07/06/2026
Ƙasar Amurka ta sake tabbatar da ƙudurinta na ci gaba da haɗin gwiwa da Najeriya a fannin yaƙi da ta’addanci, tana mai jaddada muhimmancin tsaro da kare muradun ƙasashenta tare da abokan hulɗarta na duniya.
A cikin wata sanarwa da rundunar sojin Amurka a Afirka (AFRICOM) ta fitar, ta bayyana cewa ayyukan haɗin gwiwa da Rundunar Sojin Najeriya a yankin Arewa maso Gabas na nuna muhimmancin ci gaba da aiki tare domin shawo kan matsalar rashin tsaro.
Sanarwar ta ce kasashen biyu sun ƙuduri aniyar ci gaba da aikin haɗin gwiwa wajen gano da murkushe barazanar ‘yan ta’adda, musamman ƙungiyoyin ISWAP da Boko Haram da ke addabar yankin.
Rahotanni sun nuna cewa kwanan nan an ƙara gudanar da wasu hare-haren haɗin gwiwa da s**a yi sanadiyyar hallaka wasu manyan kwamandojin ‘yan ta’adda a yankin.