ATP Hausa

ATP Hausa “Manufar tashar ATP, shine Tabbatar da Gaskiya, Kishin Ƙasa da Cigaban Dimokuraɗiyya.” Whatsapp 08079307734
(23)

05/09/2026

Na daina tallar maganin Istimnaaaeee

Fitaccen likitan Gargajiya, Abdallah Yunus Umar ya Sanar da dakatar da tallan maganin Istimnaaaeee

👉. ATP Hausa TV

05/09/2026

Yadda Ganduje da Abba Kabir Yusuf suke more kuruciya a wajen taron APC a Jihar Kano.

Zaku iya samun Zafafan labarai na Video a shafin 👉 ATP Hausa TV

Sheikh Ahmed Sulaiman Daga Farfajiyar Filin Taron APC na Yau a Jihar Kano.
05/09/2026

Sheikh Ahmed Sulaiman Daga Farfajiyar Filin Taron APC na Yau a Jihar Kano.

Jam'iyyar SDP ta gudanar da zaben fidda Gwani a Jihohin Nasarawa da Gombe. Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) ta gu...
05/09/2026

Jam'iyyar SDP ta gudanar da zaben fidda Gwani a Jihohin Nasarawa da Gombe.

Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) ta gudanar da sabon zaɓen fidda ’yan takarar gwamna a jihohin Nasarawa da Gombe, domin maye gurbin ’yan takarar da aka zaɓa a baya, waɗanda daga bisani s**a janye daga takarar.

Wannan mataki ya biyo bayan wata wasiƙa da shugabannin jam’iyyar s**a aikewa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) a ranar 24 ga Agusta 2026, inda SDP ta sanar da hukumar shirinta na gudanar da sabon zaɓen fidda gwani tare da neman INEC ta sanya ido a kan zaben.

A cikin wasiƙar mai taken “Sanarwa kan Zaɓen Fidda Gwanin na Jam’iyya domin Maye gurbin ’Yan Takara na Gwamna na Social Democratic Party”, jam’iyyar ta bayyana cewa wasu daga cikin ’yan takarar gwamna da aka zaɓa a baya sun janye daga takarar, lamarin da ya tilasta gudanar da sabon zaɓe domin samun waɗanda za su maye gurbinsu.

A baya INEC ta wallafa Musa Adamu Angbazo a matsayin ɗan takarar SDP na Nasarawa a jerin da ta fitar a ranar 30 ga Agusta, a Yanzu an Gudanar da sabon zaben fidda Gwani domin Tabbatar da sahihin ɗan takara, wanda hakan ya bawa tsohon Sufeto-Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Mohammed Abubakar Adamu, damar shiga Zaben Kai tsaye.

Erling Haaland ne ya zura kwallon da ta bai wa Manchester City nasara da ci 1–0 a kan Coventry City, inda City ta ci gab...
05/09/2026

Erling Haaland ne ya zura kwallon da ta bai wa Manchester City nasara da ci 1–0 a kan Coventry City, inda City ta ci gaba da samun cikakkiyar nasara a wasanninta uku na farko na kakar Premier League ta 2026/27...

A gefe guda, Tottenham Hotspur ta tashi 0–0 da Nottingham Forest, wanda ya bai wa Spurs maki na farko a kakar bana...

Dan takarar shugaban kasa a Jam'iyar NDC, Atiku Abubakar, yace, gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ba ta t...
05/09/2026

Dan takarar shugaban kasa a Jam'iyar NDC, Atiku Abubakar, yace, gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ba ta taɓa kare shi daga zargin cin hanci da rashawa ba...

Atiku, wanda ya kasance mataimakin shugaban ƙasa a zamanin Obasanjo, ya bayyana cewa ba a taɓa samun hukuncin da ya same shi da laifin cin hanci da rashawa ba, duk da cewa hukumomin gwamnati daban-daban sun gudanar da bincike kan zarge-zargen da ake masa...

Yace, idan akwai wanda yake da tabbatacciyar hujja kan zargin, ya gabatar da ita domin a bincika. - Inji Atiku Abubakar...

Dandazon jama'a sun halarci taron  ƙaddamar da ƙungiyar Tinubu Support Organisation a jihar Kano tare da karɓar manyan ƴ...
05/09/2026

Dandazon jama'a sun halarci taron ƙaddamar da ƙungiyar Tinubu Support Organisation a jihar Kano tare da karɓar manyan ƴan siyasa da s**a yi canja shrƙa daga jam'iyyu daban-daban.

Atiku Abubakar, Yemi Osinbajo da David Mark, duk sun halarci jana’izar mahaifiyar Rotimi Amaechi tare da sauran manyan b...
05/09/2026

Atiku Abubakar, Yemi Osinbajo da David Mark, duk sun halarci jana’izar mahaifiyar Rotimi Amaechi tare da sauran manyan baki a Jihar Rivers.

Dubban Mutane sun fito don nuna Goyon baya ga Tinubu a Jihar Kano. kungiyar TSG na jam’iyyar APC ce ta shirya don marawa...
05/09/2026

Dubban Mutane sun fito don nuna Goyon baya ga Tinubu a Jihar Kano.

kungiyar TSG na jam’iyyar APC ce ta shirya don marawa Tinubu baya a karo na Biyu.

Zaku iya samun Zafafan video a shafin mu na 👉 ATP Hausa TV

Da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Alhamis, daya daga cikin ma'aikata na, ya turo mun wani Headline line me ban mamaki. ...
05/09/2026

Da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Alhamis, daya daga cikin ma'aikata na, ya turo mun wani Headline line me ban mamaki. Duk da cewa bacci ya fara shirin k**a ni, bayan sauraron takaitaccen video Na CG Musa, mamaki ya rufe Ni. Idan ace mun AI ne zan iya yarda domin Yarda da amincewa da Yan Najeriya s**a bashi.

Bayan duba Tashar Channels TV sai na kara tabbatar da video cewa Gaskiya ne.

Inda na jiyo kalmomin nuna bangaranci da CG Musa yayi wanda yake alakanta su ga El-rufai.

Inda ya bayyana cewa, Lokacin mulkin El-rufai Ya Kawo rarrabuwar kai a sassan fadin jihar, har ya zama ɗan Kudancin Kaduna baya iya zuwa Arewacin Jihar, inji CG Musa.

Babbar ayar tambayar ita ce, shin CG Musa ya manta tarihin jihar Kaduna ne a lokacin da take fama da rikicin Kabilanci da addininci ? A lokacin Elrufa yana wani matsayi ?

Lokacin da akayi rikicin zangon Kataf da wasu sassan jihar El-rufai yana ina ?

Na tuna cewa a watan Maris na shekarar 2015, yayin da ake shirye-shiryen babban zaɓen watan Afrilu na 2015, El-Rufai, wanda a lokacin shi ne ɗan takarar gwamnan Kaduna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ya yi alƙawarin kawo ƙarshen tashin hankali da kashe-kashen da ke faruwa a yankin Kudancin Kaduna da kuma yankin Birnin-Gwari, lokacin da yake magana a shirin safe na Freedom Radio Kaduna mai suna ‘Barka da Warhaka’.

Idan babu irin waɗannan kashe-kashen a lokacin, shin batun zai kasance cikin abubuwan da ya yi amfani da su wajen neman zaɓe?

Shekaru nawa Janar Christopher Musa yake da su a shekarar 2000, lokacin da Kaduna ta fuskanci ɗaya daga cikin munanan tarzomar addini da aka taɓa gani a jihar, wadda akasari ta samo asali ne daga batun shirin aiwatar da Shari’a? Na tambayi hakan ne saboda a lokacin Mallam Nasir El-Rufai ba kunerar gwamnatin Jihar Kaduna.

A gaskiya, Makarfi ya yi ƙoƙarin hana rikicin Shari’a ya mamaye Kaduna. Bayan wannan ƙoƙari ya ci tura, shi da sauran masu ruwa da tsaki daga baya s**a cimma matsaya cewa za a aiwatar da Shari’a ne kawai a yankunan da Musulmi s**a fi yawa. Wannan lamari, ba abin da El-Rufai ya yi shekaru da dama daga baya ba, na daga cikin manyan abubuwan da s**a haifar da rarrabuwar al’umma da ta zahiri da daga baya ta zama ruwan dare a Kaduna.

Ko bayan rikice-rikicen da s**a shafi Shari’a sun lafa, Kaduna ta sake fuskantar mummunar tashin hankalin da ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2011. Ni da kaina na kasance cikin waɗanda s**a shaida wannan mummunan lokaci a tarihinmu. Daga cikin mutanen da aka kashe a faɗin ƙasar, rahotanni sun ce Kaduna ce ta fi kowane wuri, inda aka samu fiye da rabin adadin waɗanda aka kashe a ƙasar baki ɗaya. Shin a lokacin El-Rufai ne yake mulki?

Gaskiyar magana ita ce, Kaduna tana da dogon tarihin rikice-rikicen addini da ƙabilanci, musamman rarrabuwar kai da ke tsakanin arewacin jihar da Musulmi s**a fi yawa da kudancin jihar da Kiristoci s**a fi yawa. Wannan matsala ta wanzu tun kafin zamanin El-Rufai.

A lokaci guda kuma, ya k**ata gwamnati da jami’anta su riƙa taka-tsantsan wajen furta kalamai, ko a lokacin zaman lafiya ko lokacin rikici. Kalamai marasa tunani daga jami’an gwamnati na iya ƙara zurfafa rashin yarda da juna, tare da sanya ya yi wahala ga ’yan ƙasa su yarda cewa gwamnati tana tafiyar da al’amura cikin adalci da rashin nuna bambanci.

Hakika Akwai wasu abubuwa da nake da bambancin Ra'ayi da Malam Nasiru El-rufai, kuma na yake shi akan haka, duk me bin shafi na a watannin baya zai tabbatar da haka. Hakan ya samo asali ne daga wasu manufofi na Gwamnatinsa. Kamar rushewa Yan kasuwa shaguna da wasu tauraran dokoki lokacin korona.

Kalaman CG Musa akan Elrufai tsantsan son kai ne, ko nuna bangaranci, wanda hakan zai iya raunana amincewar mutane akansa.

Daga 📸— Abdul Journalist 1

Address

Abuja

Telephone

+2348079307734

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ATP Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ATP Hausa:

Shortcuts

Share