Manara RADIO

Manara RADIO Radio channel that sheds light to listeners in Africa,Middle East and across the globe, predominantly "HAUSA" on Islamic tenets and civilization

29/09/2025

LABARUN DUNIYA

SAM BA GASKIYA BA NE ZARGIN KISAN KARE DANGI GA MABIYA ADDININ KIRISTA-GWAMNATIN NAJERIYA

Gwamnatin Najeriya ta yi watsi da wasu bayanai daga wasu shafukan labaru na ketare da wasu ma’abota yanar gizo da ke cewa akwai kullalliya ta yin kisan kare dangi ga mabiya addinin kirista a Najeriya.

Ministan labaru Muhammad Idris ya baiyana haka a wata sanarwa, ya na mai cewa labarun sam ba su da tushe b***e madafa.

A nan ministan ya ce gaskiya ne Najeriya k**ar wasu kasashe na fuskantar kalubalen tsaro, amma hakan bai ware wani addini ko kabila ba, fitinar ta shafi kowa.

Ministan ya ce daga watan Mayun 2023 zuwa Febrerun bana, jami’an tsaro na gwamnatin sun hallaka fiye da ‘yan ta’adda 13,000 da kubutar da ‘yan kasa da a ka yi garkuwa da su sama da 10,000.

Don fito da abun fili, minista Idris ya ce masu yada shacifadin su sani cewa shugaban sojoji da na ‘yan sanda duk mabiya addinin kirista.

Muhmmad Idris ya ce gwamnatin shugaba Bola Tinubu na daukar duk matakan da su ka dace wajen kare rayuka da dukiyoyin dukkan ‘yan Najeriya.



KOTU TA HARAMTA KAFA GWAMNATIN SA-IDO A NAJERIYA

Babbar kotun taraiya ta yanke hukuncin haramta yunkurin kafa gwamnatin sa-ido da za ta zama tamkar kishiyar zababbiyar gwamnati.

Wannan ya biyo bayan karar da rundunar tsaron farin kaya ta DSS ta shigar da Farfesan tattalin arzikin siyasa Pat Utomi wanda ke shirya kafa gwamnatin.

Alkalin babbar kotun taraiya James Omotosho ya zaiyana irin wannan gwamnati da cewa ta yi karantsaye ga tsarin shugaba mai cikekken iko na Najeriya.

Omotosho ya zaiyana kafa gwamnatin ta sa-ido da haramtacce kuma shigo da dokokin wasu kasashen ketare ne da babu tsarin a Najeriya.

Gwamnatin sa-ido dai na aiki da shugaban kasa da ministoci tamkar yanda zababbiyar gwamnati ke yi amma ba karfin zartarwa sai dai tsara manufofin adawa da sa ido kan aiyukan gwamnatin da ke kan gado.

Utomi wanda ya taba tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyyar ADC a 2007, ya so nacewa cewa ya na da hurumin kafa gwamnatin bisa dokar fadar albarkacin baki.



A NA NUNA DAMUWA KAN RIKICIN MATATAR DANGOTE DA KUNGIYAR PENGASSAN

A na nuna damuwa kan matsalar da za a samu a sanadiyyar takaddamar kungiyar manyan ma’aikatan fetur da iskar gas PENGASSAN da matatar fetur ta Dangote.

Dambarwar dai ta sa PENGASSAN umurtar hana kai danyen mai da iskar gas zuwa matatar ta Dangote da ke Lagos.

Damuwar ta shafi musamman iskar gas da karancin ta zai haddasa katsewar wutar lantarki na kasa.

PENGASSAN ta bukaci membobin ta su kawo cikas ga lamuran aiki a matatar don nuna fushi kan korar wasu membobin daga aiki.

Kungiyar ta manyan ma’aikatan na fetur da gas ta zargi matatar da daukar matakan da su ka ci karo da dokokin kwadago hakanan da amfani da damar wajen yada bayanan da ba su da inganci.



AMURKA TA BAIYANA SHIRI MAI KARFI NA SAMUN SULHU A YAKIN GAZA

Amurka ta baiyana shiri mai karfi na samun daidaitawar dakatar da yaki a Gaza da ya doshi shekaru 2.

Tuntuni a ka tabbatar da kashe fiye da Falasdinawa 62,000 a Gaza da kuma jefa wasu dubban cikin galabaita.

Trump na magana ne gabanin ganawar sa a litinin din nan da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a fadar White House.

Mataimakin shugaban Amurka JD Vance ya ce manyan jami’an Amurka na ganawa da Isra’ila da shugabbanin Larabawa don samar da maslaha.

In za a tuna mummunan harin da Isra’ila ta auna kan masu tattaunawar sulhu na Hamas da ita a birnin Doha ya karya guiwar Larabawa inda har Sarkin Katar Sheikh Tamim bin Hamad Al-Thani ya zaiyana Isra’ila da cewa tamkar kasa ce da ke gaba da makwabtan ta.

24/09/2025

LABARUN DUNIYA

BABBAR KOTUN TARAIYA TA AIYANA RANAR YANKE HUKUNCI KAN BUKATAR AMSA RASHIN LAIFI NA KANU

Babbar kotun taraiya ta aiyana ranar 26 ga watan nan na Satumba 2025 don yanke hukunci kan bukatar shugaban ‘yan aware na Biyafara/IPOB Nnamdi Kanu na zama marar laifi.

Tun farko alkalin babbar kotun taraiya James Omotosho ya aiyana ranar 10 ga watan gobe ta zama ranar yanke hukunci kan bukatar.

Lauyan Nnmadi Kano Aloy Ejimakor ya baiyana rage tsawon lokacin yanke hukuncin kan bukatar su ta a aiyana Kanu a matsayin wanda bai aikata wani laifi ba ko wanda ba wata tuhuma a kan sa.

Gwamnatin Najeriya ta na tuhumar Nnamdi Kanu da laifin cin amanar kasa da ta’addanci da ya kai ga kashe mutane da dama musamman a kudu maso gabashin Najeriya.

Kanu na hannun jami’an tsarin farin kaya DSS inda daga nan ne a ke kawo shi kotu don fuskantar tuhuma.



MATA SUN YI GANGAMI A ABUJA DA BUKATAR BA SU DAMAR TAKARA TA KUJERAR MATA ZALLA A SIYASA

Kungyoyin mata sun yi gangami a babban birnin Najeriya Abuja su na bukatar lallai a yi gyaran doka don ba wa mata hurumin tsayawa takara a muk**an siyasa na mata zallah.

Wannan dai ya biyo bayan taron jin bahasin jama’a da majalisar dokoki ta kira don jin ra’ayin mutane kan bukatar ta mata.

Su dai matan na son daga kan kansila har zuwa muk**an majalisa a ware mu su wata kujera guda daya da su kadai ne za su rika tsayawa takara don haka koma dai waye ta ci zaben za ta zama mace ce.

Misali a duk jiha akwai ‘yan majalisar dattawa uku, sai matan ke bukatar a kara kujera daya su zama hudu amma ta takarar mata zallah don wakiltar muradun mata.



FUBARA YA ZIYARCI FADAR A*O ROCK

Gwamnan jihar Ribas Siminalayi Fubara ya ziyarci fadar A*o Rock inda ya gana da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Ziyarar ta zo ne ‘yan kwanaki kalilan bayan dawowar Fubara kujerar sat a gwamna yayin da wa’adin dokar ta baci na tsawon wata 6 ya k**ala.

Siminalayi Fubara ya ce ya zo ya godewa shugaba Tinubu don yanda ya shiga tsakani a ka dakatar da tsamar siyasa a iihar Ribas din.

Fubara ya yi alwashin zai yi aiki da duk masu ruwa da tsaki na jihar Ribas ciki da ‘yan majalisar dokokin taraiya don cigaban jihar.



ISRA’ILA BARAZANA CE GA MAKWABTAN TA-TAMIM AL-THANI

Sarkin Katar Sheikh Tamim bin Hamad Al-Thani ya ce lallai kasar Isra’ila barazana ce ga makwabtan tad a ke son zaman lafiya.

Sheikh Al-Thani na magana ne a taron zauren majalisar dinkin duniya a birnin New York din Amurka.

Sarkin ya ce sam Isra’ila ba ta zama kasar dimokradiyya da ke zagaye da kawaye makiya ba, amma Isra’ila makiyiya ce ga makwabtan ta masu kaunar zaman lafiya.

A ‘yan kwanakin bayan nan ne Isra’ila ta kai farmaki birnin Doha na Katar don neman kashe jami’an Hamas da ke zaman sulhu da Isra’ilar inda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 6 ciki dad an asalin katar daya.

Al-Thani ya nuna damuwa cewa har Firaministan Isra’ila na tinkaho da hana kafuwar kasar Falasdinawa da lasar takobi sam hakan ba zai tabbata ba.

Al-Thani ya godewa kasashen duniya da ma majalisar dinkin duniya wajen yin Allah wadai da farmakin da Isra’ila ta kai kan Doha.

20/09/2025

LABARUN DUNIYA

SAKATARIYAR LAFIYA TA ABUJA TA KWARANYE SAMUWAR CUTAR EBOLA

Sakatariyar lafiya ta babbar birnin Najeriya Abuja ta kwaranye samuwar cutar EBOLA mai kisa da a ka yi fargabar samuwar ta.

Shugabar ofishin Dokta Dolapo Fasawe ta ba da tabbacin hakan ne a jawabin da ta yi wa manema labaru don fito da hakikanin halin da a ke ciki.

Fasawe ta ce an gudanar da bincike inda a ka tantance cutar da a ka gano ba Ebola ba ce kuma ba wannan ne karo na farko da a ke samun irin wannan yanayi da bincike kan gano ba cutar da a ke fargaba ba ne.

Lamarin ya auku ne daga wani matafiyi da ya je wani yanki a kasar Rwanda mai makwabtaka da kasar Dimokradiyyar Kongo inda a ke samun cutar.

Marar lafiya ya je asibiti inda a ka kebe shi kuma daga bisani a ka gano ba Ebola ke damun sa ba.



DON BUKATUN ZAMAN LAFIYA YA SA BAN KALUBALANCI AIYANA DOKAR TA BACI A RIBAS BA-GWAMNA FUBARA

Gwamnan jihar Ribas Siminalayi Fubara ya ce don bukatar zaman lafiya ya sa bai kalubalanci aiyana dokar ta baci da ta dakatar da gwamnatin sa na tsawon wata 6 ba.

In za a tuna tun a watan Mayu ne shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya aiyana dokar kuma a ranar Laraba gabanin ‘yan sa’o’i wa’adin ya kammala sai shugaban ya sanar da janye dokar da hakan kai tsaye ya dawo da gwamnan da majalisar dokokin jihar kan aiki.

Tsohon hafsan rundunar ruwa Mr.Ibas ne gwamnatin taraiya ta tura ya zama kantoman riko na Ribas tsawon wa’adin.

Siminalayi Fubara da ke jawabi ga al’ummar jihar ta talabijin ya ce zai fuskanci lamuran mulki ne don cigaba da aiyukan raya kasa da sulhu.

Fubara ya yabawa shugaba Tinubu ya na mai cewa ya sulhunta su da tsohon gwamna Nyesom Wike da su ka yi ta tsamar siyasa.

Fubara ya bukaci al’ummar jihar su jure don ya ce jihar ta shiga mawuyacin yanayi a tsawon dokar ta baci amma an koyi darusa.



SHUGABA TINUBU YA ZIYARCI GIDAN BUHARI A KADUNA

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci gidan marigayi shugaba Buhari a Kaduna inda ya gana da uwargidan marigayin Aisha da sauran ‘yan gidan.

Shugaba Tinubu wanda kazalika ya shiga Kaduna don buki da ya shafi iyalin Sanata Abdul’aziz Yari, ya shaidawa iyalin Buhari cewa gwamnatin sa za ta cigaba da raya irin muradun marigayin kuma su sani ba su kadai ke cikin juyayin rashin marigayin ba.

A maida jawabi Aisha Buhari ta godewa shugaban da bukatar al’ummar Najeriya su yi koyi da dabi’un marigayi Buhari.

In za a tuna gwamnatin taraiya ta sake gina gidan na Buhari a Kaduna inda marigayin bai ma dade da fara amfani da gidan ba ciwon ajali ya riske shi.



ISRA’ILA ZA TA YI AMFANI DA KARFI NA FITAR HANKALI KAN GARIN GAZA DA BUKATAR MAZAUNA SU FICE

Isra’ila ta shirya amfani da karfi na fitar hankali kan babban garin Gaza don haka ta bukaci mazauna su fice da birnin.

Wannan na faruwa ne yayin da tsananin yunwa ta kara tsananta a Zirin cikin yakin da ya kusa cika shekaru biyu kan al’ummar Gaza.

Kazalika wannan matakin na Isra’ila na zuwa ne mako daya gabanin wani taron majalisar dinkin duniya inda Faransa da Burtaniyya ke niyyar aiyana amincewa da kafuwar kasar Falasdinu.

Tuni ma Isra’ila ta rufe fitacciyar hanyar ketarawa daga arewaci zuwa kudancin Gaza ta Salahaddin don kara zuba ido kan masu ficewa da zummar murkushe mayakan Hamas.

Matakin na Isra’ila ya sa majalisar dinkin duniya zargin Firaminista Netanyahu da zuga kisan kare dangi kan al’ummar Gaza.

Isra’ila ba ta bata lokaci ba wajen martini da karyata majalisar da nuna an canja bayanan gaskiya.

Babban birnin Gaza na dauke da kimanin mutum miliyan daya kuma nan ne kashin bayan Gaza da Isra’ila ke ganin in ta karbe ikon sa ta gama da Hamas.

15/09/2025

LABARUN DUNIYA

SHUGABA TINUBU YA KAMMALA HUTUN SA NA SHEKARA

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya k**ala hutun sa na shekarar bana 2025 inda ya ke dawowa Abuja a Talatar nan.

Sanarwa daga mai taimakawa shugaban kan labaru Bayo Onanuga ta baiyana cewa shugaban dama ya fara hutun ne daga ranar 4 ga watan nan na Satumba inda ya fara isa birnin Paris.

In za a tuna sai da shugaba TInubu ya kai ziyararaiki kasar Japan don halartar taron tattalin arzikin Afurka na 9 a Tokyo kafin ya dawo don fara hutun.

Hakanan dama hutun zai kasance ne tsakanin birnin Paris na kasar Faransa da kuma London na kasar Burtaniya.

A birnin Paris shugaba Tinubu ya gana da shugaban Faransa Emmanuel Macron a fadar Elyasee inda su ka tattaunawa kan huldar arziki ta kasashen biyu.



HAJJIN 2025 NE NA DAGA MAFIYA INGANCIN AIYUKAN HAJJI DA NAHCON TA JAGORANTA-DOKTA MAKARFI

Masani a kan lamuran aikin hajji na Najeriya Dokta Shehu Makarfi ya ce hakika aikin hajjin 2025 da ya gudana shi ne ko kuma na daga cikin mafi nasarar aiyukan hajji da hukumar alhazan Najeriya NAHCON ta jagoranta.

Dokta Makarfi na magana ne a taron nazari da ba da kyautukan ban girma ga hazikan jami’an aikin hajji da kamfanin jaridar labarum alhazai mai zaman kan ta HAJJ INDEPENDENT REPORTERS ta gabatar a babban dakin taro na babban masallacin taraiya a Abuja.

Makarfi wanda ya yi aiki a bangarori daban-daban na aikin hajji, ya ce ba zai yiwu a samu nasara 100% amma hakika duk wanda ya halarci aikin hajjim zai ba da shaidar yanda a ka kula da jin dadin alhazan daga Madina, Makkah zuwa Masha’ir.

Daya daga masu jawabi Sheikh Abubakar Sadiq ya bad a shawarar daukar matakin matso da alhazan Najeriya kusa da gadar jifar shaidan a Muna.

Sheikh Sadiq da ke da kamfanin jirgin yawo COMEREL ya ce akwai zango 5 a Muna inda a ka ajiye alhazai, amma alhazan Najeriya kan samu kan su a can baya da hakan ke sa dawainiyar doguwar tafiya kafin zuwa jifa.

A nan Sadiq ya ba ba shawarar a duba kauro da alhazan zuwa zango na 3 don saukakawa alhazan.

Da ya ke Karin bayani, kwamishinan aiyuka na hukumar alhazan Prince Anofi Olanrewaju Elegushi, ya ce hukumar NAHCON za ta so alhazai su matso kusa da gadar jifa amma duk matsawa gaba da za a yi zai haddasa tsadar kudin kujera ne da a ke daukar matakan saukakawa.

Taron wanda ya samu halartar wakilan wasu gwamnoni k**ar Jigawa da Sokoto da kuma masu hannu a lamuran aikin hajji, ya gudana karkashin jagorancin tsohon kwamishina a hukumar alhazan Dr.Yusuf Adebayo.

An ga jami’an kafar labarum INDEPENDENT HAJJ REPORTERS irin su Muhammad Ibrahim, Sani Tukur, Nasir Jafar da sauran su na kai kawo don tabbatar da nasarar taron.



A NA CIGABA DA MUHAWARA KAN SULHU DA ‘YAN BINDIGA A KATSINA

Jama’a na cigaba da muhawara kan taron sulhun da al’ummar Faskari a jihar Katsina ta yi da ‘yan bindiga.

Muhawarar ta karade kafafen sadarwar yanar gizo inda wasu da ke jihohin makwabtan Katsina ke ganin ba wata nasara da sulhun zai haifar.

An ga daya daga gaggan barayin daji Adamu Alero na zantawa da wani a faifan bidiyo da a ka yayata ya na nuna muhimmancin sulhun da kore dawo da fitina a baya daga ‘yan bindigar bayan an yi irin sulhun ko sasanci.

A wani taro da ya shafi kungiyar taraiyar turai, gwamnan Katsina Dikko Radda ya ce an kaddamar da sulhun a sassa daban-daban da zummar samar da zaman lafiya mai dorewa.

Farkon hawan sa karagar mulki, gwamna Radda na kan gaba wajen kaucewa duk wani batu na sulhu da ‘yan bindiga har ma ya dauki rundunar sa-kai don murkushe ‘yan ta’addan.



ISRA’ILA NA NEMAN WARGAZA ZAMAN SULHU NE DA HARI KAN HAMAS-SHEIKH AL-THANI

Shugaban kasar Katar Sheikh Tamim bin Hamad Al-Thani ya ce Isra’ila na neman wargaza sulhun da a ke gudanarwa ne ya sat a kai farmaki kan shugabannin Hamas a Doha.

In za a tuna Isra’ila ta kai farmaki da zummar kasha dukkan shugabannin Hamas da ke birnin Doha musamman da ke kula da zaman sulhu kan yakin Gaza.

Sheikh Al-Thani na magana ne a taron shugabannin Larabawa na bitar hulda da Isra’ila bayan mummunan matakin da a ta dauka.

Sarkin na Katar ya nuna mamakin yanda Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya shirya farmakin alhali kuma Isra’ila na zaman sulhu da Hamas.

A nan Al-Thani ya yi tambayar shin in Netanyahu na son kashe shugabannin Hamas ne, to me ya sa Isra’ila ke zaman sulhu da su?.

Sarkin ya zargi Netanyahu da kokarin fadada izzar sa a yankin Larabawa da hakan babban aibu ne, kazalika da rashin damuwa da halin da k**ammun fursunonin Isra’ila ke ciki a Gaza.

Hakika harin da Isra’ila ta kai kan shugabannin Hamas a Katar ya batawa Larabawa rai don haka su ke nazarin daukar mataki na bai daya kan Isra’ila da duba riba ko akasin haka na huldar su da Isra’ila.

MUJADDADI DAN FODIYO SAK, ‘YAN KWANGILA SAM!Nasiru Adamu El-hikaya  manhaja Na ga ya dace na dora alkalami don jan hanka...
07/09/2025

MUJADDADI DAN FODIYO SAK, ‘YAN KWANGILA SAM!

Nasiru Adamu El-hikaya manhaja

Na ga ya dace na dora alkalami don jan hankali kan wasu da su ka takarkare sai sun aibanta Mujaddadi Shehu Usmanu Danfodiyo. Aikin wadanan mutanen na nan a kafafen sada zumunta inda su ke jefa miyagun sunaye da alakanta mummunan tarihi ga Shehun malamin. Wadanda ke kwangilar nan sun tsara wata loga don samun saukin yada manufofin su inda su ka rubuta “FODIYANCI SAM MUSULUNCI SAK” kuma ba ma lallai mutanen nan musulmi ba ne don haka ba wani abun da ya hada su da musulunci har ya zama sak a wajen su. Idan har musulunci sak ne wajen wadannan miyagun ba yanda za a yi su dauko wannan kwangilar. Wani ma in ka duba askin kan sa ka san shashasha ne da bai samu tarbiyya ba amma damar yanar gizo da ‘yar wayar salula ta ba shi kafa ya zagi Shehu Usmanu ya yi tsilli-tsilli da ido don ya san ya yi rasar kunya. Duk talaucin musulmin kirki ba zai karbi kwangilar yaki da aiyukan sambarka da Mujaddadi ya assasa ba. Rayuwar Mujaddadi babban alheri da Afurka ta yamma da ma duk mutanen arziki za su cigaba da shan romon sa har karshen rayuwa. Labarun karya daga miyagun iri ba za su shafe alherin Mujaddadi ba. Bayan Allah ya rayu daga 1754-1817 wato kwata-kwata shekaru 63 ya yi a duniya amma ya shuka alherin da zuwa yau shekaru 271 da barin sa duniya a ke cin gajiya inda wasu kuma 'yan kwangila su ka dukufa ga aibanta shi. Miyagun iri sun sani ko ba su sani ba an shawarci maci kasa ya kiyayi ta shuri.

Tun a na abun k**ar da wasa wajen batanci ga mujaddadi Shehu Usmanu har abun ya zama da gaske. Masu yin wannan abun kuma su ke hura wutar kabilanci tsakanin Hausawa da Fulani. Hakika ba a na nufin in an ce Hausa/Fulani a na nufin Hausawa da Fulani sun narke sun zama kabila daya ba ce, a’a manufa a nan an samu kabilu biyu da su ke hade da juna ta fuskar addini, aurataiya da mu’amalar rayuwa a mazauni daya. Kazalika makiyaya da a kasari Fulani ne na kasuwanci da zolaya tsakanin su da mahauta da akasari Hausawa ne. In mu ka duba yawan makiyaya a cikin Fulani kakaf ba za su fi kashi 5% hakanan in mun duba yawan mahauta a cikin Hausawa su ma dai ‘yan tsiraru ne. Dole makiyaya na daji inda miliyoyin jama’ar da harkar su ba ce na kauyuka da birane. Wannan alakar ce ma ta sa yankin arewa ke da karfi da ya gagari hatta Turawa canja ma sa al’adu da addini. Za mu lura iyayen mu a karbo ‘yanci daga Burtaniya su Sir Ahmadu Bello da Sir Abubakar Tafawa Balewa kan shiga London ko ma majalisar dinkin duniya daure da rawani a kan su. Zamanin su duk wannan shakiyancin na bambanci babu shi. A hankali yanzu wasu na nuna jihadin Shehu Mujaddadi shi ne su Bello Turji ke rayawa!. Dole ne ko in ce hakki ya rataya a kan mu da sauran masu nazari mu tashi tsaye don ceto yankin mu daga masu neman kifar da shi ta hanyar murde wuyan tarihi da kawo labarun da a ka canjawa fuska a ka yi Karin gishiri ko ma a ka kirkira don yaudarar matasa masu tasowa su dauka k**ar wani ne a can baya ya danne mu su ‘yancin su. Idan na yi shiru kan abun da na karanta a littattafai tun lokacin da ilimi ma kyauta ne makarantu, ina ganin ban kyauta ba. S**a da furta bakaken maganganu na za su sa a yi kasa a guiwa wajen wannan gagarumin aiki ba. An so a makara kuma abun kalubalen wasu na shakkar yin magana don kar ‘yan bana bakwai su yi mu su dirar mikiya. Mu dai da mu ke raye yanzu a yankin arewa da ke zantawar nan a nan a ka haife mu kuma ba mu da wata kasa mu da iyaye da kakanni da ta zama gida a gare mu irin yankin na arewa. Mu taimakawa juna mu taimakawa wannan yanki ya aminta daga sharrin makirai. Ba na son kai tsaye na nuna addinin Islama a ke kai wa hari amma tabbas biri ya yi k**a da mutum. Ma’ana idan mu ka lura da kyau wadanda ke yayata kamfen din na la’antar Mujaddadi matasa ne da ba wani tarihi ko wata gudunmawa da su ka taba ba wa addinin musulunci hakanan da yawa daga masu mara mu su baya ba ma musulmi ba ne. Wasu ma daga ganin sunayen su ka san ‘yan sholisho ko ‘yan duniya hayakin taba. Duk ai’ummar da addini ba zai hada ta ba to akasin hakan na sharholiya zai hada ta. Wanda bai san tarihi ba da mai karancin shekaru ka iya fadawa tarkon wadannan miyagun da ke ikirarin wai kishin Huasawa su ke yi da Shehu Danfodiyo ya yaki kakannin su ya kwace mu su sarauta. Hakika cikin wadanda su ka yi aikin jaddada musulunci tare da Shehu akwai kabilu daban-daban. Hasalima Shehu ba manufar sa kafa runduna don yakar kowa ba don hatta abun da a ke cewa ya yi yakin ne sai bayan da a ka kai ma sa farmaki har inda ya yi hijira da almajiran sa. Asalin aikin Shehu Mujaddadi shi ne yakar yanda a ka dabaibaye addinin musulunci da miyagun al’adu na bokanci da shirka. Hakanan jihadin ya shafi matsafa da masu bautar gumaka hatta a birnin Kano na wancan zamanin. Har dai mutum zai samu sahihin tarihin zamanin Shehu da yankunan da ya tura runduna don kakkabe miyagun akidu zai iya fahimtar zuwan Shehu babbar rahama daga Allah don ceto al’ummar tsohon zamanin daga zama cikin tsafe-tsafe da bautar gumaka da ma zama karkashin azzaluman sarakuna masu kashe duk wanda su ka ga dama su kwace dukiyar wanda su ka tsana. Ina fata mutane za su bi tarihin akasarin sarakunan da jihadin Shehu ya kawar za su gane me ya faru a wancan zamanin. Da yawa daga abun da ya auku a jihadin Shehu shi ne tawagar mutane da su ka rungumi kyakkyawar akida kan tashi su tafi wajen Shehu su nemi izini ya ba su dama don jaddada musulunci a yankunan su. Shehu kan ba su dama da baiyana mu su ka’idojin wannan aiki na addini. Shi n ko kunsan akwai garuruwan da Shehu bai taba takawa ba a yankin arewa da sauran sassa da da’awar sat a kai? Shin ko kunsan Shehu bai samu damar zuwa Makkah don gudanar da aikin hajji ba don shagalta da ya yi da karantarwa don ceto al’umma daga halaka? Idan mu na son sanin aiyukan Shehu mu karanta littattafan sa da na kanin sa Abdullahi Gwandu. Bayin Allah ne da su ka share rayuwar su gaba daya wajen karatu da hidima ga addini. Gaba daya ba wata sharholiya ko jin dadin rayuwa da ke gaban su. Allah yak are Shehu daga yunkurin kashe shi da a ka yi ta yi har ya samu damar yada ilimi mai tsabta da yau mu ke cin gajiya. Addinin musulunci ba zai rayu ba tare da ilimi ko karatu da karatarwa ba bias akida mai kyau. Manzon Allah mai tsira da aminci ya fara da karantar da jama’a ne tauhidi don su tsaya kyam ga sanin Allah shi kadai ne ba a hada shi da kowa wajen bauta. Don haka duk mai wa’azi ya zama mai muhimmanci ya jaddada tauhidi don al’umma su zauna kan mikakkiyar hanya don samun rabauta a duniya da lahira. A tarihin Shehu lokacin da ya dauko wannan aiki na da’awa ya samu farmaki daga wasu sarakuna wadanda ke ganin hakan barazana ce ga sarautar su.

Jihadin Shehu ba kasar Hausa kawai ya ratsa ba, ya shiga yankunan wasu kabilun daban k**ar Bauchi inda Modibbo Yakubu ya kafa kasa da tutar Shehu kuma ba ma Bafulatani ba ne don haka jihadin ba yi da alaka da kabilanci k**ar yanda msu murduda tarihi ke neman yayatawa. Jihadin ya shiga Gombe inda nan ma ba kasar Hausawa ba ce a ka samu Modibbo Bubayero ya kafa kasa. Jihadin ya shiga yankin da yau a ke kira Adamawa kuma ba kasar Hausa ba ce inda Modibbo Adama ya kafa kasa don aikin yada addinin musulunci. Sassa da dama a jihadin ya shiga ba ko kamshin musulunci gabanin isar kiran Shehu. Mu duba kiran Shehu ya shiga kasar Ilori wato Kwara inda kasar Yarbawa ce. Shigar jama’ar Shehu da aurataiya tsakanin Yarbawa da Fulani ya sa har wasu masu kabilanci a Yarbawa ke daukar su a matsayin jabun Yarbawa ko ma ba Yarbawa ba ne. Sunan su yanzu Gambari.



KAMMALAWA

Zan yi amfani da wannan dama wajen kira ga mai alfarma Sarkin Musulmi Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar ya karfafa aiyukan wallafa litattafan tarihi na Daular Shehu Mujaddadi. A wallafa littattafan da dama a raba su kusan kan farashi mai rahusa a fadin Najeriya. A rubuta litattafan da Turanci a fassara da manyan harsunan Najeriya don mutane su gane aiyukan Shehu. Baya ga mai alfarma ina kira ga tsangayoyin tarihi k**a daga jami’ar Usmanu Danfodio, Jami’ar Byaero ta Kano, Jami’ar Ahmadu Bello da sauran su, su rika shirya tarukan baje kolin tarihin abubuwan da su ka faru a arewa gabanin jihadin Shehu da bayan jihadin zuwa zuwan turawa har su ka kashe sultan na hadaddiyar Daular Attahiru a Bormi da ke yankin Funakaye a jihar Gombe. A faiyace shin a yau masu sarauta a arewa almajiran Shehu ne ko an samu sauyi? Shin in da Shehu zai dawo ya ga sarakunan da su ka zo bayan kutsowar ‘yan mulkin mallaka zai yi alfahari da su? Mun san an ragewa sarakuna karfi amma har gobe ruwa na maganin dauda don haka su ma hakki ya rataya a wuyan su, su fito da aiyukan Shehu a aikace da kakkabe masu zagon kasa kan Mujaddadi ta amfani da makircin ‘yan kwangila masu burin haddasa yakin basasa tsakanin manyan kabilun arewacin Najeriya.

Nasiru Adamu El-hikaya

06/09/2025

LABARUN DUNIYA

KUKAN MAKIRCI OLASIJIMO OGUNDELE YA KE YI YA KARKATAR DA NAIRA BILIYAN 5.7-ENUGU

Gwmnatin jihar Enugu ta bukaci jama’a kar su saurari mai kamfanin kwangilar gina gidajen alfarma Olasijimo Ogundele kan fashewa da kuka da ya yi a martini bayan hukumar EFCC ta aiyana neman sa ruwa a jallo.

Gwamnatin ta Enugu ta ce Ogundele mai kamfanin Sujimoto Luxury Construction ya damfare ta Naira biliyan 5.7.

Ogundele ya ce kwabila ya shiga da gwamnatin jihar ta Enugu inda kaya su ka rika tsada har ta kai ba ma zai ci ribar ginin da a ka ba shi ba.

Dan kwangilar ya ce gwamna ya nemi ya gina ma sa mafi tsawon gini a Najeriya mai hawa 69 kuma ya zana ya mika inda a ka karkatar da shi kan wani aikin daban.

A nan Ogundele ya bugi kirjin zai baiyana a gaban hukumar EFCC don wanke kan sa kana bun da ya zaiyana bata sunan kamfanin sa.

Ita dai gwamnatin Enugu ta ce a yi watsi da koke-koken Ogundele don dan damfara ne kawai.



AN GUDANAR DA TARON GABATAR DA LITTAFIN “WHERE I STAND” DA DOKTA JALO YA JUYA ZUWA LARABCI

An gudanar da taron gabatar da fassarar littafin WHERE I STAND na Sheikh Abubakar Mahmud Gumi da Dokta Jalo Jalingo ya juya zuwa Larabci.

Manyan malamai da su ka hada da masu shirya taron karkashin Sheikh Abdullahi Bala Lau su ka halarci taron da Sanata Abdul’aziz Yari ya gabatar.

Babban limanin masallaci Sultan Bello Dokta Muhammad Sulaiman ya gabatar da bitar littafin inda Dokta Ahmad Gumi ya kasance a taron a madadin iyalan marigayi Sheikh Abubakar Gumi.

Sheikh Jalingo ya gudanar da wasu muhimman aiyukan da su ka hada da juya muhimman litattfan fiqihun malikiyya daga zube zuwa wake.

Sauran aiyukan sun hada da littafin Al’AKIDATUS SAHIHA, IZZIZYYA, ISHMAWI, RISALA da AHALARI da Dokta Jalingo ya juya su zuwa wake don kara fito da ma’anonin su na zurfin ilimi.



HUTUN SHUGABA TINUBU NA SHEKARA YA SHIGA WUNI NA BIYU

Hutun shekara da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya fara daga ranar Alhamis din da ta gabata ya shiga wuni na biyu.

Shugaban dai k**ar yanda tuni sanarwa daga kakakin sa Bayo Onanuga ta baiyana zai shafe kwana 10 kafin ya dawo Abuja.

Shugaban dai zai kasance tsakanin kasar Faransa da kuma Burtaniya a lokacin hutun wato duk zaman zai zama a turai kenan.

Ba mamaki in shugaban ya yi amfani da dammar hutun na sa wajen kara duba lafiyar sa don wartsakewa ga aikin jagorancin kasa.

Gabanin tafiyar ta sa, shugaba Tinubu ya ce tun a watan jiya Najeriya ta cimma nasarar tara kudin shiga na bana bias has ashen da a ka yi ta hanyar sassan da ke waje da man fetur.



NAHCON TA MAIDA MA’AIKATAN ARO ZUWA MA’AIKATUN SU NA ASALI

A cikin hanyoyin bunkasa aiyukan ta, hukumar alhazan Najeriya NAHCON ta maida ma’aikatan aro zuwa ma’aikatun su da cibiyoyin su na asali.

Mataimaakiyar daraktar labaru ta hukumar Fatima Sanda Usara ta baiyana haka a sanarwa ta musamman, ta mai cewa a zaman hukumar kula da NAHCON ne a ka dau matakin.

Sanarwar ta ce an mika takardun shaidar maida ma’aikatan wajen aiyukan su na asali inda a ka yi amanna matakin zai kara habaka kwazon ma’aikan hukumar.

Hakanan sanarwar ta ce an yi Karin girma ga wasu ma’aikan don yabawa irin kwazon da su ke nunawa kan aiki.

NAHCON karkashin jagorancin Farfesa Abdullahi Saleh Usman ta nanata kudurin tabbatar da kula da walwalar maniyyata aikin hajji.



BABBAN ZAUREN MDD YA AMINCE DA SHIRIN FARANSA DA SAUDIYYA NA DAWO DA TATTAUNAWAR KAFA KASAR FALASDINU

Babbar zauren majalisar dinkin duniya ya amince da shirin kasar Saudiyya da Faransa na dawo da tattaunawa don neman kafa kasar Falasdinu gefe da ta Isra’ila a ranar 22 ga watan nan.

Saudiyya da Faransa sun samu daidato da juna kan cewa kafa kasar Falasdinu mai ‘yanci ne zai kawo maslaha a fitinar Falasdinawa da Yahudawan Isra’ila.

Wannan duk na gudana ne yayin da lamuran tsaro su ka kara tabarbarewa don munanan hare-hare kan Gaza da kuma tsananin adawa daga Isra’ila da Amurka da ke zaiyana yunkurin a matsayin na cimma muradun siyasa.

Gabanin kada kuri’a don amincewa da dawo da tattaunawar, wakilin Saudiyya a majalisar Abdul’aziz Alwasil ya ce ba su da wata manufar marawa wani gefe baya amma sun dau matsayar ce don samar da maslaha mai dorewa tsakanin Falasdinawa da Isra’ila.

MUN CIMMA NASARAR CIKA MA’AUNIN KUDIN SHIGA NA BANA A WATAN AGUSTA-SHUGABA TINUBUShugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ...
03/09/2025

MUN CIMMA NASARAR CIKA MA’AUNIN KUDIN SHIGA NA BANA A WATAN AGUSTA-SHUGABA TINUBU

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatin sat a cimma nasarar cika ma’aunin kudin shiga da a ka tsara na bana a watan jiya na Agusta.

Shugaban na magana ne a fadar A*o Rock lokacin ganawa da ‘yan narkakkiyar jam’iyyar CPC ta marigayi tsohon shugaba Buhari da kuma makusantar marigayin karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Nasarawa Tanko Umar Almakura.

Shugaba Tinubu ya ce an cimma nasarar c eta hanyar fadada tattalin arziki don mafi tsokar kudin da a ka samu daga sassan da ke waje da man fetur ne.

A wasu sassan na tattalin arziki, shugaba Tinubu ya ce yanzu mutum ba ya bukatar sai ya san gwamnan babban banki Yemi Cardoso kafin ya samu kudin ketare wajen odar kayan cinikaiya.

Shugaban ya nuna yanzu loakcin amfani da dimbin kudi don kasuwancin kudin ketare ya wuce don dan kasa na iya sanin tabbacin halin da kasuwa ta ke ciki.

03/09/2025

LABARUN DUNIYA

MUN CIMMA NASARAR CIKA MA’AUNIN KUDIN SHIGA NA BANA A WATAN AGUSTA-SHUGABA TINUBU

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatin sat a cimma nasarar cika ma’aunin kudin shiga da a ka tsara na bana a watan jiya na Agusta.

Shugaban na magana ne a fadar A*o Rock lokacin ganawa da ‘yan narkakkiyar jam’iyyar CPC ta marigayi tsohon shugaba Buhari da kuma makusantar marigayin karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Nasarawa Tanko Umar Almakura.

Shugaba Tinubu ya ce an cimma nasarar c eta hanyar fadada tattalin arziki don mafi tsokar kudin da a ka samu daga sassan da ke waje da man fetur ne.

A wasu sassan na tattalin arziki, shugaba Tinubu ya ce yanzu mutum ba ya bukatar sai ya san gwamnan babban banki Yemi Cardoso kafin ya samu kudin ketare wajen odar kayan cinikaiya.

Shugaban ya nuna yanzu loakcin amfani da dimbin kudi don kasuwancin kudin ketare ya wuce don dan kasa na iya sanin tabbacin halin da kasuwa ta ke ciki.



WAJIBI NE KOWA YA SHIGA INSHORAR LAFIYA-DOKTA ALI PATE

Ministan lafiya Dokta Muhammad Ali Pate ya ce ya zama wajibi duk ‘yan Najeriya su shiga a dama da su a shirin inshorar lafiya.

Ministan na magana ne a taron zauren tattaunawa kan hanyoyin samar da kudi don kula da lafiyar al’umma da a ka gudanar a Abuja.

Dr.Pate ya ce sai wasu sun sadaukar don wasu su amfana kan kiwon lafiya don lamarin lafiya ya shafi kowa.

A nan Dr.Pate ya ce gwamnati za ta cigaba da daukar matakai don bunakasa lamuran kiwon lafiya da zai rage dawainiyar jama’a kan neman magani.

Taron ya bukaci ‘yan Najeriya su rika amfana da cibiyoyin kiwon lafiya su kuma hada hannu da jami’an lafiya don musamman rage mutuwar mata yayin haihuwa da cutukan da kan yi sanadiyyar rasa ran yara ‘yan kasa da shekara 5.

Kungiyoyin al’umma da ma wakilan ofishin kungiyar gwamnoni sun halarci taron da ya gudana a dakin taro na CONGRESS da ke Transcorp Hilton.



BA MA GOYON BAYAN CIN ZARAFIN MUTANE A SHOSHIYAL MIDIYA-MUSA H MUSA

Matashin mai yada labaru ta shoshiyal midiya Malam Musa H Musa ya ce ba daidai ba ne amfani da kafafen yanar gizo wajen cin zarafin jama’a.

Malam Musa na magana ne a bita da masu yada labaru ta yanar gizo na kungiyar JIBWIS a arewa ta tsakiya su ka gudanar a garin Keffi jihar Nasarawa.

A nan Musa ya ce bin diddigin mutum a kan sai an gano laifin sa ba manufa ce mai kyau don haka ya na da muhimmanci masu yada labaru a yanar gizo su guji hakan.

Masu gabatar da makala daban-daban sun yi jawabai a taron da karfafa yada gaskiya a labarum yanar gizo don gujewa yaudarar jama’a.

Kazalika an ga hankalin mahalarta muhimmancin bin ka’idojin rubutu da kuma yayata labaru masu muhimmanci da za su amfani zaman lafiya da cigaban kasa.

Shugaban tafiyar na kasa Ibrahim Baba Sulaiman ya bukaci amfani da darussan da a ka koyar da yin aiki tare don cimma nasarar rairaye karya daga labarum yanar gizo.

Ibrahim Baba Sulaiman ya ce babban shafin tafiyar wato JIBWIS NIGERIA na da fiye da mabiya 800,000 kuma duk labarum da a kan yayata sai an tantance sahihancin su.



ISRA’ILA TA KIRA DUBBAN SOJOJIN DA KE ZAMAN KWATA KWANA DON SHIRIN KWACE BABBAN BIRNIN GAZA

Isra’ila ta kira dubun dubatan sojojin ta da ke zaman jiran kwata kwana don shirin karshe na kwace ikon babban birnin Zirin Gaza.

Rahotanni sun baiyana cewa sojoji 40,000 sun fito don shiga wannan yakin na a yi tat a kare don karbe babban birnin.

Dama tuni sojojin Isra’ila su ka yi ta barin wuta a gefen birnin don shirin karbe shi gaba daya bisa muradin firaminista Benjamin Netanyahu wanda a ka ba shi shawara ya janye shirin amma ya toshe kunnen sa.

An samu musayar kalamai masu tsauri a taron majalisar tsaro da Netanyahu ya jagoranta, inda ministocin gwamnatin mai marmarin yaki su ka dage lallai a gaggauta kwace birnin na Gaza amma a gefe guda shugaban sojoji Eyal Zamir ya bukaci Netanyahu ya shiga sulhun tsagaita wuta.

Zamir da wasu ministoci 4 sun yi gargadin aukawa babban birnin na Gaza zai jefa rayuwar fursunonin da ke hannun Hamas a hatsari kuma hakan zai kara jigata sojojin da tuni yakin ya riga ya jijjiga su.

Zuwa yanzu fiye da Falasdinawa 62,000 sojojin Isra’ila su ka kashe tun fara wannan yakin a watan Oktoba na 2023.

Address

Utako District
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Manara RADIO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Manara RADIO:

Share

Category