11/06/2026
LABARUN DUNIYA
GWAMNATIN NAJERIYA NA KARA DAUKAR MATAKAN KARIYA DAGA CUTAR EBOLA
Gwamnatin Najeriya na kara daukar matakan hana shigowar cutar Ebola daga wasu kasashen Afurka da cutar ta bulla.
Cikin matakan har da kwamiti na musamman da shugaba Tinubu ya kafa don daukar matakan kariya daga cutar inda tuni shugaban ya ware Naira biliyan 10 don wannan aiki.
Shugaban ma’aikata na fadar A*o Rock Femi Gbajabiamila shi ne shugaban kwamitin inda masu ruwa da tsaki k**ar hukumar shige da fice, hukumar kula da filayen jirage da ma’aikatar cikin gida ke da wakilici.
Matakin karin azama ne ga cibiyar yaki da bazuwar cutuka NCDC don zuba ido kan duk fasinjoji masu shigowa Najeriya da duba yanayin jikinsu kafin wucewa cikin kasa.
An ba da umurnin zuba ido musamman ga jiragen Kenya, Ethiopia don cutar ta bayyana a kasar Dimokradiyyar Kongo da Uganda da ke makwabtaka da juna.
Hakanan za a ware sassa na killace duk wanda a ka samu da alamun cutar a filin saukar jiragen sama na Lagos da Abuja.
SHUGABA TINUBU YA JINJINAWA JAGORNACIN FIRAMINISTAN INDIYA NARENDRA MODI
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yabawa jagorancin firaministan Indiya Narendra Modi don yadda ya ke jagorantar daya daga fitattun kasashen Asiya na tsawon shekaru.
Modi dai a yanzu ya zama mafi samun damar tsawon jagoranci a tsakanin wadanda su ka rike kujerar firaminista a Indiya bayan samun nasarar zabe a wa’adi uku.
A sanarwa daga kakakin shugaba Tinubu Bayo Onanuga, shugaban ya ce hakika Modi ya karfafa dangantakar Najeriya da Indiya ta fannin diflomasiyya.
Bola Tinubu ya zayyana Modi a matsayin abokin Najeriya ya na mai taya shi murnar nasara a madadin dukkan ‘yan Najeriya.
Modi dai na daga shugabannin da ke rike da mukamin babban kwamanda na Najeriya wato CCON da ke zama lamba ta biyu mafi daraja bayan GCFR.
WATA GOBARA TA K**A WANI SASHEN NA MAJALISAR DATTAWAN NAJERIYA
An samu wata gobara da ta k**a wani sashe na dakunan tarukan majalisar dattawan Najeriya.
Gobarar ta taso ne bayan kammala zaman kwamitin hukumar kula da yankin Neja Delta inda ya tantance Zainab Marwa a matsayin memba ta hukumar mai wakiltar Arewa maso gabar.
An fahimci cewa wutar ta auku ne daga dakin cin abinci na dakin taro na 107 daga na’urar dumama abinci MICROWAVE da a ka bari ba tare da kula ba.
Wadanda su ka wajen sun yi gaggawar tafiya tudun tsira yayin da hayaki ya turnuka dakin kuma na samu shawo kan wutar gabanin fantsama zuwa wasu sassa.
An tabbatar ba a samu raunuka ba kuma ba a samu salwantar wata takarda ko wani abu ba a sanadiyyar gobarar.
A ALHAMIS DIN NAN MAJALISAR WAKILAN NAJERIYA ZA TA KADA KURI’A KAN RUNDUNAR ‘YAN SANDAN JIHA
A Alhamis din nan majalisar wakilan Najeriya za ta kada kuri’a don duba amincewa da gyaran dokar kafa rundunar ‘yan sandan jiha.
Mataimakin kakakin majalisar Ben Kalu da ‘yan majalisa 14 ke daukar nauyin kudurin kuma su ka nuna kwarin guiwar samun nasara.
An ruwaito Kalu na nuna ba mai dakatar da wannan kuduri kuma an yi hakan ne don inganta tsaro.
Masu daukar nauyin kudurin sun nuna kasa cimma nasarar dakile ‘yan ta’adda da sauran miyagun iri ya sa muhimmancin neman kafa rundunar ‘yan sanda ta matakin jihohi.
Gwamnatin shugaba Tinubu na mara baya ga kafa wannan runduna don karfafa harkokin tsaro daga yawan satar mutane da ta’addanci da ke ta’azzara.
IRAN TA AYYANA RUFE MASHIGAR RUWA TA HORMUZ
Kasar Iran ta ayyana rufe mashigar ruwan teku ta Hormuz mai muhimmanci ga sufurin danyen man fetur.
Wannan na zuwa ne bayan Amurka ta kai hare-hare cikin Iran da hakan ya illata yarjejeniyar tsagaita wuta a yakin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran.
Tuni Iran ta ce ta kai farmaki bugun jiragen dakon mai biyu da su ka yi yunkurin wucewa ta mashigar.
Iran ta ce mashigar Hormuz za ta cigaba da kasancewa a rufe ruff har wani lokaci ta na mai gargadi kar kowace kasa a yankin ta sako jirgi ya nemi wucewa don zai fuskanci matakin farmaki.
Shugaba Trump dai dama ya yi alwashin kai farmaki mai zafi kan Iran da hakan kuwa ya kawo babbar tangarda ga tsagaita wuta.