Maryam revenge

Maryam revenge ATUL SALIHA #
ماشاءاللہ
ya Allah ka shige mana gaba a dukkan lamuranmu kabamu ikon ai kata daidai Maryam revenge
(2)

FALALOLIN AURE GUDA 20:1. Cika Sunnah ta Manzon Allah ﷺ– Aure daga cikin sunnoninsa ne."Wanda ya ƙi sunnata, ba daga cik...
06/07/2025

FALALOLIN AURE GUDA 20:

1. Cika Sunnah ta Manzon Allah ﷺ
– Aure daga cikin sunnoninsa ne.

"Wanda ya ƙi sunnata, ba daga cikinmu bane." (Bukhari da Muslim)

2. Tsaron Mutunci da Izzah
– Aure yana hana zina da ɓarna.

3. Kwanciyar Hankali da Natsuwa

"Daga cikin ayoyinsa ne ya halitta muku matanku domin ku samu nutsuwa daga gare su." (Suratul Rum: 21)

4. Samar da Zuri’a (’Ya’ya)
– Zuri’a ta gari na daga babbar falalar aure.

5. Samar da Soyayya da Rahama
– Allah ya sanya soyayya da rahama tsakanin ma’aurata. (Rum: 21)

6. Tsarkakewa daga Sha'awace-sha'awace
– Aure yana hana kallon haram da tunani mai cutarwa.

7. Samar da Taimako da Juna
– Miji da mata na taimakon juna wajen ibada da rayuwa.

8. Lada da Sakamako mai Girma
– Ma’aurata suna samun lada har a jima’i. (Muslim)

9. Cikakken ‘Yanci daga Sharrin Shaidan
– Aure na rufe kofa ga sharrin Shaidan.

10. Tsarkake Al’umma
– Aure yana gina al’umma masu tsafta da doka.

11. Yin Koyi da Annabawa
– wasu daga cikin Annabawa sun yi aure.

12. Inganta Zamantakewa da Girmamawa
– Aure yana kawo ladabi da zaman lafiya.

13. Samar da Sutura (Kariya)
– Ma’aurata suna zama sutura ga juna. (Suratul Baqarah: 187)

14. Gina Gida na Musulunci
– Aure yana kafa tushen gidan musulunci mai tsafta.

15. Zama Uba ko Uwa Mai Hakki
– Yin aure yana baka damar samun daraja ta uwa/uba.

16. Goyon Bayan Juna a Lokacin Wahala
– Ma’aurata na kasancewa tare a cikin ƙalubale.

17. Nuna Rahama da Kulawa da Juna
– Aure yana koya wa mutum juriya da tausayi.

18. Samun Albarka a Rayuwa da Arziki
– Allah yana albarkatar da ma’aurata masu tsoronSa.

19. Karfafa Alaka da Zumunci
– Aure yana ƙarfafa zumunci da alaƙar iyalai.

20. Ceto a Lahira Idan An Godewa Allah
– Idan an gina aure bisa tsoron Allah, yana iya zama hanyar zuwa Aljannah.

😱 Matar da Ta Tsorata Mijinta da Tambayoyi irin na kabari.Wata mata ce mai barkwanci ta ce:Wata safiya na tashi da wuri,...
06/07/2025

😱 Matar da Ta Tsorata Mijinta da Tambayoyi irin na kabari.

Wata mata ce mai barkwanci ta ce:
Wata safiya na tashi da wuri, sai na ce bari na tashi mijina.
Nauyin barci ne da shi, sai na rufe ɗakin, na daidaita labulaye, na kashe fitila. Sai da na tabbatar da cewa dakin yayi duhu gaba daya.
Na sa masa bargo na rufe shi daga sama har ƙasa, sai na matsa kusa da kunnensa na yi magana da siririyar murya:

“Wa ne Ubangijinka?”
“Mene ne addininka?”
“Wa ne Annabinka?”

Cikin firgici sai ya tashi yayi tsalle yana ihu:
“Allah shi ne Ubangijina!
Addinina shine Musulunci!
Annabina shine Annabi Muhammad (SAW)!”

Yana ta kewaye a cikin dakin har Allah ya taimake shi hannunsa ya kai ga kunna fitila, sai ya ganni ina kwance ina dariya.

Nan take ya dauko bulala, ya yi min dukan tsiya har sai da na fara karanto kalmar shahada! 😅

Alhamdulillah yanzu dai an sallame ni daga asibiti.
Ina ci gaba da yin jinya a gida, gani na ya fara dawowa, sannan kuma ana tunanin zan iya fara takawa da kafata zuwa nan da sati biyu.

Allah ya shirye shi — wasu mazan basa ɗaukar wasa!
😂😂😂

Prof din larabci ne Kai bana ilimin hadisi ko Qur'ani ba. Ka bari Mai gidan ka sheikh Shariff sale yayi magana. Dr Rabiu...
06/07/2025

Prof din larabci ne Kai bana ilimin hadisi ko Qur'ani ba. Ka bari Mai gidan ka sheikh Shariff sale yayi magana. Dr Rabiu Umar r/Lemo ya fika ilimin hadisi wlh. Kai fa prof makara duk Mai hankali ya fahimce ka baka bada amsar komai direct sai dai kayita kame kame. Da farko cewa kayi ,Kai baka saurari abunda Abduljabbar ya fada ba, Kuma kace saboda kazantar abinda ya fada bazaka iya saurere ba. Amma yanzu Kai ne kake goyon bayansa.
Kuma kamar baka saurari muqabalar ba, su cewa s**ayi shi ne yake fadar abubuwan da irin fassarar sa Amma ba haka suke a hadisin ba, ya tabbatar da su sannan Kuma sai a zo maganar korewa. Wallahi ban taba ganin prof mara tsoron Allah Irinka ba. Kawai Kai sai ka kawo rikici da sunan ilimi. Walh kaji kunya girmanka ya fadi

GAYYATAR MUKABALA"Idan Prof. Makari ya shirya kare maganganun da Abduljabbar ya yi na batanci ga Manzon Allah S.A.W wada...
06/07/2025

GAYYATAR MUKABALA

"Idan Prof. Makari ya shirya kare maganganun da Abduljabbar ya yi na batanci ga Manzon Allah S.A.W wadanda aka yi zaman titsiye a kan su, to ni ma na shirya, ya sa rana mu zauna ya yi mana bayanin yadda wadannan maganganu s**a zama Ilzami!!."

Dr. Muhammad Rabi'u Rijiyar Lemo

Ya ku ma'abota hankali ku saurara 👌🗣️ Surutu mai yawa — yana bude ƙofa ga ƙarya, domin harshe baya da iyaka sai an tsare...
06/07/2025

Ya ku ma'abota hankali ku saurara 👌

🗣️ Surutu mai yawa — yana bude ƙofa ga ƙarya, domin harshe baya da iyaka sai an tsare shi.

🎭 Wayewa ba tare da iyaka ba — tana haifar da raini da girman kai, har mutum ya manta da tushe.

🗯️ Jayayya akai-akai — tana sa zuciya ta ƙi gaskiya, gaba da kiyayya su shiga tsakanin mutane.

💰 Son dukiya fiye da kima — yana sa zuciya ta kamu da rashin kunya da cin haram.

🧠 Wayo da dabara idan s**a wuce iyaka — zalunci da cuta s**an biyo baya.

💪 Karfi idan bai haɗu da tausayi ba — zai sauya zuwa mugunta da danniya.

😄 Wasa da barkwanci mai yawa — tana sa mutum ya manta da nufin rayuwa, shagala ya mamaye hankali.

🤲 Roƙo da neman taimako ba kakkautawa — yana jawo rashin daraja da wulaƙanci.

🚫 Saɓon Allah akai-akai — yana jawo fushin Ubangiji da rushewar albarka.

🖤 Baƙin ciki idan ya ɗauki zuciya gaba ɗaya — yana haifar da matsaloli iri-iri da shakku a zuciya.

🌿 Rayuwa tana buƙatar daidaito. Halaye da yawa ba su da matsala, sai idan an wuce iyaka.

🕊️ Allah Ka tsare mu daga halayen da ke hallaka zuciya, Ka cika rayuwarmu da natsuwa da albarka. 🤲

BUƊAƊƊEN KIRA ZUWA GA Prof. Ibrahim Maqari Assalamu Alaikum Warahmatullah Ta'ala wa Barakatuh.Allah yagafarta Mallam, ka...
06/07/2025

BUƊAƊƊEN KIRA ZUWA GA Prof. Ibrahim Maqari

Assalamu Alaikum Warahmatullah Ta'ala wa Barakatuh.

Allah yagafarta Mallam, kamar a kwanakin baya naji wani jawabin ka da ka bayyana cewa kunnuwan ka sun kasa sauraren kalaman Abduljabbar Kabara wanda ake tuhumar sa a kai.

Kamar dai a cikin jawabin naka ka nuna cewa kaunar ka ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Álihi wa sallam bazata juri sauraren kalaman da Abduljabbar ɗin ya jingina su ga Manzon Allah (S.A.W) ɗin ba.

Bisa girmamawa gareka Farfesa, yanzu kasamu dama ne kayi musu sauraren nutsuwa shiyasa ka fahimci cewa Abduljabbar ɗin Ilzami yasamu aka jirkita masa magana don a cutar dashi?

Idan har kasamu wannan damar, ina ganin nauyi ne yanzu a kanka, ko dai ka amsa gayyatar da naga Ustaz Rabi'u Umar rijiyar Lemo yayi maka, ko kuma kai a karan kanka kasamu lokaci a majlisin dakake bada karatu ka ɗakko Wadannan Hadisai da Abduljabbar ɗin yake iƙirari akwai su a littafan Sunnah ka karanta su da sigar da ya karanta tareda bayyana litattafan da suke ciki da lambobin Hadisan a Fihirar litattafan.

A fahimta ta, yin hakan zai taimaka Kwarai wajen bayyana gaskiyar Abduljabbar ɗin tareda kuɓutar dashi akan yadda aka juya masa karatun sa.

Ina fatan wannan saƙon zai kai ga kunnuwan Farfesa, ina kuma fatan zakayi hakan don warware zare da abawa.

Ma'assalam.

06/07/2025

Idan matar mutum ta rabu dashi sbd bashi da kudi, shin kudi ya kamata ya nema ko wata matar zai Auro? 😅😅😅

Azumin da akayi jiya da yau, Allah yasa ya zamo sanadin shigar mu Aljannar Fiddausi da sanadin yayewar damuwar mu.
06/07/2025

Azumin da akayi jiya da yau, Allah yasa ya zamo sanadin shigar mu Aljannar Fiddausi da sanadin yayewar damuwar mu.

Mutum ya fadi juzu'i da shafi da lambar hadisi ya ce, a je duba a can ya gano munanan maganganun da ya jinginawa Manzon ...
06/07/2025

Mutum ya fadi juzu'i da shafi da lambar hadisi ya ce, a je duba a can ya gano munanan maganganun da ya jinginawa Manzon Allah (S.A.W) amma yau wani mai son zuciya ya zo ya ce wai ilzami yake!!!.
Allah ka raba mu da son zuciya da neman yardar mutane.

IKON ALLAH KENANYarinya ka ganta lukui lukui maa shaa ALLAHU ta girma, tana da dan farin jinin ta ana kaunar ta da aure ...
06/07/2025

IKON ALLAH KENAN

Yarinya ka ganta lukui lukui maa shaa ALLAHU ta girma, tana da dan farin jinin ta ana kaunar ta da aure tana gudu, nan da wani lokaci kuma tana kaunar auren mazaje na gudu,

Kanwata kiyi amfani da damar ki, in ba a ci Sa'a ba daga karshe ta faɗa mummunar dabi'a,

Kada ki yaudari kanki ko a yaudare ki yanzu kin yi kankanta matukar kina da shekara 18, yanzu ne ma k**e dai-dai naki, kuma aure a irin wannan lokaci yafi kyautatuwa Kyakkyawar turba,

Sau da dama wasu yanmata sun fada harkar banza ne saboda irin wannan sakacin ga shi sun girma suna bukatar aure babu miji, duk kuma Wanda zai zo gun su sai dai da soyayya amma aure sai yaje ya nemo yarinya karama.

Kiyi tinani akan wannan maganar

Ya isheka mafi girman Arziki ka koma ga ALLAH a wanzu ana maka shaida da soyayyar MANZON ALLAH (S.A.W), wannan shine sha...
06/07/2025

Ya isheka mafi girman Arziki ka koma ga ALLAH a wanzu ana maka shaida da soyayyar MANZON ALLAH (S.A.W), wannan shine shaida mafi girman tsada..!

Sheikh yusif abu u'naisah obj hafizahullah

Babban Kuskuren Da Zaki Yi...Babban kuskuren da zaki iya aikatawa a rayuwarki shi ne ki ɗauki hoton jikinki (Tsirara) ko...
06/07/2025

Babban Kuskuren Da Zaki Yi...

Babban kuskuren da zaki iya aikatawa a rayuwarki shi ne ki ɗauki hoton jikinki (Tsirara) ko a siffar da bata dace ba, ki turawa saurayi da sunan soyayya ko wayewa.

Kada ki ruɗe da kalmomin soyayya, ki mance da mutuncinki.
Kada ki ruɗe da "Ina sonki" ki manta da tsoron Allah.
Kada ki sa hotonki ya zamo makamin barazana a gobe.

🧨 Yau kina masa dariya, gobe sai ya rikice yana yi miki barazana da hotonki.
💔 Yau kina tunanin ya damu dake, gobe sai ya zama abin da k**e mafarkin gujewa.

Ki sani, ko mijinki ne, ba dukkan hotuna ya dace ki tura masa ba, b***e kuma saurayi wanda ba shi da wata alkibla a kanki.

⚠️ Hoton jikinki, alfarma ne.
⚠️ Mutuncinki, amana ce.
⚠️ Sirrinki, darajarki ce.

Ki kare kanki tun da wuri kafin ki fara nadama.
Soyayya ba ta buƙatar hoto mai ɓata mutum, ta buƙaci gaskiya, biyayya da tsafta.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Maryam revenge posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Maryam revenge:

Share