KSM Hausa

KSM Hausa Shafin Labarai Da Rahotanni Na Cikin Gida Najeriya Da Kasashen Ketare A Cikin Harshen Hausa
kanostatemedia

Shugaba Bola Tinubu, a ranar Litinin, ya gana da sabbin shugabannin rundunonin tsaro da aka nada a Fadar sa da ke Abuja.
27/10/2025

Shugaba Bola Tinubu, a ranar Litinin, ya gana da sabbin shugabannin rundunonin tsaro da aka nada a Fadar sa da ke Abuja.

Saratu Hashimu Mai Capacity💗Wane fata zaku yi mata?
27/10/2025

Saratu Hashimu Mai Capacity💗

Wane fata zaku yi mata?

Ina matukar tausayin mazaje masu mata daya, akwai nutsuwa tattare da auren mace fiye da daya, in ji wani Sanata daga kud...
27/10/2025

Ina matukar tausayin mazaje masu mata daya, akwai nutsuwa tattare da auren mace fiye da daya, in ji wani Sanata daga kudancin Nijeriya

Sanata Ned Nwoko ya ce yana tausayin maza masu mata ɗaya, yana mai jaddada cewa auren mace fiye da ɗaya na kawo daidaito da kwanciyar hankali ga maza.

Dan majalisar da ke wakiltar Delta North ne ya bayyana hakan yayin da yake tattaunawa a shirin Politics Today na tashar Channels Television.

27/10/2025

YANZU-YANZU: Jami'an Tsaron Yan Sanda Sun Fara Harba Tiyagas kan Masu Zanga-zangar Neman a Saki Omoyele Sowore a harabar Kotun Majistiri dake Kuje, Abuja.

27/10/2025

Waƙa Daga Bakin Mai Ita...

Majalisa ta amince a ƙirƙiro jihohi shida a Najeriya
27/10/2025

Majalisa ta amince a ƙirƙiro jihohi shida a Najeriya

15/10/2025

LABARAI: Daga yanzu daliban sakandire bangaren Art basa bukatar lallai sai sunci lissafin Mathematics a jarabawar WAEC ko NECO, inji ministan ilimi.

Ministar Harakokin Mata a Najeriya, Imaan Sulaiman-Ibrahim ta ce auren wuri na haifar da talauci tare da hana ’yan mata ...
11/10/2025

Ministar Harakokin Mata a Najeriya, Imaan Sulaiman-Ibrahim ta ce auren wuri na haifar da talauci tare da hana ’yan mata ilimi da tauye musu haƙƙin faɗar albarkacin baki da kuma hana su bayar da gudummawa ga al’umma.

Ministan ta ce auren wuri na kawo koma baya a Najeriya, inda ta ce a yanzu kashi 44 cikin 100 na ’yan mata ana aurar da su kafin su kai shekaru 18, wasu kashi 18 cikin 100 kuma kafin su kai shekaru 15.

Ta bayyana haka ne a wajen bikin zagayowar Ranar ’Ya mace ta Duniya ta 2025, wanda ya gudana a jiya Juma’a a Abuja, wanda Save the Children International (SCI) Nigeria da Pink Up for Girls Initiative suka ɗauki nauyi.

11/10/2025

Ko me yasa ake ta rufe gidajen mai?

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Katsina ta samu nasarar cafke mutum 168 da ake zargi da aikata laifuka 105 a cikin watan Sa...
11/10/2025

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Katsina ta samu nasarar cafke mutum 168 da ake zargi da aikata laifuka 105 a cikin watan Satumba.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a hedikwatar ‘yan sanda da ke Katsina ranar Juma’a.

A cewar DSP Aliyu, cikin wadanda aka kama akwai:
• Mutum 12 da ake zargi da fashi da makami,
• Mutum 5 da ake zargi da kisan kai,
• Sama da mutum 20 da ake zargi da fyade,
• Mutum 9 da ake zargi da lalata kadarorin gwamnati,
• Mutum 2 da ake zargi da safarar makamai,
• Mutum 3 da aka kama da mallakar bindigogi ba bisa ka’ida ba,
• Mutum 14 da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi,
• Da kuma wasu da ake zargi da laifuka daban-daban.

DSP Aliyu ya ƙara da cewa rundunar ta hana wasu hare-haren ‘yan ta’adda, ta kashe ‘yan bindiga biyar, tare da ceto mutane sama da 80 da aka yi garkuwa da su a lokacin ayyukan.

Kayayyakin da aka samu sun haɗa da:
• Alburusai 1,298,
• Bindigogi biyu kirar AK-47 da guda ɗaya GPMG,
• Bindiga ɗaya ta gida da harsashi guda ɗaya,
• Motoci 5 da babura 5 da ake zargin an sace su,
• Kwayoyin Tramadol 1,096, Exol 42, da wiwi,
• Da kuma igiyoyin lantarki da aka lalata.

DSP Aliyu ya gode wa Gwamnatin Jihar Katsina da mazauna jihar bisa goyon bayan da suke bai wa ‘yan sanda, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da rahoton duk wani abin da suke zargi ga hukumomin tsaro.

BAYAN YAFIYAR TINUBU: “Na ji kamar an wanke min zunubaina” - Farouk Lawan
11/10/2025

BAYAN YAFIYAR TINUBU: “Na ji kamar an wanke min zunubaina” - Farouk Lawan

11/10/2025

Shahararran Ɗan Wasan Kwaikwayo A Harkar Fina Finan Hausa 100009200401285:2048:Mustapha Nabraska Ya Jaddada Goyon Bayansa Akan Sanatan Kano Ta Arewa 61551432367350:2048:Barau I. Jibrin Maliya A Matsayin Gwamnan Jihar Kano A Kakar Zaɓen Shekarar 2027

Me Zakuce Akan Hakan ?
100069360026200:2048:KSM Hausa Part 7

Address

Street Road
Abuja
900001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KSM Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KSM Hausa:

Share