Nigerian Post

Nigerian Post Call Or Whatsapp On This No.: +2348031568031

Kungiyar United Nigeria Chaplaincy ta Nada Shugaban Shiyyar Jihar Katsina tare da Karrama Sheikh Dr. Isma’il Zakariyya A...
20/09/2025

Kungiyar United Nigeria Chaplaincy ta Nada Shugaban Shiyyar Jihar Katsina tare da Karrama Sheikh Dr. Isma’il Zakariyya Alkashanawi da Lambar Girmamawa

Kungiyar United Nigeria Chaplaincy (UNC) ta gudanar da babban taron ta na kasa a dakin taro na makarantar KCK da ke Katsina, inda ta sanar da nadin sabon shugaban shiyyar Katsina na kungiyar tare da karrama fitattun mutane da lambar yabo.

Daga cikin waɗanda aka karrama akwai babban malamin addini, Sheikh Dr Isma’il Zakariyya Alkashanawi, wanda ya samu lambar girma ta National Muslim Affair.

A jawabin maraba da ya gabatar, sabon shugaban ƙungiyar a shiyyar Katsina, Malam Bello, ya bayyana farin cikinsa da yadda jama’a s**a halarci taron cikin natsuwa da kwazo, tare da bayyana wasu daga cikin manufofin kungiyar musamman wajen wanzar da zaman lafiya a kasa.

Shi ma da yake nasa jawabin, Dr Isma’il Zakariyya Alkashanawi ya gode wa Allah bisa wannan yabo, tare da bayyana cewa wannan alhaki ne babba da ke bukatar hada kai. Ya kara da cewa:

“Kungiyar tana bukatar matasa, malamai, da ‘yan siyasa su bada gudummawar su domin kara tabbatar da ci gaban kungiyar da kuma wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma.”

Hakazalika, Alaramma Malam Kalu ya yi kira ga masu hannu da shuni da su tallafa wa tafiyar kungiyar, domin ganin an cimma burin tabbatar da zaman lafiya.

Shi ma Rev. Luka Yohana wanda aka tabbatar dashi a matsayin Uban ƙungiyar, ya nuna jin dadinsa tare da kira ga jama’a da su hada kai wajen inganta zaman lafiya da hadin kai a kasa.

Daga karshe, an karrama wasu fitattun shugabanni da ‘yan siyasa, ciki har da Hon. Aliyu Abubakar Albaba, dan majalisar da ke wakiltar karamar hukumar Katsina, Ambassador Khadija Sulaiman Saulawa, Alaramma Malam Habibu ƙalu da sauran shugabannin al’umma.

Nigerian Post ta bibiyi cewa, taron dai ya samu halartar jami'an gwamnati, jami’an tsaro, malamai, da shugabannin kungiyoyin al’umma maza da mata, lamarin da ya nuna cikakken hadin kai wajen tallafa wa ci gaban kasa da raya zaman lafiya.

Gwamna Radda Ya halarci Bikin Karrama Mawaki Dauda Kahutu Rarara Da Digirin GirmamawaGwamnan jihar Katsina Ya halarci Bi...
20/09/2025

Gwamna Radda Ya halarci Bikin Karrama Mawaki Dauda Kahutu Rarara Da Digirin Girmamawa

Gwamnan jihar Katsina Ya halarci Bikin Karrama Mawaki Dauda Kahutu Rarara Da Digirin Girmamawa A Jami’ar European American University.

Shahararren mawaƙin siyasa, Dauda Kahutu Rarara, ya samu girmamawa ta musamman daga Jami’ar European American University, wacce ta karrama shi da digiri (Doctorate Degree) saboda gudummawarsa wajen raya al’adu da siyasa a Najeriya.

Bikin karramawar ya samu halartar manyan baki, ciki har da Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, wanda ya bayyana farin cikinsa kan yadda aka yi wa Rarara wannan girmamawa, yana mai cewa wannan yabo zai ƙara ƙarfafa matasa wajen ganin muhimmancin fasaha a siyasa da zamantakewa.

Haka zalika, Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Rimi/Charanchi/Batagarawa, Hon. Usman Murtala Banye, da na Katsina, Hon. Sani Aliyu Danlami, tare da S.A. na musamman ga Gwamna, Hon. Abdullahi Aliyu Turaji, suma sun kasance cikin mahalarta wannan tarihi.

Rahotanni sun tabbatar da cewa, karramawa ga Rarara ya nuna yadda wakokin siyasa s**a zama wani muhimmin ɓangare na wayar da kan al’umma, tare da ƙara haskaka sunansa a fagen siyasa da al’adu a Najeriya.

Zargin Ta'addanci: Ƙungiyar Masu Kishin Al'ummar Zamfara ta kirayi Gwamnatin Tarayya ta Gaggauta Ɗaukar Mataki Akan Sana...
20/09/2025

Zargin Ta'addanci: Ƙungiyar Masu Kishin Al'ummar Zamfara ta kirayi Gwamnatin Tarayya ta Gaggauta Ɗaukar Mataki Akan Sanata Shehu Buba

Ƙungiyar masu kishin Al'ummar Zamfara (CCZ) ta yi magiya ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta ɗaukar mataki akan Santa Shehu Umar Buba da ke wakiltar yankin Bauchi ta Kudu a Majalisar Dattawan Nijeriya bisa zargin sa da hannu a ayyukan ta'addancin yankin Arewa maso Yamma.

A kwanakin baya aka ga sanatan a wani faifan bidiyo mai ta da hankali yana jagorantar zuba wasu maƙudan kuɗaɗe a wata mota a gidansa da tarin wasu babura da ƴan bindiga ke amfani da ire-irensu wajen kai farmaki a garuruwan Arewacin Nijeriya.

A wata takarda da ke ɗauke da sanya hannun Daraktan hulɗa da jama'arta, Dakta Yazidu Muhammad Namoriki, CCZ ta bayyana cewa yayin da jami'an tsaro suke ƙoƙarin daƙile ayyukan ta'addanci da dawo da zaman lafiya a shiyyar da sauran sassan ƙasa, ƙulla makirci daga manyan ƙasa ka iya haifar wa hakan tsaiko da jefa sassan arewacin Nijeriya cikin hatsari mafi muni.

Ta ce, Sanata Buba a matsayinsa na Shugaban kwamitin tsaron ƙasa a Majalisar Dattawa ya sauya akalar muƙaminsa wajen kitsa ayyukan ta'addancin ƴan bindiga a yankin Arewa ta Yamma da wasu yankunan Arewa ta Gabas.

A cewarta, rahotanni sun nuna cewa yana da hannu a tallafa wa ƴan bindiga da tada zaune-tsaye a garuruwa wajen haɗa faɗa tsakanin ƙabilu.

Don haka ƙungiyar take ganin hakan a matsayin abinda zai iya shafar kimar ofishinsa na shugaban kwamitin harkar tsaro ganin yadda al'umma ke sa ran samun adalci daga gare shi akan lamuran tsaron rayuka da dukiyoyinsu a ko'ina suke a ƙasar.

Haka kuma, CCZ ta yi ikirarin cewa Sanatan yana ɗaukar nauyin safarar ƴan bindigar da aka raunata daga Zamfara zuwa Ƙaramar Hukumar Toro a Bauchi don ba su magani, wanda hakan ke nuna goyon bayansa ga ayyukan ta'addanci.

Saboda haka ta ke kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta ɗaukar matakin da ya dace akan Santan.

"Muna buƙatar gwamnati da ta bada umarnin kamawa, bincike da gurfanar da Sanata Buba matuƙar aka samu hujja mai ƙarfi da ke nuna yana da hannu a ayyukan ta'addanci."

Kazalika, ta nemi gwamnatin da ta ƙwace kadarorin da aka mallaka ta haramtattun hanyoyi kamar na kuɗaɗe fansa, lamarin da acewarta zai taimaka wajen mayar wa waɗanda aka karɓa daga hannunsu da kuma hana wasu shiga aikata ire-iren ayyukan.

Gwamnan Jihar Borno Farfesa, Farfesa Babagana Umara Zulum Ya Kai Ziyarar Ta'aziyya Ga Shugaban Jam'iyyar APC Na Kasa, Fa...
19/09/2025

Gwamnan Jihar Borno Farfesa, Farfesa Babagana Umara Zulum Ya Kai Ziyarar Ta'aziyya Ga Shugaban Jam'iyyar APC Na Kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda Bisa Rasuwar Mahaifiyarsa

CIKIN HOTUNA:Hotunan yadda Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda Yayi Rakiyar Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu Zuw...
19/09/2025

CIKIN HOTUNA:

Hotunan yadda Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda Yayi Rakiyar Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu Zuwa Gidan Marigayi Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a Kaduna.

Gwamnan ya kasance cikin manyan shugabanni da s**a tarbi Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu yayin ziyarar ban girma da shugaban ƙasar ya kai gidan Marigayi Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a Kaduna a ranar Juma’a 19/9/2025.

Maryamu Idris, ‘yar asalin Jihar Katsina, ta samu nasarar zama wakiliyar Najeriya a Ƙungiyar Ƙasashe Masu Fitar da Ɗanye...
19/09/2025

Maryamu Idris, ‘yar asalin Jihar Katsina, ta samu nasarar zama wakiliyar Najeriya a Ƙungiyar Ƙasashe Masu Fitar da Ɗanyen Mai (OPEC).

Wannan babban mukami da ta samu ya sanya sunanta cikin jerin matasa mata ‘yan Najeriya da ake sa ran za su taka muhimmiyar rawa a harkokin ƙasa da ƙasa, musamman a fannin makamashi da diplomasiya.

CIKIN HOTUNA:Yadda Shugaba Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya sa albarka ga auren dan Abdulaziz Yari a Kaduna
19/09/2025

CIKIN HOTUNA:

Yadda Shugaba Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya sa albarka ga auren dan Abdulaziz Yari a Kaduna

Gwamnatin Kano Ta Sanya Sunan Sheikh Ja’afar Adam A Sabon Gadar DorayiDuba da irin gudunmawar da Marigayi Sheikh Ja’afar...
19/09/2025

Gwamnatin Kano Ta Sanya Sunan Sheikh Ja’afar Adam A Sabon Gadar Dorayi

Duba da irin gudunmawar da Marigayi Sheikh Ja’afar Mahmud Adam ya bayar wajen yaɗa ilimi da bunƙasa Addinin Musulunci, Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sanya sunan Malamin a kan wani sabon gada da gwamnatin jihar ta kammala a yankin Dorayi.

Sabon gadar, wanda aka radawa suna “Sheikh Ja’afar Adam Road”, na daga cikin muhimman ayyukan raya birni da gwamnatin Kano ke aiwatarwa domin:
• Inganta harkokin sufuri,
• Rage cunkoson ababen hawa,
• Da kuma girmama fitattun mutane masu tasiri wajen ci gaban al’umma.

Rahoton ya tabbatar da cewa, hakan wani mataki ne da gwamnatin Kano don haka ya kasance wani nau’i na tunawa da marigayi Sheikh Ja’afar, wanda ya kasance fitaccen malami mai kishin addini da al’umma, kuma darussansa har yanzu na ci gaba da haskaka zukatan Musulmai a gida da kasashen waje.

Ɗiyar Shugaban Kamaru Ta Kira Da Kada A Zaɓi Mahaifinta A Zaɓen 2025Brenda Biya,  ‘yar shugaban ƙasar Kamaru Paul Biya, ...
19/09/2025

Ɗiyar Shugaban Kamaru Ta Kira Da Kada A Zaɓi Mahaifinta A Zaɓen 2025

Brenda Biya, ‘yar shugaban ƙasar Kamaru Paul Biya, ta fito fili ta roƙi ‘yan ƙasar kada su zaɓi mahaifinta a zaɓen watan Oktoba 2025.

A cikin wani shirin kai Tsaye na manhajar TikTok, inda ake kiranta da “King Nasty”, Brenda ta dora laifin talauci, rashin aikin yi da durƙushewar tattalin arziki a Kamaru bisa ga irin shugabancin mahaifinta na tsawon shekaru 43. Wannan shi ne karon farko a tarihin siyasar Afirka da ɗiyar shugaban ƙasa mai ci ta fito fili ta yi adawa da mulkin mahaifinta tare da kira ga jama’a da su ƙi sake zaɓensa.

Paul Biya, wanda ke da shekaru 92 a duniya, yana daga cikin shugabannin da s**a fi dadewa a akan karagar mulki a duniya. Mulkinsa ya sha s**a kan batutuwan kama-karya, rashawa da kuma uwa uba magudin zaɓe da ake zargin shi da aikatawa.

Sai dai masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa Brenda, wadda take rayuwa a ƙasashen waje tana adawa da mahaifinta ne saboda bambancin ra'ayi kawai, ba kalubale ko tsadar rayuwar yan kasar Kamaru ya sanyata yin adawa da mahaifin nata ba.

19/09/2025

Yadda Farashin Abinci Ke Ci-gaba Da Yin Rugu-rugu A Wasu Kasuwannin Jihar Yobe Da Kaduna

Shugaba Tinubu ya ziyarci matar marigayi tsohon shugaban Nijeriya Aisha Buhari a Kaduna
19/09/2025

Shugaba Tinubu ya ziyarci matar marigayi tsohon shugaban Nijeriya Aisha Buhari a Kaduna

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nigerian Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nigerian Post:

Share