ATP Hausa

ATP Hausa Zaku iya tallata hajarku a tashar ATP Hausa, tare da bayyana Ra'ayoyinku: 👉 08079307734 Whatsapp
(25)

An Fara Auna Kayan Alhazan Jihar Gombe A Birnin Makka A Shirye-Shiryen Fara Dawowar Su Gida Nijeriya...
03/06/2026

An Fara Auna Kayan Alhazan Jihar Gombe A Birnin Makka A Shirye-Shiryen Fara Dawowar Su Gida Nijeriya...

03/06/2026

Young Alajerh ya ja kunnen mabiyansa. Masu bukatar yayi magana kan sha'anin tsaro.

A cikin wata sanarwa da mai taimakawa Atiku na musamman kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce duk d...
03/06/2026

A cikin wata sanarwa da mai taimakawa Atiku na musamman kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce duk da cewa INEC ta yi ƙoƙarin kwantar wa ‘yan Najeriya da hankali da cewa ba a yi kutse daga cikin tsarin bayananta ba, amma a lokaci guda ta amince cewa an samu shiga cikin muhimman bayanan masu kaɗa ƙuri’a ta hanyar amfani da sahihan bayanan shiga (credentials) na jami’anta, sannan aka fitar da su ba tare da izini ba.

Ya ce wannan amincewa daga INEC ta haifar da tambayoyi masu yawa fiye da amsoshin da ta bayar.

“Sanarwar INEC ta tabbatar da cewa wannan batu ya wuce zato ko jita-jita.

Hukumar ta amince cewa an shiga bayanan masu kaɗa ƙuri’a ta hanyar bayanan shiga da aka bai wa ma’aikatan da ke aikin rajistar CVR, sannan aka fitar da bayanan ba tare da izini ba. Wannan kaɗai ya isa ya tayar da hankalin kowane ɗan Najeriya,” in ji shi.

Atiku ya bayyana cewa rashin samun kutse daga waje ba ya rage girman matsalar, sai ma ya ƙara tsananta ta, domin har yanzu akwai tambayoyi da ba a amsa ba dangane da tsarin tsaro na cikin gida, kariyar bayanai da kuma yiwuwar katsalandan na siyasa da gangan.

Ya ƙara da cewa: “Abin da ya sa ba za a iya yin watsi da wannan batu ba shi ne, bayanan da ake magana a kansu ba wani mai tona asiri (whistleblower), ɗan jarida mai bincike ko wata hukumar yaƙi da cin hanci ba ce ta fitar da su. Mista Lere Olayinka, mai magana da yawun Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ne ya wallafa su a bainar jama’a.”

Atiku ya kuma tunatar da cewa kwanaki kaɗan kafin wannan cece-kuce ta taso, Minista Wike ya bayyana da cikakken yaƙini cewa Atiku Abubakar ba zai samu ko kashi 10 cikin 100 na ƙuri’un Jihar Rivers ba a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

“Wannan ikirari ya ba mutane mamaki. Ba wai saboda ‘yan siyasa ba, yin hasashe ba ne, amma saboda irin tabbaci, ƙayyadaddun alkaluma da kuma yadda aka bayyana lamarin kamar an riga an yanke hukunci,” in ji Atiku.

An Fara Auna Jakunkunan Alhazan Jihar Kebbi Jirgi Na Farko, A Yayin Da Suke Kokarin Dawowa Gida Nijeriya Bayan Da Aka Ka...
03/06/2026

An Fara Auna Jakunkunan Alhazan Jihar Kebbi Jirgi Na Farko, A Yayin Da Suke Kokarin Dawowa Gida Nijeriya Bayan Da Aka Kammala Hajjin 2026...

02/06/2026

Fitaccen malamin Addinin musulunci, kuma Shugaban kungiyar Izalah me Shelkwatar a Jos, Sheikh Sani Yahaya jingir, ya bayyana cewa, ya bukaci a daina zaginsa akan azo abi tsarin Muslim-muslim.

‎Acewar malamin akwai wata mata wacce ba musulma ba, ta amfana da tsarin Muslim-muslim, sakamakon wa'azin da yakeyi a Jos.

‎Malamin ya bayyana haka ne wa mabiyansa yayin ziyarar gonakinsa.

Akpabio: Muna Neman Hanyoyin Taimaka wa Sanatocin da S**a Fadi Zaben Fitar da Gwani, da Neman “Tikitin Komawa”Shugaban M...
02/06/2026

Akpabio: Muna Neman Hanyoyin Taimaka wa Sanatocin da S**a Fadi Zaben Fitar da Gwani, da Neman “Tikitin Komawa”

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa shugabancin Majalisar na duba matakan da za su taimaka wa wasu sanatoci da s**a kasa samun tikitin jam’iyyunsu a zaben fidda gwani da aka kammala kwanan nan, gabanin babban zaben 2027.

Akpabio ya yi wannan bayani ne yayin da yake mayar da martani kan sakamakon zaben fidda gwani, wanda ya ga wasu daga cikin ‘yan majalisar dokoki masu ci sun kasa komawa Majalisar Dattawa.

Ya ce shugabancin Majalisar Dattawa bai yi tsammanin za a samu yawan wadanda za su fadi zaben ba, amma ya nuna mamaki kan yawan sanatocin da s**a rasa damar samun tikitin komawa.

A cewarsa, ana ci gaba da tattaunawa kan yadda za a magance lamarin ta hanyar da za ta amfani da ‘yan majalisa da abin ya shafa a jam’iyyu daban-daban.

Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun sauye-sauyen siyasa bayan zaben fidda gwani, wanda ya canja yanayin tseren neman kujerun majalisa na 2027.

Yawancin sanatocin da abin ya shafa yanzu suna cikin rashin tabbas kan makomarsu ta siyasa, yayin da yanke shawarar jam’iyyu ke ci gaba da sauya jerin ‘yan takara na babban zabe mai zuwa.

ATP English 👈👈👈

Alhazan Jihar Bauchi Sun Fara Karɓar Manyan Jakunkuna Guda Biyu Masu Nauyin Kilo 23 Domin Zuba Kayayyakin Su, Yayin Da Z...
02/06/2026

Alhazan Jihar Bauchi Sun Fara Karɓar Manyan Jakunkuna Guda Biyu Masu Nauyin Kilo 23 Domin Zuba Kayayyakin Su, Yayin Da Zasu Fara Dawowa Gida Nijeriya...

‎Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Barau I. Jibrin, ya sake ƙara wa jam'iyyar APC ƙarfi a Kano bayan ya k...
02/06/2026

‎Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Barau I. Jibrin, ya sake ƙara wa jam'iyyar APC ƙarfi a Kano bayan ya karɓi ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano mai wakiltar Mazabar Makoda, Muhammad Ahmad Tomas, wanda ya dawo jam'iyyar APC daga NDC. Rahotanni sun nuna cewa Tomas ya sanar da komawarsa APC ne bayan ganawa da Sanata Barau a Abuja.

‎Wannan ci gaba na zuwa ne bayan ɗan majalisar ya bar APC a baya, inda aka karɓe shi a sabuwar jam'iyyarsa tare da jagoran siyasa a Kano, Rabiu Musa Kwankwaso. Komawarsa APC cikin kankanin lokaci na nuna yadda tasirin siyasar Sanata Barau ke ci gaba da ƙarfafa jam'iyyar APC a Kano ta Arewa.

‎Allah Ya ci gaba da ba APC nasara tare da haɗin kan al'umma domin cigaban Jihar Kano da Najeriya baki ɗaya.

02/06/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Sowore Ya Soki Wike, Ya Ce “Mutum Ne Marar Hankali” Kan Batun Sace Mutane A Oyo

ATP English 👈👈👈

02/06/2026

“Duk wadanda suke haddasa wannan fitina ta matsalar tsaro duk inda suke ko da kuwa suna tare da mu ne, Allah ya tona asirinsu kuma Allah ya yi maganin su. In kuma masu shiryuwa ne, Allah ya shirye su ”

- Tsakure cikin Jawabin Gwamna Uba Sani lokacin da ya kai ziyara tantunan alhazan Jihar Kaduna a Mina, Makkah

Address

Abuja

Telephone

+2348079307734

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ATP Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ATP Hausa:

Share