Nigerian Post

Nigerian Post Call Or Whatsapp On This No.: +2348031568031

31/07/2025

Yadda Farashin Abinci Ke Ci-gaba Da Faduwar Ƙasa Warwas A Sassan Kasuwannin Najeriya

31/07/2025

Kai Tsaye:Karatun Alkur'ani Mai Tsarki Daga Gidan Khadimul Qur'an (AUDUN MALAN)

Asibitoci a Najeriya Sun Shiga Cakwakiya Saboda Yajin Aikin Nas-Nas da Ma’aikatan UngozomaAsibitoci a sassa daban-daban ...
31/07/2025

Asibitoci a Najeriya Sun Shiga Cakwakiya Saboda Yajin Aikin Nas-Nas da Ma’aikatan Ungozoma

Asibitoci a sassa daban-daban na Najeriya sun shiga cikin cakwakiya a ranar Litinin bayan da ƙungiyar Nas da Ma’aikatan Ungozoma ta Najeriya (NANNM) ta fara yajin aikin gargadi na mako guda.

Kungiyar ta ce yajin aikin ya zama dole ne saboda rashin kyawun yanayin aiki, karancin kayan aiki, da kuma jinkirin biyan haƙƙoƙin ma’aikata. Shugaban ƙungiyar, Comrade Michael Nnachi, ya bayyana cewa gwamnati ta kasa cika alƙawuran da ta ɗauka duk da shawarwari da dama da aka bata.

Rahotanni daga manyan asibitoci sun nuna yadda marasa lafiya ke cikin halin Ƙunci, musamman mata masu juna biyu da masu buƙatar kulawar gaggawa.

Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya ta ce tana ƙoƙarin sasantawa da shugabannin ƙungiyar don daƙile tasirin yajin aikin, sai dai har yanzu ba a kai ga cimma matsaya ba.

Duk wanda ya yi silar buɗe idon wani Allah kaɗai ne yasan irin ladar da zai Shimfiɗa ma sa- Inji Isah Muhammad Mai'aduaY...
31/07/2025

Duk wanda ya yi silar buɗe idon wani Allah kaɗai ne yasan irin ladar da zai Shimfiɗa ma sa- Inji Isah Muhammad Mai'adua

Ya bayyana haka a lokacin da ake horar da jami'an lafiya a matakin farko (Primary Health Workers) inda ake ɗaukar kowanne mutum ɗaya a cikin mazaɓu 361 na sassan Katsina, a wasu daga cikin al-ummar Katsina ta tsakiya a ranar Laraba 30 ga watan Yuli 2025 a jihar Katsina.

Tun da farko dai, ma'aikatar lafiya ta jiha, ta shirya bada horon na kwana 2 kan kula da lafiyar Idanu a matakin farko (PRIMARY EYE CARE) a Katsina ta tsakiya.

Wanda Gwamnatin jihar Katsina, a ɓangaren Ma'aikatar lafiya ta jiha, ta shirya bada horon na kwana 2 kan kula da lafiyar Idanu a matakin farko (PRIMARY EYE CARE) a Katsina ta tsakiya, bayan sun kammala kwana 2 kan bada horo a Shiyya Funtua.

An gudanar da taron a mazaɓar Gabas 01 dake cikin Shiyyar Katsina ta tsakiya, wanda kafin fara gudanar da horaswar, jami'an sun tsara cewa, daga kowacce mazaɓa sun ɗauki mutum ɗaya, daga cikin Mazaɓu 361 dake jihar Katsina, domin ba su horo kan inganta lafiyar idanu.

Kazalika, horon wanda aka fara bi Shiyyar Funtua don bada horo, tare da kammalawa da Shiyyar Funtua, inda ya zuwa yanzu ake ci gaba da gudanarwa a Katsina ta tsakiya, da kuma Shiyyar Daura nan ba da jimawa ba.

Nigerian Post ta samu cewa, tunda farko, Kwamishinan Lafiya na jihar Katsina, Hon. Musa Adamu Funtua, shi ne ya umarci jami'an da su ɗauki Mutum ɗaya kowacce mazaɓa don ganin shirin ya inganta a sassan jihar.

Ya shaida ma su da su kasance masu bin kanun abubuwan da aka koyar da su, tare da bada ilimin da aka ba su ga al'ummar jihar Katsina don ganin kwalliya ta biya kuɗin sabulu.

Shirin horaswar wanda gwamnatin jihar Katsina ta ɗauki nauyi, ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umaru Raɗɗa, za a kammala nan ba da daɗewa ba a jihar Katsina.

Ana horar da jami'an lafiya a matakin farko (Primary Health Workers) inda ake ɗaukar kowanne mutum ɗaya a cikin mazaɓu 361 na sassan Katsina.

Horon ya samu kulawar; Perm Sect, Dr. Ahmed Tijjani Hamza da Director Public Health, Dr. Ma'awuya Aliyu, da kuma Director Planning SPHCA,Dr. Ibrahim Nalado, da sauran su.

Gwamnan Jihar Benue Rev. Fr. Hyacinth Alia Ya Rushe Majalisar Zartaswa ta JiharGwamnan Jihar Benue, Rev. Fr. Hyacinth Al...
30/07/2025

Gwamnan Jihar Benue Rev. Fr. Hyacinth Alia Ya Rushe Majalisar Zartaswa ta Jihar

Gwamnan Jihar Benue, Rev. Fr. Hyacinth Alia, ya sanar da rushewar Majalisar Zartaswa ta Jihar (State Executive Council – SEC) a ranar Laraba, matakin da ke nuna sabon salo a tafiyar da gwamnatinsa.

A wata sanarwa da aka fitar daga ofishin sakataren yaɗa labarai na gwamnan, an bayyana cewa rushewar ta shafi dukkan kwamishinoni da sakatarorin dindindin da ke cikin majalisar zartaswa.

Gwamna Alia ya gode wa mambobin majalisar bisa gudunmawar da s**a bayar tun lokacin da ya hau mulki, yana mai cewa matakin yana daga cikin tsarin sake fasalin gwamnati don samun sabbin dabaru da kuzari a tafiyar da al’amuran jihar.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa sakatarorin ma’aikatu za su cigaba da gudanar da muhimman ayyukan yau da kullum, har zuwa lokacin da za a nada sabbin kwamishinoni.

Rushewar Majalisar Zartaswar ta zo ne yayin da gwamnatin Alia ke cika fiye da shekara guda a mulki, kuma ana kallon matakin a matsayin yunkuri na sake fasalin gwamnati domin samun ingantacciyar hidima ga al’umma.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nigerian Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nigerian Post:

Share