Jaridar Najeriya

Jaridar Najeriya Jaridar Najeriya kafa ce dake watsa labarai cikin harshen Hausa zalla tare da muradin kare hakkin dan adam a fadin Najeriya. Jaridar Najeriya
(1)

Kuna iya tuntubar wannan lamba ta what’sapp 08067569012 domin antayo da bukatunku a kowane lokaci domin ganin an samu saukin rayua

16/10/2025

Akwai Masoya Manzon Allah SAWW da ba su yi barci ba su zo mu gaida Shugaba Muhammadur Rasulullah?

Matasa mu Farka: Lokaci Ya Yi da Za mu Mallaki Tunani a Siyasa‎‎Daga: Abubakar Bashir Adam Yakasai‎‎A yau, siyasar ƙasar...
15/10/2025

Matasa mu Farka: Lokaci Ya Yi da Za mu Mallaki Tunani a Siyasa

‎Daga: Abubakar Bashir Adam Yakasai

‎A yau, siyasar ƙasar nan ta zama fili da wasu kalilan ke amfana dashi, yayin da yawancin matasa s**a zama masu kallo daga gefe — ko kuma s**a zama kayan aiki ga ‘yan siyasa marasa kishin ƙasa. Wannan lamari yana barazana ga makomar Najeriya, domin duk wata al’umma da matasanta s**a gaza fahimtar rawar da siyasa take takawa, to makomarta tana cikin haɗari.

‎Matasa sune ginshiƙin ƙasa, su ne ƙarfinta da fata na gobe. Amma a yanzu, da yawa daga cikinsu sun bar kansu a hannun ‘yan siyasa, suna bin su saboda kudi ko alƙawarin banza. Wasu ma sun ɗauki siyasa a matsayin hanyar samun abinci kawai, ba hanyar gyara ƙasa ba.

‎Yakamata matasa su dawo su fahimci cewa siyasa ba wai fada bace, ko karya juna a kafafen sada zumunta ba. Siyasa hanya ce ta neman cigaban ƙasa da kare martabar jama’a. Idan matasa s**a gyara akidarsu, s**a fahimci siyasa ta gaskiya, ba shakka za su zama jagororin da za su fitar da ƙasar nan daga halin da take ciki.

‎Lokaci ya yi da matasa za su mallaki tunaninsu, su zama masu kishin kasa, ba masu bin ‘yan siyasa don abin duniya ba. Su daina bari miyagun ‘yan siyasa suna bautar musu da tunani da zuciya. A yau Najeriya na bukatar matasa masu hangen nesa, masu akida, masu kishin al’umma — ba matasa masu tsoro da bin son rai ba.

‎Siyasa tana bukatar gyara, kuma wannan gyaran dole ne ya fara daga zukatan matasa.


Bayan kammala taron gamayyar Malaman addinin musulunci na arewacin Najeriya, Sheikh Abubakar Lawan Triumph ya tsaya domi...
15/10/2025

Bayan kammala taron gamayyar Malaman addinin musulunci na arewacin Najeriya, Sheikh Abubakar Lawan Triumph ya tsaya domin gabatar da taƙaitacciyar muhadara a masallacin Sultan Bello na Kaduna tare da sauran malamai.

ALLAHU AKBAR: Wannan Shi Ne Kabarin Sayyiduna Usman Sahabin Manzon Allah SAWW.Allah ya karawa Annabi Daraja.
15/10/2025

ALLAHU AKBAR: Wannan Shi Ne Kabarin Sayyiduna Usman Sahabin Manzon Allah SAWW.

Allah ya karawa Annabi Daraja.

YANZU-YANZU: Iran Ta Kammala Gina Wa Kiristocin Kasar Tashar Jirgin Kasa A TehranKasar Iran ta kammala gina katafaren ji...
15/10/2025

YANZU-YANZU: Iran Ta Kammala Gina Wa Kiristocin Kasar Tashar Jirgin Kasa A Tehran

Kasar Iran ta kammala gina katafaren jirgin kasa da aka sanya wa tashar suna “Merry”, wadda ke kusa da babban cocin kasar mai suna Saint Sarkis Church a birnin Tehran.

Wannan tashar jirgin kasa an gina ta ne domin saukaka zirga-zirgar Kiristocin da ke yankin, tare da nuna irin kulawar da gwamnatin kasar ke nunawa ga al’umman Kirista da sauran mabiya addinai daban-daban.

Fuskokin wasu daga cikin manyan Malaman Najeriya a wurin taron Malaman Arewa da ke gudana a Kaduna a yau Laraba. 📸 Ibrah...
15/10/2025

Fuskokin wasu daga cikin manyan Malaman Najeriya a wurin taron Malaman Arewa da ke gudana a Kaduna a yau Laraba.

📸 Ibrahim Shehu Giwa

TIRKASHI: Rundunar sojin Isra’ila ta bayyana cewa ɗaya daga cikin gawarwakin da ƙungiyar Hamas ta mika mata a daren jiya...
15/10/2025

TIRKASHI: Rundunar sojin Isra’ila ta bayyana cewa ɗaya daga cikin gawarwakin da ƙungiyar Hamas ta mika mata a daren jiya, ba gawar ɗaya daga cikin jami’anta ba ce.

Wannan sanarwar ta biyo bayan yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas, wadda ta haɗa da musayar fursunoni da dawo da gawarwakin wasu daga cikin mutanen da aka yi garkuwa da su a yankin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun ce suna ci gaba da bincike don gano asalin wanda gawar ta fito daga gare shi, tare da tabbatar da cewa ana gudanar da duk matakan kimiyya da bincike na DNA kafin a fitar da ƙarin bayani.

MU YI RAHA: Jarumar Kennywood Momee Gombe Ita ce mace daya tilo da ta zama tattalin arziki garin Gombe.In Kuma Akwai Wat...
15/10/2025

MU YI RAHA: Jarumar Kennywood Momee Gombe Ita ce mace daya tilo da ta zama tattalin arziki garin Gombe.

In Kuma Akwai Wata A Kawo Ta.

DA DUMI-DUMI: Jarumin Kennywood Abba Galadima Tare Da Wacce Ake Saran Zai Aura.Wace fata zaku musu?
15/10/2025

DA DUMI-DUMI: Jarumin Kennywood Abba Galadima Tare Da Wacce Ake Saran Zai Aura.

Wace fata zaku musu?

YANZU-YANZU: Motocin Red Cross sun karaso don karbar Gawarwakin Isra'ila biyu dake Gaza. Wannan na cikin yarjejeniyar za...
14/10/2025

YANZU-YANZU: Motocin Red Cross sun karaso don karbar Gawarwakin Isra'ila biyu dake Gaza.

Wannan na cikin yarjejeniyar zaman lafiya da a gudanar tsakanin Isra'ila da Hamas.

YANZU-YANZU: Najeriya taci kasar Binin kwallo 🇳🇬3-0🇧🇯 A wasan share fagen shiga Gasar Cin Kofin Duniya ta shekara ta 202...
14/10/2025

YANZU-YANZU: Najeriya taci kasar Binin kwallo 🇳🇬3-0🇧🇯 A wasan share fagen shiga Gasar Cin Kofin Duniya ta shekara ta 2026.

DA ƊUMI-ƊUMI: Sojojin Madagascar Sun Karɓe Mulki Bayan Rusa Majalisar Dokoki Da Shugaba Rajoelina Ya Yi.Rikicin siyasa a...
14/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Sojojin Madagascar Sun Karɓe Mulki Bayan Rusa Majalisar Dokoki Da Shugaba Rajoelina Ya Yi.

Rikicin siyasa a ƙasar Madagascar ya shiga sabon salo, bayan da rundunar sojin ƙasar ta sanar da cewa ta karɓe mulki daga hannun Shugaba Andry Rajoelina, wanda a kwanakin baya ya rusa majalisar dokokin ƙasar domin kauce wa yunƙurin ’yan'adawa na tsige shi.

A cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters, rundunar sojin ta tabbatar da karɓar mulkin a safiyar Talata, yayin da AFP ta ruwaito wani soja mai muƙamin Kanal, Michael Randrianirina, shugaban rundunar tsaron fadar shugaban ƙasa, yana karanta sanarwar a gidan radiyon ƙasar.

A cikin sanarwar, Kanal Randrianirina ya ce: “Mun karɓe mulki daga yanzu.” An ce rundunar da ke tsaron fadar shugaban ƙasa ta juya masa baya ne a ƙarshen mako, ta hanyar shiga cikin zanga-zangar masu neman shugaban ya yi murabus.

Tun a baya, Shugaba Rajoelina ya rusa majalisar dokokin ƙasar domin hana ’yan'adawa kada kuri’ar tsige shi, bayan makonni biyu na zanga-zangar da ta rikide ta zama tashin hankali, wadda matasa s**a jagoranta suna zargin gwamnati da cin hanci da rashawa da kuma zalunci.

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana a wata sanarwa cewa dokar rusa majalisar “ta fara aiki nan take bayan wallafawa ta rediyo ko talabijin.”

Duk da kiraye-kirayen da ake masa da ya yi murabus, Rajoelina ya ci gaba da kare matakinsa a shafukan sada zumunta, yana cewa matakin ya zama wajibi domin dawo da doka da oda da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyya.

Sai dai rahotanni sun nuna cewa shugaban ya tsere daga ƙasar a ƙarshen makon nan a cikin jirgin soja na Faransa, duk da cewa hukumomin Faransa ba su tabbatar da hakan ba.

Rajoelina, tsohon magajin garin babban birnin Antananarivo, ya ce yana cikin “wuri mai tsaro” bayan yunkurin kisan shi, amma bai bayyana inda yake ba.

Kamar yadda Jaridar Taskar Labarai ta tattaro, Zanga-zangar dai ta fara a ranar 25 ga Satumba ta ƙara ƙamari bayan da wasu sojoji da jami’an tsaro s**a koma gefen masu zanga-zanga, suna kir

Address

Gimbiya Street
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Najeriya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Najeriya:

Share