ASK HAUSA NEWS

ASK HAUSA NEWS ALHAMDULILLAH An bude shafin ASK HAUSA NEWS Facebook ne ranar 24 ga watan August 2021 domin wallafa labarai.

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin jihar Gombe ta haramta sana'ar yin jari Bola.
05/01/2026

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin jihar Gombe ta haramta sana'ar yin jari Bola.

Suma a garin Offa na jihar Kwara State ansamu dirar wani abin fashewa da ya ya faɗo cikin dare ya yi sanadin rushe gine-...
26/12/2025

Suma a garin Offa na jihar Kwara State ansamu dirar wani abin fashewa da ya ya faɗo cikin dare ya yi sanadin rushe gine-gine. A Jiya da dare.

Wasu mutane ɗauke da mak**ai sun sace mutanen da s**a haɗa da mata da yara a Filato, a hanyarsu ta tafiya bikin Maulidi ...
24/12/2025

Wasu mutane ɗauke da mak**ai sun sace mutanen da s**a haɗa da mata da yara a Filato, a hanyarsu ta tafiya bikin Maulidi ranar Lahadi.

Mai magana da yawun ƴansanda a jihar Alabo Alfred ya ce sun tura jami'ansu wurin da lamarin ya faru a wani ƙoƙarin ceto mutanen.

Shugaban APC na kasa ya nada tsohon Sanata,  Imran Mohammed da wasu mutane 14 a matsayin mataimakaShugaban Jam’iyyar APC...
24/12/2025

Shugaban APC na kasa ya nada tsohon Sanata, Imran Mohammed da wasu mutane 14 a matsayin mataimaka

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa Nentawe Yilwatda, ya amince da nadin mataimaka 15, ciki har da tsohon sanata da wani mashahurin mai amfani da kafafen sada zumunta, domin karfafa ayyukan gudanarwa da tsare-tsaren jam’iyyar.

Nadin sun hada da mashawarta na musamman da mashawarta, da manyan mataimakan musamman, kuma an tsara su ne domin bunkasa hadin kai, tsara manufofi, da kuma hulda da masu ruwa da tsaki a Babban Ofishin Jam’iyyar.

Wannan ya fito ne a cikin wata sanarwa da Mustapha Dawaki, Babban sakataren shugaban kasa na APC, ya fitar.

Sanarwar ta ce ana sa ran wadanda aka nada za su yi amfani da gogewa da kwarewarsu wajen tallafawa shugaban jam’iyyar wajen gudanar da ayyukansa.

Daga cikin wadanda aka nada akwai tsohon sanata Danladi Sankara, wanda zai zama Mashawarci na Musamman kan Al’amuran Siyasa.

Daniel Reyenieju Oritsegbubemi an nada shi Mashawarci na musamman kan Al’amuran majalisar dokoki, yayin da Sorochi Longdet ya zama Mashawarci na Musamman kan bincike, tsare-tsare da shirye-shirye.

Wasu daga cikin mashawartan sun hada da Jibrin Abdullahi Surajo (Hulda da Al’umma), Paul Domsing (Ayyuka na Musamman), da Suleiman Bukari.

Taiwo Ajibolu Balofin kuma an nada shi a matsayin Mashawarci na girmamawa kan hadin kai da tattara ‘yan ƙasashen waje.

A matakin manyan mataimakan musamman, mashahurin mai amfani da kafafen sada zumunta, Imran Mohammed, an nada shi a matsayin Babban Mataimaki na Musamman kan Sabbin Kafafen Sadarwa.

Mildred Bako an nada ta Babban Mataimaki na Musamman kan Kungiyoyin Al’umma, Yusuf Dingyadi ya zama Babban Mataimaki na Musamman kan Kafofin Watsa Labarai, yayin da Enenedu Idusuyi aka nada shi Babban Mataimaki na Musamman kan tsari da sauransu.

Sanarwar ta ce nadin mataimakan wani bangare ne na kokarin da ake ci gaba da yi don kara inganci a shugabancin kasa na jam’iyyar.

Bello Matawalle Allah Ya Isar Maka Ga Duk Wanda Ya Alakanta Ka Da Goyon Bayan Ta'aďďanci, Cewar Surajo Sa'idu Sokoto
12/12/2025

Bello Matawalle Allah Ya Isar Maka Ga Duk Wanda Ya Alakanta Ka Da Goyon Bayan Ta'aďďanci, Cewar Surajo Sa'idu Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Kaduna kuma jigo a jam'iyyar ADC Malam Nasir El-Rufai tare da mahaifiyarsa a masallacin Manzon Alla...
11/12/2025

Tsohon gwamnan jihar Kaduna kuma jigo a jam'iyyar ADC Malam Nasir El-Rufai tare da mahaifiyarsa a masallacin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam da ke birnin Madina na Saudiyya a ziyarar Umarah da su ka kai ƙasar.

📸 Muryoyi

Aliko Dangote ze raba dukiyarsa kashi hudu ya bayar da kashi daya sadaka.Attajirin da ya fi kowa kudi a nahiyar Afirka, ...
11/12/2025

Aliko Dangote ze raba dukiyarsa kashi hudu ya bayar da kashi daya sadaka.

Attajirin da ya fi kowa kudi a nahiyar Afirka, Aliko Dangote ya bai wa gidauniyar Aliko Dangote kwata na dukiyarsa.

Dangote ya bayyana hakan ne a Legas ranar Alhamis a wajen kaddamar da shirin ilimi na Aliko Dangote Foundation.

Ya ce tuni ya bai wa mahaifiyarsa da ‘ya’yansa uku wasiyar hakan saboda halin mutuwa.

Ya sanar da kaddamar da zuba jarin N100bn a shekarar 2026 don tallafawa almajirai 155,009

Zai ba wa makarantar marayun yan mata N590m kowace shekara a Maiduguri muddin makarantar ta ci gaba da wanzuwa.

Source: Business Day ✍️

Da Dumi Dumi.Hukumar Hisba Ta Jihar Kano Ta Fashe Kwaleben Giya Kimanin Dubu Hudu Da Ɗari Tara Da Ashirin 4,920
11/12/2025

Da Dumi Dumi.

Hukumar Hisba Ta Jihar Kano Ta Fashe Kwaleben Giya Kimanin
Dubu Hudu Da Ɗari Tara Da Ashirin 4,920

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa Waɗannan su ne gawakin mata guda 9 da ake zargin sojoji da kashewa bayan sun buɗa wa masu zanga-z...
09/12/2025

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa

Waɗannan su ne gawakin mata guda 9 da ake zargin sojoji da kashewa bayan sun buɗa wa masu zanga-zanga wuta a Ƙaramar Hukumar Lamurde ta jihar Adamawa a jiya Litinin.

SUN RASA RANSU A GURIN NEMAN HALALWasu matasa guda hudu a garin Banki dake karamar hukumar Bama jihar Borno wanda suke s...
06/12/2025

SUN RASA RANSU A GURIN NEMAN HALAL

Wasu matasa guda hudu a garin Banki dake karamar hukumar Bama jihar Borno wanda suke sana'ar jari-bola sun rasa rayukansu

Sun tsinci wani tarkace a bola, basu sani ba ashe b0mb ne, suna kokarin kwancewa sai ya tarwat$e da su, duk su hudun sun rasa ra¥ukansu, abin ya faru jiya juma'a

Muna fatan Allah Ya karbi $hahadarsu

Ministan Jihohi na Ci gaban Yankuna, Uba Maigari Ahmadu, ya karyata zargin cewa ya boye ya samo umarnin kotu domin k**a ...
05/12/2025

Ministan Jihohi na Ci gaban Yankuna, Uba Maigari Ahmadu, ya karyata zargin cewa ya boye ya samo umarnin kotu domin k**a Abdulmumin Imam, ɗan fafutukar ƙasa daga Taraba, wanda ke yawan s**ar yadda Gwamnatin Tarayya ta gudanar da batun rushewar gadar Namnai da kuma zargin karkatar da biliyan N16.5 da aka amince a yi amfani da su wajen sake gina gadar.

Rarara Ya Sakawa Masalacin Da Ya Gina A Garinsu Na Kahutu Sunan Ma Haifinsa Malam Adamu.Ya Allah Ka Horewa Kowa Arzikin ...
05/12/2025

Rarara Ya Sakawa Masalacin Da Ya Gina A Garinsu Na Kahutu Sunan Ma Haifinsa Malam Adamu.

Ya Allah Ka Horewa Kowa Arzikin Da Zai Gina wa Mahaifansa Masallaci Domin Su Dinga Samun Lada Na Har Abada Ameeeeen 🙏🙏😊

Daga Abdulhadi Abdullahi

Address

Abuja

Telephone

+2348144493602

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ASK HAUSA NEWS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ASK HAUSA NEWS:

Share