afirka da izinin Allah .


A halin yanzu watan da muke ciki na Ramadhan Ya samu kwanaki 29 da sa'o'i kusan bakwai da haihuwa inda ya qure dukkan wani haske na sa da ya tsururuta daga Rana (Illumination) kuma ba zai qara samun wani ba har zuwa bacewarsa tunda ya kai darajajin qarshe (Last Degrees)har 357° a halin yanzu kenan sai dai mu jira jinjirin Watan da Allah (SWT) zai qara halitta nan da kimanin sa'o'i 4 da daqiqoqi 24 zuwa 25 . A daidai lokacin da Junjirin wata yake lullube bai kai qwarin bude idon da zai iya karbar hasken rana ba ballanta na ya haska kansa idaniya ta iya ganinsa .

Akarshe kamar yadda mai girma sarkin musulmi ya bada na cewa kowa ya duba watan sabon jinjijirin wata ayau 29 ga Ramadan, muna fatan kowa zai himmatu, ga wanda Allah yasa yadace da ganinsa, ya sanar zuwaga hanyoyin da aka samar domin tabbatarwa.

Sanya Hannu :
Muhammad Misbahu
Hamza Ahmad (Falaki);

Amadadin :
Shugaban Kwamitin Bincike na Kasa.

Allah yasa mudace.
Allah ya amsa Ibadun mu. Amin
[email protected]

Tunanin Duniya ne ya Cika Zuciyoyin Maluman Dake Ganin Taron Qur'an Festival Amatsayin Taron Wasa da Al'qur'ani, Kamar Y...
22/01/2025

Tunanin Duniya ne ya Cika Zuciyoyin Maluman Dake Ganin Taron Qur'an Festival Amatsayin Taron Wasa da Al'qur'ani, Kamar Yadda Shine Ake Zaton Ya Cika na Masu Shiryawa____Inji Sheikh Assufiyyu

Shugaban kungiyar Malamai Masana Ilimin Falaki na Kasa, Falaki Network, Sheikh Imam Habibi Abdallah Assufiyyu yace " Tunanin Duniya ne ya cika zuciyoyin Malumar dake ganin taron Qur'an Festival amatsayin taron wasa da Al'qur'ani, kamar yadda ake zaton shine ya cika na masu shiryawa.

Amatsayin mu na musulmai wadanda basu da wani babban littafi da yafi Al'qur'ani, kamata yayi ace duk wata magana akansa shi Qur'anin ya zama abun dumama zuciya da jindadi, farin ciki, tareda kyautata zato akai koda kuwa awajen wadanda s**a shirya hakan yanada wata manufa ta daban.

Su kuma maluman dake ganin cewa baza'ayi wannan taron Qur'an Festival din ba, don suna ganin wani shiri ne na yaudara da yan siyasa s**a shirya da kuma wasu maluma don amfanuwa da abun duniya, yakamata mugane cewa irin wannan halin na kalubalen tar dukkan alamari da yazo mana musamman ta fuskan addini don tunanin za'a yaudare mu bazai taba kawo mana cigaba da gyara atsarin shugabanci ko halin shugabanni ba akasar nan, wannan sai dai addua da kuma gyaran halin mu.

Amma idan muka zama bamu da wayau sai na Allah, bamu da dabara sai na Allah, to duk wanda yace da addini zai yaudare mu karshensa baza tayi kyau ba, domin fadar zata koma bana namu bane, Allah ne dakansa zaiyi yaqi da abun. In kana kokonto kajaraba kagani !

Saboda haka idan ana maganar Allah da Annabi da Al'qur'ani to bamu ganin komai kuma ba mujin komai sai shi Allann, Annabin da Al'qur'anin, musamman dama duk wanda yasan sufaye da kalar wannan dabi'ar akasan su, saidai kuma yan zamani masu addini tare da rawar kai.

A tawa fahimtar gwanda wasu ginshikai na addinin mu su zama mana rauni wajen jarabtuwa da mummunar dabi'ar yaudarar al'umma da yan siyasa sukeyi abisa, wani karamin abun duniya da zai iya zama abun kunya agaremu a idon bayin Allah dashi kansa Allah madaukakin sarki.

Akarshe ina kira da cewa maluma da suke tada jiniyar wuya akan wannan alamari, idan bazasu je ba, to su bar masu zuwa suje, su kuma masu shiryawa su gane koda al'ummar musulmi sun halarta wannan taro, to bawai dubarar su bane da wayansu yasanya akaje, a'a Allah da Annabi da Al'qur'ani aka hango s**a sanya kuma akaje, ba wani abu daban ba. In ma abunda ake zato akansu hakan. Allah yasa mu dace. Amin

Daga Cikin Sunayen da Iyaye Ke Sanyawa Jarirai idan an haifesu, Suna Sanya Ma Yaran Dabi'ar Mai Wuyar Sha'ani ___Kungiya...
11/01/2025

Daga Cikin Sunayen da Iyaye Ke Sanyawa Jarirai idan an haifesu, Suna Sanya Ma Yaran Dabi'ar Mai Wuyar Sha'ani ___Kungiyar Malaman Falaki na Najeriya

Anyi Kira ga al'umma da su daina sanyawa jararai kowanne kalar suna ayayin da aka haifesu batare da tantance kalar dabi'ar da yaron zai iya tasowa da ita ba

Kungiyar Malamai Masana Ilimin Falaki na Najeriya wato (Falaki Network) tayi kira ga ma'aurata dasu zama masu "Daukar saiti akan dabi'ar da yaro zai taso da ita daga sanda aka haifeshi zuwa girmansa, alamari ne mai girma acikin ilimin Falaki, wanda kuma yin hakan zai taimaka wajen inganta goben yaro dana iyayen sa, domin babu shakka dabi'ar kowanne dan Adam da Allah ya halitta tana taka muhimman rayuwa wajen samun cigaban sa arayuwa musamman akan irin fata da buri da iyayensa ke rokon Allah akansa.

A Cewar maluman wannan kungiya " Idan mahaifin yaro ya zama yanada dabi'ar wuta, wanda a hukunci na bai daya, yana kasancewa mutum mai dabi'ar gaggawa, saurin yanke shawara, fadar gaskiya, zafin jini wajen kaiwa da komo musamman wajen neman arziki da alamuran yau da gobe, babu shakka yakamata yasamu mafi galibin yaransa su kasance masu dabi'ar dake ta alaka da irin tasa, idan basu kasance masu dabi'ar wuta ba, suna iya kasancewa masu dabi'ar iska.

Idan an lura akwai yaran da suke zuwa da arziki acikin zuriya, wanda tundaga samuwar cikinsu zuwa haifuwar su da raino ana ganin budi da samuwar arziki atare da wannan iyali, mafi galibin irin hakan nafaru ne adalilin dace war dabi'ar mahaifi dana jaririn da za'a haifa ko wanda aka haifa, yana iya kasancewa asamu sani akan faduwar hakan abisa doron hujja ta wannan ilimi kuma ana iya ganin hakan ta akasin hakan, babu shakka Allah madaukakin sarki yana juya yanayi yadda yaso.

kungiyar na malamai Masana alkaluma ta Najeriya taja hankalin al'umma da cewa " akwai sunaye da iyaye ke sanyawa jarirai wacce ke dauke da Dabi'ar dake tsananta sha'awa da son Mata ga jarirai tun suna yara zuwa ga girmansu, wanda idan Allah bai kiyaye ba sai asamu matsala, idan yaro ya girma ga ilimi, kyakkyawar asali amma dabi'ar bin Mata da ayyukan lalaci sun masa yawa.

Ya zama wajibi iyaye su maida hankali wajen tantance sunaye, ma'anarsu da kuma kalar da dabi'ar dake dacewa da ita ayayinda aka narkar da ita da sunan mahaifa, a bisa lissafi na ilimin Falaki.

Domin a dalilin sunan da ake sanyawa jarirai ba bisa ka'idar wannan ilimi ba, yana danya iyaye shan wahala wajen tarbiyantar yaran nasu, kuma hakan yana taimakawa wajen da kushe alamuran cigaban rayuwar su da kaso mai girma acikin dari.

Duniya Zata Fuskanci Sabbin Alamura Tareda Kasancewar Ke Bantattun Abubuwa a Najeriya a Shekarar 2025. Da sunan Allah ma...
05/01/2025

Duniya Zata Fuskanci Sabbin Alamura Tareda Kasancewar Ke Bantattun Abubuwa a Najeriya a Shekarar 2025.

Da sunan Allah mai Rahama mai Jin Kai. Allah yayi dadin tsira ga Shugaba Annabi Muhammad, Sallallahu Alaihi wassalam.

Bayanan Alkaluma na Kungiyar Malamai Masana Ilimin Falaki Na Najeriya ( Falaki Network ) Wanda Tasaba fitarwa Duk Sabuwar Shekarar Miladiyyya da Nabawiyya.

A yayin da Duniya ta shiga sabon fasalin shekarar Miladiyyya ta 2025, sabbin muhimman alamura ne zasu cigaba da wakana kamar yadda Alqalumar binciken Ilimin Falaki (Astronomy) s**a bayyana.

Duniya zata samu bunkasa da cigaba mai girma ta fuskan alamuran kasuwanci tareda yayewar matsalolin tsaro da talauci a Kasashen dake fama da matsin rayuwa, inda kasuwanci ta bangarorin yanar gizo zai cigaba da zama sanadin yayewar talauci ga mutane masu yawa a duniya.

A bangaren harkokin gwamnatin kasa Najeriya, shakakar 2025 zata samarwa gwamnatin kasa da manyan daman maki wajen farfado da tattalin arzikin kasa inda al'umma zasu samu damar kafa sabbin sana'o'i, adaidai lokacin da bincike ke nuni zuwa ga muhimmancin daukar sabbin matakai domin tunkarar matsalar tsaron Kasa ciki da waje.

A bangaren kasashen Africa maso yammaci kuwa musamman kasa Najeriya, zata iya fuskantar karuwar aljannu fiye da kowacce shekara wanda hakan zai iya bude sabbin kofofin ayyukan bokanci dana yan bori. Mun fitar da addu'o'i domin neman kariya za'a gani a karshen rubutun nan.

Lambar sirri ta shekarar 2025, ta alaqantu da abubuwan tarzoma da tada hankula abisa dabi'ar wuta, ana iya fuskantar yawan misanyan miyau kan rashin fahimta atsakanin kasashen duniya da shugabannin yan siyasa tareda kuma yawan, Allah ya kiyaye. Amin

Bincike ya nuna cewa Alqalumar shekarar 2025, basu dace da yanayi da dabi'ar lambar sirri na kasa Najeriya ba, hakan yana sanar da muhimmancin kulawa da harkokin kawance da alamuran cigaba tsakanin Najeriya da sauran kasashen duniya, domin kaucewa fadawa tarkon da zai cutar da kasa da al'ummar cikinta.

Shekarar 2025, na dauke da damina mai albarka cikin yardar Allah, inda ake sanya rai da cewa manoma zasu samu albarkar kayan gona fiye da yadda aka samu a cikin shakakar 2024. Insha Allah

Binciken ya tabbatar da cewa mafi galibin aure da aka daura acikin shekarar 2024 da kuma wasu daga cikin wadanda ake shirin daurawa a farkon shekarar 2025, suna bisa sabani da ka'idoji da kyakkyawan gidajen aure na ilimin Falaki, wanda hakan ke nuni da yiwuwar fuskantar yawan mutuwar aure a cikin sabuwar shekarar 2025, musamman duba da cewa ya hukunci yahadu da dabi'ar dake kan wannan shakarar 2025, Allah ya kiyaye.

Za'a fuskanci faduwar giwaye daga cikin manyan Shugabanni kasashe da s**a hada da gida Najeriya, abisa dalilin ayyukan Maita, Kambun Baka da Tsafi, domin lambar sirri ta duniya zata shiga yanayi a 2025 dake baiwa alamura irin wadannan tasiri wajen gurbata ruhin Bil Adama masu madafun iko.

Za'a yawaita haifuwar jarirai maza da kaso saba'in da biyar acikin dari (75%) a bisa Mata a duniya baki daya acikin wannan shekara ta 2025, koma bayan shekarar data gabata ana kyautata samuwar haifuwar jarirai mata sama da adadin jarirai Maza.

Za'a samu saukin ciwon zazzabin sauro, da kananun cutuka da kaso sittin da biyar ( 65%) acikin dari abisa na shekarar 2024 abisa dalilin dabi'ar lambar sirrin duniya wacce ta alaqantu da ruwa, amma za'a fuskanci yawan zafin jiki atare da halittar dan Adam abisa dalilin dumamar yanayi lokaci zuwa lokaci, musamman a kasashen Niger, Mali, Cameroon da Najeriya, a yankin Africa maso yammaci.

Za'a samu kulluwar alaqoqin soyayya masu tsari ba bisa yaudara ba, wanda hakan zai haifar da yanayi na yawan auratayya atsakanin al'ummar duniya baki daya. Insha Allah

A Najeriya kuwa acikin wannan shakarar ta 2025, dabi'un al'umma zai sauya daga yanayi na fadar karya da yaudara da cin amana zuwa fadar gaskiya da kaso mai girma, inda kai tsaye Alqalumar sun tabbatar da yiwuwar samun tonuwar asirai na mutanen banza da manyan yan fashi da barayi cikin wannan shekarar, da ikon Allah.

Mun gano cewa, ana amfani da ayyukan bokanci da tsafi wajen sauya dabi'un yan Najeriya musamman Shugabanni, daga aikata ayyukan alkhairi zuwa na mugunta, da yiwuwar wannan shakarar za'a samu saukin hakan da kaso 75% acikin dari (100%), insha Allah.

ADDU'O'I
___________

Neman tsari (kariya) : lahaula wala quwwata illa billahil Aliyul azim, sau dari tara (900) kwana tara (9)

Neman Arzki : Astagfrullah, sau dari tara (900), wallahu galibun ala amri, sau tara, lahaula wala quwwata illa billahil Aliyul, sau tara (9), kwana tare (9),

Neman Farin Jini : La'ilaha illallahu Muhammadur rasulullahi sallallahu Alaihi wassalam, sau dari tara (900) ya wadudu, kafa tara, kwana tara 9.

Allah yasa mudace. Amin

Domin neman Karin bayani :
[email protected]
Facebook : Falaki Network of Islamic Scholars
Tick-tock : FALAKI NETWORK

Yin Zaben Shugaban Kasa a Ranar Kun Asabar a Najeriya, Shike Sa Al'umma Basajin Dadin Kowacce Gwamnatin Da Aka Kafa_____...
13/10/2024

Yin Zaben Shugaban Kasa a Ranar Kun Asabar a Najeriya, Shike Sa Al'umma Basajin Dadin Kowacce Gwamnatin Da Aka Kafa_____FANIS

Kungiyar Malamai Masana Ilimin Falaki na Najeriya, FANIS, gudanar da Zaben Shugaban Kasa a Duk Ranar Asabar a Najeriya, Shike Jefa Kasar nan Cikin Yanayi Na Rashin Cigaba kuma ke sanyawa aka kasa samun shugabanci da al'umma zasuji dadinta.

Shugaban kungiyar Imam Sheikh Habib Abdallah Assufiyyu yace, binciken mu ya gano mana cewa ranar Asabar, rana ce da bata dace da yanayi da za'a gudanar da duk wani alamari dake da alaka da shugabanci ba, musamman idan yazama shine mafari alamarin sa, kuma ilimin Falaki ya tabbatar da cewa duk shugabancin da aka ginashi a rana irinta Asabar, zai kasance cike da manyan kalubale da zai hana shugaban kasa gudanar da ayyukan cigaba da raya al'umma kasa baki daya.

Domin babu shakka dayawa daga cikin shugaban nin da s**a gabata wadanda ake ganin gwamnatin su batayiwa al'umma dadi ba, rashin kyawun ranar da aka zabe su amatsayin shugabanni ya bada gudumawa mai girma wajen hanasu samun natsuwa da kyakkyawan tunani na yadda za'a ciyar da kasa gaba ballantana har al'umma suji dadi.

Assufiyyu yakara da cewa, kasa shen duniya da dama wadanda suke amfani da ilimin Falaki, (astronomy), basu kasance suna gudanar da zabukan kasar su ba aranar Asabar, da wannan muke ganin yakamata gwamnati da hukumar zabe na Najeriya suyi duba zuwa ga daidaito akan doran ilimi na gudanar da komai a muhallin sa, yin hakan zai baiwa zababben shugaba tabbatar da kyawawan manufofin da yake da su kafin azabe shi.

Shugaban ya kuma gargadi gwamnati da cew, rashin sauya ranar zabe daga rana kun Asabar zuwa rana kun da s**a dace abisa doran wannan ilimi, zai cigaba da haifarwa kasar nan koma baya tareda manyan kalubale ga gwamnati da lafiyar shugaban dake kan kujerar mulki, dama sauran al'umman kasa baki daya, saboda al'umma baza su taba samun irin Shugabancin da ake mafarkin samu ba.

Akarshe kuma ya tabbatar da cewa, Kungiyar mu a shirye take domin bada gudumawa idan gwamnati da kuma hukumar zabe sun shirya sauraro da kuma duba zuwa ga wannan alamari da muka gano.

Zamu Iya Sai tawa Mutum Kaddara Mai Kyau Tareda Kyakkyawan Dabi'u Tun Kafin Samun Cikin sa Zuwa Yazo Duniya___Imam Assuf...
28/09/2024

Zamu Iya Sai tawa Mutum Kaddara Mai Kyau Tareda Kyakkyawan Dabi'u Tun Kafin Samun Cikin sa Zuwa Yazo Duniya___Imam Assufiyyu

Imam Habibi Abdallah Assufiyyu, Shaha rarren Malami kuma Shugaban Kungiyar Malamai Masana Ilimin Taurari Na Kasa (FANIS) yace " zamu Iya saitawa wanda ba'a haifa ba kyakkyawan kaddara da dabi'u masu inganci tun kafin asamu cikin sa zuwa a haife shi yazo duniya, akarshe kuma yasamu muwafaqa mai girma a rayuwa. saboda haka wannan alamari ne da iyaye yakamata su maida hankali akai domin samarwa 'ya'yan su kyakkyawar gobe.

Shehin Malamin yace " Kuma ashirye muke domin taimaka ma dukkan wanda yakeson yaga haka tafaru ga rayuwar 'ya 'yansa, wanda zai sa su samu sauki wajen tarbiyar yantar da su arayuwa.

Ta hanyar amfani da Ilimin Falaki dan Adam zai samu ingantacciyar rayuwa mai cike da tsari da manyan nasarori wadanda tunani ko hankali bazai iya hikayo su ba, batare da jingina ga doron ilimi ba.

Mai zaku ce ?

ILIMI KOGI: Akwai Mutane  Dake Iya Sake Dawowa Duniya Don Yin Sabuwar Rayuwa Bayan Mutuwar su Awani Lokaci a Baya____Ima...
24/09/2024

ILIMI KOGI: Akwai Mutane Dake Iya Sake Dawowa Duniya Don Yin Sabuwar Rayuwa Bayan Mutuwar su Awani Lokaci a Baya____Imam Assufiyyu

Shugaban Kasar Malamai Masana Falaki (Taurari) na Najariya, FANIS, Imam Habibi Abdallah Assufiyyu yace "Kungiyar mu ta gano cewa " wasu daga cikin halittun mutane na iya dawowa doron Duniya don cigaba da sabuwar rayuwa bayan shafe tsawon shekaru suna rayuwa a wani zamani daban daya shude.

Shehin Malamin yace " Shiyasa wasu wadanda irin wannan alamarin ya faru da rayukansu s**an fuskanci ganin wasu abubuwa a rayuwa amatsayin kamar wani abu daya taba faruwa da a wani lokaci ko amafarki.

Bakomai yake sanya hakan ya zama yana faruwa ba sai ga irin mutanen da adadin lambar ruhiyyarsu ta dan Adam tazama 9, na insaniyya ma ta zama 9, musamman kuma idan dabi'unsu na rayuwar farko s**a zama dangogin iska da wuta a lissafin ilimin ƙididdiga lambobi, babu shakka wadann sune mafi shu'umancin dabi'u acikin guda hudu da ake dasu a wannan ilimin.

Imam Assufiyyu yaja hankali da cewa " Yazama dole kuma adunga yiwa mutanen masu irin wannan baiwar uzuri ayayin da akaga suna wata kalar rayuwa data sha banban da sauran na mutane saboda dalilai irin wadan nan.

Mai Zaku Iya Cewa ?

15/09/2024

Barkan mu da yammaci mabiya wannan shafi mai albarka 🙏

DA DUMI-DUMI : Mutane Nan Gaba Zasu IyA Bace wa Kamar AljannuShugaban Kungiyar Malamai Masana Ilimin Taurari na Najeriya...
31/08/2024

DA DUMI-DUMI : Mutane Nan Gaba Zasu IyA Bace wa Kamar Aljannu

Shugaban Kungiyar Malamai Masana Ilimin Taurari na Najeriya, sheikh Imam Habibi Abdallah Assufiyyu ya bayyana cewa " Mun gano cewa kowanne dan Adam yana dauke da wata lambar sirri wacce ubangiji ya halicce shi da ita, da mutane zasu iya tantance nasu da kowa zai iya bace wa kamar yadda jinsin aljannu ke bace wa, kuma da kowa zai iya magana da dan uwansa batare da kiran waya ba ko haduwa ta zahiri ako ina suke a doran kasa "

Ya Kara da cewa " da yiwu war hakan zai fara kasancewa a shekaru masu zuwa "

HASASHEN YANAYI : DAGA KUNGIYAR FANIS " Za'a Tabka Mamakon Ruwan Sama Daga Yau Lahadi, 25/08/2024 Zuwa Ranar Talata, 27/...
25/08/2024

HASASHEN YANAYI : DAGA KUNGIYAR FANIS

" Za'a Tabka Mamakon Ruwan Sama Daga Yau Lahadi, 25/08/2024 Zuwa Ranar Talata, 27/08/2024 "

Jihohin da lamarin zai wakana sune Borno, Jigawa, Taraba, Adamawa, Bauchi da Gombe.

Cikin Ikon Allah

WATA SABUWA: Ina samari da yan Mata, ku matso kusa kungiyar malamai Masana ilimin taurari na Najeriya tayi zazzafar fash...
08/08/2024

WATA SABUWA: Ina samari da yan Mata, ku matso kusa kungiyar malamai Masana ilimin taurari na Najeriya tayi zazzafar fashin baki.

Mai zaku ce akan hakan ?

Muna Kira Da Shawartar Al'ummar Nijariya Da Su Dage Źànga-Zangar Lumana Da Za A Gudanar Zuwa Wani Lokaci, Inji Kungiyar ...
26/07/2024

Muna Kira Da Shawartar Al'ummar Nijariya Da Su Dage Źànga-Zangar Lumana Da Za A Gudanar Zuwa Wani Lokaci, Inji Kungiyar Malamai Masana Ilimin Taurari (Falaki Network)

Kungiyar malamai masana ilimin Alkaluma (Falaki ), na Nijeriya, tayi kira da cewa al'umma kasa masu shirin yin zanga-Zanga luma su dakatar da fara wannan shiri daga kwanaki 5 masu zuwa, zuwa wani lokaci da yakai tsawon sati domin samun kyakkyawar sakamakon da ake nema.

Wannan Kiran da kungiyar yayi ya biyo bayane a sakamakon wani bincike muka gabatar dangane da shirin nayin zanga-Zangar lumana wanda akace an shirya ne don nusar da gwamnati halin matsi da matsalar tsaro da al'umma kasa ke ciki.

Shugaban kungiyar sheikh Imam Habibi Abdallah Assufiyyu, ya bayyana cewa kungiyar su tana kan kokari na bada gudumawar Addu'o'i da s**a da ce, da nufin Allah ya kawar da faruwar dukkan abun tsoro da abunqi ayayin gudanar da wannan zanga-Zangar ta lumana, domin babu shakka irin wannan gudumawar ce dukkan malamai yakamata su bada, duba da cewa zuwa yanzu gwamnati da al'umma kasa basu samu daidaito akan dakatarwa ko yiwuwar zanga-Zangar ba.

Shugaban ya jaddada kira da roko akan cewa, al'umma ayi hakuri abaiwa wannan kungiya tamu damar bada gudumawa wajen kawo cigaban kasa ta fuskan addua, kuma da yiwuwar hakan zai zama wani dama na gwamnati tayi abunda al'ummar kasa keso kafin ranar karewar wa'adin kwana 7 da muka nemi a kari kafin gudanar da zanga-Zangar ta lumana.

Munada manyan dalilai akan wannan Kira da mukayi ga al'umma na kada a gudanar da wannan alamari acikin kwana biyar masu zuwa, wanda bamu bukatar fitarwa acikin wannan sanarwa tamu, fatan mu da manufar mu shine asamu nasara da kuma haifuwar da mai ido.

Domin tuntubar wannan kungiya da neman karin bayani akan wannan roko, al'umma zasu iya magana Shugabannin sashin binciken kwaf na taurari akan lambobin waya kamar haka.

Sayyadi Imam Muhammad Al'falaki : 09016619909
Sayyadi Imam Misbahu Ahmad : 0906138 0493

SANARWA: Kungiyar Malamai Masana Ilimin Alkaluma Na Nijeriya, Wato Falaki Network Of Islamic Scholars (FANIs) Ta Shirya ...
17/07/2024

SANARWA: Kungiyar Malamai Masana Ilimin Alkaluma Na Nijeriya, Wato Falaki Network Of Islamic Scholars (FANIs) Ta Shirya Karbar Sabbin Membobi

Kungiyar tana sanar da daukacin al'umma musamman malamai, limamai, da yan uwa almajiran ilimi, cewa dama tasamu, domin kungiyar ya bude kofar daukar sabin Membobi a fadin kasa baki daya, da makwabtan Kasashen na Africa.

Domin tuntubar sashin sayar da fom, ku kirayi lambobin waya kamar hakakamar haka :

Sayyadi Malam Lawal :
+234 806 092 9145

Sayyadi Imam Abdullahi
+234 814 014 4330

Sayyadi Malam Gaddafi:
+234 806 803 2317

Email : [email protected]

KA'IDOJIN YANKAR FOM :
_________________________

A. Dole yazama ka kasance daga cikin musulmin Kwarai.

B. Malami, Limami ko Almajirin ilimi.

C.Ilimin fanni daya daga cikin fannonin ilimin taurari( Falaki) ; Hisabi, Ramli, Auqat.

D. Ga wanda ya rasa ka'idar A da B na ka'idojin da aka lissafa a sama, dole yazama ya mallaki takardar karatun sakandiri, difloma, digiri, mastas ko matakin farfesa.

GAME DA KUNGIYAR FALAKI
______________________

Kungiyar malamai masana ilimin Alkaluma wato Falaki Network of Islamic Scholars (FANIs), kungiya ce na zakakuran maluma, gwanayen Al'qur'ani mai girma, da sauran muhimman bayin Allah nagari, a fadin kasa baki daya, takasance mai zaman kanta tareda sadaukar da kai wajen yin amfani da ilimin taurari wajen fitar lokaci, kwanakin wata, yin addu’o’in wajen magance matsalolin mutane tareda Addu'o'in kawo cigaban kasa (Nijeriya), taimako ga Mata zawara da kananun Yara da gina rayuwar yara Almajirai a Nijeriya.

BABBAR MANUFA

- Kungiya malaman Falaki, kungiya mai albarka tanada babbar manufa guda daya daga cikin manyan manufofinta wanda yakasance shine nazamowa babbar kungiya ta malaman addinin musulunci wacce ke amfani da ilimin Alkaluma (taurari) tahanyar da yayi daidai da ka'idojin musulunci tareda amfani da Al'qur'ani mai girma don warware matsaloli da al'umma ke fuskanta da kuma samar da gagarumin cigaba a kasa baki daya.

SAURAN MANUFOFI:

- Domin kare marbata, daraja da hakkokin membobin kungiya daga fuskantar tawaya ko bazarana kowacce kala a bisa tsarin dokar musulunci dana kasa.

- Domin Koyar da ilmin taurari da tarihinsa a wayewar Musulunci, da gudummawar da yake bayarwa a fannin kimiyya da lissafi, da yadda taurari a duniyoyi keda alaka da dan Adam da rayuwarsa, wanda zai baiwa mutum daman sanin kansa da kuma abubuwar da s**a dace dashi a rayuwa.

- Domin hidimomin kallon kalanda da ganin wata: sanar da al'umma ilimin kwanakan wata da kuma samar da kalanda na watan Musulunci bisa kididdigar ilmin taurari abubuwa ne wadanda ke da muhimmanci ga bukukuwan addini, da alamuran yau da kullum, hakan zai bada dama wajen gudanar da komai acikin kyakkyawar sa'a data dace da abunda mutum ke son aiwatar tareda samun nasara cikin yardar Allah.

- Tsarawa tareda gudanarwa na Addu'o'i domin magance matsalolin annoba dana matsalar tsaro domin samar da cigaba a kasa : Tare da ilimi da gogewar ƙwararrun masana taurari na Islama na wannan kungiya na Falaki Network, mun maida hankali wajen fitar da addu'o'i masu ƙarfi daga cikin Alƙur'ani mai girma tareda lissafin alkaluma na ilimin hisabi.

- Gina rayuwar yara almajirai domin kawar da yawan bara ce-bara ce tareda tallafawa wajen inganta tsarin karatun Al'qur'ani dana boko ( basics mathematics da basics English communication skills) a tsangayu da makarantun Islamiiyya.

- Tallafawa Mata zawarawa, Marayu da gajiyayyu.

Allah ya bamu nasara, zaman lafiya da cigaba mai dorewa. Amin

Address

Abuja
P.OBOX17JAJI

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Aku posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Aku:

Share