Nigerian Post

Nigerian Post Our platform covers a wide range of topics includes politics, governance, security, and others
(2)

Nigerian Post is an independent digital news and media platform committed to delivering credible, timely, and fact-based news from Nigeria and across the globe.

‎An Tsinci Jarirai Biyu da Aka Jefari da Su a Abuja‎‎Rundunar ’yan sandan babban birnin tarayya Abuja (FCT Police Comman...
04/09/2026

‎An Tsinci Jarirai Biyu da Aka Jefari da Su a Abuja

‎Rundunar ’yan sandan babban birnin tarayya Abuja (FCT Police Command) ta ceto jarirai biyu da aka yi watsi da su a wurare daban-daban.

‎A cewar rundunar, an gano jariri namiji a Kurudu, yayin da aka samu jaririya mace a Gwagwalada, a wasu abubuwa biyu da s**a faru daban.

‎A halin yanzu, jariran na samun kulawar lafiya yayin da jami’an ’yan sanda ke ci gaba da bincike domin gano iyayensu, musamman iyayensu mata, da kuma kokarin mayar da su ga iyalansu.

‎Sanata Babba Kaita Ya Bukaci a Dauki Matakan Gaggawa Kan Hare-haren Funtua, Jihar Katsina ‎‎Ɗan takarar gwamnan Jihar K...
04/09/2026

‎Sanata Babba Kaita Ya Bukaci a Dauki Matakan Gaggawa Kan Hare-haren Funtua, Jihar Katsina

‎Ɗan takarar gwamnan Jihar Katsina a ƙarƙashin jam’iyyar ADC, Sanata Ahmad Babba Kaita, ya jajanta wa al’ummar Funtua bisa hare-haren ’yan bindiga da s**a addabi garin a wannan makon.

‎Sanata Kaita ya bayyana matuƙar damuwarsa kan yadda hare-haren ke ci gaba da faruwa, yana mai cewa lamarin ya wuce gona da iri, musamman ganin yadda aka shafe kwanaki ana kai wa al’ummar garin farmaki.

‎A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na kamfen ɗinsa, Abubakar Ahmed, ya fitar ranar Juma’a, Sanata Kaita ya ce akwai buƙatar hukumomin tsaro su ɗauki matakan gaggawa domin dakile hare-haren da kuma kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

‎Ya kuma jajanta wa iyalan waɗanda s**a rasa rayukansu sak**akon hare-haren, tare da addu’ar Allah Ya jikansu da rahama, Ya kuma ba waɗanda s**a rasa dukiyoyinsu madadinsu.

‎Sanata Kaita, wanda sanarwar ta ce yana ci gaba da samun sauƙi bayan an yi masa wani aikin tiyata a asibiti a Turai, ya kuma bayyana damuwa kan halin da al’ummomi daban-daban a Jihar Katsina ke ciki sak**akon ayyukan ’yan bindiga.

‎Ya ce hare-haren da ake kai wa al’ummar jihar na buƙatar haɗin gwiwar gwamnati da hukumomin tsaro domin magance matsalar cikin gaggawa.

‎Jagoran ADC a Jihar Katsina ya sake yin kira ga gwamnati da hukumomin da ke da alhakin tsaro da su ƙara kaimi wajen yaƙi da ’yan bindiga, tare da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

‎Sanata Kaita ya ce matsalar rashin tsaro ta daɗe tana jefa al’ummar Najeriya cikin fargaba, yana mai buƙatar ɗaukar ingantattun matakai domin kawo ƙarshen ta’asar.

‎BBC Ta Nada Haruna Ibrahim Kakangi Sabon Editan Sashen Hausa‎‎Hukumar BBC ta nada fitaccen ɗan jarida, Haruna Ibrahim K...
04/09/2026

‎BBC Ta Nada Haruna Ibrahim Kakangi Sabon Editan Sashen Hausa

‎Hukumar BBC ta nada fitaccen ɗan jarida, Haruna Ibrahim Kakangi, a matsayin sabon Editan Sashen Hausa na BBC.

‎Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa Kakangi ya samu wannan matsayi ne bayan kammala zagaye biyu na tantance ‘yan takarar da za su maye gurbin tsohon Editan Sashen Hausa, Aliyu Abdullahi Tanko, wanda ya bar mukamin a baya.

‎Kakangi, wanda ya kasance babban ɗan jaridar dijital a BBC World Service, ya dade yana aiki a Sashen Hausa, inda ya rike muhimman ayyuka a fannin aikin jarida da shirye-shiryen rediyo da na zamani.

‎An kuma tabbatar da cewa Kakangi ya kasance cikin ma’aikatan BBC Hausa da kuma masu gabatar da shirye-shiryen sashen a baya.


‎Tinubu, Shettima da Gwamnonin Arewa ta Tsakiya za su tsara shirin ci-gaban shekaru 20‎‎Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu,...
04/09/2026

‎Tinubu, Shettima da Gwamnonin Arewa ta Tsakiya za su tsara shirin ci-gaban shekaru 20

‎Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima da gwamnonin jihohin Arewa ta Tsakiya na shirin halartar taron masu ruwa da tsaki da za a gudanar domin tsara shirin ci-gaban yankin na tsawon shekaru 20.

‎Za a gudanar da taron ne a ranakun 14 da 15 ga Satumba 2026 a Abuja, inda za a tattauna hanyoyin bunƙasa tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa da inganta ci gaban al’umma a yankin.

‎Taron, mai taken “The Great Leap Forward: A 20-Year Economic, Infrastructural and Social Development Plan for the North Central Region,” na ƙarƙashin jagorancin Hukumar Raya Arewa ta Tsakiya (NCDC), kuma zai haɗa gwamnoni, shugabannin gargajiya, masana, ’yan kasuwa da sauran masu ruwa da tsaki.

Ɗan KAROTA Ya Rasu Bayan Karaya 6 da ya samu Sak**akon wani direba da ya buge shi ya gudu a DambattaWani jami’in Hukumar...
04/09/2026

Ɗan KAROTA Ya Rasu Bayan Karaya 6 da ya samu Sak**akon wani direba da ya buge shi ya gudu a Dambatta

Wani jami’in Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA), Nasiru Mai Jihadi, ya rasu a Asibitin Murtala Muhammad da ke Kano, bayan ya kwashe kwanaki yana jinya sak**akon raunin da ya samu a wani hatsarin mota a Dambatta.

Arewa Updates ta rawaito cewa, Jami’in KAROTA mai kula da shiyyar Dambatta, OC Ali Mustapha Rabatsu, ne ya tabbatar da rasuwar jami’in a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa, wani direban mota ne ya buge Nasiru Mai Jihadi a Dambatta, sannan ya tsere daga wurin.

Rahoton ya ce hatsarin ya yi sanadin samun jami’in karaya har guda shida a hannayensa da kafafunsa, lamarin da ya kai ga kwantar da shi a Asibitin Murtala domin samun kulawar lafiya.

Sai dai daga bisani, Nasiru Mai Jihadi ya rasu yayin da yake jinya.

Hukumar KAROTA ta bayyana alhininta da jimaminta kan rasuwar jami’in nata, tare da jajanta wa iyalansa da sauran abokan aikinsa.

’Yan Sanda Sun K**a Yan Fashi 11, Sun Ceto Wanda Aka Yi Garkuwa Da Shi a NasarawaRundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa ta ...
04/09/2026

’Yan Sanda Sun K**a Yan Fashi 11, Sun Ceto Wanda Aka Yi Garkuwa Da Shi a Nasarawa

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa ta ce ta yi nasarar ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi tare da k**a mutane 11 da ake zargi da fashi da makami a wasu samamen da ta gudanar a sassa daban-daban na jihar.

Mai magana da yawun rundunar, SP Ramhan Nansel, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Ya ce jami’an tsaro tare da haɗin gwiwar mafarauta na cikin gida da matasan al’umma sun ceto wata mata mai suna Favour Innocent, wadda aka yi garkuwa da ita daga gidanta da ke ƙauyen Ajyga a ranar 3 ga Agusta, 2026.

An ceto matar ne a ranar 4 ga Agusta a yankin dajin Nunku, cikin ƙaramar hukumar Akwanga.

Bayan an ceto ta, an kai ta Cibiyar Kula da Lafiya ta Farko da ke Andaha domin samun kulawar likita, inda aka ce an sallame ta cikin ƙoshin lafiya sannan aka mayar da ita ga iyalanta.

A wani samame kuma, rundunar ta samu rahoton cewa wasu ’yan fashi da makami sun kai hari wani gidan baki da ke Area One, Masaka, da misalin ƙarfe 2:00 na dare a ranar 4 ga Satumba.

Rahoton ya ce ’yan fashin sun kwashe wayoyin hannu, kuɗi da sauran kayayyaki daga hannun mutanen da ke gidan.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Shetima Jauro Mohammed, ya bayar da umarnin tura jami’an sintiri zuwa wurin.

Da ’yan fashin s**a hango motar ’yan sanda, sai s**a tsere, amma jami’an s**a bi sawunsu har zuwa maboyarsu, inda aka k**a mutane 11.

Daga cikin waɗanda aka k**a akwai manya tara da ƙananan yara biyu masu shekaru 16 da 15.

Jami’an tsaron sun ce sun kwato bindiga kirar gida, adduna, wuƙaƙe, katin SIM guda takwas, kayan rufe kai, almakashi, kuɗaɗen ƙasashen waje na bogi da wasu takardu.

Kwamishinan ’Yan Sandan ya umarci jami’an da su gano iyayen ƙananan yaran biyu domin ɗaukar matakin da ya dace, yayin da aka tura manyan waɗanda ake zargin zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar domin ci gaba da bincike da gurfanar da su.

Rundunar ta ce tana ci gaba da ƙoƙarin k**a sauran waɗanda s**a tsere tare da kwato sauran kayayyakin da aka sace.

Ta kuma yabawa jami’an ’yan sanda, mafarauta da matasan al’umma bisa taimakon da s**a bayar wajen gudanar da ayyukan, musamman wajen ceto wanda aka yi garkuwa da shi.

Rundunar ta buƙaci jama’a da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai cikin gaggawa domin taimakawa wajen dakile aikata laifuka da k**a masu aikata laifuka.

‎EFCC Ta Samu Wa’adin Kwanaki 14 Ta Sake Binciken Atiku Kan Zargin Almundahana‎‎Tsohon ɗan majalisar wakilai, Ehiozuwa A...
04/09/2026

‎EFCC Ta Samu Wa’adin Kwanaki 14 Ta Sake Binciken Atiku Kan Zargin Almundahana

‎Tsohon ɗan majalisar wakilai, Ehiozuwa Agbonayinma, ya nemi Hukumar Yaƙi da Yiwa Tattalin Arzikin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC) da ta sake buɗe bincike tare da gurfanar da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, kan zargin laifukan kuɗi.

‎Agbonayinma, ta hannun lauyansa Hannibal Uwaifo na Sagitarian Law Firm, ya bai wa EFCC wa’adin kwanaki 14 da ta ɗauki mataki kan buƙatar.

‎A cikin wasiƙar mai kwanan wata 27 ga watan Agusta, wadda EFCC ta karɓa ranar 1 ga watan Satumba, lauyan ya ce buƙatar ta samo asali ne daga wani bincike da rahoton da hukumar ta gudanar kan zarge-zargen da s**a shafi Atiku tsakanin 2005 da 2006.

‎Ya nemi EFCC ta sake duba batun tare da ɗaukar matakin da ya dace bisa sak**akon binciken da aka gudanar a baya.

‎Atiku, wanda ke cikin manyan ƴan siyasar da ke neman shugabancin Najeriya a 2027, shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC.

‎A halin yanzu, EFCC ba ta bayyana matsayinta kan buƙatar ba.

‎Miyetti Allah Ta Nemi Tinubu Ya Sa Baki Wajen Sakin Shugabanta‎‎Kungiyar Miyetti Allah Kautal H**e ta shiyyar Arewa ta ...
04/09/2026

‎Miyetti Allah Ta Nemi Tinubu Ya Sa Baki Wajen Sakin Shugabanta

‎Kungiyar Miyetti Allah Kautal H**e ta shiyyar Arewa ta Tsakiya ta yi kira ga Shugaba Bola Tinubu da sauran hukumomin gwamnati da su sa baki domin a sake shugabanta na ƙasa, Abdullahi Bello Bodejo, wanda aka sake k**a shi bayan an sake shi daga hannun EFCC.

‎Shugaban kungiyar na Arewa ta Tsakiya, Idris Bebeji, ne ya yi kiran a wani taron manema labarai da aka gudanar a Karu, Jihar Nasarawa.

‎Bebeji ya ce Bodejo ya shafe kusan watanni huɗu a hannun EFCC bayan da DSS ta k**a shi a Jalingo, Jihar Taraba, a lokacin da yake shirin bayyana aniyarsa ta neman kujerar Sanata mai wakiltar Taraba ta Tsakiya.

‎Ya ce bayan Bodejo ya cika sharuddan sakin da aka gindaya masa kuma aka sake shi, jami’an DSS sun sake k**a shi a ranar 28 ga Agusta, 2026.

‎Kungiyar ta nemi Tinubu, Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, Ministan Shari’a Lateef Fagbemi, shugabannin APC da DSS su duba batun, domin tabbatar da cewa ana mutunta haƙƙin ɗan Adam da bin tsarin doka.

‎Bebeji ya jaddada cewa kungiyar ba ta neman a fifita Bodejo a kan doka, sai dai ta bukaci a bi tsarin shari’a yadda ya k**ata. Ya kuma yi kira ga mambobin kungiyar da al’ummar Fulani makiyaya su kasance cikin nutsuwa tare da bin doka yayin da ake kokarin warware matsalar ta hanyar tattaunawa da tsarin kundin tsarin mulki.

Burna Boy Ya Zama Mawaki Dan Najeriya na Farko da Ya Samu Masu Kallo Biliyan 4 a Page Dinsa na YouTube Shahararren mawak...
04/09/2026

Burna Boy Ya Zama Mawaki Dan Najeriya na Farko da Ya Samu Masu Kallo Biliyan 4 a Page Dinsa na YouTube

Shahararren mawakin Najeriya kuma wanda ya lashe kyautar Grammy, Damini Ogulu, wanda aka fi sani da Burna Boy, ya kafa sabon tarihi bayan ya zama mawakin Najeriya na farko da ya samu kallon bidiyo sama da biliyan hudu a YouTube.

An cimma wannan matsayi ne sak**akon jimillar kallon bidiyoyin wakokinsa da sauran abubuwan da ke shafinsa na YouTube.

Wannan nasara ta kara nuna yadda wakokin Burna Boy ke samun karbuwa a fadin duniya, tare da yadda wakokin Afrobeats ke kara samun karbuwa a kasashen duniya.

Daga cikin fitattun wakokin mawakin da s**a samu dimbin kallo a YouTube akwai Ye, On The Low, Last Last da For My Hand, wadanda s**a tara miliyoyin kallo a dandalin.

Burna Boy ya taba kafa tarihi a shekarar 2021, lokacin da ya zama mawakin Najeriya na farko da ya ketare kallon bidiyo biliyan daya a YouTube.

Sabuwar nasarar ta zo ne a daidai lokacin da mawakin ke ci gaba da kafa wasu tarihi a fagen wakokin duniya, inda wakokinsa ke samun masu sauraro a Afirka, Turai, Arewacin Amurka da sauran sassan duniya.

Masana harkar nishadi sun bayyana cewa wannan nasara na nuna muhimmiyar rawar da kafafen yada abubuwan dijital ke takawa wajen tallata wakokin Najeriya zuwa ga masu sauraro a duniya.

Haka kuma, wannan matsayi ya kara sanya Burna Boy cikin jerin fitattun mawakan Afirka da s**a samu dimbin mabiya a YouTube, tare da kafa sabon ma'auni ga mawakan Najeriya.

‎Bayan Ce-ce-ku-ce, Dantakarar Gwamnan Oyo na APC Ya Bayyana Dalilin da Ya Sa Dalibi Ya Zauna a Kan Cinyarsa‎‎Kungiyar y...
04/09/2026

‎Bayan Ce-ce-ku-ce, Dantakarar Gwamnan Oyo na APC Ya Bayyana Dalilin da Ya Sa Dalibi Ya Zauna a Kan Cinyarsa

‎Kungiyar yakin neman zaben ɗan takarar gwamnan jihar Oyo na jam’iyyar APC, Sanata Sharafadeen Alli, ta yi karin bayani kan wani faifan bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta, inda aka ga wani dalibi namiji daga Polytechnic ta Ibadan zaune a kan cinyar dan siyasar.

‎A cikin faifan bidiyon da ya yadu a kafafen sada zumunta, an ga dalibin zaune a kan cinyar Alli a lokacin da yake ganawa da wasu dalibai a ofishinsa na yakin neman zabe da ke Mokola, Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

‎Haka kuma, faifan ya nuna Alli yana shafar cinyar dalibin, lamarin da ya janyo cece-kuce da martani daga masu amfani da kafafen sada zumunta.

‎Da take martani kan lamarin a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, kungiyar yakin neman zaben ta ce dalibin da wasu takwarorinsa daga sashen koyar da ayyukan Banki da Kudi na Polytechnic ta Ibadan sun ziyarci Alli ne domin gayyatarsa zuwa wani shiri da s**a shirya tare da yi masa hira.

‎Kungiyar ta ce daliban sun isa ofishin ne a lokacin da babu isassun kujeru ga dukkan mutanen da ke wurin, lamarin da ya sa Alli ya nemi daya daga cikin daliban ya zauna a cinyarsa.

‎A cewar kungiyar, abin da ya faru “abin da ya zo ba zato ba tsammani ne kuma dabi’ar uba ce”, kuma ba shi da wata manufa marar dacewa.

‎Ta ce yawan mutanen da s**a halarci taron ya zarce adadin kujerun da ke akwai, don haka ba kowa ne ya samu wurin zama ba.

‎Kungiyar ta kuma zargi wasu kafafen intanet da kokarin mayar da lamarin zuwa wata ma’ana ta daban, tana mai cewa irin wannan fassarar ba ta dace ba kuma tana da alaka da siyasa.

‎Ta ce abin takaici ne yadda ake karkatar da wata mu’amala tsakanin jagoran siyasa da daliban da s**a zo neman goyon bayansa domin gudanar da shirinsu zuwa wata fahimta marar kyau.

‎Kungiyar ta bayyana cewa mutanen da s**a san Sanata Sharafadeen Alli sun san yadda yake mu’amala da matasa da kuma irin alakar uba da yake da su.

‎Ta kuma bukaci kafafen yada labarai da masu amfani da kafafen sada zumunta da su yi taka-tsantsan wajen yada labarai kan lamarin, tana mai bayyana martanin da ya biyo bayan faifan bidiyon a matsayin “siyasar bata suna”.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nigerian Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nigerian Post:

Shortcuts

Share