One News Hausa

One News Hausa Ra'ayoyinku.

08064672794 (WhatsApp Zalla)
(3)

ONE NEWS HAUSA Jarida ce dake kawo muku labarai da ɗumi-ɗumi, rahotannin gida da na waje a cikin harshen Hausa, ƙarƙashin Kamfanin 5STARS MEDIA PRODUCTION✅️

DOMIN TALLATA:
Kasuwancinku.

Ƙasar Amurka ta sake tabbatar da ƙudurinta na ci gaba da haɗin gwiwa da Najeriya a fannin yaƙi da ta’addanci, tana mai j...
07/06/2026

Ƙasar Amurka ta sake tabbatar da ƙudurinta na ci gaba da haɗin gwiwa da Najeriya a fannin yaƙi da ta’addanci, tana mai jaddada muhimmancin tsaro da kare muradun ƙasashenta tare da abokan hulɗarta na duniya.

A cikin wata sanarwa da rundunar sojin Amurka a Afirka (AFRICOM) ta fitar, ta bayyana cewa ayyukan haɗin gwiwa da Rundunar Sojin Najeriya a yankin Arewa maso Gabas na nuna muhimmancin ci gaba da aiki tare domin shawo kan matsalar rashin tsaro.

Sanarwar ta ce kasashen biyu sun ƙuduri aniyar ci gaba da aikin haɗin gwiwa wajen gano da murkushe barazanar ‘yan ta’adda, musamman ƙungiyoyin ISWAP da Boko Haram da ke addabar yankin.

Rahotanni sun nuna cewa kwanan nan an ƙara gudanar da wasu hare-haren haɗin gwiwa da s**a yi sanadiyyar hallaka wasu manyan kwamandojin ‘yan ta’adda a yankin.

Wani Ɗan Takara Me Yafi Dacewa Da Najeriya A Zaɓen 2027?A: PDPB. APCC. ADCD. NDCNajeriya Ina Mafita?
07/06/2026

Wani Ɗan Takara Me Yafi Dacewa Da Najeriya A Zaɓen 2027?

A: PDP

B. APC

C. ADC

D. NDC

Najeriya Ina Mafita?

Allah Ya yi wa Hajiya Salma Hassan rasuwa, wadda ta kasance ‘yar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Birniwa/Guri/Kirikas...
07/06/2026

Allah Ya yi wa Hajiya Salma Hassan rasuwa, wadda ta kasance ‘yar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Birniwa/Guri/Kirikasamma a Jihar Jigawa, Hon. Abubakar Hassan Fulata.

Marigayiyar ta rasu ne a daren ranar Asabar, inda ta bar mijinta Salim tare da ‘ya guda ɗaya.

A cewar sanarwar da iyalanta s**a fitar, za a gudanar da sallar jana’izarta da misalin ƙarfe 1:30 na ranar yau Lahadi, a Masallacin Uthman Bin Affan da ke kusa da Banex Plaza a Aminu Kano Crescent, Wuse 2, Abuja.

Muna roƙon Allah Ya gafarta mata, Ya rahamta ta, Ya kuma sa Aljanna ce makomarta, Ya ba iyalanta hakurin jure wannan babban rashi.

Tsohon gwamnan jihar Ebonyi kuma ministan ayyuka na yanzu, Engr. David Umahi, ya ce sai da lokacin zaɓe yazo tukunna ras...
07/06/2026

Tsohon gwamnan jihar Ebonyi kuma ministan ayyuka na yanzu, Engr. David Umahi, ya ce sai da lokacin zaɓe yazo tukunna rashin tsaro ke ƙara ta’azzara, amma duk da haka suna yiwa shugaban ƙasa Tinubu fatan nasara tare fatan bayyana waɗanda suke da hannu a lamarin tabarbarewar tsaro.

“Matsalar rashin tsaro ba ta fara a gwamnatin Shugaba Tinubu ba. Me ya sa duk lokacin da zaɓe ke gabatowa, matsalar rashin tsaro ke ƙaruwa? Wannan ba adalci ba ne. Allah na kallon waɗanda ke da hannu a wannan rashin tsaro. Muna yi wa Shugaba Tinubu addu’a", Inji shi.

Najeriya Ina Mafita?

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya buƙaci mambobin harkar shari’a da su rungumi nauyin da ke kansu wajen gina ƙ...
07/06/2026

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya buƙaci mambobin harkar shari’a da su rungumi nauyin da ke kansu wajen gina ƙasa, yana mai jaddada cewa makomar Najeriya tana rataye ne kan hukumomin Shari'a, da gina adalcin da martaba bangaren.

Jonathan ya yi wannan kira ne a ranar Asabar yayin da yake jawabi a wajen bikin buɗe Makon Shari’a na 2026 na reshen Nigerian Bar Association na Yenagoa a Jihar Bayelsa State.

Da yake jawabi a wani zaman tattaunawa, tsohon shugaban ƙasar ya buƙaci lauyoyi da jami’an shari’a da su kiyaye ƙa’idojin adalci, gaskiya da bin doka wajen gudanar da ayyukansu.

Ya bayyana mambobin kotuna da lauyoyi a matsayin masu kula da tsarin doka da ka’idojin ƙasa.

A cewarsa, ci gaba da zaman lafiyar ƙasa sun dogara ne da ikon cibiyoyi su yi aikinsu cikin ‘yanci da inganci ba tare da tsoma bakin da bai dace ba.

Najeriya Ina Mafita?
—ATP Hausa

Tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, ya yi kira ga gwamnatin Najeriya da kuma ƙasashen duniya da su haɗa k...
07/06/2026

Tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, ya yi kira ga gwamnatin Najeriya da kuma ƙasashen duniya da su haɗa kai wajen magance matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara a sassan ƙasar.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Dalung ya bayyana damuwa kan yadda ‘yan bindiga, ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane ke ci gaba da kai hare-hare a yankuna daban-daban, lamarin da ke jawo asarar rayuka da raba mutane da muhallansu.

Ya jaddada cewa kundin tsarin mulkin Najeriya ya ɗora wa gwamnati nauyin kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa, inda ya buƙaci a nuna ƙwarin gwiwa da ɗaukar matakan da s**a dace domin kawo ƙarshen matsalar tsaro.

Dalung ya kuma yi nuni da dokokin ƙasa da ƙasa, musamman tsarin Majalisar Ɗinkin Duniya na “Responsibility to Protect (R2P)”, inda ya buƙaci a ba Najeriya tallafi ta hanyar doka da haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa domin dawo da zaman lafiya.

Ya ƙara da cewa magance matsalar tsaro a Najeriya na buƙatar haɗin kai, gaskiya da jajircewa domin kare rayukan jama’a da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a ƙasar.

Nafisat Abdullahi ta bayyana a cikin wani faifan bidiyo cewa maza sune matsalolin wannan duniyar, idan aka kwashe duk ma...
07/06/2026

Nafisat Abdullahi ta bayyana a cikin wani faifan bidiyo cewa maza sune matsalolin wannan duniyar, idan aka kwashe duk maza aka mayar da su wata duniya ta daban, hakan zai kawo ƙarshen matsalolin da duniyar ke fama da shi.

Jarumar ta yi wannan furuci ne a cikin wata tattaunawa da ta janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda wasu s**a ɗauki maganar a matsayin raha ko ra'ayi na kashin kai, yayin da wasu kuma s**a nuna rashin amincewarsu da kalaman.

Maganar ta ci gaba da jan hankalin masu amfani da kafafen sada zumunta, inda ake ta muhawara kan ko furucin na nuni da gaskiyar matsalolin da ake fuskanta a duniya ko kuma magana ce ta barkwanci da ta fito daga yanayin tattaunawar, kamar yadda Sawaba Radio ta naƙalto.

Najeriya Ina Mafita?

Babajide Sanwo-Olu, gwamnan jihar Legas, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su kasance a haɗe tare da mara wa Shugaba Bola A...
07/06/2026

Babajide Sanwo-Olu, gwamnan jihar Legas, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su kasance a haɗe tare da mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da hukumomin tsaro baya wajen yaki da ta’addanci da tashin hankali a ƙasar.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Sanwo-Olu ya ce matsalolin tsaro da ake fuskanta a sassa daban-daban na ƙasar bai kamata su rage ƙudurin ’yan Najeriya ba.

Ya ce dole ne a guji kallon batun tsaro ta fuskar siyasa ko bangaranci, yana mai cewa masu aikata laifuka na kai hari ga kowa ba tare da la’akari da bambancin siyasa ba.

Gwamnan ya nuna tausayawa ga waɗanda abin ya shafa, tare da yin kira da a yi addu’a ga malamai da ɗaliban da aka sace a ƙaramar hukumar Oriire ta Jihar Oyo.

Ya ce Najeriya ta taɓa fuskantar matsaloli masu tsanani a baya kuma ta rika shawo kansu, don haka za ta kuma shawo kan halin da ake ciki yanzu.

Sanwo-Olu ya jaddada cewa gwamnati kaɗai ba za ta iya kayar da masu laifi ba tare da haɗin kan al’umma, musamman ta hanyar bayar da bayanan sirri.

Ya kuma yi kira ga matasa da iyalai da su kasance masu fata da juriya, yana mai tabbatar da cewa Najeriya za ta yi nasara a wannan yaƙi da rashin tsaro.

Rahotanni daga Jihar Borno sun tabbatar da cewa ƙungiyar Boko Haram ta saki mata da yara 416 da ta yi garkuwa da su a ya...
07/06/2026

Rahotanni daga Jihar Borno sun tabbatar da cewa ƙungiyar Boko Haram ta saki mata da yara 416 da ta yi garkuwa da su a yankin Ngoshe da ke jihar.

Wani shugaban matasa a yankin ya tabbatar da sakin mutanen, inda ya bayyana cewa an sako su ne a ranar 6 ga watan Yuni. Sai dai ba a bayyana cikakken bayanin yadda aka gudanar da sakin ba ko kuma sharuɗan da s**a biyo baya.

Mazauna yankin sun bayyana jin daɗi tare da sauƙin zuciya bisa dawowar waɗanda aka sace, inda aka yi kira da a ƙara ƙoƙari wajen tabbatar da tsaro a yankunan karkara.

Hukumomi ba su fitar da cikakken bayani ba kan lamarin zuwa lokacin hada wannan rahoto, yayin da ake ci gaba da bibiyar halin da lamarin ke ciki.

07/06/2026

Ko da Kuɗi ko ba kuɗi Tinubu za mu zaɓa 2027, za mu yi shi dan Allah ne, In Ji wasu mata a Najeriya.

Najeriya Ina Mafita?

Address

Abuja
740102

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when One News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to One News Hausa:

Share