Malumfashi Post

Malumfashi Post Marubuci,Dan Jarida,Blogger,Malamin Makaranta.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UNAlhaji Hussani Sarkin Malamai Funtua Ya Rasu A Jihar KatsinaAllah Ya Yi Wa Alhaji Huss...
03/12/2022

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Alhaji Hussani Sarkin Malamai Funtua Ya Rasu A Jihar Katsina

Allah Ya Yi Wa Alhaji Hussani Sarkin Malamai Filin Kwallo Funtua Ta Jihar Katsina Rasuwa A Cikin Daren Yau Asabar.

Za'a Yi Jana'izarsa Da Misalin Karfe 11:00 Na Safiyar Gobe Lahadi.

Allah Ya Jikansa Da Rahama!

Sabuwar Jarida Mai Suna "Arewa Daily News Hausa"Ku shiga wannan link din kuyi Liked din shafin jaridar domin samun ingan...
03/12/2022

Sabuwar Jarida Mai Suna "Arewa Daily News Hausa"

Ku shiga wannan link din kuyi Liked din shafin jaridar domin samun ingantattun labarai na yankin Arewa;

👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇
https://www.facebook.com/Arewa-Daily-news-Hausa-105316078571847/

"Yankin Arewa A Yau" Sabuwar jarida ce da zata dinga kawo muku ingantattun labaran yankin Arewa, tare da sharhi fashin baki, wayar dakan al-ummar yankin, kan dukkannin wani abu da ya shige musu duhu.

Haka zalika jaridar zata dinga baku dama wurin isarda sakonninku zuwa ga inda kuke bukatan isarwa cikin sauki.

Muna Addu'ar Allah ya bamu sa'a da Nasara, mu gabatar da ayyukanmu cikin gaskiya da tsoron Allah. Amin

Sun Taba Wakiltar Mu Basuyi Komai Ba, Kuma Yanzu Sun Kawo Wani Suna so Ya Zama Su Bishi Chan Su Anshe Hakkin Al'umma____...
03/12/2022

Sun Taba Wakiltar Mu Basuyi Komai Ba, Kuma Yanzu Sun Kawo Wani Suna so Ya Zama Su Bishi Chan Su Anshe Hakkin Al'umma_____ Inji Hon. Malam Ya'u Ahmad Nowa

Shugaban Karamar Hukumar Dandume Jihar Katsina Hon. Malam Ya'u Ahmad Nowa Ya Furta Haka A Yayin Taron Bude Ofishin Yakin Neman Zaben Hon. Barrister Abubakar Ahmad Muhammad (Gardi) Dan Takarar Kujerar Majalisar Wakilai Mai Neman Wakiltar Kananan Hukumomin Funtua Dà Dañdume Jihar Katsina Karkashin Inuwar Jam'iyyar APC, Na Karamar Hukumar Dandume Wanda Masoya Da Magoya Bayansa S**a Gina Domin Bada Tasu Gudummawa, A Ranar Asabar 03/12/2022.

Inda Ya Chigaba Da Cewa, Dan Takarar Da S**a Kawo Bai Iya Bayyana Akwatunan Zaben Dake Mazabar Dantankari, Baisansu Ba, Ballantana Akwatunan Zaben Dake Karamar Hukumar Dandume Ko Funtua, To Ya Za'ayi Mutumin Da Baisan Yankunan Ba, Kuma Yace Zai Waklice Su, Bayan Ko Gida Baidashi A Karamar Hukumar Dandume,

Daga Karshe Ya Chigaba Da Cewa "Kada Ku Yarda Wani Ya Yaudareku Da Maganar Matsalar Tsaro, Domin Tun A Mulkin Jam'iyyar Su Aka Fara, Ni Ina Daya Daga Cikin Wanda Aka Kashe Ma Dan Uwa A Gona Lokachin Mulkinsu, Matsalar Tsaro Bata Da Nasaba Da Jam'iyya, Bace Muyi Addu'ar Allah Yakawo Mana Zaman Lapiya".

Ajawabin Hon. Barrister Abubakar Ahmad Muhammad (Gardi) Ya Bayyana Godiyarsa Ga Al'ummar Kananan Hukumomin Funtua Dà Dañdume Bisaga Amince Da Karamci Da Kyawawan Zato Da Sukeyi Agreshi, Tareda Godiya Ga Al'ummar Da S**a Samu Damar Halaktar Taron Bude Ofishin Yakin Neman Zabensa Daga Karshe Ya Rufe Da Addu'ar Nema Ma Kasa Zaman Lapiya.

Taron Yasamu Halaktar Shugaban Karamar hukumar Dandume Hon. Malam Ya'u Ahmad Nowa Da Shugaban Jam'iyyar APC Alh. Nasiru Garba Da Hon. Muntari Dandutse Wanda Ya Samu Wakilci Alh. Abdu Isah Funtua Da Katukan Katsina Hakimin Dandume Alhaji Jafaru Ibrahim Wanda Yasamu Wakilci Alh. Shamsuddeen Jafar (Mai Garin Jiruwa) Da Hon. Abubakar Wada Nas Funtua Dà Alh. Haruna Abdulrashida Da Alh. Ibrahim Mai Bula, Da Tawagar Kansilolin Karamar hukumar Dandume Da Sauran Maza Da Mata Da Dattijai Da Matasa Yan Gwagwarmaya Yan Asalin Kananan Hukumomin Funtua Dà Dañdume Da Sassan Jihar Katsina Da Kasa Baki Daya.

Ni a wajena duk ƴan Najeriya na ɗaukesu tamkar ƴaƴan dana haifa a ciki na babu bambanci kowa ɗana ne~Aisha Buhari. Ƙarin...
03/12/2022

Ni a wajena duk ƴan Najeriya na ɗaukesu tamkar ƴaƴan dana haifa a ciki na babu bambanci kowa ɗana ne~Aisha Buhari. Ƙarin bayani

Daga Mubarak Sama Bala

Bayan janye karar Aisha Buhari matashi Aminu zai gana da shugaba Buhari a fadar saMatashin dan jihar Jigawan da ya zagi ...
02/12/2022

Bayan janye karar Aisha Buhari matashi Aminu zai gana da shugaba Buhari a fadar sa

Matashin dan jihar Jigawan da ya zagi Hajiya Aisha Buhari, uwargidar shugaban kasa, Aminu Mohammed Adamu, ya samu yanci.

Aminu wanda tuni an sakeshi daga kurkukun Suleja zai gana da mijin Aisha, Shugaba buhari kafin ya koma wajen iyayensa, Kamar yadda Leadership, ta ruwaito.

Daga Mubarak Sama Bala

Wasu Mata Kenan Magoya Bayan Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Kaduna A Karkashin Jam'iyyar APC, Sanata Uba Sani
02/12/2022

Wasu Mata Kenan Magoya Bayan Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Kaduna A Karkashin Jam'iyyar APC, Sanata Uba Sani

WATA SABUWA: ƴan Najeriya basu girmama shugabanni da yin biyayya a garesu yadda ya k**ata, yanzu idan mutun ya isa ai ak...
02/12/2022

WATA SABUWA: ƴan Najeriya basu girmama shugabanni da yin biyayya a garesu yadda ya k**ata, yanzu idan mutun ya isa ai akwai mai Unguwa, ko Hakimi a inda yake yaje ƙofar gidansu ya zage su ko yaci mutuncin iyalinsu yaga idan za'a bar shi ya tafi ba tare da an ɗauki mataki a kansa ba.

Daga Mubarak Sama Bala

Bari mu Gwada Wanda yafi farin jini  wa zaku zaba ranar zabe tsakanin wadannan Yan Takarkarun na shugaban ƙasa?(A ) Atik...
02/12/2022

Bari mu Gwada Wanda yafi farin jini wa zaku zaba ranar zabe tsakanin wadannan Yan Takarkarun na shugaban ƙasa?

(A ) Atiku Abubakar

(B ) Sanata Rabi'u Musa kwankwaso

(C) Bola Ahmad Tunibu

(E) Peter Obi

Daga Mubarak Sama Bala

Ziyarar Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa A Ƙarƙashin Jam'iyyar APC, Sanata Bola Ahmed Tinubu Da Mataimakinsa Kashim Shettima A ...
01/12/2022

Ziyarar Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa A Ƙarƙashin Jam'iyyar APC, Sanata Bola Ahmed Tinubu Da Mataimakinsa Kashim Shettima A Birnin Yanaguwa Ta Jihar Bayelsa Yau Alhamis

Ban yarda a yiwa Aminu Muhammad shari'a a boye ba cewar Dr Hakim Baba AhmadDaga Abubakar Dan ArewaNa ce a yi wa Aminu Mo...
01/12/2022

Ban yarda a yiwa Aminu Muhammad shari'a a boye ba cewar Dr Hakim Baba Ahmad

Daga Abubakar Dan Arewa

Na ce a yi wa Aminu Mohammed shari’a yadda doka ta tsara, tunda an ce sai an tsugunar da shi.Shi ma idan an ci masa zarafin sa, a fitar masa da hakkin sa.Bana goyon bayan cin zarafin kowa, babba ko yaro, kuma ina so in ga ‘ya’yan mu sun samu tarbiyya mai kyau.Siyasar zamani da social media ba bujja bace a rika yin abin da Allah da al’adumnmu s**a hana. Wanda ke da iko kuma dole ne yayi adalci, kuma Ya tuna shi ma Allah zai yi masa hukunci.Haka kuma bai k**ata a nuna wa matasa dabiu’n da basu k**ata ba, saboda siyasa.
Wadanda ke ganin siyasa a cikin wannan maganar suna da laifi.Idan ana jin zafin shari’a Aminu, k**ata yayi mu sa ido mu ga an yi masa adalci. Idan akwai dokokin da ya karya, a fade su a koto kuma a ba lauyar shi dama ya kare shi.
Idan yayi laifi, bamu da hujjan da zamu ce kada a hukunta shi saboda irin siyasar sa ko tamu.Idan akwai wadanda zasu iya sa baki a samu sulhu, su yi, saboda da Allah Ya ce sulhu alheri ce.
Zage-zagen juna ba zai taimaki Aminu ba.Allah Ya nisance mu daga Shaidan.

Gwamnatin Najeriya Ta Gargadi 'Yan Siyasa Wajen Amfani Da 'Yan Bangar Siyasa,Daga Abbakar Aleeyu AnacheGwamnatin Najeriy...
01/12/2022

Gwamnatin Najeriya Ta Gargadi 'Yan Siyasa Wajen Amfani Da 'Yan Bangar Siyasa,

Daga Abbakar Aleeyu Anache

Gwamnatin Najeriya ta gargadi Gwamnonin jihohin kasar 26 da su kaucewa yin amfani da yan bangar siyasa wajen hana abokan hamayyarsu gudanar da tarurrukan yankin neman zabe musamman ganin lokacin zaben shekara mai zuwa na karatowa,

Mai baiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara akan harkokin tsaro Manjo Janar Babagana Monguno ya gabatar da wannan gargadi inda yake cewa an baza jami'an tsaro a fadin kasar domin murkushe duk wani yunkurin haifar da tashin hankali wajen zaben mai zuwa,

Monguno yace abin takaici ne yadda Gwamnonin ke amfani da karfin mulki wajen tirsasawa abokan adawarsu maimakon gabatar da ayyukan da s**a yi domin janyo hankalin masu kada kuri'u su zabi wadanda suke marawa baya,

Rahotanni sun ce jam'iyyun adawa na cigaba da fuskantar matsaloli sosai wajen tallata yan takararsu ta hanyar manna fastoci ko ta kafofin yada labarai ko kuma gudanar da tarurrukan yankin neman zabe,

A makwannin baya ne kwamitin wanzar da zaman lafiya dake karkashin jagorancin tsohon shugaban kasa Janar Abddulsalam Abubakar ya jagoranci jam'iyyun siyasar da kuma yan takarar sun a shugaban kasa wajen rattaba hannu akan yarjejeniyar kaucewa tashin hankali lokacin yankin zaben da kuma yayin gudanar da zaben,

Har ila yau an gudanar da irin wadannan bukukuwan rattaba hannu a matakan jihohi domin tabbatar da cewar shugabanin siyasar da yan takara sun mutunta dokar kaucewa tashin hankalin ko tinzira magoya bayansu haifar da rigima,

Sai dai rahotanni dake fitowa daga wasu jihohi na nuna yadda ake kaucewa yarjejeniyar wajen musgunawa jam'iyyun dake adawa da gwamnatin dake ci a matakan jihohin,

DA ƊUMI DUMINTA: ƙungiyar ɗaliban Najeriya NANS zasu fara gudanar da zanga - zanga ranar litinin game da lamarin k**a wa...
01/12/2022

DA ƊUMI DUMINTA: ƙungiyar ɗaliban Najeriya NANS zasu fara gudanar da zanga - zanga ranar litinin game da lamarin k**a wannan matashin Aminu muhammad wanda yayi kalaman ɓantanci ga Aisha Buhari

Me za ku ce ???

Daga Mubarak Sama Bala

Yan Najeriya Sun Yi Allah Wadai Game Da Tasa Keyar Aminu Da Ake Zargi Ya Caccaki Aisha Buhari A Kafar Sadarwa Ta Tiwita ...
01/12/2022

Yan Najeriya Sun Yi Allah Wadai Game Da Tasa Keyar Aminu Da Ake Zargi Ya Caccaki Aisha Buhari A Kafar Sadarwa Ta Tiwita Zuwa Gidan Yari,

Daga Abbakar Aleeyu Anache

Wannan batu na k**a matashin mai suna Muhammad Aminu tare da gurfanar da shi a gaban kulliya ya haifar da muhawara mai zafi a kafofin yada labarai da na sada zumunta a Najeriya,

Inda da dama ke ganin an wuce gona da iri wajen daukar hukunci lakada masa duka daga bisani kotu ta bada umurnin a tura shi gidan yari kafin a cigaba da yi masa shari'a,

Tuni dai kungiyoyin kare hakkin bil'adama ta kasa da kasa a Najeriya irinsu Amnesty international su ka yi Allah wadai da matakin k**a Muhammad tare da zargin an take masa hakkinsa na bil'adama,

Na daya dai an ce wannan laifin a jigawa aka yi sannan aka aika jami'an tsaro s**a k**a yaron s**a je su ka kulle shi aka rika jibgar sa wannan ya keta dokar kasa ya keta dokar bil'adama a cewar Auwal Musa Rafsanjani shugaban gudanarwa na kungiyar Amnesty international,

Bayanai na nuni da cewa uwar gidan shugaban kasa Aisha Buhari ce ta bai wa jami'an tsaro umurnin dauko mata Aminu daga jihar jigawa bayan ya wallafa wasu kalamai a kanta na zargin ta yi rub da cikin da kudin jama'a kalamai da ba su mata dadi ba,

Da ta ke tsokaci kan lamarin Hajiya Naja'atu Muhammad kwamishiniya a hukumar yan sandan kasar ta ce ya k**ata a k**a uwar gidan shugaban kasar saboda ta keta doka ita kanta,

GAYYATA !! GAYYATA !!!Daya Daga Cikin Jigon Jam'iyyar APC A Karamar hukumar Dandume Jihar Katsina Hon. Abduljalil Ahmad,...
01/12/2022

GAYYATA !! GAYYATA !!!

Daya Daga Cikin Jigon Jam'iyyar APC A Karamar hukumar Dandume Jihar Katsina Hon. Abduljalil Ahmad, Zai Angonce Da Amaryarsa Malama Shafa'atu Lawal

Za'a Daura Ranar:- 04/12/2022

Wajen Daura Aure:- Kwakwaci Kusada Asasiddeen Islamiya Gwarjo Jihar Kano

Lokaci: 12:00 Na Rana.

Allah Yabada Ikon Zuwa!

Ina kira ga ɗaukacin ƴaƴa na ƴan Najeriya Maza da Mata yara da manya akan su zama masu ɗa'a da dattako don samar da al'u...
01/12/2022

Ina kira ga ɗaukacin ƴaƴa na ƴan Najeriya Maza da Mata yara da manya akan su zama masu ɗa'a da dattako don samar da al'umma ta gari.

Sannan su yafe mana kura kuren da muka yi~ Aisha Buhari

Daga Mubarak Sama Bala

Nima Uwa ce k**ar ko wacce Uwa, na haifa inada zuri'a kuma ƴaƴana suna jin zafi idan aka taɓa mutunci na k**ar yadda kow...
01/12/2022

Nima Uwa ce k**ar ko wacce Uwa, na haifa inada zuri'a kuma ƴaƴana suna jin zafi idan aka taɓa mutunci na k**ar yadda kowa yake ji idan aka taɓa mutuncin mahaifi ko mahaifiyarsa.

Cin mutuncin mutane ba abune mai kyau ba ko a addinance ya k**ata kowa ya san wannan.

Daga Mubarak Sama Bala

Masu Gonakin Da A Ka Gano Man Fetur A Arewacin Najeriya Sun Koka,Daga Abbakar Aleeyu AnacheMako guda kenan da kaddamar d...
01/12/2022

Masu Gonakin Da A Ka Gano Man Fetur A Arewacin Najeriya Sun Koka,

Daga Abbakar Aleeyu Anache

Mako guda kenan da kaddamar da shirin hako man fetur a jihohin Bauchi da Gombe da ke arewacin Najeriya

Sai dai mutanen da aka yi amfani da gonakinsu da filayensu wajen gudanar da aikin sun bukaci a biya su diyya,

Sai dai an samu rudani wajen biyan diyyar yayin da wasu s**a karbi hakkokin su inda wasu ke dakon nasu kason,

Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani Isa Ali Ibrahim, a lokacin da ya kai wata ziyarar aiki, wajen Shugabar wata ...
30/11/2022

Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani Isa Ali Ibrahim, a lokacin da ya kai wata ziyarar aiki, wajen Shugabar wata Jami'ar kimiyya da fasaha da ke Kasar Masar, Farfesa Reem Bahgat.

📸 Ma'aikatar Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share