Labarun Kafar Labaru

Labarun Kafar Labaru Kasance da wannan kafa domin samun sahihan labaru ko yaushe

An miƙa al’amuran tsaron Najeriya a hannun da ya dace - in ji tsohon hafsan tsaron Najeriya, CG Musa
02/11/2025

An miƙa al’amuran tsaron Najeriya a hannun da ya dace - in ji tsohon hafsan tsaron Najeriya, CG Musa

KAJI RABO: Sabuwar jarumar Masana'antar Kannywood ta mallaki motar GLK daga shigowar talamarin da yasa masoyan ta ke gan...
02/11/2025

KAJI RABO: Sabuwar jarumar Masana'antar Kannywood ta mallaki motar GLK daga shigowar talamarin da yasa masoyan ta ke ganin ta shigo da kafar dama

Motar GLK dai mota ce mai tsada kuma wacce jaruman Kannywood mata suke burin mallaka

Wacce fata za kuyi mata ?

02/11/2025
Malam Na Ta'ala na cikin shirin wasan kwaikwayo na Dadin Kowa ya rasu. Majiyoyi sun ce ya rasu ne a daren yau Lahadi a w...
02/11/2025

Malam Na Ta'ala na cikin shirin wasan kwaikwayo na Dadin Kowa ya rasu.

Majiyoyi sun ce ya rasu ne a daren yau Lahadi a wani asibiti a garin Maiduguri na jihar Borno.

Allah Ya yi masa rahma

Dattijuwa mai shekaru 69 ta fara karatun digiri a Jami’ar Ibadan kuma ta ci alwashin kammala wa da maki mai ƙololuwar da...
02/11/2025

Dattijuwa mai shekaru 69 ta fara karatun digiri a Jami’ar Ibadan kuma ta ci alwashin kammala wa da maki mai ƙololuwar daraja.....

Daga Ibrahim s.d kusfa zaria city

Wata tsohuwa mai shekara 69 mai suna Mrs. Kate Bosede Akomolafe na daga cikin dalibai sama da 5,000 da aka karɓa a Cibiyar Koyo daga Nesa ta Jami’ar Ibadan (Distance Learning Centre, UI) domin karatun shekarar karatu ta 2024/2025.

Sabuwar dalibar, wadda ke karatun aikin zamantakewa (Social Work), manomiya a halin yanzu, bayan ta yi ritaya shekaru da s**a gabata daga kamfanin RT Briscoe inda ta yi aiki a matsayin jami'ar tattara bayanai. Yanzu tana yin digiri na farko mai tsawon shekaru huɗu.

An haifi Mrs. Akomolafe a ranar 22 ga Disamba, 1956, kuma ta samu takardar shaidar makarantar sakandare ta Yammacin Afirka (WAEC) a shekara ta 1976 daga Government Secondary School, Creek Road, Port Harcourt. Sai dai a bara ta sake zama jarabawar WASSCE da NECO domin ta sami isassun maki da za su bata damar shiga jami’a don yin digiri.

Bisa bayanin da Jami’ar Ibadan ta fitar, ta zaɓi fannin Social Work ne domin faɗaɗa iliminta da kuma samun ƙwarewa wajen gudanar da kungiyarta mai zaman kanta mai suna Christ’s Care for the Widow.

Mrs. Akomolafe, wadda uwa ce ga ‘ya’ya huɗu masu nasara kuma kakar jikoki, ta bayyana cewa tana da niyyar yin fice a karatunta tare da burin kammalawa da First Class a ƙarshen karatunta.

Zargin kisan kiristoci: Kwankwaso ya magantu akan kalaman Trump..... Daga Ibrahim s.d kusfa zaria city Tsohon Gwamnan Ji...
02/11/2025

Zargin kisan kiristoci: Kwankwaso ya magantu akan kalaman Trump.....

Daga Ibrahim s.d kusfa zaria city

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya nuna damuwarsa kan wasu kalamai da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi a kan Najeriya.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso ya ce maganganun da Trump ke yawan furtawa da kuma ayyana Najeriya a matsayin “ƙasa mai matsaloli na musamman” sun haifar da damuwa mai tsanani da ke bukatar magance su ta hanyar diflomasiyya.

Ya jaddada cewa Najeriya ƙasa ce mai cikakken ƴancin kai wadda ke fuskantar matsalolin tsaro iri-iri daga ‘yan ta’adda a sassa daban-daban na ƙasar, inda ya ce rikice-rikicen ba su bambanta mutane bisa addini, ƙabila ko siyasa ba.

“Rashin tsaron da muke fuskanta baya bambance mutane bisa addini, ƙabila ko ra’ayin siyasa,” in ji Kwankwaso.

Tsohon gwamnan ya roƙi gwamnatin Amurka da ta taimaka wa Najeriya da fasahohin zamani wajen yaki da rashin tsaro maimakon yin barazana wacce za ta iya ƙara rarrabuwar kawuna a ƙasar.

Haka kuma, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta nada jakadu na musamman da kuma na dindindin domin su tattauna da gwamnatin Amurka da kare muradun Najeriya a matakin duniya.

Kwankwaso ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su haɗa kai wajen fuskantar matsin lamba daga waje da na cikin gida, yana mai jaddada muhimmancin ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya

Na bar shan sigari ne saboda kare mutunci na - Yemi Alade...... Daga Ibrahim s.d kusfa zaria cityShahararriyar mawaƙiyar...
02/11/2025

Na bar shan sigari ne saboda kare mutunci na - Yemi Alade......

Daga Ibrahim s.d kusfa zaria city

Shahararriyar mawaƙiyar Nijeriya, Yemi Alade ta baiyana cewa ta dena shan taba sigari ne saboda kare mutuncin ta.

A wata tattaunawa a shirin WithChude da ake watsawa ta yanar gizo, Alade ta ce ta fuskanci cewa shan sigari ya zame mata jiki har tana jin ba daɗi idan ba ta yi ba.

A cewar Alade, duk sanda ta zo kwanciya sai ya zuzzuki sigari, inda ta ce bata samun damar sha da rana saboda shiga cikin mutane.

A cewar ta, ɓoye shan sigari a bainal jama'a ne ya sa ta ga cewa gwara ma ta yarda ƙwallon mangwaro ta huta da ƙuda.

Sojan Amurka Dan Asalin Najeriya, Sulaiman Isa, Ya Ce Ba Zai Mamaye Ƙasarsa Ba Saboda Labarin Ƙarya Akan Kisan Kiristoci...
02/11/2025

Sojan Amurka Dan Asalin Najeriya, Sulaiman Isa, Ya Ce Ba Zai Mamaye Ƙasarsa Ba Saboda Labarin Ƙarya Akan Kisan Kiristoci.....

Daga Ibrahim s.d kusfa zaria city

Wani soja dan asalin Najeriya mai suna Sulaiman Isa, wanda ke cikin rundunar sojin Amurka, ya bayyana cewa ba zai taɓa mamaye ƙasarsa ta haihuwa ba, kuma ba zai kashe iyayensa ko ‘yan uwansa ba saboda wani raɗe-raɗin ƙarya da ake yadawa game da kisan gillar Kiristoci a Najeriya.

Sulaiman, wanda asalin jiharsa Kano ce, ya bayyana hakan ne cikin wani sakon da ya wallafa, inda ya jaddada cewa yana Allah wadai da kisan duk wani ɗan Najeriya — Musulmi ko Kirista.

A cewarsa, ’yan ta’adda k**ar Shekau, Bello Turji, Dogo Gide da sauransu ba sa kai hari bisa bambancin addini, domin suna kashe mutane ne ba tare da la’akari da Musulmi ko Kirista ba.

Shigo-shigo ba zurfi Trump ke yi maka, Primate Ayodele ga Tinubu..... Daga Ibrahim s.d kusfa zaria city Shugaban cocin I...
02/11/2025

Shigo-shigo ba zurfi Trump ke yi maka, Primate Ayodele ga Tinubu.....

Daga Ibrahim s.d kusfa zaria city

Shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual Church, Primate Elijah Ayodele, ya gargadi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya kasance cikin shiri game da rahotannin kisan kiyashi da ake ta yadawa daga ƙasar Amurka.

Gwamnatin Amurka ta zargi gwamnatin Najeriya da yin shiru kan kashe-kashen Kiristoci da ake yi a sassan ƙasar, lamarin da ya sa shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin soja kan Najeriya.

Jaridar Tribune ta rawaito cewa a wata sanarwa da mai taimaka masa a harkokin yada labarai, Osho Oluwatosin, ya sanyawa hannu, Primate Ayodele ya bayyana cewa ya dade yana magana kan tsoma bakin Amurka cikin harkokin gwamnatin Tinubu, amma aka yi biris da shi.

Ya bayyana cewa wannan wani shiri ne na adawa domin hambarar da Tinubu daga mulki kafin shekarar 2027 ko a lokacin.

“Ina ta magana tun da dadewa cewa Amurka za ta yi fada da gwamnatin Tinubu, amma ba su dauka da muhimmanci ba. Lokacin da na yi magana kan yiwuwar juyin mulki, wasu masu sharhin siyasa sun soki maganata, amma ga abin da ke faruwa yanzu.

“Gwamnatin Tinubu kada ta yi sakaci da wannan batu; shiri ne na ganin an cire shi daga mulki a shekarar 2027. Bayan zarge-zargen da ake yi, akwai wani shiri na ɓoye domin a fitar da Tinubu daga karagar mulki. Shugaban bai ga hakan daga wannan hangen ba.”

Ya kara da cewa wannan dabarar ce ta raunana karfin gwamnatin Tinubu da kuma kokarin hana ta yin tasiri domin ‘yan adawa su samu dama.

Ya bayyana cewa ‘yan adawa sun kammala tattaunawa da wasu kasashen duniya domin samun goyon bayan cire Tinubu daga ofis, yana kuma kira ga gwamnatin da ta farka daga bacci ta dauki mataki.

Fitacciyar mawakiyar ƙasar Argentina, Nicki Nicole, ta bayyana cewa ta rabu da dan wasan Barcelona, Lamine Yamal, saboda...
02/11/2025

Fitacciyar mawakiyar ƙasar Argentina, Nicki Nicole, ta bayyana cewa ta rabu da dan wasan Barcelona, Lamine Yamal, saboda abin da ta bayyana a matsayin rashin daidaituwa da ita a al’amuran soyayya, da sha'ani.

Ta bayyana hakan ne a wata hira da kafar labarai ta cikin gida, inda ta ce rabuwarsu ta zo ne bayan sun fahimci cewa suna da banbanci a halaye da dabi’un juna musamman bangaren al'amurran yau da kullum.

YANZU-YANZU: Yadda Jami'an Tsaro S**a Kewaye Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, Domin Bashi Kariya A Yayin Gabatar...
02/11/2025

YANZU-YANZU: Yadda Jami'an Tsaro S**a Kewaye Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, Domin Bashi Kariya A Yayin Gabatar Da Ibadar Umra A Kasar Saudi Arabia..

BA MUSULMI BANE KE KASHE KIRISTOCI  A NAJERIYA. Cewar Gorge Udom Kirista daga Arewacin Najeriya:Matsalar son addini (Rel...
02/11/2025

BA MUSULMI BANE KE KASHE KIRISTOCI
A NAJERIYA. Cewar Gorge Udom Kirista daga Arewacin Najeriya:

Matsalar son addini (Religious Bigotry) ba daga Arewa ta fara ba.

Mu koma baya kadan zuwa shekara ta 1962, lokacin da Musulmin Arewa, Sir Abubakar Tafawa Balewa, ya saka Najeriya cikin Majalisar Ikklisiyoyi ta Duniya (World Council of Churches), sannan a 1963 ya kuma saka ta cikin International Bible Society, babu wani kuka daga Musulman Arewa.

Asabar tana daga cikin ranakun aiki a Najeriya har zuwa shekara ta 1973, lokacin da Gowon, wanda yake Kirista daga ƙananan kabilu na Arewa, ya ayyana ta a matsayin ranar hutu don bai wa Seventh Day Adventist Church damar yin ibada — babu wani kuka daga Musulman Arewa.

A watan Fabrairu na 1979, Olusegun Obasanjo ya hana shahararren mai wa’azin Musulunci, Ahmed Deedat, shiga Najeriya — babu kuka daga Musulman Arewa.

A shekara ta 1982, Pope John Paul II ya ziyarci Najeriya, kuma Musulmi ne, Alhaji Shehu Shagari, ya tarbe shi.

Reinhard Bonnke, malamin Kirista mai wa’azi, yana shigowa Najeriya yadda yake so — babu kuka daga Musulman Arewa.

Abacha ma ya tarbi Pope John Paul, ya kuma kafa Papal Square a kusa da hanyar Kubwa Expressway — babu kuka daga Musulmai.

Amma a 1986, lokacin da Babangida ya saka Najeriya cikin Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi (OIC), sai tarzoma ta tashi a Lagos, Port Harcourt da Enugu — wanda CAN (Christian Association of Nigeria) ta shirya.

Don Allah, wa ne ke nuna son addini a nan?

A ‘yan kwanakin nan, Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci ta Najeriya (NSCIA) ta bayyana cewa ba ta da hannu cikin siyasa — amma ya ya da CAN?

A shekara ta 2013, an k**a jirgin sama mallakin shugaban CAN a Afirka ta Kudu cike da kuɗin waje — me da za a ce da jirgin nan idan mallakin Sarkin Musulmi ne?

Don haka mu tambayi kanmu: Su waye masu son addini a gaskiya? Kafin mu sake yin kuskure a matsayin al’umma.

Address

No 20 Jimmy Carter Street
Abuja

Telephone

+2348065847174

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labarun Kafar Labaru posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labarun Kafar Labaru:

Share