Manara RADIO

Manara RADIO Radio channel that sheds light to listeners in Africa,Middle East and across the globe, predominantly "HAUSA" on Islamic tenets and civilization

NAHCON TA BUKACI MASU YAYATA LABARU DA JAMA’A SU RIKA TAKATSANTSANHukumar alhazan Najeriya NAHCON ta bukaci masu yayata ...
22/08/2025

NAHCON TA BUKACI MASU YAYATA LABARU DA JAMA’A SU RIKA TAKATSANTSAN

Hukumar alhazan Najeriya NAHCON ta bukaci masu yayata labaru da sauran jama’ar kasa su rika takatsantsan da labarun da ba a tantance ba.

A ‘yan kwanakin nan mutane musamman a yanar gizo na yada labaru da ke nuna gudanar da bincike a hukumar daga hukumar yaki da cin hanci EFCC.

A nan NAHCON ta sanarwa daga jami’ar labarun hukumar Fatima Sanda Usara ta ce NAHCON a matsayin ta na hukumar gwamnati ta na aiki tare da dukkan hukumomin gwamnati ciki har da na yaki da cin hanci.

NAHCON kan maida hankali wajen tabbatar da kula da kare muradun maniyyata aikin hajji wajen gudanar da aikin cikin walwala da nasara.

Don haka NAHCON na ganin adalci shi ne a rika tabbatar da sahihancin labari da kuma fahimtar nauyin da ya rataya kan hukumar shi ne na kula da kare hakkokin maniyyata; kuma ba abun da za ta boye da ya shafi wani bincike don kofar ta a bude ta ke ga duk mai son karin haske kan wani labari.

22/08/2025

LABARUN DUNIYA

NAHCON TA BUKACI MASU YAYATA LABARU DA JAMA’A SU RIKA TAKATSANTSAN

Hukumar alhazan Najeriya NAHCON ta bukaci masu yayata labaru da sauran jama’ar kasa su rika takatsantsan da labarun da ba a tantance ba.

A ‘yan kwanakin nan mutane musamman a yanar gizo na yada labaru da ke nuna gudanar da bincike a hukumar daga hukumar yaki da cin hanci EFCC.

A nan NAHCON ta sanarwa daga jami’ar labarun hukumar Fatima Sanda Usara ta ce NAHCON a matsayin ta na hukumar gwamnati ta na aiki tare da dukkan hukumomin gwamnati ciki har da na yaki da cin hanci.

NAHCON kan maida hankali wajen tabbatar da kula da kare muradun maniyyata aikin hajji wajen gudanar da aikin cikin walwala da nasara.

Don haka NAHCON na ganin adalci shi ne a rika tabbatar da sahihancin labari da kuma fahimtar nauyin da ya rataya kan hukumar shi ne na kula da kare hakkokin maniyyata; kuma ba abun da za ta boye da ya shafi wani bincike don kofar ta a bude ta ke ga duk mai son Karin haske kan wani labari.



AN SAMU AKASI A DALORI JIHAR BORNO KAN JAMI’AI MASU TAIMAKAWA MANOMA

An samu rahoton samun akasi a yankin Dalori da ke karamar hukumar Konduga a jihar Borno inda ‘yan ta’adda su ka kai hari kan tawagar jami’an tsaro masu kare manoma.

Rahotanni sun baiyana cewa gamaiyar rundunar tsaro da ke raka manoma don isa gonakin su lafiya sun ci karo da kwantan bauna na ‘yan ta’dda.

A cikin wannan aiki na tsaro an samu asarar kimanin jami’ai hudu daga cikin masu tsaron lafiyar manoman kuma an sace wasu daga wadanda ‘yan ta’addan su ka kai wa farmakin.

Ba Karin bayani daga hukumomi kan wannan akasin na kwantan bauna da ‘yan ta’addan su ka yi a wannan yanki da ba shi da nisa daga jami’ar Maiduguri.

‘Yan ta’adda dai sun koma yin kwantan bauna wajen kai hare-hare ba k**ar a baya da su kan iya mamaye garuruwa ko ma mulkar wasu kananan hukumomi ba.



SHUGABA TINUBU YA NUFI BURAZIL DAGA JAPAN

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nufi kasar Burazil bayan kammala taruka da halartar babban taron Tokyo na 9 na lamuran tattalin arzikin Afurka.

Kakakin shugaban Bayo Onanuga ya baiyana cewa shugaba Tinubu ya gudanar da zama na hulda tsakanin Japan da Najeriya kafin k**a hanyar Burazil inda zai dan dakata a Los Angeles din Amurka.

Shugaba Tinubu zai sauka a Brasilia babban birnin kasar Burazil a Amurka ta kudu don fara ziyarar aiki daga ranar 24 ga watan nan na Agusta.

Shugaban a wannan doguwar tafita na tare da tawaga da ta hada da ministan harkokin waje Yusuf Tuggar.



SOJOJIN ISRA’ILA SUN TAKARKARE GA RUWAN WUTA KAN GAZA GARI

Sojojin Isra’ila sun matsa kaimi ga rowan wuta kan Gaza Gari gabanin shirin mamaye garin gaba daya.

Wannan sabon babin na farmakin da Isra’ila ke yi kan Hamas a Gaza tsawon wata 23 na da zummar wargaza abun da Isra’ila ke dauka tungar karshe ta Hamas.

Cikin shirin akwai gaiyato sojoji 60,000 da ke jiran kota-kwana don cimma wannan burin na gwamnatin firaminista Benjamin Netanyahu.

Jagoran sojojin na Isra’ila Eyal Zamir ya ce sojojin su na aiki a wajen Gaza gari kuma za a tura wasu sojojin ma su tarar da wadanda ke farmakin.

Ba mamaki Isra’ila na ganin za ta kwato sauran k**ammun Isra’ilawa da ke hannun Hamas da hakan zai ba da dammar mamaye dukkan Gaza.

Abu ne mawuyaci Hamas ta daina wannan yakin matukar akwai ko da gomman mayakan ta ne da su ka saura a Gaza ko wajen Zirin.

19/08/2025

LABARUN DUNIYA

AMURKA TA JINJINAWA NAJERIYA DON CAFKE JAGORORIN KUNGIYAR TA’ADDANCI TA ANSARU

Kasar Amurka ta jinjinawa Najeriya don cafke kwamandojin kungiyar ta’addancin ANSARU biyu a ‘yan kwanakin nan.

Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya fitar da sanarwar yabon ta hanyar shafin sa na sandalin X.

Amurka ta ce wannan gagarumar nasara ce a fannin yaki da ta’addanci day a addabi Najeriya da sassan duniya.

In za a tuna mai ba wa shugaba Tinubu shawara kan tsaro Malam Nuhu Ribadu ya baiyana cafke mutanen biyu da su ka hada da Abu Bara’a da Malam Mamuda.

Anasaru da Boko Haram duk na da alaka da manyan kungiyoyin da a ke zargi da aiyukan ta’addanci a duniya.



KOTU TA YI WATSI DA BUKATAR WANI DAN NAJERIYA DA YA ARCE ZUWA KANADA DA NUNA BOKO HARAM SUN ADDABE SHI BAYAN SHIGA ADDININ KIRISTA

Kotu a kasar Kanada ta yi watsi da karar da wani dan Najeriya ya shigar don bukatar ba shi dama da iyalin sa ya samu mafaka a can da nuna ‘yan Boko Haram sun addabe shi biyo bayan riddar sa daga musulunci zuwa addinin kirista.

Dan Najeriyar Adeniyi Muftau Gbadamosi ya fice daga Najeriya a 2018 da matar sa Olabisi sai ‘ya’yan su biyu Olamilekan Malik da Olamiposi Shuaib.

A watan Disamba 2018 din ya shigar da takardun neman zama a Amurka amma ya gaza zuwa amsa tambayoyi don haka a 2019 ya shiga Kanada.

Gbadamosi ya ce sauya addinin sa ya sa Boko Haram su ka saka shi a gaba har su ka kasha kenwar gidan sad a kuma yunkurin sace dan sa.

Jami’I mai shigar da kara ya shawarci Gbadamosi yak aura zuwa Fatakwal jihar Ribas inda ke da karancin tasirin Boko Haram.

Mai shari’a Roger Lafreniere ya soki yanda Gbadamosi ya fara neman mafaka a Amurka kafin shigowa Kanada sai kuma rashin ganin dalili mai karfi na tsangwamar Boko Haram a kudancin Najeriya.

A nan Lafrenere ya yi watsi da bukatar Gbadamosi don haka za a iza keyar iyalin zuwa Najeriya indai ba wata kotun c eta dakatar da hakan ba.



SHUGABA TINUBU YA SAUKA A JAPAN DON TARON TATTALIN ARZIKI

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sauka a kasar Japan gabanin fara taron Tokyo na 9 na lamuran tattalin arzikin Afurka.

Za a gudanar da taron daga 20-22 a Facifico Yokohama kuma ya na samun halartar shugabannin Afurka.

Wannan taron na duniya na zama na hadin guiwa ne tsakanin Japan da Afurka da ma hukumar raya kasashe ta majalisar dinkin duniya.

Bayan k**ala taron, k**ar yanda sanarwa daga kakakin shugaban Bayo Onanuga ta baiyana, shugaba Tinubu zai zarce kasar Burazil.



MAJIYA TA NUNA HAMAS TA AMINCE DA YARJEJENIYAR TSAGAITA WUTA

Majiya ta ba da tabbacin cewa kungiyar Hamas mai mulkin Gaza ta amince da shirin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ta da Isra’ila.

Hamas da kawayen ta na gwagwarmaya da su ka hada da ISLAMIC JIHAD sun amince ba da bukatar gyare-gyare ba da aiwatar da sabuwar yarjejeniyar da masu shiga tsakani da su ka hada da Masar da Katar su ka tsara.

Yanzu dai za a yi sa ran sanar da lokacin da za a koma tattaunawa da Isra’ila a birnin Doha na kasar Katar.

Ba martini na nan take daga Isra’ila kan wannan bayani ta bangaren Hamas da sojojin Isra’ila ke son ganin bayan su.

Sabuwar yarjejeniyar na tsara tsagaita wuta na tsawon kwana 60 inda Hamas za ta sako k**ammun Isra’ila 10 da wasu gawawwaki.

A yakin da ya shiga wata na 23, Isra’ila ta kashe fiye da Falasdinawa 62,000 kuma akasari fararen hula ne.

LABARUN DUNIYA NAJERIYA TA RUTSA DA MANYAN ‘YAN TA’ADDA BIYU ABU BARA’A DA MALAM MAMUDANajeriya ta samu nasarar cafke wa...
17/08/2025

LABARUN DUNIYA

NAJERIYA TA RUTSA DA MANYAN ‘YAN TA’ADDA BIYU ABU BARA’A DA MALAM MAMUDA

Najeriya ta samu nasarar cafke wasu manyan wadanda a ke zargi da ta’addanci biyu da ke bakin littafin Amurka, Burtaniya har ma da majalisar dinkin duniya.

Babban mai ba wa shugaba Tinubu shawara kan tsaro Malam Nuhu Ribadu ya baiyana cewa mutanen biyu sun shafe shekaru su na addabar Najeriya da ta’addanci daga kungiyar nan ta ANSARU.

Mutanen biyu da a yanzu su ke tsare sun hada da Mahmud Muhammad Usman da a ka fi sani da Abu Bara’a da Mahmud Annajeriy da a ka fi sani da Malam Mamuda.

A na zargin Abu Bara’a da zama jagoran rundunonin ta’adda daban-daban, sace mutane, fashi da makami da samar da kudi don daukar nauyin ta’addanci.

Shi kuma Malam Mamuda na ta’addancin sa ne wajajen Kainji har zuwa jamhuriyar Benin kuma ya samu horon aiyukan ta’addanci daga Afurka ta arewa.

Kazalika an tabbatar da hannun mutanen biyu wajen fasa gidan yarin Kuje a Abuja a shekara ta 2022.



‘YAN BINDIGA SUN YI KISAN GILLA GA MA’AIKACIN KARAMAR HUKUMA A KATSINA

‘Yan bindiga sun yi kisan gilla ga daya daga ma’aikatan karamar hukumar Malumfashi a jihar Katsina.

Malumfashi na daga fitattun kananan hukumomi a jihar Katsina da ked a hada-hadar tattalin arziki.

Baya ga kisan gilla ga ma’aikacin mai suna Aminu OVER OVER, ‘yan bindigar sun sace tsohon mataimakin shugaban karamar hukumar Nasiru Dayi yayin da ya je gonar sa.

Bayanai sun nuna ba a daukar kwana biyu a yankin na Malumfashi ba tare da samun irin wannan akasin ba daga ‘yan bindigar.



MAJALISAR DOKOKIN JIHAR FILATO TA KI AMINCEWA DA KAURAR DA CIBIYAR HORARWA KAN LAMURAN MA’SANA’ANTU DAGA JOS

Majalisar dokokin jihar Filato ta ki amincewa da batun yiwuwar kaurar da cibiyar horarwa kan lamuran masana’antu daga Jos.

Duk da raderadi ne amma majalisar a zaman ta a tsohon gidan gwamnatin Filato da ke Rayfield a Jos, ta nuna damuwa ga wannan yanayi na barazanar kaurar da cibiyar.

Majalisar ta ce kaurarwar za ta shafi harkokin tattalin arziki da rasa aiyukan yi da ke tattare da cibiyar.

A nan majalisar ta bukaci gwamnatin jihar ta hada kai da gwamnatin taraiya ko ma’aikatar kasuwanci da masana’antu don janye batun.

Filato a arewa ta tsakiya na da masana’antu da harkokin tattalin arziki musamman a shekarun baya gabanin samun fitinar tsaro a jihar.



KASASHEN LARABAWA SUN YI WATSI DA FURUCIN NETANYAHU NA FADADA KASAR YAHUDAWA

Ministocin wajen kasashen Larabawa da ma wasu kasashen musulmi sun yi watsi da furucin firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu na fadada kasar Yahudawa zuwa sassan tan a tarihi wato tun zamanin Annabawa kenan.

Kasashen da su ka hada har da na Afurka k**ar Najeriya da Aljeriya sun yi gargadin wannan mataki ba zai haifar da alheri ba.

Sanarwar ta nuna shirin Isra’ila na mamaye yankunan Falasdinawa mummunan mataki ne da zai kara jefa Falasdinawa a ukuba.

Kazalika sanarwar ta nuna hushi kan yanda Isra’ila ke karantsaye ko biris da dokokin duniya da kaucewa yarjejeniyar 1967 da ta amince da kafa kasar Falasdinawa mai helkwata a gabashin birnin Kudus.

Zuwa yanzu sojojin Isra’ila sun kashe fiye da Falasdinawa 61,000 tun fara yakin Gaza na wannan karo daga ranar 7 ga Oktobar 2023.

14/08/2025

LABARUN DUNIYA

SHUGABA TINUBU ZAI FARA ZIYARAR AIKI DAGA ALHAMIS DIN NAN ZUWA JAPAN BA BURAZIL

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu zai fice daga Abuja a Alhamis din nan don ziyarar aiki zuwa Japan da Burazil.

A yayin wannan tafiya, shugaba Tinubu zai dakata a Dubai babbar Daular Larabawa kafin wucewa Japan don halartar taron Japan na 9 kan raya tattalin arzikin Afurka.

Baya ga taron na Japan, shugaba Tinubu zai gana da wasu kamfanonin Japan da ke da hannayen jari a Najeriya.

A sanarwa daga kakakin shugaban Bayo Onanuga, shugaba Tinubu a ranar Lahadi mai zuwa zai bar Japan don isa kasar Burazil bias gaiyatar shugaba Inacio Lula Da Silva.

A Burazil din, Tinubu zai tattauna kan lamuran huldar kasashen biyu da ganawa da ma’abota zuba jari.



DA ALAMU WIKE NA RIKE DA AKALAR PDP DA APC A RIBAS

Da alamu minsitan babban birnin taraiya Abuja Nyesom Wike na rike da akalar jam’iyyar PDP da APC a jihar sat a Ribas.

Wike wanda tsohon gwamnan Ribas ne amma a zaben 2023, ya mara baya ga shugaba Tinubu na APC ya barranta dad an takarar jam’iyyar sa ta PDP Atiku Abubakar.

A wajen kaddamar da kamfen na zaben kananan hukumomi a Ribas, shugaban PDP na jihar Aoron Chukwuemeka ya jinjinawa Wike a matsayin uban jam’iyyar maimakon dakataccen gwamna Siminalayi Fubara.

Shi ma shugaban APC na Ribas din Tony Okocha mukarrabin Nyesom Wike ne.

Hatta dakataccen shugaban majalisar dokokin jihar Martin Omawhule ya jagoranci dandazon ‘yan majalisar wajen rufawa Wike baya.

Gwamna Fubara dai a yanzu ya daidaita da Wike bayan mummunan sabani amma ba a san ko zai iya tasiri a sha’anin PDP ba.



TURKIYYA DA SIRIYA SUN GARGADI ISRA’ILA TA DAINA HARE-HARE KAN SIRIYA

Kasar Turkiyya da Siriya sun gargadi Isra’ila da ta daina kai hare-haren neman kara cinna wuta a Siriya da tuni yaki ya daidaita.

Ministan wajen Siriya wato Sham da takwaran san a Turkiyya ne su ka yi gardagin a taron manema labaru a birnin Ankara na Turkiyya.

Ministan wajen Turkiyya Hakan Fidan ya aza alhakin neman birkita Sham kan kasar Isra’ila da nuna ba za a lamunci hakan ba.

Kazalika Fidan ya kara jaddada matsayar kasar sa cewa ba za ta amince da turjiyar mayakan Kudawa na PKK da ke hada-hadar su a yankin arewa maso gabashin Sham din ba.

Fidan ya ce tamkar birkita kasar Siriya na daga abun da Isra’ila ke maida fifiko a kai da daukar hakan na da amfani ga tsaron Isra’ilar.

A cewar Fidan tun kawar da gwamnatin Bashar Al’Asad, Isra’ila c eta zama babbar mai kutse wajen hargitsa lamura a Sham.

Ministan wajen Sham Asaad Al-Shaibani ya ce Sham na fuskantar tsoma baki na kai tsaye da a kaikaice daga ketare da zummar kunna Karin fitina a kasar.

Al-Shaibani ya yi magana kan yankin masu bin addinin DRUZE da ke kudu maso yammacin Sham da nuna lallai hakkin Sham ne kawo salama a yankin don mallakar kasar Sham din ne.

Al-Shaibani ya kara da nuna shirin ladabtar da wadanda su ka haddasa fitina a yankin na Druze na mabiya wata darikar da ta samo asali daga Ibraniyanci masu imanin in an mutu a kan iya dawowa rayuwa a duniya.

Turkiyya na kan gaba a kasashen da su ka ba da gudunmwa wajen kawar da gwamnatin Damaskas ta Al’Asad inda jagoran mayakan Tahrir wato Ahmad Al-Sharaa ya zama mukaddashin shugaban kasar.



SABON HARIN ISRA’ILA A GAZA YA YI SANADIYYAR KISAN GILLA GA FALASDINAWA 123

Sabon harin da sojojin Isra’ila su ka kai kan Gaza ya yi sanadiyyar kisan gilla ga Falasdinawa 123 a Gaza.

Wannan dai ya zo ne gabanin shirin karbe Gaza da Isra’ila ke shirin yi don muradin murkushe duk wata gwagwarmaya ta Hamas.

Wannan kisa cikin sa’a 24 shi ne mafi muni a lokaci daya tun sabon yakin da ya barke kimanin shekaru 2 da su ka wuce da ya kawo tsanantar rayuwa ga mazauna Gaza miliyan 2.

A yayin da wannan ke faruwa, wakilan Hamas na ganawa da masu shiga tsakani na Masar don samun tsagaita wuta.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu na karfafa manufar da shugaban Amurka Donald Trump ya kawo na al’ummar Gaza su fice daga Zirin salun-alun.

Netanyahu ya ce duk kasashe masu maraba da karbar Falasdinawa su bude kofar su kawai don karbar Falasdinawan su kuma daina yi wa Isra’ila surutai.

Kasashen Larabawa da wasu da dama a shugabannin duniya na kin jinin duk wani shiri na kaurar da Falasdinawa daga kasar su ta gado.

Hatta gwamnatin Falasdinawa ta Mahmud Abbas a birnin Ramallah na daukar kawar da Falasdinawa a Gaza tamkar yakin da ya auku ne 1948 inda a ka tilastawa dubban Falasdinawa barin kasar su a arangamar da a ke yi wa taken NAKBA.

Majiya na nuna kwace Gaza zai faru a ‘yan makwanni in ba dai an samu cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ba, da ke samun cikas don sharadin Isra’ila na neman wargaza Hamas; inda ita kuma Hamas ta ce faufau hakan ba mai yiwuwa ba ne.

MARIGAYI SHUGABA BUHARI YA SHAIDA MIN ABUN DA YA FI WAHALAR DA SHI-SHEIKH ISA ALI PANTAMITsohon ministan sadarwa da tatt...
10/08/2025

MARIGAYI SHUGABA BUHARI YA SHAIDA MIN ABUN DA YA FI WAHALAR DA SHI-SHEIKH ISA ALI PANTAMI

Tsohon ministan sadarwa da tattalin arzikin fasahar zamani Farfesa Isa Ali Pantami ya baiyana cewa marigayi Janar Muhammadu Buhari ya shaida ma sa abun da ya fi zama kalubale a rayuwar sa.

Sheikh Pantami wanda ya ce a halin yanzu ya na ma rubuta littafin tarihin marigayin, ya na magana ne a lokacin karbar tambayoyin sakon ta’aziyya a Abuja.

Isa Pantami wanda ya yi aiki a matsayin dan majalisar zartarwa da ke alaka ta kud da kud da marigayin, ya ce ciwon hakori ne ya kai marigayi London amma a nan Allah ya yi ajali ya riske shi k**ar yanda ya ke kan dukkan talikai.

A nan malamin ya zaiyana irin baiwar da Allah ya yi wa marigayin tun daga tasowa a matsayin maraya zuwa rike muk**ai har shugaban mulkin soja ya na matashi har zuwa rasuwar sa a shekaru 82.

Sheikh Pantami ya kara nanata addu’ar neman rahama ga marigayin da sauran magabata da Allah ya yi wa rasuwa.

10/08/2025

LABARUN DUNIYA

EFCC TA CAFKE WANI DAN DAMFARAR YANAR GIZO DA KANANAN BINGIGOGI 2

Hukumar yaki da cin hanci ta Najeriya ta k**a wani dan damfarar yanar gizo rike da kananan bindigogi 2 a jihar Ogun.

Samamen ya auku ne a wani otal mai suna K-Hotel a karamar hukumar Ewekoro da ke jihar ta Ogun.

EFCC ta wallafa labarin ba tare da ambatar sunan dan damfarar ba, amma ta ce a samame ne kan wadanda a ka zargi da damfarar yanar gizo ta cafke shi tare da wasu mutum 55.

Baya ga bindigogi, EFCC ta ba da labarin samun motocin alfarma 6, wayoyin salula 86, na’urori masu kwakwalwa da dama da takardu.

EFCC ta ba da tabbacin duk wadanda a ke tuhumar za su gurfana gaban kotu bayan k**ala bincike.



MARIGAYI SHUGABA BUHARI YA SHAIDA MIN ABUN DA YA FI WAHALAR DA SHI-SHEIKH ISA ALI PANTAMI

Tsohon ministan sadarwa da tattalin arzikin fasahar zamani Farfesa Isa Ali Pantami ya baiyana cewa marigayi Janar Muhammadu Buhari ya shaida ma sa abun da ya fi zama kalubale a rayuwar sa.

Sheikh Pantami wanda ya ce a halin yanzu ya na ma rubuta littafin tarihin marigayin, ya na magana ne a lokacin karbar tambayoyin sakon ta’aziyya a Abuja.

Isa Pantami wanda ya yi aiki a matsayin dan majalisar zartarwa da ke alaka ta kud da kud da marigayin, ya ce ciwon hakori ne ya kai marigayi London amma a nan Allah ya yi ajali ya riske shi k**ar yanda ya ke kan dukkan talikai.

A nan malamin ya zaiyana irin baiwar da Allah ya yi wa marigayin tun daga tasowa a matsayin maraya zuwa rike muk**ai har shugaban mulkin soja ya na matashi har zuwa rasuwar sa a shekaru 82.

Sheikh Pantami ya kara nanata addu’ar neman rahama ga marigayin da sauran magabata da Allah ya yi wa rasuwa.



TSOHON MINISTAN NOMA AUDU OGBEH YA RIGA MU GIDAN GASKIYA

Tsohon ministan noma Audu Ogbeh ya riga mu gidan gaskiya ya na mai shekaru 78 a duniya.

Iyalin marigayin sun fitar da sanarwar labarin mutuwar Mr.Ogbeh da baiyana cewa za su sanar da lokacin da za a gudanar da jana’izar sa.

Ogbeh dan asalin jihar Binuwai, ya yi karatu a Faransa kuma ya shiga harkokin siyasa da har ya zama shugaban jam’iyyar PDP da ta yi mulkin Najeriya daga 1999-2015.

Dalilin rashin amincewa da neman tazarcen tsohon shugaba Obasanjo ya yi sanadiyyar murabus din Ogbeh daga shugabancin PDP a shekara ta 2005.

Ogbeh ya samu shiga sahun ministocin marigayi shugaba Buhari inda ya yi aiki a matsayin ministan noma kuma a nan ya zama dan jam’iyyar APC.



HARIN ISRA’ILA A GAZA YA YI SANADIYYAR MUTUWAR MUTUM 34

Rundunar tsaron lafiyar farar hula a Gaza ta baiyana cewa sabon harin da Isra’ila ta kai Zirin ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 34.

Kakakin rundunar Mahmud Bassal ya ce cikin wadanda harin ya kashe akwai mutum 9 da ke jiran karbar kayan agajin abinci a mashigar arewacin Gaza ta Zikim inda kuma harin ya raunata wasu mutum 181.

Fiye da mutum 12 da a ka kashe farar hula ne sannan wani harin a tsakiyar Gaza ya yi sanadiyyar kisa ga Falasdinawa 6 da raunata wasu mutum 30.

Kullum dubban mutane kan taru a wajen karbar kayan agaji inda 4 daga cikin su Amurka da Isra’ila ke kula da su.

Rundunar sojan Isra’ila kan ce ta na harbi ne don hana cunkoso amma hakan ya yi sanadiyyar kashe fiye da mutum 1000.

08/08/2025

LABARUN DUNIYA

SHUGABA TINUBU YA NADA SABON SHUGABAN HUKUMAR KULA DA WUTAR LANTARKI

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada sabon shugaba ga hukumar kula da lamuran wutar lantarki NERC.

Wanda a ka nadan Injiniya Abdullahi Garba Ramta matashi ne mai shekaru 39 kuma ya na da ilimi har na matakin dokta.

Kazalika shugaban ya nada sabbin kwamishoni biyu ga hukumar da kan kaiyade farashin wutar lantarki.

Sabbin kwamishinonin sun hada da Abubakar Yusuf da zai kula da sashen ma’abota amfani da wuta da kuma Dokta Fouad Olayinka Animashun da zai kula da sashen kudi da gudanarwa.

Gabanin samun tantancewa daga majalisa, shugaban hukumar na rikwan kwarya zai cigaba da aiki.



KEYAMOYA DAKATAR DA MAWAKIN FUJI AYINDE DAGA SHIGA JIRGI

Ministan jiragen sama Festus Keyamo ya dakatar da mawakin Fuji (wakar Yoruba) daga shiga jirage a Najeriya don rashin da’ar da ya nuna.

Mawakin Wasiu Ayinde Marshal ya nemi hana jirgin Valuejet tashi ne bayan an dakatar da shi daga shiga jerin yayin da ya ki yarda a duba kayan da ya rike a hannun sa da a ke ce barasa ce.

Ayinde mai shekaru 68 da a ka fi sani da Kwam 1 ya nemi shan gaban jirgin inda sai da jami’an tsaro su ka shiga tsakani.

Keyamo ya ba da umurnin a hana Kwam 1 shiga jirgi na gida ko ketare sai an kammala bincike.







MAJALISAR ZARTARWAR TSARON ISRA’ILA TA YANKE SHAWARAR KARBE IKON BIRNIN GAZA

Majalisar zartarwar lamuran tsaro ta Isra’ila ta yanke matsayar amshe iko da Garin Gaza wanda shi ne ya fi yawan jama’a a Zirin Gaza.

Wannan na daga matakan cigaba da yakin wata 22 da ya faro tun daga kutsawar Hamas cikin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktobar 2023.

Bisa alkaluman ma’aikatar lafiya ta Gaza, yakin dai zuwa yanzu ya yi sanadiyyar kashe fiye da Falasdinawa 61,000 da jefa Zirin cikin yunwa don tsananin karancin abinci inda mutane kan kanjame su mutu don rashin samun abinci na kwanaki.

Gabanin fara taron majalisar tsaron a jiya alhamis, Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce gwamnatin sa na son mamaye dukkan Gaza ta hanyar kwace Zirin inda za ta mika ragamar sa ga wasu dakarun Larabawa da ba sa ga-maciji da Hamas “mu na son karbe Gaza don tabbatar da tsaron mu, mu kawar da Hamas daga Zirin, mu ba wa al’umma aminci daga Gaza” Inji Netanyahu “mu na son mika Gaza ga sojojin Larabawa da za su mulki yankin yanda ya k**ata ba tare da yi ma na bazaraba ba; inda za su samawa Gazawa rayuwa mai kyau”

Wani Janar na sojan Isra’ila ya nuna fargabar karbe ikon Birnin Gaza ko daukacin Zirin zai jefa rayuwar kimanin k**ammun Isra’ilawa 20 da ke hannun Hamas cikin hatsari, hakanan zai kara wahalar da sojojin kasar da ke yaki na tsawon watanni.

‘Yan uwan k**ammun ma na adawa da wannan shirin na Netanyahu wanda har ya jawo zanga-zanga a gewayen dakin da a ke gudanar da taron na tsaro.

Ba a san adadin mutanen da ke zaune a Gaza-Gari ba tun da an sha umurtar jama’a su fice daga garin amma wasu sun dawo a lokacin da a ka samu tsagaita wuta da shirin ya wargaje inda Isra’ila ta cigaba da rowan boma-bomai kan sassan Gaza “ba sauran wajen da ba a mamye ba a Gaza, ai ba ma abun da ya saura na Gaza” inji Maysaa Al-Heila da ke zaune a sansanin gudun hijira.

Yankunan Gaza sun hada da Gaza-Gari, Jabalia, Khan Younis, Rafa, Deir al-Balah da Bait Hanoun.

Sojojin Isra’ila kan bude wuta kan masu taruwa don gwagwarmayar samun tallafin abinci inda ta kashe fiye da Falasdinawa 1000.

Batun taron tsagaita wuta a birnin Doha da Masar da Katar ke jagoranta tare das a hannun Amurka ya shiga tangal-tangal don rashin samun cimma sharadin Isra’ila na lallai Hamas ta wargaza mayakan ta.

Hamas dai t ace fau-fau ba za ta daina gwagwarmaya ba sai an kafa kasar Falasdinu mai babban birni a gabashin Birnin Kudus.



JIRGIN JODAN NA JEFO TALLAFIN ABINCI GA AL’UMMAR GAZA

Jirgin sama daga kasar Jodan ya cigaba da shawagi don jefa tallafin kayan abinci ga al’ummar Gaza daga cikin mawuyacin yanayi na yunwa.

Jirgin kan taso daga Jodan da ke makwabtaka ya bi samaniyar Gaza ya na jefa kayan tallafi a sassan da sun zama kangaye.

Dakatar da shigar da tallafi yankin na tsawon wata 9 da Isra’ila ta yi ya jawo yunwa ta addabi al’umma kuma hakan salon Isra’ila ne da zummar murkushe Hamas.

Jodan na hada kai da wasu kasashe wajen aikin jefa kayan agajin kuma a baya ma Sarki Abdullah da kan sa ya shiga jirgi don jefa kayan agajin.

07/08/2025

LABARUN DUNIYA

SHUGABA TINUBU YA YI TA’AZIYYA GA SHUGABAN GHANA BISA HATSARIN JIRGI DA YA YI SANADIYYAR MUTUWAR MINISTOCI A KASAR

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya mika sakon ta’aziyya ga shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama da al’ummar Ghana bisa hatsarin jirgi mai saukar angulu da ya yi sanadiyyar rasa ran ministoci biyu da wasu mutum 6.

Hatsarin na jirgin ya yi sanadiyyar mutuwar ministan tsaron Ghana Edward Omane Boamah da ministan muhalli Ibrahim Murtala Muhammed sai wasu mutum 6 da ba mu samu sunan su ba.

Ghana ta auka yanayi na makoki bisa wannan rashi ta hanyar wannan kaddara.

Shugaba Tinubu ya jajantawa iyalan marigayan da baiyana cewa gwamnatin sa da al’ummar Najeriya na taya al’ummar Ghana juyayi.



RUNDUNAR ‘YAN SANDA TA TSARE MAWALLAFIN JARIDAR SAHARA SOWORE

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tsare mawallafin jaridar yanar gizo ta Sahara Omoyele Sowore yayin da ya isa helkwatar rundunar don amsa gaiyatar bincike.

Sowore wanda kan jagoranci zanga-zanga a Abuja na kiran juyin juya hali, ya fuskanci tuhuma kan takardun bogi da kuma bata suna.

Da alamun sabuwar tuhumar da a ke yi wa madugun zanga-zangar ta kauda zargin yunkurin ingiza jama’a su tada tarzoma.

Gabanin amsa gaiyatar, Sowore ya caccaki sahihancin tuhumar da ma kururuta bukatar babban sufeton ‘yan sanda IGP Egbetokun ya yi murabus.

Wasu lauyoyi da kungiyar kare hakkin dan-adam ta Amnesty sun bukaci a sake Sowore ba da gindaya sharadi ba.





JIHAR KADUNA ZA TA GUDANAR DA RIGAKAFIN KYANDAR BIRI

Jihar Kaduna a arewa ta tsakiyar Najeriya ta sanar da shirin gudanar da allurer rigakafin kyadar biri da ta shafi kananan hukumomi da daman a jihar.

Jami’in ilmantarwa na hukumar kula da lafiya matakin farko na jihar Isa Yusha’u ya baiyana shirin a taron masu ruwa da tsaki.

Yushau ya ce annobar ta shafi kananan hukumomi da dama na jihar don haka za a gudanar da rigakafin da zummar hana bazuwa cutar zuwa wasu yankunan.

Hukumar kula da lafiya ta kasa a rahaoton da a ka ruwaito daga Isa Yusha’u ta amince da rigakafin don tabbatar da kula da lafiyar al’ummar jihar.



ISRA’ILA TA HARAMATAWA MUFTIN BIRNIN KUDUS SHIGA MASALLACIN BAITUL MUKADDAS

Hukumomin Isra’ila sun haramtawa babban mufi na birnin Kudus da yankunan Falasdinawa Sheikh Muhammad Hussein shiga masallacin AQSA baitul mukaddas na tsawon wata 6.

Matakin ya biyo bayan wata hudubar da ya gabatar da ta nuna takaici ga matakan cusa yunwa ga al’ummar Gaza.

Gabanin wannan matakin, a karshen watan jiya hukumomin na Isra’ila sun gaiyaci Sheikh Hussein bayan wata hudubar;c su ka haramta ma sa shiga masallacin na tsawon kwana 8 da kuma yiwuwar tsawaita haramcin.

Gwamnatin Falasdinawa a birnin Ramallah karkashin shugaba Mahmud Abbas ta yi Allah wadai da wannan matakin.

Ma’aikatar harkokin addini ta Falasdinawa ta ce hakan shiri ne na Isra’ila na cigaba da mamaye birnin Kudus, Zirin Gaza da ma yankunan yammacin kogin Jodan da kakkabe hannun ma’abota addini daga masallacin na Al’aqsa.

Wannan na zuwa daidai lokacin da sojojin Isra’ila kan bude wuta kan sashen masu taruwa don karbar kayan agaji a Gaza da kan jawo asarar rayuka.

05/08/2025

LABARUN DUNIYA

KOTU TA BA DA UMURNIN KARBE MOTOCIN ALFARMA DA KUDI NA DAN DAMFARA ONORIEDE

Babbar kotun taraiya da Ikoyi Lagos ta ba da umurnin karbe motocin alfarma da a ka samu a hannun wani dan damfara mai suna German Daniel Onoriede.

Kotun ta yanke hukuncin ne biyo bayan shigar da kara da hukumar yaki da cin hanci EFCC ta yi kan wanda a ke cigaba da tuhuma kan wasu laifuka.

Kazalika kotun ta ba da umurnin rike kudi na wucin gadi daga hannun Onoriede da su ka hada da dala 20,000 da CFA 110,000 da wata mota kirar NISSAN.

Hukumar EFCC ta kai samame a 2023 anguwar Lekki da ke Lagos inda ta samu motocin alfarmar guda biyu da su ka hada da Bentley Coupe.

EFCC ta gamsar da kotu cewa Onoriede ya sayo motocin ne da kudin damfara kuma ya na da ma’ajiyun banki da daman a Naira da Dala da ya kai ga samun Naira miliyan 500 daga 2018-2023.



BADEGGI YA BA DA HAKURI GA GOMNA BAGO BISA TAKADDAMAR RUFE GIDAN REDIYON SA NA BADEGGI

Shugaban gidan rediyon Badeggi FM da ke Minna Jihar Neja Alhaji Shu’aibu Badeggi ya nemi gomna Umar Bago ya yi hakuri kan takaddamar da ta jawo gommnan ya nemi rufe ofishin gidan rediyon.

Badeggi wanda tsohon jami’in gwamnati ne a jihar Neja, ya ce bai san takamemmen laifin da su ka aikata ba amma ya kawo misalan labarun da ya ce sun hada kan shan ruwa da ka iya kawo amai da gudawa, ba wa ‘yan siyasa dama su fadai ra’ayin su da labarun da su ka shafi tsaro.

A zantawar sa da dan jarida Mustapha Nasiru Batsari a Minna, Badeggi ya ce rediyon na cigaba da aiki duk da an shafa banki na maki a jikin dakin wucin gadi da su ke yada shirye-shirye a harabar gidan talabijin na NTA a Minna kuma hayar filin su ka dauka.

Tun farko ministan labaru Muhammad Idris Malagi ya bukaci kwantar da hankali da nuna hukumar kula da gidajen rediyo da talabijin NBC ke da hurumin kan wannan lamarin.



A NA FARGABAR KASHE MUTUM 11 DA SACE WASU A JIHAR ZAMFARA

A na fargabar kashe kimanin mutum 11 da sace wasu a yayin harin barayin daji a yankin karamar hukumar Bakura da ke jihar Zamfara.

Rahotanni sun baiyana isowar ‘yan bindigar su na harbin kan mai uwa da wabi inda baya ga kisa sun kuma sace wasu mutanen.

Yankin na jikin babban dajin Gundumi da ke zama mafakar manyan ‘yan ta’adda da ke addabar jihar Zamfara da ma wasu jihohin arewa maso yamma.

Jami’an tsaro sun sha arangama da ‘yan ta’addan inda a ka samu sauki musamman lafiyar hanyar Abuja zuwa Kaduna da dajin Birnin Gwari.



KIMANIN FALASDINAWA 40 SUN RASA RAN SU A GAZA

Kimanin Falasdinawa 40 sun rasa ran su a Gaza ciki da 10 da ke kokarin karbar kayan agaji a cibiyar da Amurka ke jagoranta wajen raba kayan tallafi.

Wasu mutum 5 ma sun mutu don tsananin yunwa a yayin da karancin abinci ke adabbar mazauna Zirin.

Kazalika sojan Isra’ila sun kashe wasu Falasdinawa kimanin 13 da su ka taru a mashigar Zikim ta shiga arewacin Gaza inda a ke raba kayan agaji.

Mutane kan yi nasarar karbar buhun fulawa bayan gwagwarmayar ko kuma su dawo a kan makara don rasa rai.

Falasdinawa kan taru don zaman makoki a asibitin Al-Shifa inda a kan kawo wadanda su ka samu raunuka da gawawwaki.

Majalisar dinkin duniya ta ce fiye da Falasdinawa 1000 su ka rasa rai a yunkurin karabar kayan abinci na agaji.

Address

Utako District, Abuja Nigeria
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Manara RADIO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Manara RADIO:

Share

Category