One News Hausa

One News Hausa Ra'ayoyinku.

08064672794 (WhatsApp Zalla)
(2)

ONE NEWS HAUSA Jarida ce dake kawo muku labarai da ɗumi-ɗumi, rahotannin gida da na waje a cikin harshen Hausa, ƙarƙashin Kamfanin 5STARS MEDIA PRODUCTION✅️

DOMIN TALLATA:
Kasuwancinku.

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta damke  wani mutum da ake zargi da yin basaja a matsayin jami’in ’yan sanda tare da da...
09/09/2026

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta damke wani mutum da ake zargi da yin basaja a matsayin jami’in ’yan sanda tare da damfarar masu neman aiki, ta hanyar yi musu alkawarin samar musu da guraben aikin ’yan sanda.

Ana zargin mutumin da amfani da hotunan jami’an ’yan sanda da aka yi wa kwaskwarima ta hanyar fasahar AI, domin ya nuna kansa a matsayin jami’in rundunar tare da ƙara wa ikirarin nasa sahihanci.

A cewar rundunar, wanda ake zargin ya dade yana tuntuɓar mutane tare da neman kuɗi ko wasu bayanai, bisa alkawarin zai taimaka musu wajen samun aikin ’yan sanda.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

Sanarwar ta ce bayan rundunar ta samu bayanai kan lamarin, jami’an tsaro s**a gudanar da bincike, wanda ya kai ga cafke wanda ake zargin.

Rundunar ta gargadi jama’a da su yi taka-tsantsan da mutanen da ke neman kuɗi ko bayanan sirri da sunan samar da aikin yi, musamman ta kafafen sada zumunta.

Ta kuma shawarci masu neman aiki da su tabbatar da sahihancin duk wani bayani game da ɗaukar ma’aikata daga hukumomin da abin ya shafa, domin kauce wa fadawa hannun masu damfara.

A ranar Talata, 8 ga Satumba, aka buɗe ƙofar soma yaƙin neman zaɓen gwamna da ’yan Majalisun Dokokin Jihohi a faɗin Naje...
09/09/2026

A ranar Talata, 8 ga Satumba, aka buɗe ƙofar soma yaƙin neman zaɓen gwamna da ’yan Majalisun Dokokin Jihohi a faɗin Najeriya, bisa jadawalin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fitar.

A cewar jadawalin INEC na zaɓen 2027, an fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da ’yan Majalisar Tarayya tun ranar 19 ga Agusta.

Jihohi 28 ne za su gudanar da zaɓen gwamna, inda ’yan takara za su fara gabatar da manufofinsu ga masu zaɓe ta hanyar taruka, kafafen yaɗa labarai da sauran hanyoyin neman ƙuri’a.

Jam’iyyun APC, NDC da ADC na daga cikin manyan jam’iyyun da s**a tsayar da ’yan takarar gwamna a jihohin 28.

Sai dai wasu manyan jam’iyyun har yanzu ba su kammala kafa ko ƙaddamar da kwamitocin yaƙin neman zaɓensu ba, duk da fara lokacin yakin neman zaɓen.

Rahotanni sun ce APC na nazarin wasu naɗe-naɗen da ta yi a kwamitin yaƙin neman zaɓenta bayan samun koke-koke kan wasu mambobin kwamitin.

Haka kuma, NDC, ADC da PDP ba su ƙaddamar da wasu daga cikin tsare-tsaren yaƙin neman zaɓensu ba.

Masana siyasa na danganta jinkirin da rikice-rikicen da s**a biyo bayan zaɓukan fidda gwani, ƙarancin kuɗi da tattaunawar ƙulla ƙawance gabanin zaɓen.

Aminiya ta ruwaito cewa ba za a gudanar da zaɓen gwamna a jihohin Imo, Ondo, Osun, Bayelsa, Edo, Kogi, Ekiti da Anambra ba, saboda jadawalin zaɓensu ya bambanta da na sauran jihohin.

Dalibai 44 na makarantar M***a da ke ƙaramar hukumar Askira-Uba a jihar Borno, sun cika kwanaki 117 a hannun ’yan ta’add...
09/09/2026

Dalibai 44 na makarantar M***a da ke ƙaramar hukumar Askira-Uba a jihar Borno, sun cika kwanaki 117 a hannun ’yan ta’adda tun bayan da aka sace su a ranar 5 ga watan Mayun 2026.

Rahotanni sun ce ’yan ta’addan sun kai hari makarantar tare da yin awon gaba da ɗaliban lamarin da ya jefa iyaye da sauran al’ummar yankin cikin fargaba.

Tun daga lokacin da aka sace su, iyalan ɗaliban ke ci gaba da jiran ganin an kuɓutar da ’ya’yansu, yayin da ake neman bayanai kan halin da suke ciki.

Tsawon kwanaki 117 da ɗaliban s**a shafe a hannun masu garkuwa da su ya ƙara janyo kira ga hukumomin tsaro da gwamnatin jihar Borno da su ɗauki matakan gaggawa domin tabbatar da ganin an dawo da ɗaliban lafiya.

Lamarin ya kuma sake haifar da damuwa kan tsaron makarantu a yankunan da ke fama da hare-haren ’yan ta’adda a arewa maso gabashin Najeriya.

"Har ga Allah farin jinina a filin kada kuri'a ya fi a dandalin sada zumunta domin duka haka alkaluma su ka nuna."- In j...
09/09/2026

"Har ga Allah farin jinina a filin kada kuri'a ya fi a dandalin sada zumunta domin duka haka alkaluma su ka nuna."- In ji Farfesa Isah Ali Pantami, ɗan takarar Gwamna a Gombe a jam'iyyar PDP.

Kasashen Turai 12 sun sanar da shirin kakaba takunkumin kasa-kasa kan cinikayyar kayayyakin da s**a fito daga garuruwan ...
09/09/2026

Kasashen Turai 12 sun sanar da shirin kakaba takunkumin kasa-kasa kan cinikayyar kayayyakin da s**a fito daga garuruwan da Isra’ila ta kafa da ake kallonsu a matsayin wadanda s**a saba da dokokin kasa da kasa.

Ministan harkokin wajen Faransa, Jean-Noël Barrot, ne ya bayyana hakan a ranar Talata, bayan kasashen 12 sun fitar da wata sanarwa ta hadin gwiwa.

Kasashen sun hada da Faransa da Birtaniya da Canada da Denmark da Spain da Finland da Ireland da Iceland da Norway da Poland da Portugal da Sweden.

Sun ce suna duba yiwuwar daukar matakan kasa-kasa na hana ko takaita cinikayyar kayayyakin da aka samar a wadannan garuruwa da kuma goyon bayan irin wannan mataki a matakin Tarayyar Turai.

Kasashen sun kuma yi maraba da matakan da tuni wasu kasashe, ciki har da Ireland da Spain da Netherlands da Norway da Belgium s**a riga s**a dauka kan kayayyakin da s**a fito daga matsugunan.

"Ni dai ban ga dalilin da zai sa ka ajiye Atiku Abukakar a 2027, ka ɗauki Tinubu ba, idan kana da cikakken hankali." –Sa...
08/09/2026

"Ni dai ban ga dalilin da zai sa ka ajiye Atiku Abukakar a 2027, ka ɗauki Tinubu ba, idan kana da cikakken hankali." –Saratu Hashimu

Me zaku ce?

Shahararren mawaƙin hausa a Najeriya, Ado Isa Gwanja, ya bayyana hakan ne a shafinsa na Facebook a ranar Talata, biyo ba...
08/09/2026

Shahararren mawaƙin hausa a Najeriya, Ado Isa Gwanja, ya bayyana hakan ne a shafinsa na Facebook a ranar Talata, biyo bayan jita-jitar da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta cewa yana fama da matsananciyar rashin lafiya.

Progress Radio ta tuntuɓi makusantan Gwanja kan batun, kuma sun tabbatar da cewa yana cikin ƙoshin lafiya.

"Zaman duniya na buƙatar mutum ya riƙe mutuncinsa da darajarsa, kada ka ɓata lokacinka wajen neman yardar kowa. Ka rayu bisa gaskiya da kyakkyawar zuciya," In ji Gwanja.

Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti kuma tsohon Ministan Ma’adinan Ƙasa, Kayode Fayemi, ya bayyana alkawarin ɗan takarar shugaban...
08/09/2026

Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti kuma tsohon Ministan Ma’adinan Ƙasa, Kayode Fayemi, ya bayyana alkawarin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, na dawo da tallafin man fetur a matsayin dabarar siyasa ta neman kuri’u, ba manufar tattalin arziki ba.

Fayemi ya kwatanta matakin na Atiku da tikitin Muslim-Muslim.da jam’iyyar APC ta yi amfani da shi a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Ya bayyana hakan ne a wata hira da shirin Prime Time na Arise Television ranar Litinin.

Fayemi ya ce alkawarin dawo da tallafin man fetur zai iya samun karɓuwa daga ’yan Najeriya da cire tallafin ya fi shafa, musamman masu ƙaramin ƙarfi da ke fama da tsadar rayuwa.

Sai dai ya sake jaddada cewa yana goyon bayan cire tallafin man fetur, yana mai cewa ya daɗe yana fafutukar ganin an cire shi tun lokacin da yake shugaban ƙungiyar gwamnonin Najeriya.

A cewarsa, Shugaba Bola Tinubu ya gaji wani aiki da gwamnatin da ta gabata ta riga ta kammala a kan cire tallafin, amma ya ce matsalar da yake da ita ita ce yadda aka aiwatar da manufar.

Fayemi ya kuma ce tun kafin cire tallafin, gwamnonin jihohi sun yi aiki tare da gwamnatin tarayya da Bankin Duniya wajen samar da wani tsarin tallafa wa masu ƙaramin ƙarfi, domin rage musu radadin tasirin cire tallafin.

Ya ce Atiku na amfani da wahalhalun tattalin arzikin da ’yan Najeriya masu ƙaramin ƙarfi ke fuskanta wajen samun goyon bayan jama’a ta hanyar alkawarin dawo da tallafin.

Fayemi ya ce yawancin ’yan Najeriya ba sa mayar da hankali kan muhawarar tattalin arziki da ake yi kan tallafin, illa dai suna son samun damar biyan bukatun yau da kullum, ciyar da iyalansu da kuma tura ’ya’yansu makaranta.

Ya kuma danganta talauci da rashin daidaito da matsalar tsaro, yana mai cewa matsin tattalin arziki na daga cikin abubuwan da ke taimakawa wajen ci gaba da samun ayyukan ’yan ta’adda da ’yan bindiga a Najeriya.

Gwamnatin Jihar Kano ta yanke shawarar kafa karin sansanonin sojoji tare da tura jami’an tsaron dazuzzuka zuwa kananan h...
08/09/2026

Gwamnatin Jihar Kano ta yanke shawarar kafa karin sansanonin sojoji tare da tura jami’an tsaron dazuzzuka zuwa kananan hukumomin da ake fama da matsalolin tsaro.

An cimma wannan matsaya ne a wani taro da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi da shugabannin kananan hukumomi 44 na jihar ranar 5 ga Satumba, 2026.

Kwamishinan kananan hukumomi da harkokin Sarauta, Muhammed Tajo Othman, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai.

Taron ya samu halartar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Kwamishinan Kananan Hukumomi da Harkokin Sarauta, da kuma Akanta-Janar na jihar.

A cewar kwamishinan, matakan tsaron sun biyo bayan tattaunawar da Gwamna Yusuf ya yi da Ministan tsaro na Najeriya.

Gwamnatin ta ce sabon tsarin tsaron za ta taimaka wajen karfafa tsarin da ake da shi na rundunar ’yan sanda da kuma jami’an tsaron unguwanni, domin samun daukin gaggawa yayin barazanar tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Haka kuma, gwamnatin ta amince da kafa cibiyoyin CBT da ICT a kowace daga cikin kananan hukumomi 44 na jihar, inda ta ce tuni aka bayar da kwangilolin ayyukan, kuma za a fara su nan take.

Address

Abuja
740102

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when One News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to One News Hausa:

Shortcuts

Share