12/05/2026
LABARUN DUNIYA
SHUGABA TINUBU YA SAUKA A NAIROBI KENYA DON TARON BUNKASA AFURKA
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sauka a babban birnin kasar Kenya, Nairobi don halartar taron bunkasa Afurka.
Taron dai mai taken FORWARD AFRICA a turance na da zummar tattaunawa kan hanyoyin bunkasa tattalin arzikin nahiyar Afurka ne.
Shugaban Kenya Williams Ruto da shugaban Faransa Emmanuel Macron ne za su jagoranci taron.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai yI amfani da damar wajen wasu zantawa da masu ruwa da tsaki na kasashe don nausa diflomasiyyar Najeriya gaba.
Ministoci da su ka hada da ta kasashen waje Bianca Ojukwu, na aikin noma Abubakar Kyari da na tattalin arzikin teku Adegboyega Oyetola na cikin tawagar shugaban.
Shugaba Tinubu dai ya isa Kenya daga ziyarar aiki da ya ke yI a kasashe uku kuma ciki da Faransa.
SHUGABA TINUBU YA NADA FAMADEWA A MATSAYIN MAI BA DA SHAWARA NA MUSAMMAN KAN TSARON CIKIN GIDA
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada Manjo Janar Adeyinka Famadewa mai ritaya a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida.
Wannan na kunshe a sanarwa daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya Mr.George Akume.
Sanarwar ta bayyana Famadewa a matsayin kwararre kan harkokin tsaro kuma ya ma yI aiki a matsayin shugaban ma'aikata na ofishin babban mai ba da shawara na kasa kan harkokin tsaro daga 2015-2021.
Shugaba Tinubu ya nuna amanna Famadewa zai yI amfani da kwarewarsa wajen inganta tsaro na cikin gida da aiki tare tsakanin sassan tsaro.
Sanarwar ba ta fayyace bambancin aikin Famadewa da na babban mai ba da shawara na kasa kan tsaro Malam Nuhu Ribadu ba.
Daga nazartar sanarwar Malam Nuhu Ribadu na da ayyuka mabambanta fiye da tsaron cikin gida don ya na taja muhimmiyar rawa da kasashen duniya kan inganta dangantakar diflomasiyyar tsaro da kasashe irin Amurka, nan Afurka da hulda da kasashen Larabawa.
PA FASIRABTI YA CIKA SHEKARU 100 A DUNIYA
Dattijon siyasar kasashen Yarbawa Pa Reuben Fasoranti ya cika shekaru 100 a duniya.
Shugaba Tinubu ya taya Fasoranti murnar cika shekaru 100 a duniya da gode ma sa bisa goyon baya da ya ke ba shi.
Pa Fasoranti na daga dattawa kalilan da su ka rage a mukarraban uban siyasar Yarbawa Chief Obafemi Awolowo.
Fasoranti jagora ne a kungiyar nan ta kare muradun Yarbawa wato Afenifere kuma ya yI jam'iyyar AG a jamhuriya ta farko sai UPN a jamhuriya ta biyu.
Dattijon ya yI digiri a harshen turanci da nazarin taswirsr duniya a jami'ar Badun inda ya zurfafa ilimi a Burtaniya da Australia.
TRUMP YA YI ALWASHIN MATSIN LAMBA KAN MASHIGAR HORMUZ
Shugaban Amurka Donald Trump ya yI alwashin cigaba da daukar matakan bude mashigar ruwan Hormuz don safarin jiragen dakon man fetur.
Wannan dai ya biyo bayan tangarda a yarjejeniyar neman sulhun dakatar da yaki kan Iran da ya kai mako na 10.
Trump ya bullo da salon rakiyar jiragen dakon mai don wuxewa ta Hormuz amma daga bisani sa'a 48 ya janye don bude babin diflomasiyya.
Trump ya ce Iran ba za ta iys farfado da shirinta na nukiliya ita kadai ba kuma ya na da yakinin za ta mika wuya a karshe.
A bangaren Iran da ke cigaba da rude mashigar Hormuz don tilasta Amurka ta janye tare ma ta hanyar wucewar jiragen ruwa, ta bukaci diyya ga barnar da a a ka yI ma ta a sanadiyyar wannan yaki da Amurka da Isra'ila su ka auka ma ta.
Rufe mashigar Hormuz ta haddasa dan karen tsadar man fetur a duniya