Nigerian Post

Nigerian Post Call Or Whatsapp On This No.: +2348031568031

18/10/2025

Kaiysaye tattaunawa da shugaban ƙungiyar YOWICAN, Praise Isaiah bayan ƙaddamar da tallafi ga mutane 600 a Katsina

18/10/2025

Kaitsaye tattaunawa da Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, wanda ya samu wakilcin Dr. Abubakar Ahmad Tsanni, bayan kammala taron bada tallafi ga ƙungiyar YOWICAN a Katsina.

Ma'aikatar Kasafin Kuɗi Da Tsare-tsaren Tattalin Arzikin Jihar Katsina A Karkashin Jagorancin Alhaji Malik Anas Ta Kamma...
18/10/2025

Ma'aikatar Kasafin Kuɗi Da Tsare-tsaren Tattalin Arzikin Jihar Katsina A Karkashin Jagorancin Alhaji Malik Anas Ta Kammala Taron Kare Kasafin Kuɗin Shekarar 2026, Wanda Hukumomi Da Ma'aikatun 117 S**a Gabatar Da Kasafin Kuɗinsu, Domin Samun Tsabtattaccen Kasafin Kuɗin Shekara 2026, Jiya Juma'a

‎Ƙungiyar Magoya Bayan APC Ta Ondo Ta Yi Wa Tinubu Alƙawarin Ƙuri’u 400,000 A Zaɓen 2027 ‎‎Wata kungiya ta magoya bayan ...
18/10/2025

‎Ƙungiyar Magoya Bayan APC Ta Ondo Ta Yi Wa Tinubu Alƙawarin Ƙuri’u 400,000 A Zaɓen 2027

‎Wata kungiya ta magoya bayan jam’iyyar APC a Jihar Ondo, mai suna Ondo APC Aborigines, ta sha alwashin tara aƙalla kuri’u 400,000 domin sake zaɓen Shugaba Bola Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

‎Kungiyar, wacce ta ƙunshi shugabanni da dattawan jam’iyya daga ƙananan hukumomi 18 na jihar, ta bayyana wannan kuduri ne a taronta da ta gudanar a Akure, babban birnin jihar, a jiya Alhamis.

‎Da ya ke jawabi a taron, jagoran kungiyar kuma tsohon Jakadan Najeriya a ƙasar Togo, Sola Iji, ya ce ‘yan asalin APC a jihar na nan daram da biyayya ga jam’iyya da kuma gwamnatin Tinubu.

‎Ya bayyana cewa an shirya taron ne da nufin ƙarfafa tsarin kungiyar da haɗa kan mambobinta gabannin zaɓen 2027.

‎Ya ce, “Ba za mu taɓa yarda a rage mana ƙima ba dangane da sadaukarwa da biyayyar mu ga jam’iyya da gwamnati. Ba za mu kuma bari a haɗa mu da waɗanda ke ƙoƙarin ɓata gwamnati ko kawo rikici cikin jam’iyyarmu ta APC ba.”

Gwamna Namadi Ya Halarci Taron Samar Da Wutar Lantarki A Kasashen Afrika A MoroccoGwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namad...
18/10/2025

Gwamna Namadi Ya Halarci Taron Samar Da Wutar Lantarki A Kasashen Afrika A Morocco

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya halartar taron koli dake gudana na tsawon kwanaki biyu da aka ware domin tattaunawa kan ci gaban bangaren samar da wutar lantarki a ƙasashen Afirka, wanda ake gudanarwa a birnin Marrakech na ƙasar Morocco.

Taron, wanda aka kira "High-Level Electricity Sector Symposium", ya haɗa gwamnonin Jihar Kano, Katsina, da Jigawa, tare da manyan kamfanonin samar da mak**ashi irin su Kano Electricity Distribution Company (KEDCO) da Future Energies Africa (FEA).

A cewar bayanan da s**a fito daga tawagar Gwamna Namadi, tattaunawar ta mayar da hankali ne kan yadda za a inganta haɗin gwiwar yankin Arewa maso Yamma wajen janyo masu sanya hannun jarin cikin sashen wutar lantarki, musamman ta fannin sabbin hanyoyin samar da mak**ashi mai tsafta da dorewa.

Daga cikin muhimman batutuwan da ake tattaunawa sun haɗa da:

Faɗaɗa damar samun wutar lantarki daga hasken rana da sauran mak**ashi masu sabuntawa,

Inganta rarraba lantarki a tsakanin jihohin Kano, Katsina da Jigawa,

Da kuma binciken sabbin tsare-tsaren samun kuɗaɗen gudanar da ayyukan mak**ashi mai tsafta.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana cewa Jihar Jigawa tana da babbar damar saka hannun jari a fannin mak**ashin mai amfani da hasken rana (solar energy), inda ya jaddada aniyar gwamnatinsa wajen janyo masu zuba jari don wutar kauyuka, masana’antu, da aikin gona.

Ya ce, wannan shiri na daga cikin matakan gwamnatin Jigawa na tabbatar da ci gaba mai ɗorewa da samar da ingantaccen wutar lantarki domin bunƙasa masana’antu, sarrafa amfanin gona, da ƙirƙirar ayyukan yi ga matasa.

Halartar Gwamna Namadi a wannan taron, in ji sanarwar, na nuna ƙudurinsa na kawo ci gaba mai dorewa da sabbin hanyoyin mak**ashi a jihar Jigawa, tare da tabbatar da cewa jihar ta kasance gaba-gaba a harkar amfani da mak**ashi mai tsafta a Najeriya.

Sojoji Sun Ceto Mutane 21 Wanda ‘Yanbindiga S**a Sace A Jihar KogiDakarun Sojojin Nijeriya runduna Division 2/sector 3, ...
18/10/2025

Sojoji Sun Ceto Mutane 21 Wanda ‘Yanbindiga S**a Sace A Jihar Kogi

Dakarun Sojojin Nijeriya runduna Division 2/sector 3, da su ke Operation Fansa Yama, sun samu nasarar ceto mutane 21 daga hannun ‘yanbindiga a tsakanin Kwara da Kogi.

Mutanan sun haɗa da Maza 14, Mata 5, jariri 1 da ‘yan China 4, waɗanda a ka k**a su daga wurare daban-daban da ke wannan ƙasa.

Yanzu dai mutanan na karɓar magani a wajen sojojin kafin haɗa su da iyalansu, k**ar yadda shafin HQ Nigerian Army ya ruwaito.

Yan Sanda Sun Gano Wayoyi 72 da aka Sace a Akwa Ibom, Da Kimar su ta Kai Naira Miliyan 2Rundunar ‘yan sandan Jihar Akwa ...
18/10/2025

Yan Sanda Sun Gano Wayoyi 72 da aka Sace a Akwa Ibom, Da Kimar su ta Kai Naira Miliyan 2

Rundunar ‘yan sandan Jihar Akwa Ibom ta, tabbatar da gano wasu kayayyaki da s**a haɗa da wayoyi hannu guda 72 da kimar su ta kai kusan Naira miliyan biyu, bayan da ta cafke wasu ‘yan fashi da makami huɗu da ake zargi da satar su daga hannun jama’a.

Kakakin rundunar, ASP Timfon John, ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a madadin Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Waheed Ayilara, k**ar yadda jaridar Daily Post ta ruwaito.

“Rundunar ta gudanar da samame a wasu unguwanni na birnin Uyo inda ta cafke mutane huɗu da ake zargi da fashi da makami. An gano wayoyi 72 da darajar su ta kai kusan naira miliyan biyu, da kuma wasu mak**ai daga hannunsu,” in ji ASP Timfon.

Ta ƙara da cewa jami’an rundunar sun samu nasarar gano wurin da ake ajiye kayayyakin da aka sace ne bayan samun bayanai daga wasu masu taimakon jami’an tsaro a yankin.

“Bincike yana ci gaba domin gano sauran abokan harkar su da kuma inda suke sayar da kayan jama’a,” ta ƙara da cewa.

ASP Timfon ta kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da wadanda aka k**a a gaban kotu da zarar an kammala bincike, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da ba ‘yan sanda bayanai masu muhimmanci don hana aikata laifika.

‎Madugun Darikar Kwakwasiyya Dr. Rabi'u Kwankwaso Ya Yi Ganawar Sirri Da Janar Babangida ‎‎Jagoran Jam’iyyar NNPP na ƙas...
17/10/2025

‎Madugun Darikar Kwakwasiyya Dr. Rabi'u Kwankwaso Ya Yi Ganawar Sirri Da Janar Babangida

‎Jagoran Jam’iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi wata ganawa da tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (rtd), a gidansa dake Hilltop, Minna, Jihar Neja, a yau Jumma’a.

‎A yayin ziyarar, Sanata Kwankwaso ya samu rakiyar Shugaban Jam’iyyar NNPP na ƙasa, Dakta Ahmed Ajuji, inda s**a gudanar da ganawar sirri da tsohon Shugaban Ƙasar, k**ar yadda mai taimakawa Kwankwaso a bangaren kafafen yada labarai, Saifullahi Hassan, ya wallafa a shafinsa na Facebook.

17/10/2025

"Bamu Yarda da Aqidar Karantarwar Alqur'ani Zallah ba dole mu tashi mu yaƙi wannan barnar" Inji Shugaban Izala na ƙasa Sheikh Abdullahi Bala Lau

CIKIN HOTUNA:Gwamnonin jahohin Katsina, Kano da Jigawa - Gwamna Radda, Abba Gida-Gida da Namadi Sun Halarci Sallar Juma’...
17/10/2025

CIKIN HOTUNA:

Gwamnonin jahohin Katsina, Kano da Jigawa - Gwamna Radda, Abba Gida-Gida da Namadi Sun Halarci Sallar Juma’a a Kasar Morocco

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, PhD, CON, tare da takwarorinsa na Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, da na Jihar Jigawa, Malam Umar A. Namadi, sun halarci Sallar Juma’a a ƙasar Morocco a ranar Juma’a, 17 ga Oktoba, 2025.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nigerian Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nigerian Post:

Share