05/09/2026
Da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Alhamis, daya daga cikin ma'aikata na, ya turo mun wani Headline line me ban mamaki. Duk da cewa bacci ya fara shirin k**a ni, bayan sauraron takaitaccen video Na CG Musa, mamaki ya rufe Ni. Idan ace mun AI ne zan iya yarda domin Yarda da amincewa da Yan Najeriya s**a bashi.
Bayan duba Tashar Channels TV sai na kara tabbatar da video cewa Gaskiya ne.
Inda na jiyo kalmomin nuna bangaranci da CG Musa yayi wanda yake alakanta su ga El-rufai.
Inda ya bayyana cewa, Lokacin mulkin El-rufai Ya Kawo rarrabuwar kai a sassan fadin jihar, har ya zama ɗan Kudancin Kaduna baya iya zuwa Arewacin Jihar, inji CG Musa.
Babbar ayar tambayar ita ce, shin CG Musa ya manta tarihin jihar Kaduna ne a lokacin da take fama da rikicin Kabilanci da addininci ? A lokacin Elrufa yana wani matsayi ?
Lokacin da akayi rikicin zangon Kataf da wasu sassan jihar El-rufai yana ina ?
Na tuna cewa a watan Maris na shekarar 2015, yayin da ake shirye-shiryen babban zaɓen watan Afrilu na 2015, El-Rufai, wanda a lokacin shi ne ɗan takarar gwamnan Kaduna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ya yi alƙawarin kawo ƙarshen tashin hankali da kashe-kashen da ke faruwa a yankin Kudancin Kaduna da kuma yankin Birnin-Gwari, lokacin da yake magana a shirin safe na Freedom Radio Kaduna mai suna ‘Barka da Warhaka’.
Idan babu irin waɗannan kashe-kashen a lokacin, shin batun zai kasance cikin abubuwan da ya yi amfani da su wajen neman zaɓe?
Shekaru nawa Janar Christopher Musa yake da su a shekarar 2000, lokacin da Kaduna ta fuskanci ɗaya daga cikin munanan tarzomar addini da aka taɓa gani a jihar, wadda akasari ta samo asali ne daga batun shirin aiwatar da Shari’a? Na tambayi hakan ne saboda a lokacin Mallam Nasir El-Rufai ba kunerar gwamnatin Jihar Kaduna.
A gaskiya, Makarfi ya yi ƙoƙarin hana rikicin Shari’a ya mamaye Kaduna. Bayan wannan ƙoƙari ya ci tura, shi da sauran masu ruwa da tsaki daga baya s**a cimma matsaya cewa za a aiwatar da Shari’a ne kawai a yankunan da Musulmi s**a fi yawa. Wannan lamari, ba abin da El-Rufai ya yi shekaru da dama daga baya ba, na daga cikin manyan abubuwan da s**a haifar da rarrabuwar al’umma da ta zahiri da daga baya ta zama ruwan dare a Kaduna.
Ko bayan rikice-rikicen da s**a shafi Shari’a sun lafa, Kaduna ta sake fuskantar mummunar tashin hankalin da ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2011. Ni da kaina na kasance cikin waɗanda s**a shaida wannan mummunan lokaci a tarihinmu. Daga cikin mutanen da aka kashe a faɗin ƙasar, rahotanni sun ce Kaduna ce ta fi kowane wuri, inda aka samu fiye da rabin adadin waɗanda aka kashe a ƙasar baki ɗaya. Shin a lokacin El-Rufai ne yake mulki?
Gaskiyar magana ita ce, Kaduna tana da dogon tarihin rikice-rikicen addini da ƙabilanci, musamman rarrabuwar kai da ke tsakanin arewacin jihar da Musulmi s**a fi yawa da kudancin jihar da Kiristoci s**a fi yawa. Wannan matsala ta wanzu tun kafin zamanin El-Rufai.
A lokaci guda kuma, ya k**ata gwamnati da jami’anta su riƙa taka-tsantsan wajen furta kalamai, ko a lokacin zaman lafiya ko lokacin rikici. Kalamai marasa tunani daga jami’an gwamnati na iya ƙara zurfafa rashin yarda da juna, tare da sanya ya yi wahala ga ’yan ƙasa su yarda cewa gwamnati tana tafiyar da al’amura cikin adalci da rashin nuna bambanci.
Hakika Akwai wasu abubuwa da nake da bambancin Ra'ayi da Malam Nasiru El-rufai, kuma na yake shi akan haka, duk me bin shafi na a watannin baya zai tabbatar da haka. Hakan ya samo asali ne daga wasu manufofi na Gwamnatinsa. Kamar rushewa Yan kasuwa shaguna da wasu tauraran dokoki lokacin korona.
Kalaman CG Musa akan Elrufai tsantsan son kai ne, ko nuna bangaranci, wanda hakan zai iya raunana amincewar mutane akansa.
Daga 📸— Abdul Journalist 1