08/08/2025
LABARUN DUNIYA
SHUGABA TINUBU YA NADA SABON SHUGABAN HUKUMAR KULA DA WUTAR LANTARKI
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada sabon shugaba ga hukumar kula da lamuran wutar lantarki NERC.
Wanda a ka nadan Injiniya Abdullahi Garba Ramta matashi ne mai shekaru 39 kuma ya na da ilimi har na matakin dokta.
Kazalika shugaban ya nada sabbin kwamishoni biyu ga hukumar da kan kaiyade farashin wutar lantarki.
Sabbin kwamishinonin sun hada da Abubakar Yusuf da zai kula da sashen ma’abota amfani da wuta da kuma Dokta Fouad Olayinka Animashun da zai kula da sashen kudi da gudanarwa.
Gabanin samun tantancewa daga majalisa, shugaban hukumar na rikwan kwarya zai cigaba da aiki.
KEYAMOYA DAKATAR DA MAWAKIN FUJI AYINDE DAGA SHIGA JIRGI
Ministan jiragen sama Festus Keyamo ya dakatar da mawakin Fuji (wakar Yoruba) daga shiga jirage a Najeriya don rashin da’ar da ya nuna.
Mawakin Wasiu Ayinde Marshal ya nemi hana jirgin Valuejet tashi ne bayan an dakatar da shi daga shiga jerin yayin da ya ki yarda a duba kayan da ya rike a hannun sa da a ke ce barasa ce.
Ayinde mai shekaru 68 da a ka fi sani da Kwam 1 ya nemi shan gaban jirgin inda sai da jami’an tsaro su ka shiga tsakani.
Keyamo ya ba da umurnin a hana Kwam 1 shiga jirgi na gida ko ketare sai an kammala bincike.
MAJALISAR ZARTARWAR TSARON ISRA’ILA TA YANKE SHAWARAR KARBE IKON BIRNIN GAZA
Majalisar zartarwar lamuran tsaro ta Isra’ila ta yanke matsayar amshe iko da Garin Gaza wanda shi ne ya fi yawan jama’a a Zirin Gaza.
Wannan na daga matakan cigaba da yakin wata 22 da ya faro tun daga kutsawar Hamas cikin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktobar 2023.
Bisa alkaluman ma’aikatar lafiya ta Gaza, yakin dai zuwa yanzu ya yi sanadiyyar kashe fiye da Falasdinawa 61,000 da jefa Zirin cikin yunwa don tsananin karancin abinci inda mutane kan kanjame su mutu don rashin samun abinci na kwanaki.
Gabanin fara taron majalisar tsaron a jiya alhamis, Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce gwamnatin sa na son mamaye dukkan Gaza ta hanyar kwace Zirin inda za ta mika ragamar sa ga wasu dakarun Larabawa da ba sa ga-maciji da Hamas “mu na son karbe Gaza don tabbatar da tsaron mu, mu kawar da Hamas daga Zirin, mu ba wa al’umma aminci daga Gaza” Inji Netanyahu “mu na son mika Gaza ga sojojin Larabawa da za su mulki yankin yanda ya k**ata ba tare da yi ma na bazaraba ba; inda za su samawa Gazawa rayuwa mai kyau”
Wani Janar na sojan Isra’ila ya nuna fargabar karbe ikon Birnin Gaza ko daukacin Zirin zai jefa rayuwar kimanin k**ammun Isra’ilawa 20 da ke hannun Hamas cikin hatsari, hakanan zai kara wahalar da sojojin kasar da ke yaki na tsawon watanni.
‘Yan uwan k**ammun ma na adawa da wannan shirin na Netanyahu wanda har ya jawo zanga-zanga a gewayen dakin da a ke gudanar da taron na tsaro.
Ba a san adadin mutanen da ke zaune a Gaza-Gari ba tun da an sha umurtar jama’a su fice daga garin amma wasu sun dawo a lokacin da a ka samu tsagaita wuta da shirin ya wargaje inda Isra’ila ta cigaba da rowan boma-bomai kan sassan Gaza “ba sauran wajen da ba a mamye ba a Gaza, ai ba ma abun da ya saura na Gaza” inji Maysaa Al-Heila da ke zaune a sansanin gudun hijira.
Yankunan Gaza sun hada da Gaza-Gari, Jabalia, Khan Younis, Rafa, Deir al-Balah da Bait Hanoun.
Sojojin Isra’ila kan bude wuta kan masu taruwa don gwagwarmayar samun tallafin abinci inda ta kashe fiye da Falasdinawa 1000.
Batun taron tsagaita wuta a birnin Doha da Masar da Katar ke jagoranta tare das a hannun Amurka ya shiga tangal-tangal don rashin samun cimma sharadin Isra’ila na lallai Hamas ta wargaza mayakan ta.
Hamas dai t ace fau-fau ba za ta daina gwagwarmaya ba sai an kafa kasar Falasdinu mai babban birni a gabashin Birnin Kudus.
JIRGIN JODAN NA JEFO TALLAFIN ABINCI GA AL’UMMAR GAZA
Jirgin sama daga kasar Jodan ya cigaba da shawagi don jefa tallafin kayan abinci ga al’ummar Gaza daga cikin mawuyacin yanayi na yunwa.
Jirgin kan taso daga Jodan da ke makwabtaka ya bi samaniyar Gaza ya na jefa kayan tallafi a sassan da sun zama kangaye.
Dakatar da shigar da tallafi yankin na tsawon wata 9 da Isra’ila ta yi ya jawo yunwa ta addabi al’umma kuma hakan salon Isra’ila ne da zummar murkushe Hamas.
Jodan na hada kai da wasu kasashe wajen aikin jefa kayan agajin kuma a baya ma Sarki Abdullah da kan sa ya shiga jirgi don jefa kayan agajin.