04/09/2026
’Yan Sanda Sun K**a Yan Fashi 11, Sun Ceto Wanda Aka Yi Garkuwa Da Shi a Nasarawa
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa ta ce ta yi nasarar ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi tare da k**a mutane 11 da ake zargi da fashi da makami a wasu samamen da ta gudanar a sassa daban-daban na jihar.
Mai magana da yawun rundunar, SP Ramhan Nansel, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.
Ya ce jami’an tsaro tare da haɗin gwiwar mafarauta na cikin gida da matasan al’umma sun ceto wata mata mai suna Favour Innocent, wadda aka yi garkuwa da ita daga gidanta da ke ƙauyen Ajyga a ranar 3 ga Agusta, 2026.
An ceto matar ne a ranar 4 ga Agusta a yankin dajin Nunku, cikin ƙaramar hukumar Akwanga.
Bayan an ceto ta, an kai ta Cibiyar Kula da Lafiya ta Farko da ke Andaha domin samun kulawar likita, inda aka ce an sallame ta cikin ƙoshin lafiya sannan aka mayar da ita ga iyalanta.
A wani samame kuma, rundunar ta samu rahoton cewa wasu ’yan fashi da makami sun kai hari wani gidan baki da ke Area One, Masaka, da misalin ƙarfe 2:00 na dare a ranar 4 ga Satumba.
Rahoton ya ce ’yan fashin sun kwashe wayoyin hannu, kuɗi da sauran kayayyaki daga hannun mutanen da ke gidan.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Shetima Jauro Mohammed, ya bayar da umarnin tura jami’an sintiri zuwa wurin.
Da ’yan fashin s**a hango motar ’yan sanda, sai s**a tsere, amma jami’an s**a bi sawunsu har zuwa maboyarsu, inda aka k**a mutane 11.
Daga cikin waɗanda aka k**a akwai manya tara da ƙananan yara biyu masu shekaru 16 da 15.
Jami’an tsaron sun ce sun kwato bindiga kirar gida, adduna, wuƙaƙe, katin SIM guda takwas, kayan rufe kai, almakashi, kuɗaɗen ƙasashen waje na bogi da wasu takardu.
Kwamishinan ’Yan Sandan ya umarci jami’an da su gano iyayen ƙananan yaran biyu domin ɗaukar matakin da ya dace, yayin da aka tura manyan waɗanda ake zargin zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar domin ci gaba da bincike da gurfanar da su.
Rundunar ta ce tana ci gaba da ƙoƙarin k**a sauran waɗanda s**a tsere tare da kwato sauran kayayyakin da aka sace.
Ta kuma yabawa jami’an ’yan sanda, mafarauta da matasan al’umma bisa taimakon da s**a bayar wajen gudanar da ayyukan, musamman wajen ceto wanda aka yi garkuwa da shi.
Rundunar ta buƙaci jama’a da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai cikin gaggawa domin taimakawa wajen dakile aikata laifuka da k**a masu aikata laifuka.