18/10/2025
Gwamna Namadi Ya Halarci Taron Samar Da Wutar Lantarki A Kasashen Afrika A Morocco
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya halartar taron koli dake gudana na tsawon kwanaki biyu da aka ware domin tattaunawa kan ci gaban bangaren samar da wutar lantarki a ƙasashen Afirka, wanda ake gudanarwa a birnin Marrakech na ƙasar Morocco.
Taron, wanda aka kira "High-Level Electricity Sector Symposium", ya haɗa gwamnonin Jihar Kano, Katsina, da Jigawa, tare da manyan kamfanonin samar da mak**ashi irin su Kano Electricity Distribution Company (KEDCO) da Future Energies Africa (FEA).
A cewar bayanan da s**a fito daga tawagar Gwamna Namadi, tattaunawar ta mayar da hankali ne kan yadda za a inganta haɗin gwiwar yankin Arewa maso Yamma wajen janyo masu sanya hannun jarin cikin sashen wutar lantarki, musamman ta fannin sabbin hanyoyin samar da mak**ashi mai tsafta da dorewa.
Daga cikin muhimman batutuwan da ake tattaunawa sun haɗa da:
Faɗaɗa damar samun wutar lantarki daga hasken rana da sauran mak**ashi masu sabuntawa,
Inganta rarraba lantarki a tsakanin jihohin Kano, Katsina da Jigawa,
Da kuma binciken sabbin tsare-tsaren samun kuɗaɗen gudanar da ayyukan mak**ashi mai tsafta.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana cewa Jihar Jigawa tana da babbar damar saka hannun jari a fannin mak**ashin mai amfani da hasken rana (solar energy), inda ya jaddada aniyar gwamnatinsa wajen janyo masu zuba jari don wutar kauyuka, masana’antu, da aikin gona.
Ya ce, wannan shiri na daga cikin matakan gwamnatin Jigawa na tabbatar da ci gaba mai ɗorewa da samar da ingantaccen wutar lantarki domin bunƙasa masana’antu, sarrafa amfanin gona, da ƙirƙirar ayyukan yi ga matasa.
Halartar Gwamna Namadi a wannan taron, in ji sanarwar, na nuna ƙudurinsa na kawo ci gaba mai dorewa da sabbin hanyoyin mak**ashi a jihar Jigawa, tare da tabbatar da cewa jihar ta kasance gaba-gaba a harkar amfani da mak**ashi mai tsafta a Najeriya.