03/06/2026
A cikin wata sanarwa da mai taimakawa Atiku na musamman kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce duk da cewa INEC ta yi ƙoƙarin kwantar wa ‘yan Najeriya da hankali da cewa ba a yi kutse daga cikin tsarin bayananta ba, amma a lokaci guda ta amince cewa an samu shiga cikin muhimman bayanan masu kaɗa ƙuri’a ta hanyar amfani da sahihan bayanan shiga (credentials) na jami’anta, sannan aka fitar da su ba tare da izini ba.
Ya ce wannan amincewa daga INEC ta haifar da tambayoyi masu yawa fiye da amsoshin da ta bayar.
“Sanarwar INEC ta tabbatar da cewa wannan batu ya wuce zato ko jita-jita.
Hukumar ta amince cewa an shiga bayanan masu kaɗa ƙuri’a ta hanyar bayanan shiga da aka bai wa ma’aikatan da ke aikin rajistar CVR, sannan aka fitar da bayanan ba tare da izini ba. Wannan kaɗai ya isa ya tayar da hankalin kowane ɗan Najeriya,” in ji shi.
Atiku ya bayyana cewa rashin samun kutse daga waje ba ya rage girman matsalar, sai ma ya ƙara tsananta ta, domin har yanzu akwai tambayoyi da ba a amsa ba dangane da tsarin tsaro na cikin gida, kariyar bayanai da kuma yiwuwar katsalandan na siyasa da gangan.
Ya ƙara da cewa: “Abin da ya sa ba za a iya yin watsi da wannan batu ba shi ne, bayanan da ake magana a kansu ba wani mai tona asiri (whistleblower), ɗan jarida mai bincike ko wata hukumar yaƙi da cin hanci ba ce ta fitar da su. Mista Lere Olayinka, mai magana da yawun Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ne ya wallafa su a bainar jama’a.”
Atiku ya kuma tunatar da cewa kwanaki kaɗan kafin wannan cece-kuce ta taso, Minista Wike ya bayyana da cikakken yaƙini cewa Atiku Abubakar ba zai samu ko kashi 10 cikin 100 na ƙuri’un Jihar Rivers ba a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
“Wannan ikirari ya ba mutane mamaki. Ba wai saboda ‘yan siyasa ba, yin hasashe ba ne, amma saboda irin tabbaci, ƙayyadaddun alkaluma da kuma yadda aka bayyana lamarin kamar an riga an yanke hukunci,” in ji Atiku.