Khalifa TV

Khalifa TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Khalifa TV, TV Channel, Sani Abacha Road, Abuja.

Hajji 2026: Za a fara jigilar maniyyatan Najeriya ranar 3 ga Mayu daga Filin Jirgin Ogun​Hukumar Jin Dadin Alhazzai ta K...
28/04/2026

Hajji 2026: Za a fara jigilar maniyyatan Najeriya ranar 3 ga Mayu daga Filin Jirgin Ogun

​Hukumar Jin Dadin Alhazzai ta Kasa (NAHCON) ta sanar da cewa, za a fara jigilar maniyyata daga Najeriya zuwa Kasa Mai Tsarki domin aikin Hajjin bana na shekarar 2026 a ranar 3 ga watan Mayu.

​Tafiyar farko za ta tashi ne daga sabon Filin Jirgin Sama na Kasa-da-Kasa na Gateway da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun, inda kamfanin jirgin FlyNas zai kwashe maniyyatan jihar. Wannan shi ne karon farko da maniyyatan Jihar Ogun za su tashi kai-tsaye daga jiharsu tun bayan gina filin jirgin.

​Baya ga Jihar Ogun, sauran jiragen da za su tashi a wannan rana sun hada da Kamfanonin Umza da Max Air da za su kwashe maniyyatan jihohin Kogi da Nasarawa ​daga Abuja. Sai Kamfanin Air Peace zai kwashe maniyyatan Jihar Oyo daga Legas. ​Daga Birnin Kebbi, wani jirgin na FlyNas zai tashi da maniyyatan Jihar Kebbi.

​Yayin da ake shirin fara jigilar, tuni jami’an NAHCON da s**a hada da tawagar likitoci s**a sauka kasar Saudi Arabiya a yau Talata, 28 ga watan Afrilu, domin yin shirye-shiryen tarbar maniyyatan Najeriya.

​Hukumar ta fitar da wasu muhimman shawarwari kamar haka:

Tsarin Shiyya (Zones): Kowane kamfanin jirgi zai kwashe maniyyatan shiyya daya ne a lokaci guda. Da zarar an gama da shiyya aka koma gaba, jirgi ba zai sake dawowa wannan shiyyar ba. Duk maniyyacin da ya rasa jirginsa, zai dauki nauyin bin jirgin zuwa inda ya dosa ko kuma ya jira har sai an sake tsara tafiyarsa.

​Tsarin Rukunin Mutum 45: Dole ne kowane maniyyaci ya yi tafiya a cikin rukuninsa na mutum 45.

Katin Nusuk na maniyyata suna nan a shirye suna jiran isowarsu Saudi Arabiya.

Ana shawartar maniyyata su san sauran mambobin rukuninsu, sannan su tanadi lambobin wayar shugabannin rukuninsu da na jami’an jihohinsu.

​Shugaban hukumar NAHCON, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ya ba wa maniyyatan kasar tabbacin cewa hukumar ta kammala dukkan shirye-shiryen da s**a dace domin tabbatar da an gudanar da aikin Hajjin 2026 cikin nasara da sauki.

​A halin yanzu dai, maniyyata na ci gaba da shirin karshe na bankwana da iyalansu gabanin fara fita zuwa filayen jirgi a mako mai zuwa.

NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Domin Wayar da Kan Maniyyatan Aikin Hajji na 2026​Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhaz...
27/04/2026

NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Domin Wayar da Kan Maniyyatan Aikin Hajji na 2026

​Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON), Ambasada Ismail Yusuf Abba, ya sake jaddada aniyar hukumar na zurfafa fadakarwa da horar da maniyyata ta fuskar addini domin tunkarar aikin hajjin shekarar 2026.

​Shugaban ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, 22 ga watan Afrilun 2026, yayin taron kaddamar da Tawagar Malamai (Ulama Team) na aikin hajjin bana, wanda aka gudanar a dakin taro na gidan hajji da ke Abuja.

​Taron ya samu halartar manyan malaman Musulunci guda 120 da aka zabo daga sassan kasar nan, wadanda s**a hada da Farfesa Mansur Ibrahim Sokoto, Sheikh Bala Lau, Sheikh Abdulmuhyi Nasir (wanda ya wakilci Sheikh Sani Yahaya Jingir), Sheikh Abdulrahman Olanrewaju Ahmed, Sheikh Nasir Adam, Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe, Sheikh Usman Usman Dahiru Bauchi, da Dr. Isa Akindele Solahuddeen, da dai sauran manyan malamai.

​Babban makasudin taron shi ne tattauna yadda za a mayar da hankali wajen ilimantar da maniyyata da ba su horo na musamman.

Ambasada Abba ya dorawa malaman nauyin taimakawa hukumar wajen gudanar da darusan fadakarwa cikin harsuna daban-daban kafin tafiya da kuma lokacin gudanar da ayyukan hajji a kasa mai tsarki.

​Ya jaddada cewa malaman su tabbatar sun koya wa maniyyata sahihan rukunai da sharuddan aikin hajji dalla-dalla, domin su sauke farali yadda ya kamata.

Haka zalika, ya bukaci malaman da su kasance a shirye wajen ba da amsoshi ga tambayoyin alhazai, musamman idan s**a fuskanci kalubalen da ka iya shafar ingancin aikin hajjinsu.

​Baya ga ilimantarwa, tawagar malaman za ta shirya addu’o’i na musamman a wurare masu tsarki, musamman a filin Arfa, domin rokar wa Najeriya da shugabanninta zaman lafiya, hadin kai, tsaro, da bunkasar tattalin arziki.

​A nasa bangaren, Farfesa Bashir Umar ya bukaci malaman da su ja hankalin alhazai su yi addu'ar samun nasarar babban zaben shekarar 2027 da ke tafe, ganin cewa aikin hajjin na bana zai gudana ne a daidai lokacin da kasar ke shirin fuskantar zaben.

​Daga karshe, malaman sun jaddada muhimmancin shirya zukatan maniyyata ta fuskar hakuri, ikhlasi, da kuma sadaukar da kai ga Allah, inda s**a bayyana shirinsu na ganin 'yan Najeriya sun samu gamsasshen aikin hajji karbabbe.

24/02/2026

Address

Sani Abacha Road
Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Khalifa TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category