ATP Hausa

ATP Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ATP Hausa, Media/News Company, Wuse.
(19)

Dangote ya yi murabus daga Dangote Cement domin mayar da hankali kan matatar maiShugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Alh...
25/07/2025

Dangote ya yi murabus daga Dangote Cement domin mayar da hankali kan matatar mai

Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya sanar da murabus dinsa daga matsayin Darakta na Shugaban Kwamitin Gudanarwa na Kamfanin Dangote Cement, wanda zai fara aiki daga ranar 25 ga Yuli, 2025.

A cewar Sanarwar ya yanke wannan hukuncin ne don fuskantar sabon babin bangaren man fetur na kamfaninsa.

DA DUMI-DUMI: Shugaba Tinubu ya gana da takwarorinsa gwamnonin da s**a yi mulki daga 1999 zuwa 2007, wadanda ake kira “A...
25/07/2025

DA DUMI-DUMI: Shugaba Tinubu ya gana da takwarorinsa gwamnonin da s**a yi mulki daga 1999 zuwa 2007, wadanda ake kira “Ajin Farko na Mulkin Farar Hula a Shekarar 1999.”

Lokacin ka san Tinubu ?

YANZU-YANZU: Jagoran Juyin Juya Hali na Musulunci, Ayatollah Seyed Ali Khamenei, zai gabatar da jawabi ga Duniya nan da ...
25/07/2025

YANZU-YANZU: Jagoran Juyin Juya Hali na Musulunci, Ayatollah Seyed Ali Khamenei, zai gabatar da jawabi ga Duniya nan da wasu Yan sa'anni masu zuwa bayan cikar Manya hafsoshin sojin Iran kwanaki 40 da Rasuwa.

Matawalle da Güler sun jaddada dangantakar tsaro tsakanin Nijeriya da TurkiyyaKasashen Nijeriya da Turkiyya sun sake jad...
25/07/2025

Matawalle da Güler sun jaddada dangantakar tsaro tsakanin Nijeriya da Turkiyya

Kasashen Nijeriya da Turkiyya sun sake jaddada kudurinsu na ci gaba da karfafa dangantakar soji, bayan wata ganawa a bikin baje kolin kayan aikin tsaro na duniya karo na 17 (IDEF 2025) da ke gudana a birnin Istanbul.

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammad Matawalle, ya gana da Ministan tsaron kasar Turkiyya, Yaşar Güler, a ranar Laraba, domin zurfafa hadin guiwar tsaro tsakanin kasashen biyu.

An gudanar da ganawar a yayin taron IDEF 2025, inda s**a tattauna kan manyan fannoni k**ar hadin guiwa a bangaren masana’antar tsaro, musayar fasaha da kuma sayen sabbin kayan aikin soja na zamani.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa Matawalle kan harkokin yada labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar ta bayyana cewa an tattauna kan sayen motocin yaki, jiragen yaki, jiragen ruwa na yaki, jiragen yaki marasa matuki (UAVs), tsarin radar da kuma kunshin horo da gyare-gyare na kayan aikin soja.

Ministocin biyu sun jaddada muhimmancin karfafa ikon masana’antar tsaro a cikin gida, tare da bayyana sha’awar hadin guiwa ta dogon lokaci a fannin masana’antu domin cimma cin gashin kai ta fuskar fasaha.

Dr Matawalle ya bayyana kasar Turkiyya a matsayin amintacciya kuma abokiyar hadin guiwa a kokarin Nijeriya na sabunta tsarin tsaronta, yana mai cewa ci gaba da wannan hadin guiwa zai amfanar da kasashen biyu musamman a wannan lokaci da duniya ke fuskantar kalubalen tsaro.

Daga cikin wadanda s**a halarci taron akwai manyan jami’an tsaron Nijeriya, ciki har da Amb Gabriel Tanimu Aduda, babban sakatare na ma’aikatar tsaron Nijeriya; AVM Yusuf, wakilin Shugaban Hafsan Sojin Sama; Manjo Janar B.I. Alaya, Darakta Janar na Kamfanin Kera Kayan Aikin Soja na Nijeriya (DICON); Birgediya Janar M.L. Abubakar, Jakadan Tsaro na Nijeriya a Turkiyya; da kuma Mataimakin Shugaban Harkokin Leken Asirin Soja.

A halin yanzu, baje kolin bikin IDEF 2025, daya daga cikin manyan baje kolin kayan aikin soja na duniya, ya fara ne a ranar 22 ga Yuli kuma zai ci gaba har zuwa 27 ga Yuli a birnin Istanbul. Taron yana tattaro masana’antun kayan soji, jami’an soja da masu tsara manufofi daga sassa daban-daban na duniya domin karfafa hadin guiwar kasa da kasa.

Mahadi Shehu ya Soki Gwamnatin Tarayya Kan Kudaden Tsaro, Ya Bukaci Samar da ‘Yan Sanda na Jihohi kuma Shugabanni su Gya...
25/07/2025

Mahadi Shehu ya Soki Gwamnatin Tarayya Kan Kudaden Tsaro, Ya Bukaci Samar da ‘Yan Sanda na Jihohi kuma Shugabanni su Gyara Halayen su

Fitaccen mai sharhi kan harkokin yau da kullum, Dr. Mahadi Shehu, ya bayyana rashin jin daɗinsa kan yadda Gwamnatin Tarayya ke kashe makudan kuɗaɗe a sunan samar da tsaro da zaman lafiya, alhali kuma matsalar na ci gaba da tabarbarewa.

ATP Hausa ta ruwaito cewa ya zargi gwamnati da rashin tallafa wa jami’an tsaro da kayan aiki da albashi, wanda hakan ke rage musu ƙwarin gwiwar yaki da 'yan ta’adda da masu tada zaune tsaye. Dr. Mahadi ya bukaci gwamnonin jihohin Arewa da su ƙara himma wajen samar da rundunar 'yan sandan jiha, ba tare da jiran amincewar Gwamnatin Tarayya ba, yana mai kawo misalin wasu jihohin Kudu da s**a yi nasara a wannan fanni.

Dr. Mahadi ya kuma ce dole ne a sauya dokar da ke cikin kundin tsarin mulki wacce ke hana rundunonin tsaron jihohi mallakar manyan mak**ai. Ya ce wannan doka na hana su samun ƙarfi wajen yaki da ‘yan ta’adda. Ya kara da cewa, “Ko Allah idan ya kafa doka da ta gagari mutane, zai sauya ta don amfanin jama’a,” yana nuni da muhimmancin doka da za ta yi amfani ga rayuwar al’umma.

Da yake magana kan 'yancin kai na Najeriya, Dr. Mahadi ya bayyana cewa 'yancin da ake cewa Najeriya ta samu, kawai a rubuce yake, domin har yanzu mutane na rayuwa cikin wahala k**ar lokacin mulkin mallaka. Ya soki kasashen waje, musamman Birtaniya da ta yi wa Najeriya mulkin mallaka, da cewa ita ce ke karɓar dukiyar haramtacciyar da barayin gwamnati ke sacewa daga Najeriya, suna kuma amfani da ita wajen gina manyan gidaje da otal-otal a kasashen waje.

Dr. Mahadi ya ce, idan har Najeriya na son ta ci gaba k**ar ƙasashen China, Indonesia, Malaysia da Jamus, to dole ne ta koyi yadda suke gudanar da mulki na gaskiya da rikon amana. Ya ce a irin waɗannan ƙasashe, shugabanni ba su halarci sata ko almundahana ba, kuma kafin a zabi mutum a matsayin shugaba sai an bincike shi sosai. A wasu ƙasashen, idan mutum ya saci dukiyar ƙasa, to a kofar gidansa za a kashe shi. A wasu kuma, idan an k**a mutum da laifi, kunya na sa shi kashe kansa. Amma a Najeriya, mafi kwarewa wajen sata shi ake girmamawa da bashi mukami.

A karshe, Dr. Mahadi ya bayyana cewa matsalar tsaro da rashawa a Najeriya ba wai na gwamnati kaɗai ba ne, matsala ce ta kowa da kowa. Ya ce dole ne al’umma su tashi tsaye wajen taimaka wa jami’an tsaro, su daina ɓoye bayanan da za su taimaka a k**a masu aikata laifi. Ya kuma nuna cewa cin hanci da rashawa yana farawa tun daga lokacin zaɓe, inda ‘yan siyasa ke biyan mutane da kuɗi don su samu kuri’a. Ya ce haka na sa shugabanni su mayar da siyasa kasuwanci. Ya ƙara da cewa babu buƙatar sauya kundin tsarin mulki k**ar yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke shirin yi, illa dai shugabanni su gyara halayensu ne.

Rayuwar Marigayi Sarkin Gusau cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a —Shugaba TinubuShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu...
25/07/2025

Rayuwar Marigayi Sarkin Gusau cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a —Shugaba Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhini da jimami kan rasuwar Sarkin Katsinan Gusau, Dr Ibrahim Bello, wanda ya rasu da safiyar Juma’a a birnin tarayya Abuja yana da shekaru 71 a duniya.

A cikin wata sanarwa daga mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yada labarai da dabarun watsa bayanai, Mista Bayo Onanuga, Shugaba Tinubu ya bayyana rasuwar marigayi sarkin a matsayin babban rashi da ya wuce iyakar masarautar Gusau, yana mai cewa rayuwarsa cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a a matakai daban-daban na rayuwa.

Shugaban ƙasa ya yabawa marigayin da kishinsa da jajircewa wajen kula da walwala da ci gaban jama’arsa. Ya ce za a ci gaba da tunawa da sarkin bisa jagoranci na nagarta da baiwar jagoranci da Allah ya h**e masa.

Shugaba Tinubu ya mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnatin jihar Zamfara, al’ummar Gusau da kuma iyalan marigayin, tare da addu’ar Allah ya jikan sa, ya sa Aljannah Firdausi ta zama makoma gare shi.

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda PhD tare da Mai Ɗakinsa, Hajia Fatima Dikko Radda, Yayin da yake samun sauk...
25/07/2025

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda PhD tare da Mai Ɗakinsa, Hajia Fatima Dikko Radda, Yayin da yake samun sauki a Abuja bayan hatsarin motar da ya rutsa da shi a satin da ya gabata.

📸 -Fatima Dikko Radda.

CIKIN HOTINA: Yadda Aka Gudanar Da Sallar Juma'a a Masallacin Harami Dake Garin Makkah.Allah Yaqarama Annabi Daraja.Hajj...
25/07/2025

CIKIN HOTINA: Yadda Aka Gudanar Da Sallar Juma'a a Masallacin Harami Dake Garin Makkah.

Allah Yaqarama Annabi Daraja.

Hajji Ibadar Allah

YANZU-YANZU: Kasar Iran na Shirin Harba Tauraron Dan Adam dinta na biyu. Kasa da mako Daya, Kasar Iran ta cire tuta na H...
25/07/2025

YANZU-YANZU: Kasar Iran na Shirin Harba Tauraron Dan Adam dinta na biyu.

Kasa da mako Daya, Kasar Iran ta cire tuta na Harba manya Tauraron Dan Adam dinta.

A cewar Wata Sanarwa Da Gidan Talabijin na Press TV na kasar Iran ta fitar, ya bayyana cewa Tauraron Dan Adam Mai suna “Nahid 2” zai tashi nan ba da jimawa ba

Tauraron dan adam na Iran mai suna “Nahid 2”, wanda ƙwararrun masana na cikin gida s**a ƙera, yana shirin tashi cikin sa’o’i masu zuwa a cikin rokar Soyuz ta Rasha. Manufar wannan tauraro ita ce ƙarfafa sadarwa ta tauraron dan adam don Bunkasa fasahar Dan adam a cikin kasar.

HOTO📸 Abdul Journalist 1

25/07/2025

Wani sojan Cambodia Na bata kashi da Sojin Thailand.😆

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya sanar a ranar Alhamis cewa Faransa za ta amince da Falasdinu a matsayin ƙasa mai cin...
24/07/2025

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya sanar a ranar Alhamis cewa Faransa za ta amince da Falasdinu a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta, a wani mataki na diflomasiyya mai ƙarfi yayin da fushin duniya ke ƙaruwa kan yunwar da ke addabar mutanen Gaza. Isra’ila ta soki wannan mataki.

Macron ya bayyana hakan a wani rubutu da ya wallafa a shafin X (Twitter), inda ya ce zai tabbatar da wannan matsaya a taron Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya a watan Satumba. “Abin da yafi zama gaggawa a yau shi ne, a dakatar da yaƙin da ke Gaza kuma a ceci rayukan fararen hula,” in ji shi.

Wannan mataki duk da cewa yawanci yana da siffar alama ne yana ƙara matsin lamba na diflomasiyya kan Isra’ila, yayin da yaƙi da matsin lambar jin kai ke ci gaba da tsananta a Gaza. Faransa ta zama mafi girma daga cikin ƙasashen Yamma da s**a amince da Falasdinu, kuma hakan na iya buɗe ƙofa ga wasu ƙasashe su bi sahunta. Sama da ƙasashe 140 ne tuni s**a amince da Falasdinu a matsayin ƙasa, ciki har da sama da ɗari daga Turai.

'Yan Falasdinu na neman kafuwar ƙasarsu mai cin gashin kanta a yankunan Yammacin Kogin Jordan da Gabashin Kudus da kuma GazaGaza.

wuraren da Isra’ila ta mamaye tun yakin Gabas ta Tsakiya na 1967. Gwamnatin Isra’ila da yawancin ’yan siyasar ƙasar sun daɗe suna adawa da wannan ƙuduri, kuma yanzu suna cewa hakan zai zama lada ga 'yan ta'adda bayan harin da Hamas ta kai ranar 7 ga Oktoba, 2023.

“Mun yi tir da matakin da Shugaba Macron ya ɗauka,” in ji Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a cikin wata sanarwa. “Wannan matakin lada ne ga ta’addanci, kuma yana da haɗarin kafa wata sabuwar rundunar Iran k**ar yadda aka yi a Gaza. Ƙasar Falasdinu a irin wannan yanayi za ta zama wata maboya ce don kawar da Isra’ila.

DA ƊUMI-ƊUMI: Sakataren Gwamnatin Jihar Nasarawa, Labaran Magaji, Da Wasu 56 Sun Samu Lambar SAN Daga Babbar Mai Shari’a...
24/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Sakataren Gwamnatin Jihar Nasarawa, Labaran Magaji, Da Wasu 56 Sun Samu Lambar SAN Daga Babbar Mai Shari’a Ta Ƙasa

A wata babbar sanarwa daga babban mai rikon kujerar shari’a a Najeriya, Babbar Mai Shari’a ta Ƙasa (CJN), Kudirat Kekere-Ekun, ta amince da bai wa Sakataren Gwamnatin Jihar Nasarawa, Barrista Labaran Magaji, da wasu fitattun lauyoyi 56 lambar girmamawa ta Babban Lauyan Najeriya (SAN).

Sanarwar ta fito ne daga zaman taro na 169 na Kwamitin Ƙwararrun Lauyoyi (LPPC), wanda aka gudanar a birnin tarayya Abuja karkashin jagorancin CJN Kekere-Ekun.

Masu Nasara Sun Hada Da:

Lauyoyi 56 masu wakiltar shari’a a kotuna, da

Farfesa Chima Josephat Ubanyionwu – fitaccen malamin makaranta da aka karrama bisa gudunmuwarsa a fannin ilimin shari’a a Najeriya.

Girmamawa Ga Gwagwarmaya

Barr. Labaran Magaji, wanda ya taɓa rike muƙamin Antoni Janar na Jihar Nasarawa, ya samu wannan matsayi ne saboda bajintarsa a fannin lauya da kuma irin gudunmuwar da ya bayar a harkar mulki da shugabanci.

Wasu fitattun da aka karrama sun hada da:

Ikechukwu Uwanna – Antoni Janar na Jihar Abia kuma tsohon shugaban NBA reshen Lagos

Oluwole Jimi-Bada – Antoni Janar na Jihar Osun

Oyinkan Badejo-Okusanya da Chinyere Ekene Moneme – su ne kadai mata guda biyu da s**a samu wannan lamba a bana.

A Jihar Nasarawa, wannan lamba da aka bai wa Magaji ta haifar da murna, inda ake kallon ta a matsayin wani karin girma ga jihar a idon ƙasa da duniya.

Ranar Rantsarwa: 29 ga Satumba, 2025

Kwamitin LPPC ya bayyana cewa duka sababbin SAN za su halarci wani shiri na horo kafin a rantsar da su a hukumance ranar Litinin, 29 ga Satumba, 2025, a Abuja.

Haka kuma, kwamitin ya ce korafe-korafe guda uku da aka shigar kan wasu daga cikin ‘yan takarar an yi nazari a kansu, kuma an yi watsi da su bisa rashin cancanta, domin tabbatar da sahihancin jerin sunayen da aka fitar.

"Lambar SAN alama ce ta kwarewa, gaskiya da jajircewa wajen inganta adalci a Najeriya," in ji kwamitin.

Samar da wannan matsayi ga Barr. Labaran Magaji na nuna ƙwarewarsa a fannin shari’a da kuma irin matsayinsa da ke ƙaruwa a fagen shugabanci da mulki a ƙasa.

Majiyar Labari: Legit.ng

Address

Wuse

Telephone

+2348079307734

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ATP Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ATP Hausa:

Share