13/08/2026
LABARUN DUNIYA
SHUGABA TINUBU YA GANA DA SHUGABAN RABIDA SHEIKH AL-ISSA
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya gana da shugaban majalisar musulunci ta duniya RABIDA Sheikh Abdulkarim Al-Issa a fadar A*o Rock.
Ganawar dai ta zo ne bayan gudanar da taron majalisar ta Rabida da hadin guiwar kungiyar Izala.
Dukkan bangarorin biyu sun yaba juna yadda su ke bukatar a bunkasa fahimtar juna a tsakanin al’ummar kasa.
Baya ga shugaban JIBWIS Sheikh Abdullahi Bala Lau, akwai wasu gwamnoni da ministoci da su ka raka tawagar Sheikh Al-Issa zuwa fadar ta A*o.
Najeriya dai mai bin tsarin mulki na kowa ya yi addininsa ba tsangwama, na da mabiya addinai da tsarin rayuwa daban-daban da dama.
Duk wanda zai kawo shawarar yadda za a dinke dukkan barakar zama tare, na zama abun maraba a Najeriya.
MUSULMI DA MABIYA ADDININ KIRISTA SUN SANYA HANNU KAN YARJEJENIYAR SALAMA
Musulmi da mabiya addinin kirista sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman salama tare a lamuran yau da kullum.
Wannan na cikin babban sashen taro na duniya tsakanin RABIDA da kungiyar a Abuja wanda ya samu halartar manyan malamai daga wasu kasashen duniya daga ciki da wajen Afurka har zuwa Turai.
Jagororin musulmi da wakilan kungiyar kiristocin Najeriya CAN sun sanya hannu kan wannan yarjejeniya ya tabbatar da zaman lafiya.
Ba batun mabiya addinai su zauna a addini daya, amma tsarin na son kusantar juna da fahimtar tanadin addinin juna da girmama hakan.
Jagororin sun kawo hujjoji daga Alkur’ani da kuma Baibul inda hakan ke nuna kusaci tsakanin musulmi da mabiya addinin kirista.
Shawarwarin da a ka yanke za su zama abubuwan da a ka mikawa gwamnati don karfafasu da hakan zai kawo maslaha kan al’adu da lke kawo zaman doya da manja tsakanin musulmi da kirista.
An wallafa kundin da zai zama abun misali da amfani don kawo karshen duk wata arangama ko kiyayya tsakanin bangarorin biyu.
Traon ya nuna ba alheri ba ne musulmi ya tsangwami kirista ko kirista ya tsangwami musulmi, alhali a na zaune a kasa daya.
ZA A GUDANAR DA ZABEN GWAMNAN OSUN A RANAR ASABAR MAI ZUWA
Hukumar zaben Najeriya INEC za ta gudanar da zaben gwamnan jihar Osun ranar Asabar din nan mai zuwa.
A na kwana 3 gabanin zaben, hukumar zabn ta shigar da sunan dan takarar jami’iyyar SDP Fransis Olugbenga cikin jerin masu takara da hakan ya maida yawan ‘yan takarar 15.
Hakika alamu na nuna magoya bayan tsohon gwamnan jihar Gboyega Oyetola na son yin duk mai yiwuwa wajen kawo karshen gwamnatin Ademola Adelele.
Hakika shi ma wannan zabe na Osun zai zama raba-gardama ga yadda a ke hangen babban zaben 2027 zai gudana.
Samun nasarar gudanar da karbabben zabe a Osun zai nuna yadda musamman ‘yan takarar adawa za su shiga zaben 2027 da kwain guiwa.
Tun kwanaki hukumar zaben INEC ta gudanar da taro da duk masu ruwa da tsaki na zaben.
GWAMNAN JIHAR KEBBI YA RABA MOTOCIN SAFA 7 GA MANYAN MAKARANTUN JIHAR
Gwamnan jihar Kebbi Nasiru Idris Kauran Gwandu ya raba motocin safa 7 ga manyan makarantun jihar.
An yi bukin mika motocin ne a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.
Gwamnan ya ce ya dau matakin ne don bunkasa yanayin koyarwa a manyan makarantun jihar ta hanyar saukaka bukatun sufuri.
"A matsayina na malami na ga ya dace na tuna bangarena na kuma inganta shi.
Tun farko kwamishinan ma'aikatar ilimi mai zurfi Alhaji Isah Abubakar Tunga ya jinjinawa gwamnan don raba motocin sashen da ya dace.
Yayin da ya ke godewa gwamnan don daukar matakan bunkasa sashen ilimi, kwamishinan ya yi alwashin amfani da motocin ga abun da a ka says su na ilimin manyan makarantun jihar.
A sanarwa daga Sakataren labaru na gwamnan, Ahmed Idris, Kolejjn ilimi na Adamu Augie a Argungu, Kolejin jinya da ungozoma ta Kauran Gwandu a Ambursa, Kolejin kimiyyar lafiya da fasaha ta Jega, Jami’ar kimiyya da fasaha ta Abdullahi Gwandu a Aliero, Kolejin ilimi mai zurfi ta shari’a da ke Yauri, Kolejin ilimin lafiya ta Birnin Kebbi sai makarantar kimiyya ta jihar Kebbi da ke Dakingari
TRUMP YA CE AMURKA KE RIKE DA IKON HORMUZ
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce kasarsa ke rike da ikon kula da muhimmiyar mashigar ruwan Maliya na Hormuz.
A nan Trump ya ce Amurka za ta rike mashigar kuma Iran ba ta da wani mataki da za ta dauka.
Trump ya kara da cewa sojojin ruwan Amurka ke kula da mashigar Hormuz a halin yanzu.
Iran a na ta bangaren ta ce sam ba haka ba ne, ita ke rike da akasarin mashigar kuma ikon mashigar na hannunta.
Muhawara dai kan ikon mashigar Hormuz ba sabon abu ba ne musamman a bangaren Amueka.
A na fatan samun maslahar da za ta kawo zaman lafiya mai dorewa tsakanin Iran da Amurka kuma hakan ya dogaro a wani fannin da sulhu kan Hormuz.
An dai samu tsagaitawar hare-hare kan Iran da ramuwar gayyar Iran kan cibiyoyin sojan Amurka da ke gabar ta tsakiya.