ATP Hausa

ATP Hausa ATP Whatsapp:08079307734
(20)

Shugaban hukumar tallafa wa masu neman bashi ta ƙasa (NCGC), Yakubu Dogara, ya ce, shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya gaji m...
18/09/2025

Shugaban hukumar tallafa wa masu neman bashi ta ƙasa (NCGC), Yakubu Dogara, ya ce, shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya gaji matsalar tattalin arziƙi ne a lokacin da ya k**a mulki a watan Mayun 2023 wanda shi ne dalilin da ya tilasta masa ƙaddamar da sauye-sauye domin guje rugujewar ƙasar nan.

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin gaggawa na kula da lafiyar jarirai a Jihar KanoHukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (...
18/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin gaggawa na kula da lafiyar jarirai a Jihar Kano

Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIA) ta kaddamar da wani sabon shiri na gaggawa domin rage mace-macen jarirai da ƙara samun damar kula da lafiyar jarirai a asibitocin gwamnati a faɗin ƙasar nan.

An kaddamar da wannan shirin ne a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ke jihar Kano, inda shugaban NHIA, Dr Kelechi Ohiri, ta ce shirin zai mayar da hankali kan jarirai da ke fuskantar matsalolin gaggawa bayan haihuwa.

Dr Ohiri, wadda Dr Salawudeen Sikiru ya wakilta, ya bayyana cewa shirin ya samo asali daga wani tsari na kulawa da lafiyar iyaye mata da aka fara fiye da shekara guda da ta gabata.

“Mun fara wannan shiri ne don rage mace-macen iyaye mata da jarirai. Matakin farko ya shafi uwa, yanzu kuma mun kaddamar da bangaren jarirai domin magance matsalolin gaggawa bayan haihuwa,” in ji shi.

Ya ce yanzu haka NHIA tana ɗaukar nauyin kuɗin magani ga jarirai a asibitocin gwamnati, inda asibitoci ke karɓar kudaden da s**a kashe a kowane mako bayan an tabbatar da bayanan jinya.

“Ayyukan da shirin ya ƙunsa sun haɗa da kula da jariran da aka haifa ba su gama girma ba, matsalolin rashin numfashi bayan haihuwa, rawayar ido da fata (jaundice), cutar jini (sepsis) da matsalolin tiyata ga jarirai,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa shirin ba zai tsaya kawai kan kulawar gaggawa ba, domin bayan an ceto jaririn za a yi masa rajista a kan inshorar lafiya ta ƙasa domin ya ci gaba da samun kulawa.

Shirin zai shafi iyalai marasa galihu ne kawai, tare da buƙatar lambar NIN domin tabbatar da sahihancin rajista.

A cewarsa, wannan matakin na farko zai gudana har zuwa shekarar 2027, tare da burin ganin kowane jariri mai buƙata ya samu kulawa a asibitocin da s**a shiga cikin shirin.

Shugaban Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, Farfesa Abdulrahman Sheshe, ya yaba wa Gwamnatin Tarayya da NHIA bisa wannan mataki, yana mai cewa zai taimaka wajen rage mace-macen jarirai da kuma ƙara inganta ayyukan lafiya a manyan asibitoci.

Ya kuma yi kira ga gwamnati da ta ci gaba da ɗaukar nauyin irin waɗannan shirye-shirye na dogon lokaci, yana mai cewa su ne ginshikin tabbatar da tsarin kiwon lafiya da ya dace da bukatun ’yan ƙasa.

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta sanar da cewa darasin Tarihin Najeriya zai koma cikin kundin tsarin karatun firamare da s...
18/09/2025

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta sanar da cewa darasin Tarihin Najeriya zai koma cikin kundin tsarin karatun firamare da sakandare a matsayin darasi na dole ga ɗalibai.

Wannan mataki yana daga cikin shirye-shiryen gwamnati na ƙarfafa son ƙasa, haɗin kan al’umma da kuma gina ɗalibai masu kishin ƙasa. Ana sa ran hakan zai taimaka wajen ba matasa cikakken ilimi game da asalinsu, al’adar ƙasarsu da tarihin da ya gabata, wanda zai kasance ginshiƙi wajen tsara makomar Najeriya.

A cewar gwamnatin tarayya, mayar da tarihin Najeriya cikin tsarin karatu zai taimaka wajen gina nagartattun shugabanni na gaba, da kuma tabbatar da cewa matasa sun san mahimmancin ƙasa da mutuntawa juna.

Rahoto: Comr Muhammad Kabeer Yola

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Has...
18/09/2025

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Hasheem

Shugaban ƙungiyar Arewa Media Writer’s, na ƙasa ya bayyana matuƙar takaici da bacin rai kan kisan gilla da ‘yan bindiga s**a yi wa Hakimin Dogon Daji a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, inda s**a yi masa yankan rago har lahira. Wannan lamari abin kunya ne ga ƙasa baki ɗaya kuma babban ƙalubale ne ga gwamnati da hukumomin tsaro k**ar yadda rahotan BBC Hausa da Leadership s**a kawo rahotan.

Wannan mummunan hari ya sake tabbatar da cewa lamarin tsaro a Arewacin Najeriya na ta ƙara tabarbarewa, inda ake ci gaba da kai hare-hare a ƙauyuka, sace jama’a, kona gidaje da gonaki, tare da hallaka shugabannin al’umma ba tare da tsoro ba. Wannan yanayi ya jefa dubban mutane cikin fargaba, gudun hijira, da rasa amincewa ga gwamnati.

Ya k**ata gwamnati ta gane cewa tsaro ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshiƙin kowace al’umma, kuma kariya ga rayuka da dukiyoyi wajibi ne na gwamnati. Rashin ɗaukar mataki mai tsauri na iya ƙara dagula rayuwar jama’a da kuma barazana ga makomar ƙasa baki ɗaya.

A wannan yanayi, muna kira da:

1. Gwamnati ta tashi tsaye da gaggawa wajen murkushe ‘yan bindiga da duk wata ƙungiya ta ta’addanci a Arewa.

2. A samar da kayan aiki na zamani ga jami’an tsaro, tare da horo da ƙarfafawa domin su iya gudanar da ayyukansu yadda ya k**ata.

3. A shimfiɗa tsare-tsare na dindindin don tabbatar da tsaro a ƙauyuka da birane.

A madadin al’ummar Arewa da ƙungiyar Arewa Media Writer’s, ina kira da a ɗauki wannan kisan da aka yi wa hakimin Dogon Daji a matsayin kira na musamman ga shugabanni a dukkan matakai, domin lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen wannan masifar tsaro da ta addabi yankinmu.

A ƙarshe, ina addu’a ga Allah Madaukakin Sarki Ya jikan hakimin da aka kashe, Ya ba iyalansa da al’ummarsa juriya, Ya kuma dawo da zaman lafiya mai ɗorewa ga Najeriya baki ɗaya.

✍️ Rubutawa:
Comr. Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writer’s

Mamallakin manhajar Facebook Mark Zuckerberg, ya kirkiri sabon Gilashi Me ɗauke da Fasahar Ɗan adam na (AI)
18/09/2025

Mamallakin manhajar Facebook Mark Zuckerberg, ya kirkiri sabon Gilashi Me ɗauke da Fasahar Ɗan adam na (AI)

Shugaban Rundunar Hadin Gwiwa na sojin Iran, ya bayyana cewa shirye-shiryen kare kai na Iran ya samar da makoma mai kyau...
18/09/2025

Shugaban Rundunar Hadin Gwiwa na sojin Iran, ya bayyana cewa shirye-shiryen kare kai na Iran ya samar da makoma mai kyau ga kasar, wajen taka muhimmiyar rawa wajen hana abokan gaba ƙaddamar da wani sabon hari a kasar.

Ya ce irin wannan matakin tsaro da Iran ta ɗauka ya nuna ƙwarin gwiwar rundunar Iran wajen kare martabar ƙasarta, da kuma tabbatar da cewa kowane yunƙurin hari daga makiya ba zai yi nasara ba.

Shugaban ya ƙara da cewa wannan tsayuwar daka ta nuna wa duniya cewa Iran na da cikakken ƙarfin kare kanta daga kowace barazana.

An karrama Sheikh Tamim da lambar girmamawa ta Order of Al Hussein bin AliMai girma jagoran Ƙasar Qatar, Sheikh Tamim bi...
18/09/2025

An karrama Sheikh Tamim da lambar girmamawa ta Order of Al Hussein bin Ali

Mai girma jagoran Ƙasar Qatar, Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani, ya samu lambar girmamawa ta Order of Al Hussein bin Ali mafi girman lambar yabo da ake baiwa shugabannin ƙasashe a Masarautar Jordan.

Wannan Lamban Yabo ta fito ne daga hannun Mai Martaba Sarkin Jordan, Sarki Abdullah II ibn Al Hussein, a wani biki da aka gudanar a Fadar Basman da ke birnin Amman na kasar Jordan.

Manya Hafsoshin sojin kasashen Larabawa sun Gudanar da taron koli a Birnin Doha na kasar Qatar. Don samar da hanyoyin ka...
18/09/2025

Manya Hafsoshin sojin kasashen Larabawa sun Gudanar da taron koli a Birnin Doha na kasar Qatar. Don samar da hanyoyin kare kasashen larabawa musulmai daga barazanar kasashen Abokan gaba.

Taron ya gudana ne karkashin jagorancin, Laftanar Janar (Matukin Jirgi) Jasim bin Mohammed Al Mannai, Shugaban Ma’aikatan Sojin Ƙasar Qatar.

Gwamnatin Jihar Adamawa Ta Rushe Gine-ginen Da Aka Yi Ba Bisa Ka’ida Ba a Kasuwar Jan Bulo, Jimeta Jihar Adamawa.Gwamnat...
18/09/2025

Gwamnatin Jihar Adamawa Ta Rushe Gine-ginen Da Aka Yi Ba Bisa Ka’ida Ba a Kasuwar Jan Bulo, Jimeta Jihar Adamawa.

Gwamnatin ta ce, rushe gine-ginen wani mataki ne da ta dauka domin inganta tsarin kasuwanni da kuma ba ruwa hanya, domin ruwa ya rika samun wadatacciyar hanya domin kaucema ambaliyar ruwa a jihar.

Daga
Comr Muhammad Kabeer Yola✍️

ABUN YABAWA: Shahararran Dan Kasuwa Ya Ciri Tuta Wajen Taimakon Mutane A Garin Zariya...Wani Hazikin Dan Kasuwa Me Suna,...
17/09/2025

ABUN YABAWA: Shahararran Dan Kasuwa Ya Ciri Tuta Wajen Taimakon Mutane A Garin Zariya...

Wani Hazikin Dan Kasuwa Me Suna, Alhaji Aliyu Shehu, Ya Dauki Alqawarin Tallafawa Mata Marayu Da Gajiyayyu Hijaban Islamiyya Guda (100) Domin Inganta Musu Harkan Karatun Islamiyya.

Haka Zalika Ya Ce, Ze Tallafawa Dalibai Da Almajirai Mutum Dari (100) Kayan Zaman Karatu Domin Su Kasance Cikin Tsafta Yayin Karatun Alqur'ani Mai Girma.

Alh. Aliyu Ya Jaddada Cewa Beda Babban Buri Da Yawuce Yaga Ya Tallafama Al'umma, Ya Kuma Ja Hankalin Masu Hannu Da Shuni Da Su Zama Masu Taimako Al'umma Cikin Abinda Allah Ya Basu.

Iran na da cikakken shirin kare kanta a ko wani yanayi — Shugaban soji.Shugaban Rundunar Hadin Gwiwa na sojin Iran, ya b...
17/09/2025

Iran na da cikakken shirin kare kanta a ko wani yanayi — Shugaban soji.

Shugaban Rundunar Hadin Gwiwa na sojin Iran, ya bayyana cewa shirye-shiryen kare kai na Iran sun taka muhimmiyar rawa wajen hana abokan gaba ƙaddamar da wani sabon hari a kasra.

Ya ce irin wannan matakin tsaro da Iran ta ɗauka ya nuna ƙwarin gwiwar rundunar Iran wajen kare martabar ƙasarta, da kuma tabbatar da cewa kowane yunƙurin hari daga makiya ba zai yi nasara ba.

Shugaban ya ƙara da cewa wannan tsayuwar daka ta nuna wa duniya cewa Iran na da cikakken ƙarfin kare kanta daga kowace barazana.

Dubban Mutanen Gaza na cigaba da tserewa daga Birnin zuwa kudancin kasar, adede lokacin da Isra'ila ta bude sabon babin ...
17/09/2025

Dubban Mutanen Gaza na cigaba da tserewa daga Birnin zuwa kudancin kasar, adede lokacin da Isra'ila ta bude sabon babin kai hare-haren kasa da sama a Arewacin Gaza.

Address

Area 11 Gimbiya Street
Abuja

Telephone

+2348079307734

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ATP Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ATP Hausa:

Share