Manara RADIO

Manara RADIO Radio channel that sheds light to listeners in Africa,Middle East and across the globe, predominantly "HAUSA" on Islamic tenets and civilization

12/05/2026

LABARUN DUNIYA

SHUGABA TINUBU YA SAUKA A NAIROBI KENYA DON TARON BUNKASA AFURKA

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sauka a babban birnin kasar Kenya, Nairobi don halartar taron bunkasa Afurka.
Taron dai mai taken FORWARD AFRICA a turance na da zummar tattaunawa kan hanyoyin bunkasa tattalin arzikin nahiyar Afurka ne.
Shugaban Kenya Williams Ruto da shugaban Faransa Emmanuel Macron ne za su jagoranci taron.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai yI amfani da damar wajen wasu zantawa da masu ruwa da tsaki na kasashe don nausa diflomasiyyar Najeriya gaba.
Ministoci da su ka hada da ta kasashen waje Bianca Ojukwu, na aikin noma Abubakar Kyari da na tattalin arzikin teku Adegboyega Oyetola na cikin tawagar shugaban.
Shugaba Tinubu dai ya isa Kenya daga ziyarar aiki da ya ke yI a kasashe uku kuma ciki da Faransa.

SHUGABA TINUBU YA NADA FAMADEWA A MATSAYIN MAI BA DA SHAWARA NA MUSAMMAN KAN TSARON CIKIN GIDA

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada Manjo Janar Adeyinka Famadewa mai ritaya a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida.
Wannan na kunshe a sanarwa daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya Mr.George Akume.
Sanarwar ta bayyana Famadewa a matsayin kwararre kan harkokin tsaro kuma ya ma yI aiki a matsayin shugaban ma'aikata na ofishin babban mai ba da shawara na kasa kan harkokin tsaro daga 2015-2021.
Shugaba Tinubu ya nuna amanna Famadewa zai yI amfani da kwarewarsa wajen inganta tsaro na cikin gida da aiki tare tsakanin sassan tsaro.
Sanarwar ba ta fayyace bambancin aikin Famadewa da na babban mai ba da shawara na kasa kan tsaro Malam Nuhu Ribadu ba.
Daga nazartar sanarwar Malam Nuhu Ribadu na da ayyuka mabambanta fiye da tsaron cikin gida don ya na taja muhimmiyar rawa da kasashen duniya kan inganta dangantakar diflomasiyyar tsaro da kasashe irin Amurka, nan Afurka da hulda da kasashen Larabawa.

PA FASIRABTI YA CIKA SHEKARU 100 A DUNIYA

Dattijon siyasar kasashen Yarbawa Pa Reuben Fasoranti ya cika shekaru 100 a duniya.
Shugaba Tinubu ya taya Fasoranti murnar cika shekaru 100 a duniya da gode ma sa bisa goyon baya da ya ke ba shi.
Pa Fasoranti na daga dattawa kalilan da su ka rage a mukarraban uban siyasar Yarbawa Chief Obafemi Awolowo.
Fasoranti jagora ne a kungiyar nan ta kare muradun Yarbawa wato Afenifere kuma ya yI jam'iyyar AG a jamhuriya ta farko sai UPN a jamhuriya ta biyu.
Dattijon ya yI digiri a harshen turanci da nazarin taswirsr duniya a jami'ar Badun inda ya zurfafa ilimi a Burtaniya da Australia.

TRUMP YA YI ALWASHIN MATSIN LAMBA KAN MASHIGAR HORMUZ

Shugaban Amurka Donald Trump ya yI alwashin cigaba da daukar matakan bude mashigar ruwan Hormuz don safarin jiragen dakon man fetur.
Wannan dai ya biyo bayan tangarda a yarjejeniyar neman sulhun dakatar da yaki kan Iran da ya kai mako na 10.
Trump ya bullo da salon rakiyar jiragen dakon mai don wuxewa ta Hormuz amma daga bisani sa'a 48 ya janye don bude babin diflomasiyya.
Trump ya ce Iran ba za ta iys farfado da shirinta na nukiliya ita kadai ba kuma ya na da yakinin za ta mika wuya a karshe.
A bangaren Iran da ke cigaba da rude mashigar Hormuz don tilasta Amurka ta janye tare ma ta hanyar wucewar jiragen ruwa, ta bukaci diyya ga barnar da a a ka yI ma ta a sanadiyyar wannan yaki da Amurka da Isra'ila su ka auka ma ta.
Rufe mashigar Hormuz ta haddasa dan karen tsadar man fetur a duniya

07/05/2026

LABARUN DUNIYA

GWAMNATIN NAJERIYA TA CE TA K**A HANYAR SAMAR DA JARIN DALA TIRILIYAN DAYA

Gwamnatin Najeriya ta ce ta dau matakan samar da jarin tattalin arziki da zai kai dala tiriliyan daya zuwa shekara ta 2030.
Wannan na kunshe ne a taron da shugaba Tinubu ya gudanar a birnin Paris na Faransa da cibiyoyin zuba jari.
Shugaba Tinubu ya bar Najeriya a farkon mako ya shiga tafiyar aiki ta kasashe 3.
Ministan kudi Taiwo Oyedele da ke wajen taron ya bayyana cewa a bara kadai Najeriya ta samu wadatar tattalin arziki da ya kai kashi 11.2% a bangaren dala kadai a shekarar bara.
Kamfanonin zuba jarin sun hada da CITIBANK da wasu cibiyoyi na Faransa, Burtaniya da Afurka ta kudu.

NAJERIYA TA SHIGA YARJEJENIYA DA KAMFANONIN SIN DON GYARA MATATUN FETUR

Kamfanin fetur na Najeriya ya sanya hannu kan yarjejeniyar gyara matatun man fetur don kaucewa cigaba da shigo da fetur din daga ketare.
Wannan dai ya biyo bayan matsala da a ka samu a baya ta fitar da kudi dala biliyan 2.39 amma ba tare da samun nasarar gyaran matatun ba.
Sabuwar yarjejeniyar da kamfanonin kasar Sin guda biyu za ta shafi gyara matatun fetur na gwamnati da ke Warri, Fatakwal da kuma Kaduna.
Hakika hakan in ya samu nasara zai taimaka wajen rage dan karen tsadar man fetur da ke da nasaba da tashin farashin gangar fetur a kasuwar duniya.
Matatar man fetur ta 'yan kasuwa ta Dangote da ke Lagos ka iya taimkawa ne wajen wadatar fetur din a cikin kasa ko da ya na samuwa da tsadar gaske.
Masana na nuna a kan samu kafar angulu kan yunkurin irin wadannan gyare -gyare daga 'yan jari hujja da ke kasuwancin fetur.

APC TA AMINCE KAI TSAYE DA TAKARAR TAZARCE TA SHUGABA TINUBU A ZABEN 2027

Jam'iyyar APC ta amince da takarar shugaba Tinubu ta neman tazarce a zaben 2027 ba tare da zaman tantancewa ba.
Wannan ya biyo baysn taron shugabannin gudanarwa na jam'iyyar karkashin Nantawe Yilwatda a Abuja.
Sanarwa daga sakataren labarun jam'iyyar Felix Morka ta bayyana crwa dama APC ta amince da takarar don haka ba wata riba sai shugaba Tinubu ya bayyana gaban kwamitin tantancewa don amsa tambayoyi da bitar takardunsa.
Duk da haka APC za ta yI babban taro don tabbatar da amincewa da takarar ta shugaba Tinubu ba da fuskantar zaben fidda gwani ba.
Morka ya ce hakan na daga kare muradun jam'iyyar ne don dama shugaba Tinubu ya samu gagarumin goyon bayan sake takarar.

TRUMP YA CE IRAN NA DA NIYYAR YARJEJENIYAR DAKATAR DA YAKI

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Iran ta na da niyyar amincewa da yarjejeniyar dakatar da yakin da Amurkar da Isra'ila ke yI da ita.
Trump na magana ne da manema labaru a fadar WHITE HOUSE ya tabbatar da hakan da ya zama gusawa daga matsayarsa ta shafin sa na yanar gizo TRUTH SOCIAL inda ya nuna sanyin guiwa.
Majiya ta shaidawa kamfanin dillancin labarun Iran cewa ta na bitar yarjejeniyar don samun maslaha daga yakin da ya fara daga ranar 28 ga Febrairu.
Yarjejeniyar dai za ta gudana kenan duk da ba a cimma batun bude mashigar ruwan Hormuz da dakatar da shirin kera mak**an kare dangi na Iran ba.
Amurka dai za ta janye takunkuman da ta azawa Iran da ke gurgunta tattalin arziki.

05/05/2026

LABARUN DUNIYA

APC TA TSAWAITA WA’ADIN SAYAR DA FOM DIN TAKARAR ZABEN 2027

Jam’iyyar APC mai mulki ta tsawaita wa’adin sayar da fom din neman tsayawa takara don ba da karin dama ga masu son takarar su samu sayan fom din.

Sanarwa daga sakataren yada labaru na jam’iyyar Felix Morka ta bayyana cewa jam’iyyar ta tsawaita wa’adin zuwa karshen ranar Larabar nan.

Kazalika sai kuma cikewa da dawowa da fom ga jam’iyya zai kammala a karshen ranar Alhamis din nan 7 ga watan nan na Mayu 2026.

Daga Jumma’ar nan kuma za a shiga kammala aikin tantance sunayen masu niyyar takara har zuwa ranar Talata mai zuwa.

Sanarwar ta Morka ta kare da cewa za a wallafa sunayen duk masu neman takarar da a ka tantance a ranar Laraba ta makon gobe.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da a wasu jihohi wasu daga wadanda su ka sayi fom ke korafin ba a bi dukkan ka’idar da ta dace wajen fidda sunayen ‘yan takara musamman na gomna ba.

Wadanda ke korafin sun shafi wasu jihohin da gomnonin da ke kammala wa’adi su ka daga hannun wadanda su ke son su gaje su a kujera.



A NA TA SAMUN RADERADIN WASU MANYAN ‘YAN ADAWA ZA SU SAKE CANJA JAM’IYYA DAGA ADC ZUWA NDC

A na cigaba da samun alamu ko raderadin wasu manyan ‘yan adawa na shirin sauya sheka daga hadakar adawar wato jam’iyyar ADC zuwa sabuwar jam’iyyar NDC.

Wannan dai duk da nasarar da sashen David Mark ya samu a hukuncin kotun koli na jan ragamar jam’iyyar ADC da komawa cigaba da shari’a a babbar kotun tarayya.

Tsohon gomnan jihar Bayelsa Seriake Dicson ke zama uban jam’iyyar NDC wacce tuni wasu ‘yan adawa su ka shige cikinta don samun takarar 2027.

Ba mamaki hada manyan ‘yan takara a inuwa daya na zama kalubale ga bangaren adawa a Najeriya inda manyan ‘yan siyasa ba sa sha’awar kaucewa don ba da dama ga mafi cancanta a cikinsu.

ADC dai ta tara manyan ‘yan takara da su ka tsaya zaben 2023 da shugaba Bola Tinubu amma daga inuwar jam’iyyu daban da su ka hada da Atiku Abubakar a PDP, Peter Obi a Leba sai Rabiu Musa Kwankwaso a NNPP.

Wani dalilin ka iya zama har yanzu akwai rashin tabbas na yiwuwar karewar shari’a da sak**akon da zai goyi bayan takarar ‘yan adawar.



NAJERIYA TA BUKACI BINCIKEN GASKIYA NA YADDA JAMI’AN AFURKA TA KUDU SU KA KASHE ‘YAN NAJERIYA BIYU BISA KIN JINI

Gwamnatin Najeriya ta bukaci lallai Afurka ta kudu ta yi bincike da fidda rahoton gaskiya kan yadda jami’an tsaronta su ka kashe ‘yan Najeriya biyu a sanadiyyar hare-haren kin jinin baki.

In za a tuna mun baku labarin kisa ga ‘yan Najeriya biyu a Afurka ta kudu da su ka hada da Ekpenyong Andrew da Ananamiro Emmanuel.

Ministar harkokin wajen Najeriya Bianca Ojukwu ta kira jakadan Afurka ta kudu inda ta jaddada wannan bukata daga kuma a ka samu ganawa ta musamman da jami’in ma’aikatar da ofishin jakadancin Afurka ta kudu.

A nan Najeriya ta fito da faya-fayan bidiyo da ke nuna yadda a ke kai hare-haren kin jinin baki ‘yan Afurka bakake a Afurka ta kudu.

Ma’aikatar wajen ta nemi a fito da bayanan binciken fili gare ta da ‘yan uwan wadanda a ka kashe da kuma duk matakan shari’a kan kisan.

Ba wani sabon abu ba ne kisa da lalata dukiyar baki kuma bakaken fata a Afurka ta kudu don kin jinin baki sun yi arziki a kasar da su ke bakunta fiye da ‘yan kasa.



AN GUDANAR DA JANA’IZAR SHAHARARREN DAN JARIDA SALEH SHEHU ASHAKA A BIRNIN ALKAHIRA

An gudanar da jana’izar shahararren dan jarida Saleh Shehu Ashaka wanda ya rasu bayan fama da jinya a birnin Alkahira na kasar Masar.

Saleh Ashaka wanda ya yi aiki na kimanin shekaru 12 da Muryar Amurka VOA, ya kuma kasance marubuci na darussan tattalin arziki, yaki da cin hanci da samar da gwamnati mai adalci da a kan wallafa a manyan jaridu.

Marigayin matashi da a ka haifa a 1983 a Jos din jihar Filato, ya zabi aikin jarida fiye da sauran ayyuka a rayuwa kuma ya shahara inda wasu manyan kafafen duniya irin Aljazereera da CNN kan nemi gudunmawarsa.

Saleh Ashaka ya shaidawa mahaifiyarsa Hajiya Hauwa Tafisu wasiyyar yi ma sa jana’iza a inda ya rasu kuma hakan ya kasance.

A na cigaba da gabatar da ta’aziyya da addu’oi ga marigayin kuma shafukan sada zumunta sun cika da bayanan juyayin rashin Saleh Ashaka.

30/04/2026

LABARUN DUNIYA

SHUGABA TINUBU YA NADA BIANCA OJUKWU A MATSAYIN MINISTAR HARKOKIN WAJE

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada Bianca Ojukwu a mtsayin babbar minister harkokin waje.

Wannan na kunshe ne a sanarwa daga kakakin shugaban Bayo Onanuga da ta tabbatar da nadin uwargidan marigayi madugun ‘yan awaren Biyafara da a ka yi wa ahuwa Odumegwu Ojukwu.

Dama Bianca Ojukwu ce karamar minista ma’aikatar gabanin daga darajar mukaminta da ya biyo bayan murabus din tsohon ministan ma’aikatan Yusuf Tuggar wanda ya tafi Bauchi don shiga takarar gwamna.

Kazalika shugaban ya kawo sunan Sola Enikanolaiye don zama karamin ministan harkokin wajen.

Enikanolaiye dai daga jihar Kogi ya rike mukamin mai taimakawa shugaba Tinubu na musamman kan harkokin waje.

Yanzu za a jira majalisar dattawa ta tantance sabbin ministocin biyu don fara aiki a sabbin muk**an.



RUNDUNAR ‘YAN SANDA TA KORI DAN SANDA DA MUKARRABANSA DA SU KA BUDE WUTA KAN WANI FARIN HULA DAURE DA ANKWA A DELTA

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da kora daga aiki ga mataimakin sufuritandan ‘yan sanda Nuhu Usman da mukarrabansa da a ka dauka a faifan bidiyo su na bude wuta kan wani matashi a jihar Delta.

Faifan bidiyon ya nuna yadda ‘yan sandan su ka kashe matashin wanda ke daure da ankwa a hannunsa.

Kakakin rundunar ‘yan sanda Anthony Okon ya tabbatar da umurnin babban sufeton ‘yan sanda Tunde Disu na korar ‘yan sandan don aikata kisan gilla da su ka yi da ya keta hurumin dokokin aikin ‘yan sanda.

Rahotanni sun gano sunan matashin da a ka yi sanadiyyar mutuwar ta sa da Mene Ogidi mai shekaru 28 kuma dan asalin jihar Delta.

Tun farko an kamo Nuhu Usman da mukarrabansa a ka kawo su Abuja sashen ladabtarwa inda bayan korar daga aiki kuma za a gurfanar da su gaban kotu.

Ba a fito da dalilan k**a matashin da daura ma sa ankwa har ya kai ga harbe shi ba.



GWAMNA ZULUM YA MARA BAYA GA MUSTAPHA GUBIO YA GAJE SHI A MUKAMIN GWAMNA

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya mara baya ga tsohon kwamishinansa na ayyuka Mustapha Gubio ya gaje shi a kujerar gwamna.

Zulum ya tabbatar da mara baya ga Gubio, bayan Gubiyon ya dawo daga sayan fom din takarar gwamnan a ofishin APC a Abuja.

Hakika Gubio ne ya zama kwamishinan ayyuka na Zulum da ya kula da gine-ginen da Zulum din ya aiwatar a jihar ta Borno.

Hakika wannan ba zai zama kai tsaye da mara bayan mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ba wanda shi ne maigidan gwamna Zulum kuma ya mara ma sa baya a zaben 2019 don zama gwamna.

Za a jira a ga yadda ko da amincewar Kashim ko kuwa Zulum ya yi gaban kansa ne a tsarin siyasa ko mulkin gado na jihar Borno.

A jihar Yobe ma an ga hoton gwamna Mai Mala Buni da tsohon gwamna Ibrahim Geidam na daga hannun sakataren gwamnatin jihar Baba Malam Wali don takarar 2027.

Har yanzu magoya bayan masu niyyar takara irin na tsohon shugaban majalisar dattawa Ahmed Lawan da na Sanata Ibrahim Bomai na nuna akwai sauran fata da su ke da ita ta samun takara.



SHUGABAN LEBANON AOUN YA CE LALLAI ISRA’ILA TA DAKATAR DA BUDE WUTA GABANIN FARA TATTAUNAWA

Shugaban Lebanon Mr.Joseph Aoun ya ce lallai Isra’ila ta dakatar da kai hare-hare cikin Lebanon gaba daya, gabanin amincewa da tattaunawar kai tsaye da ita.

Wannan na kunshe a sanarwa daga fadar gwamnatin Lebanon a birnin Beirut da ke nuna damuwar Aoun kan yadda Isra’ila ke cigaba da kawo hari kan Lebanon.

Hakanan Aoun ya ce Lebanon na jiran Amurka ta sanya lokacin fara tattaunawa don samun maslaha da Isra’ila.

Hakika Isra’ila na cigaba da kai farmaki kan abun da ta zayyana sassa na kungiyar Hezbollah da Iran ke marawa baya.

Wani harin Isra’ila a garin Bint Jbeil a kudancin Lebanon ya yi sanadiyyar mutuwar sojan gwamnatin Lebanon dad an uwansa wadanda ke tafiya kan babur don dawowa gida daga bakin aiki.

Kawai a nan Isra’ila ta ce za ta bincika lamarin.

28/04/2026

LABARUN DUNIYA

GWAMNATIN NAJERIYA TA AYYANA KARIN ALAWUS GA MA'AIKATA DON RAGE RADADI



Gwamnatin Najeriya ta ayyana karawa ma'aikata kudin alawus don rage mu su radadin tsadar rayuwa.

Matakan nan na gwamnatin Tinubu sun biyo bayan hauhauwar farashin kayan masarufi don yadda canjin kidu ya yI tsada ga kuma kara tashin farashin litar fetur a sanadiyyar yakin da Amurka da Israila su ka aukawa Iran.

Kudin na alawus sun shafi ayyuka na musamman da ma'aikata ke yi waje da asalin hakkin aiki na samun albashi.

Duk da ma'aikata za su yi farin ciki kan matakin amma ba mamaki hakan ya tada batun karin mafi karancin albashi.



APC TA CACCAKI GWAMNA MAKINDE KAN KALAMAI ZAFAFA NA ZARGIN MAIDA NAJERIYA MAI BIN JAM'IYYA DAYA



Jam'iyyar APC ta caccaki gwamnan jihar Oyo Seyi Makinde da kalaman tunzura fitina kan zargin maida Najeriya mai bin jam'iyya daya.

Makinde dau na magana a birnin Badun lokacin taron fashin baki na hadakar 'yan adawa ta ADC.

Makinde wanda shi kadai ya rage a gwamnonin jam'iyyar adawa ta PDP, ya zargi gwamnatin Tinubu da murkushe 'yan adawa ko maida Najeriya ta zama karkashin mulkin jam'iyya daya.

Sakataren labarun APC Felix Morka ya nuna Sam bai k**ata mai rike da kujerar gwamna ya zama da kalamai na neman tada tarzoma ba.

Morka ya ce bai dace Makinde ya zama ya na rike da kujerar gwamna ba alhali ya na furta kalamai ba takatsantsan.

A nan Morka ya bukaci jami'an tsaro su zuba ido kan Makinde, ya na mai zargin "yan adawa da huce takaicin matsalolin cikin gidansu kan gwamnatin Tinubu.



GWAMNA OLU YA DAGA HANNUN MATAIMAKINSA HAMZAT DON ZAMA MAGAJI



Gwamnan jihar Lagos Babajide Sanwo Olu ya daga hannun mataimakinsa Obafemi Hamzat don zama magajinsa a tikitin jam'iyyar APC.

Sanwo Olu ya ayyana marawa Hamzat baya ne a taron masu ruwa da tsaki na APC a Lagos.

Gwamna Olu ya ce tun fara aikinsu shekaru 7 da su ka wuce kwarewar Hamzat ta kai matsayin wanda zai ja ragamar kujerar gwamna.

Olu ya nuna k**ar da masaniya ko tsari ne da shugaba Tinubu ya dora su a kai.

Hakanan Olu ya ce Hamzat ya san ciki da wajen tsarin gwamnatin Lagos kuma ya cancanci hawa kujerar.

Tun farko Obafemi Hamzat ya ayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan Lagos a inuwsr APC a 2027.



MASU KYAMAR BAKI SUN KASHE 'YAN NAJERIYA BIYU A AFURKA TA KUDU



Masu kyamar baki na Afurka ta kudu sun kashe 'yan Najeriya biyu a yayin da hare-hare kan baki ya yI muni a kasar.

Wasu masu tsaurin ra'ayi na Afurka ta kudu har da jami'an tsaro kan aukawa baki bakaken fata da kisa da lalata mu su dukiya.

Ofishin jakadancin Najeriya ya bayyana sunayen mutanen da a ka kashe da su ka hada da Amaramiro Emmanuel da Ekpenyong Andrew.

Ofishin jakadancin ya fitar da sanarwar gargadin tsaro ta kaucewa wasu sassa da su ka hada da East London, Pretoria, Johannesburg da Kwazulu Natal.

Ofishin ya ce ya tura korafi ga hukumomin Afurka ta kudu don gudanar da binciken da ya dace da cafke wadanda su ka yI kisan gillar.

23/04/2026

LABARUN DUNIYA

SHUGABA TINUBU YA YABAWA KAMFANIN JIRGIN BURTANIYA DON INGANCIN SUFURI DA NAJERIYA



Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yabawa kamfanin sufurin jiragen sama na Burtaniya BRITISH AIRWAYS don inganta sufurin samaniya da Najeriya.

Shugaban na magana ne a lokacin tarbar shugabannin kamfanin da rakiyar jakadan Burtaniya a Najeriya Mr. Richard Montgomery a fadar A*o Rock.

Ziyarar ta zo daidai cika shekaru 90 da kamfanin na jirgin Burtaniya ya yi ya na hada-hada a Najeriya.

A nan shugaban ya ce kamfanin ya taimaka wajen karfafa huldar tattalin arziki a tsakanin kasashen biyu masu dogon tarihi.

Shugaba Tinubu ya tuna ziyarar da ya kai kwanan nan ta aiki Burtaniya inda ya ce ya samu karramawa daga Sarki Charles da sauran masu ruwa da tsaki na Burtaniya.

Jakada Montgomery ya godewa shugaba Tinubu bisa ziyarar ta aiki inda Najeriya da Burtaniya su ka sanya hannu kan muhimman lamuran raya arziki.



GWAMNATIN NAJERIYA TA CE MINISTOCIN TA BIYU SUN YI MURABUS GABANIN GARAMBAWUL A MAJALISAR ZARTARWA



Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ministocin ta biyu da a ka maye gurbinsu sun yi murabus gabanin garambawul a majalisar zartarwa.

Ministocin sun hada da tsohon ministan kudi Mr.Wale Edun da kuma na gidaje Ahmed Dangiwa.

Sanarwa daga kakakin shugaba Tinubu Mr. Bayo Onanuga ta ce Wale Edun da ke fama da jinya ya yi murabus lokacin da ya cika shekaru 70 a duniya ranar Litinin da ta gabata.

Shi ma ninistan gidaje Ahmed Dangiwa ya yi murabus gabanin 'yan sauye-sauyen.

Tuni a ka daga darajar karamin ninistan kudi Taiwo Oyedele zuwa matsayin babban minista don maye gurbin Edun.

Kazalika shugaba Tinubu ya zabi Muttaqa Rabe Darma daga Katsina don zama sabon ministan gidaje idan ya samu tantancewa daga majalisar dattawa.

Akwai wasu daga ministoci a gwamnatin Tinubu da su ka yI murabus don samun damar takarar kujerar gwamna a jihohinsu.



KOTU A KADUNA TA DAGE BA WA ELRUFAI BELI HAR ZUWA WATAN YUNI



Wata kotu a Kaduna ta yanke matsayar tura ba wa tsohin gwamnan Kaduna Nasiru Elrufai beli zuwa watan Yuni mai zuwa.

Wannan bai zama abun mamaki ba in an duba hukumomin da ke tuhumar Elrufai da kuma dama lauyansa ya yi nuna fargabar rike shi na tsawon lokaci.

Elrufai wanda ya shiga jam'iyyar adawa ta ADC ya zama mai furta kalamai masu zafi na hamayya ga gwamnatin APC ta shugaba Tinubu.

Hukumar yaki da cin hanci ta EFCC da ICPC da ma 'yan sandan farin kaya na tuhumar Elrufai kan caje-caje da su ka hada da badakala da kuma satar jin bayanan sirri na ofishin mai ba da shawara kan tsaro Malam Nuhu Ribadu.

Elrufai ya zama ba ya danyen ganye da gwamnatin Tinubu don tantance shi don samun kujerar minista inda a ka samu tangarda.

Malam Elrufai na kan gaba cikin wadanda su ka tallata kamfen din Bola Tinubu har ya lashe zaben 2023.





IRAN TA K**A JIRAGEN DAKON MAI BIYU A YAYIN DA SU KE KOKARIN BI TA MASHIGAR HORMUZ



Iran ta ba da labarin k**a jiragen dakon mai biyu a yayin da su ke kokarin keta mashigar ruwan Hormuz.

Da alamu jiragen na kasar Burtaniya da ke kokarin wucewa da danyen man fetur duk da ayyana mashigar a rufe da Iran ta yi.

Iran dai ta rufe mashigar Hormuz don matakan da Amurka ta dauka na datse tashoshin sufurin ruwa na Iran da hakan ya yi karantsaye ga yarjejeniyar tsagaita a yakin da Amurka da Isra'ila ke yi kan Iran.

Duk da haka shugaban Amurka Donald Trump na nuna za a iya cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Mai shiga tsakani wato kasar Pakistan na ganin a 'yan kwana biyu zuwa uku nan gaba za a dawo zama don samun sulhu a Islamabad.

Iran na nuna lallai Amurka ta janye tare ma ta sufurin doka don hakan ne zai kai ga samun maslaha mai dorewa.

Game da mata 8 da Iran ta samu da laifin ingiza tada tarzoma; Trump ya ce Iran ta dakatar da matakin rataye su.

A nan ma'aikatar shari'a ta Iran ta yi watsi da kalaman na Trump da nuna matan ba su ma fuskanci tuhumar kai wa ga hukuncin kisa ba.

21/04/2026

LABARUN DUNIYA

GWAMNATIN NAJERIYA TA CE RAHOTON BANKIN DUNIYA KAN TASARRUFIN KUDI BA YA NUFIN A NA SAMUN TASGARO

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa rahoton da bankin duniya ya fitar kan tasarrufin kudin shekara na Najeriya ba ya nuna karkatar da kudin gwamnati zuwa wasu lamura na daban a bayan fage.

Karamin ministan kudi Taiwo Oyedele ya bayyana haka a wata sanarwa da ke zargin wasu kafafen labaru da murde gaskiyar yadda lamarin ya ke har ma da amfani da bayanan da sun riga sun wuce.

Oyedele ya ce kudaden da a ke magana na halal ne da su ka shafi biyan basukan ayyukan da jihohi ko wasu ma’aikatu su ka gudanar da wasu hakkokin da a ka mayarwa sassan da abun ya shafa.

Karamin ministan ya ce rahoton ma na nuna a farkon shekarar bana an samu nasarar adana kudaden da a ke samu na shiga ta hanyar man fetur da hakan ke nuna gagarumar nasarar tafiyar da lamura daidai.

A nan ministan ya nanata matsayin gwamnati na tabbatar da adalci ga hanyoyin da a ke kashe kudi a shekara ta hanyar gaskiya da amana.



KAKAKIN SHUGABA TINUBU BAYO ONANUGA YA NUNA GAMSUWA CEWA A NA SAMUN GAGARUMAR NASARA KAN TSARO

Kakakin shugaba Tinubu Mr.Bayo Onanuga ya bayyana cewa ya samu gamsuwa cewa a na samun gagaruman nasarori a bangaren samar da tsaro a fadin Najeriya.

Onanuga ya ce ba k**ar yadda a ke yayata labarun da kan nuna tamkar ba a yaba kokarin jami’an tsaro soja a fagen daga, ya ce gaskiya ya samu labaru masu nuna a na cimma nasarorin yaki da miyagun iri.

Mr.Onanuga ya buga misali da labarun da ya ke samu daga kafar Zagazola cewa a na rutsawa da ‘yan ta’addan ISWAP, Boko Haram da ma ‘yan ta’addan daji.

Kakakin ya kawo wani misalin labarin da a ka yayata na sace fasinjoji 17 a wata motar safa a jihar Binuwai ciki har da amsu rubuta jarrabawar neman gurbin shiga jami’a inda 3 daga ma’abota motar su ka tsira.

Onanuga ya ce sauran mutum 14 ma an kubutar da su kuma an gano wasu miyagu ne na cikin gida na Binuwai su ka aikata mugun laifin ba ‘yan ta’addan daji ko Fulani da wasu ke ambata ba.



JAM’IYYAR APC TA FITAR DA JADAWALIN ZABUKAN FIDDA GWANI DA DUK ZA A KAMMALA A WATAN GOBE

Jam’iyyar APC mai mulki ta fitar da jadawalin sayar da fom din neman takara da zaben fidda gwani a dukkan muk**ai karkashin jam’iyyar.

Wannan dai don ya dace da kammala hada jerin sunayen ‘yan takara k**a daga majalisun jihohi, na tarayya, shugaban kasa da gwamnoni da za a mika a watan goben na Mayu.

Mafi tsadar kudin na mai son tsayawa takarar shugaban kasa ne naira miliyan 100 sai na gwamna naira miliyan 50. Masu son tsayawa takarar majalisar dattawa za su kashe miliyan 20 majalisar wakilai wakilai kuma naira miliyan 10.

Duk da haka akwai sassauci kan takarar mata, matasa da masu bukata ta musamman da za su biya kusan rabin kudin fom neman takarar.

Hukumar zabe INEC za ta fara gudanar da babban zaben 2027 daga ranar 16 ga watan Janairu mai zuwa.



TRUMP YA CE ZA A SAMU ZANTAWA MAFI DACEWA KAN TAKADDAMAR KERA MAK**AN NUKILIYA NA IRAN

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce za a samu yarjejeniya mafi dacewa ta warware takaddamar kera mak**an nukiliya na Iran.

Wannan dai sako ne k**ar yadda Trump ke yi ta hanyar kafar sadarwarsa ta yanar gizo Truth Social.

Wannan na zuwa cikin tsagaita bude wuta na mako biyu a yakin da Amurka da Isra’ila su ka aukawa Iran kimanin makonni 7 da su ka wuce.

Trump ya yi wannan bayani biyo bayan korafin da ‘yan majalisa na jam’iyyar Dimokrats su ka yi cewa Trump ya na gaggawa kan wannan yarjeniya na lamari mai muhimmanci.

Ba a tantance yadda za a cimma maslaha a dan kankanin lokaci ba amma Trump na nuna ba ya cikin matsin lamba kuma ya na da kwarin guiwar samun nasara.

16/04/2026

LABARUN DUNIYA

HUKUMAR ALHAZAN NAJERIYA TA JA HANKALI KAN MASU IKIRARIN VISA TA HAJJI TA BOGI



Hukumar alhazan Najeriya ta ja hankalin jama’a kan masu ikirarin iya yin visa ta aikin hajjin bana alhali Saudiyya tuni ta rufe damar.

Hukumar NAHCON a takaice ta sanarwa ta musamman daga jami’ar hukumar Fatima Sanda Usara ta ce akwai wasu masu cewa su 'yan kamfanoni na aikin hajji ta jiragen yawo da ke cewa da kofar yin VISA.

A nan NAHCON ta ba da tabbacin dakatar da yin visa ta hajji tun ranar 20 ga watan Maris don haka duk mai ikirarin ba mai gaskiya ba ne.

Don haka NAHCON ta bukaci yin takatsantsan ga biyewa irin wadannan kamfanoni don damfara ce.

Hakika ba yadda mutum zai iya gudanar da aikin hajji da wata visa k**ar ta ziyara, aiki ko wata bukatar daban don in an samu mai yunkurin ka iya fuskantar daurin wata 6 ko tarar riyal 20,000 ko ingiza keyar mutum gida.

NAHCON ta ce ta samu nasarar yi wa dukkan maniyata VISA kafin karewar wa'adin.



A*O ROCK TA CACCAKI KALAMAN AREGBESOLA A TARON ADC KAN SHUGABA TINUBU



Fadar A*o Rock ta caccaki sakataren bangaren jam’iyyar adawa ta ADC Rauf Aregbesola kan kalamai da ya auna kan shugaba Tinubu a babban taron jam'iyyar.

A sanarwa kakakin shugaba Tinubu wato Mr.Bayo Onanuga wanda ya zayyana taron da haramtacce, ya ce an ruwaito Aregbesola na bukatar shugaba Tinubu ya yi murabus bisa dalilan kuncin tattalin arziki da kalubalen tsaro.

A nan Onanuga ya nuna Aregbesola bai yi wa shugaba Tinubu wanda tsohon maigidansa ne adalci ba in an duba yadda ya jefa al'ummar jihar Osun a damuwa lokacin ya na gwamna da manufofin tattalin arziki ko tsarin gwamnati mai shigen na gurguzu.

Onanuga ya tuno hatta yadda Aregbesola ya rike kujerar ministan cikin gida don haka tamkar bai duba kansa ba wajen furta kalaman.

ADC dai ta yi babban taro karkashin David Mark da zargin rashin adalci don rashin halartar hukumar zabe don duba taron.

Yanzu dai hankali ya koma kan kotu don hukuncin da zai iya warware takaddamar ta ADC wacce ta kori shugaban bangare Nafiu Bala Gombe.

ADC ta yi zargin ministan Abuja Nyesom Wike ya yi yunkurin kawo kafar angulu a dandalin gudanar da taron na RAINBOW da ke yankin Arewa 11 a Abuja.



GWAMNATIN NAJERIYA TA CE FARASHIN FETUR DIN KASAR NA DA ARAHA IN AN KAWATANTA DA KETARE



Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce duk yadda a ke kuka da tsadar farashin man fetur a cikin gida amma ya na da sauki ko araha in an kwatanta da na wasu kasashe.

Bayanai daga ofishin kula da tara haraji na nuna hatta Amurka ta fi Najeriya tsadar fetur da kashi 50% haka ma wasu kasashen na duniya.

Bayanan na nuna matsalar dama ta taso ne daga hare-haren Amurka da Isra’ila kan kasar Iran inda rufe mashigar ruwan teku ta Hormuz ta tada farashin.

Akalla dai bayanan na nuna don tace man a cikin gida wato fiye da kacokan dogara ga ketare ya taimaka wajen daidaita farashin da samun man.

Don haka kira na dawo da tallafi ba shi ne zai zama mafita ba don tsadar ruwan dare ne game duniya.

Hakika farashin wasu kayan masarufi sun tashi don nasaba da tsadar kudin sufuri.



BABBAR TAWAGA TA PAKISTAN TA SAUKA A TEHRAN DON FARFADO DA SULHU DA AMURKA



Babbar tawaga daga kasar Pakistan ta sauka a babban birnin Iran, Tehran don farfado da sulhu da Amurka kan tsagaita wuta a yakin da Amurka da Isra’ila ke kai wa Iran.

Pakistan dai ita ce kan gaba a matsayin mai shiga tsakani don sulhun wanda ya samu tangarda bayan taron da a ka gudanar a Islamabad.

Gagarumin taron sulhun da ya samu targade ya samu halartar mataimakin shugaban Amurka JD Vance da ministan wajen Iran Abbas Aragchi.

Tawagar ta Pakistan a Tehran na karkashin jagorancin shugaban sojan Pakistan din Field Marshall Asim Munir.

A na sa ran sake dawo da tattaunawa nan da kwana biyu don yiwuwar samun maslaha kan yakin da ya wuce wata daya da ya haddasa asarar rayuka da dukiya ga rikita tattalin arzikin kasashen duniya da dama.

14/04/2026

LABARUN DUNIYA

RUNDUNAR TSARO TA HADIN KAI TA SOJAN NAJERIYA A BORNO TA RASA KOMANDA DA MUTUM 6

Rundunar tsaro ta sojan Najeriya da ke fafatawa da ‘yan ta’adda a jihar Borno ta rasa komanda da dakaru 6 a fagen daga.

Daya daga cikin rundunonin fafatawa da a ke yi wa taken HADIN KAI ta tsinci kai a harin bazata daga ‘yan ta’adda a yankin Monguno na jihar ta Borno.

Kakakin rundunar Sani Uba ya bayyana cewa dakarun sun jajirce don magance ‘yan ta’addan inda komandan cikin jarumtaka ya garzaya don ganewa idonsa abun da ke faruwa yayin da motarsa ta taka nakiya inda hakan ya yi sanadiyyar rasa ransa da na wasu dakaru 6.

Rundunar ta nuna juyayin rashin wadannan gwaraza da nuna duk da wannan farmaki, sojojin sun fatattaki ‘yan ta’addan kuma sun cigaba da aiki a nan Monguno.

Wata majiya ta bayyana sunan komandan da I.A. Muhammed amma ba a samu sunayen sauran dakarun ba.



MININSTAN ABUJA WKE YA CE RUWAN SAMA NE YA YI SANADIYYAR RUGUJEWAR SASHEN TASHAR ZAMANI TA SAFA TA KUGBO

Ministan Abuja Nyesom Wike ya bayyana cewa rowan sama ne k**ar dab akin kwarya ya yi sanadiyyar ruguwar sasshen tashar zamani ta safa da ke Kugbo kan hanyar Abuja zuwa Maraba a jihar Nasarawa.

Wike wanda ke magana da manema labaru ya ce ba k**ar yadda kenan a ke yayatawa cewa rashin ingancin aiki ne ya kawo akasin ba, amma hakika rowan sama ne ya yaye rufin karfe na tashar.

A nan Wike ya kara nuna yanayin inda tashar take kan tsauni ya kawo aukuwar akasin kuma hakan bai nuna sakaci na wanda ya gudanar da kwangilar aikin tashar ba.

Wike ya ce inda ginin ne ya tabu da hakan ne zai sa ya yi magana ko zargi dan kwangilar gina tashar da a ka bayanin ta lashe Naira biliyan.



JAM’IYYAR ADAWA TA ADC TA NACE ZA TA GUDANAR DA BABBAN TARONTA NA KASA A TALATAR NAN A ABUJA

Jam’iyyar adawa ta ADC tan ace lallai za ta cigaba da shirinta na gudanar da babban taro na kasa a Talatar nan a Abuja.

Wannan ya biyo bayan zanga-zanga da jagororin jam’iyyar karkashin David Mark su ka gudanar zuwa hukumar zabe da bukatar a dawo da sunayensu a matsayin shugabanni, bayan cire sunayen bangarori biyu masu hamayya da juna biyo bayan fassarar hukuncin kotu.

ADC t ace ta yi yunkurin neman wajen gudanar da taron a dandalin EAGLE da ma filin wasa na Moshood Abiola amma hakan bai samu ba, don haka za ta gudanar da taron a wani lambu mai suna RAINBOW cikin yankin Garki.

Jam’iyyar ta dawa ta zargi ministan Abuja da barazana ga mai kula da lambun cewa zai soke hakkin mallakar lambun na sa matukar ya bar ADC ta yi taro.

Wike dai tuni ya yi watsi da hannu a duk wani batu na hana ADC filin taro ya na mai cewa yarfe ne ‘yan adawar ke yi don jan hankalin jama’a su tausaya mu su.



TRUMP YA YIBARAZANAR NITSAR DA DUK WANI JIRGIN RUWAN YAKIN IRAN DA YA TINKARI KAWAR DA RUFE TA*OSHIN TEKUN IRAN DIN

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar zai nutsar da duk wani jirgin rowan yakin Iran da ya yi yunkurin bude katangar da Amurka ta yi ta toshe hanyoyin tashoshin teku na Iran.

Amurka dai ta bayyana matakin tare hanyar da duk wani jirgin ruwa da ya fito daga Iran zai bi bayan wargajewar yarjejeniyar tsagaita wuta ta mako biyu.

Dawowar mataimakin shugaban Amurka JD Vance daga teburin tattaunawa a Pakistan ba tare da samun cimma sulhu ba, ya sa Amurka ayyana wannan matakin.

Trump dai ya ce Amurka ta lalata duk karfin sojan ruwan Iran amma in ‘yan saura da ya bayyana na jiragen ruwan yaki su ka yi yunkurin tinkarar kawar da shingen, zai nitsar da su.

Har dai cikar wa’adin fara aiwatar da nitsar da jirage ya cika ba a ga Amurka ta dau matakin ba.

Pakistan da Qatar da ke shiga tsakani sun dage lallai a cigaba da tattaunawa don samun maslaha.

Address

Utako District
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Manara RADIO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Manara RADIO:

Share

Category