Sarauniya Radio

Sarauniya Radio Your Voice | Your Story | Your Sarauniya Radio | Giving humanity a voice and also a provider of trusted information
(325)

Rahotanni na cewa wasu ‘yan b!ndiga sun yi garkuwa da tsohon Kakakin Rundunar Sojojin Najeriya, Rabe Abubakar, tare da m...
30/05/2026

Rahotanni na cewa wasu ‘yan b!ndiga sun yi garkuwa da tsohon Kakakin Rundunar Sojojin Najeriya, Rabe Abubakar, tare da matarsa a daidai garin Matazu da ke Jihar Katsina.

Majiyoyi sun ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar yayin da tsohon babban jami’in sojan ke kan hanyarsa ta zuwa Katsina, inda maharan s**a tare motarsu s**a yi awon gaba da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan lamarin ba, yayin da ake ci gaba da kokarin gano inda aka kai su da kuma ceto su.

Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar matsalolin g@rkuwa da mutane da h@re-h@ren ‘yan b!ndiga a sassan Arewa maso Yammacin Najeriya.

Sarauniya Radio - Kafar Al'umma

21/05/2026

Daga Ina Kuke Bibiyar Shafin Sarauniya Radio ?

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Gombe State ta sanar da Jamilu Ishiyaku Gwamna a matsayin ɗan takarar ...
03/05/2026

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Gombe State ta sanar da Jamilu Ishiyaku Gwamna a matsayin ɗan takarar gwamna na bai daya (consensus candidate) domin zaɓen 2027.

Sanarwar ta fito ne bayan wata ganawa da shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki s**a gudanar a ranar Lahadi, inda s**a cimma matsaya kan tsayar da Gwamna a matsayin wanda zai wakilci jam’iyyar.

A wannan tsari, tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Isa Pantami, bai samu nasara ba, bayan da masu ruwa da tsaki s**a zabi Gwamna a matsayin wanda s**a amince da shi.

Rahotanni sun nuna cewa matakin na zuwa ne a kokarin jam’iyyar na kauce wa rikicin cikin gida tare da hada kai gabanin babban zaben shekarar 2027.

Sai dai har yanzu babu cikakken bayani kan ko dukkan bangarorin jam’iyyar sun amince da wannan matsaya, yayin da ake sa ran wasu za su iya nuna rashin gamsuwa.

Ana sa ran jam’iyyar za ta ci gaba da shirye-shirye domin tinkarar zaɓen, yayin da ake jiran karin bayani daga sauran ‘yan takara da masu ruwa da tsaki.

Sarauniya Radio - Kafar Al'ummar

Rahotanni da ke yawo sun ce ana wasu kungiyoyin da ke ikirarin j!h@di tare da hadin gwiwar ‘yan tawaye Azbinawa sun kai ...
26/04/2026

Rahotanni da ke yawo sun ce ana wasu kungiyoyin da ke ikirarin j!h@di tare da hadin gwiwar ‘yan tawaye Azbinawa sun kai hare-hare a sassa daban-daban na ƙasar Mali, ciki har da babban birnin Bamako.

A cewar rahotannin, h@rin da aka kai a ranar Asabar ya shafi wasu wurare, kuma ana zargin cewa ya yi sanadiyar mutuwar Ministan Tsaron ƙasar, Sadio Camara, a gidansa da ke Kati, kusa da Bamako.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga gwamnatin Mali ko hukumomin tsaro da ta tabbatar da mutuwar ministan.

Masu sharhi na tsaro na cewa yankin Sahel na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro, inda ƙungiyoyin masu ɗauke da mak@mai da kuma ‘yan tawaye ke kai h@re-h@re a kai a kai.

Saboda haka, ana kira ga jama’a da su yi takatsantsan da irin waɗannan rahotanni, har sai an samu tabbaci daga majiyoyi na hukuma.

Ana sa ran gwamnati za ta fitar da cikakken bayani kan lamarin nan gaba.

Sarauniya Radio - Kafar Al'umma

Rahotanni na cewa shugaban ƙasar Amurka Donald Trump, ya tsallake rijiya da baya bayan wani hari da wani ɗan bindiga ya ...
26/04/2026

Rahotanni na cewa shugaban ƙasar Amurka Donald Trump, ya tsallake rijiya da baya bayan wani hari da wani ɗan bindiga ya kai, lamarin da ya tayar da hankalin jama’a.

Majiyoyi sun ce an kai harin ne a wani wuri da shugaban ke halarta, inda jami’an tsaro s**a yi gaggawar daukar mataki tare da kare shugaban daga duk wani hatsari.

Har yanzu ba a fitar da cikakken bayani kan yadda lamarin ya faru ba, ko kuma ko akwai waɗanda s**a jikkata, amma hukumomin tsaro sun tabbatar da cewa suna ci gaba da bincike domin gano cikakken abin da ya faru da kuma wanda ke da hannu a harin.

Wannan lamari ya sake jaddada muhimmancin tsauraran matakan tsaro da ake ɗauka wajen kare shugabannin ƙasashe, musamman a lokutan taruka da jama’a ke taruwa.

Ana sa ran hukumomi za su fitar da ƙarin bayani yayin da bincike ke gudana.

Sarauniya Radio - Kafar Al'umma

Rahotanni na nuni da cewa jami’in soja Najeriya, da ake zargi da yin b@tanci ga Annabi Muhammad (SAW), ya goge shafinsa ...
20/04/2026

Rahotanni na nuni da cewa jami’in soja Najeriya, da ake zargi da yin b@tanci ga Annabi Muhammad (SAW), ya goge shafinsa na Facebook bayan ce-ce-ku-ce da s**a biyo bayan kalamansa.

A baya dai an ruwaito cewa jami’in mai suna Elijah Bot, ya wallafa kalamai da kuma yin barazana da s**a jawo martani mai zafi daga masu amfani da kafafen sada zumunta, musamman mabiya addinin Musulunci.

Majiyoyi sun ce an daina ganin asusun nasa a Facebook, lamarin da ya sa ake kyautata zaton cewa ya goge ko kuma an rufe shafin, bayan yawaitar s**a da kiraye-kirayen daukar mataki a kansa.

Wasu masu sharhi na ganin cewa goge shafin na iya zama yunƙurin kauce wa matsin lamba daga jama’a, yayin da wasu ke kira ga hukumomi da su ci gaba da bincike domin gano gaskiyar lamarin da kuma daukar matakin da ya dace.

Masana sun kuma gargadi jama’a da su guji ɗaukar doka a hannu, tare da jaddada muhimmancin kiyaye zaman lafiya a irin wannan lamari mai sarkakiya.

Sarauniya Radio - Kafar Al'umma

Rahotanni na cewa wani mutum mai suna Elijah Bot, wanda ake zargin jami’in soja ne a Najeriya, ya fitar da kalaman batan...
20/04/2026

Rahotanni na cewa wani mutum mai suna Elijah Bot, wanda ake zargin jami’in soja ne a Najeriya, ya fitar da kalaman batanci ga Annabi Muhammad (SAW) a kafar sada zumunta ta Facebook.

Lamarin ya samo asali ne daga wasu sharhi (comments) da ke yawo, inda aka nuna jami’in sojan yana rubuta kalamai masu tayar da hankali game da addinin Musulunci da Annabi Muhammad (SAW).

Rahotanni sun kuma nuna cewa wannan na zuwa ne bayan da jami’in ya yi wata barazana a baya, inda ya ce idan wani mai wa’azi mai suna Adam Ashaka bai daina amfani da Littafi Mai Tsarki (Bible) wajen wa’azinsa ba, zai yi batanci ga Annabi (SAW).

Wannan furuci da kuma abin da ya biyo baya sun jawo martani mai zafi daga masu amfani da kafafen sada zumunta, musamman daga bangaren Musulmi, inda da dama s**a yi Allah-wadai tare da kira ga hukumomi su dauki mataki.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga rundunar sojin Najeriya kan lamarin.

Masana sun yi gargadin cewa irin wannan batu na iya haddasa tashin hankali na addini, don haka s**a bukaci jama’a da su kasance masu kaucewa ire-iren kalaman, su kuma bar hukumomi su gudanar da bincike domin tabbatar da gaskiya da kare zaman lafiya.

Sarauniya Radio - Kafar Al'umma

Rahotanni na cewa wata cibiyar rubuta jarabawar JAMB (CBT) da ke makarantar Peter Harvard Schools a Kubwa, Abuja, ta han...
18/04/2026

Rahotanni na cewa wata cibiyar rubuta jarabawar JAMB (CBT) da ke makarantar Peter Harvard Schools a Kubwa, Abuja, ta hana wata daliba Músulma shiga jarrabawar UTME bisa cewa tana sanye da hijabi.

A wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, an ga jami’an tsaro na duba dalibai kafin shiga cibiyar, inda ake zargin wata jami’ar Nigeria Security and Civil Defence Corps ta dakatar da dalibar. Daga yadda ta nuna damuwa, ana kyautata zaton cewa hijabinta ne ya jawo matsalar.

Rahoton ya kuma nuna cewa a lokaci guda, wata daliba da ke sanye da kayan da wasu s**a bayyana a matsayin marasa cikakken sutura an bar ta ta shiga ba tare da wata matsala ba, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a.

Sai dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga JAMB ko mahukuntan makarantar da ke tabbatar da faruwar lamarin ko kuma bayani kan abin da ya haddasa shi.

Lamarin ya tayar da muhawara kan ’yancin addini da kuma daidaito wajen aiwatar da dokoki a cibiyoyin jarabawa. Wasu na kira ga JAMB da hukumomin da abin ya shafa da su yi bincike tare da fitar da sahihin bayani domin kauce wa rudani.

Ana sa ran hukumomi za su yi karin haske kan lamarin nan ba da jimawa ba.

Sarauniya Radio - Kafar Al'umma

Rahotanni na cewa ana zargin gwamnatin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ayyana fiye da fararen hula 200 da s**a mutu...
13/04/2026

Rahotanni na cewa ana zargin gwamnatin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ayyana fiye da fararen hula 200 da s**a mutu a h@rin kasuwar Jilli a matsayin ‘yan ta’.

A cewar majiyoyi, mutanen da s**a rasa rayukansu sun hada da ’yan kasuwa da mazauna yankin, bayan wani h@rin da ake zargin rundunar sojin Najeriya ta kai ta hanyar jefa b@ma-b@mai daga sama a yankin da ke iyakar jihohin Yobe da Borno.

Sai dai ba wannan ne karo na farko da sojojin Najeriya ke kai wa fararen hula wayanda basu san hawa ba, bare dauka h@re-h@re daga bisani su ayyana h@rin a matsayin 'kuskure'

Rahotanni na baya-bayan nan sun nuna cewa fiye da mutane 200 sun rasa rayukansu a h@rin da rundunar sojin Najeriya ta kai a kasuwar Jilli da ke kan iyakar jihohin Yobe da Borno. Mafi yawan waɗanda s**a mutu ’yan kasuwa ne da ke gudanar da harkokinsu a lokacin da aka kai h@rin.

Lamarin ya sake jawo hankalin jama’a kan yawaitar zargin h@re-h@ren kuskure da ke shafar fararen hula a yayin ayyukan soji a yankunan da ake fama da rik!ci, sai dai a wannan lokacin Gwamnatin Tinubu Ta ayyana wayanda h@rin kasuwar Jilli a Jihar Yobe ya rutsa da su a matsayin 'yan ta'

Bincike daga rahotannin kungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da kafafen yaɗa labarai ya nuna cewa:

Cikin shekaru 3 na mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, sojojin Najeriya sun kai h@re-haren b@ma-bamai sama da sau 7 kan fararen hula [Bisa Abin Da Suke Kira Kuskure] daga shekarar 2023 zuwa Shekarar 2026 wanda ya yi sanadiyar mútüwar darurunwan fararen hula tare da raun@ta wasu da dama a jahohin , , , , , , da duk a

Kimanin makonni biyar cif-cif bayan da wani jirgin yaƙin s0jojin Najeriya ya yi aman wúta bisa 'kuskure' kan farar hula a ƙaramar hukumar Maradun ta jihar Zamfara da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 15, sai ga shi ranar Asabar 16 ga watan Fabrairun 2025, an kuma sake samun irin wannan haɗarin wani abu da ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula guda shida.

Ga jerin hare-haren da sojojin Najeriyan s**a kai bisa kuskure a ƙasar:

1) A ranar Jama'a 27 ga watan Janairu shekarar 2023 wani ƙazamin harin jirgin sama sojojin Najeriya ya yi sanadin kashe fararen hula aƙalla 28, a ƙauyen Rukubu na ƙaramar hukumar Doma cikin jahar Nasarawa da ke kan iyaka da jahar Binuwai.

2) A daren ranar Lahadi 3 ga watan Disambar shekarar 2023 wani jirgi maras matuƙi na rundunar sojin Najeriya ya kai hari kan cincirindon fararen hula wanda sun taru ne don bikin Mauludi kamar yadda s**a saba yi shekara-shekara a garin Tudun Biri daga jahar Kaduna wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula sama da 100 tare da raunata wasu da dama.

3) A ranar Laraba 25 ga watan Disamba shekarar 2024 Hare-haren da sojojin Najeriya na sama da na ƙasa s**a kai a wasu ƙauyuka Silame da ke jahar Sokoto sun yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum 15 da raunata wasu da dama.

4) A ranar Asabar 11 ga watan Janairu shekarar 2025 ne wani jirgin yaƙin sojin Najeriya ya yi ɓarin wuta inda ya rutsa da 'yan sa-kai da jama'ar garuruwa da dama da s**a kai ɗauki, domin dakile wani hari da 'yan bindiga s**a kai garin Dangeɓe na yankin ƙaramar hukumar Zurmi a jahar Zamfara.

5) A ranar Lahadi 16 ga watan Fabairun shekarar 2025 Wani jirgin yakin sojojin Najeriya ya yi luguden wuta ya kashe mutum shida tare da raunata wasu a ƙauyen Zakka da ke ƙaramar hukumar Safana na jahar Katsina

6) A farkon shekarar 2026 wani jirgin yaƙin rundunar sojin sama ta Najeriya ya saki wúta kan fararen hula, bisa abin da hukumomin soji s**a bayyana a matsayin kuskure na aiki.

Majiyoyi daga yankin sun ce lamarin ya haifar da firgici da asarar r@yuka/r@unuka (adadin na nan ana tantancewa), yayin da jama’a ke nuna damuwa kan yadda abin ya faru.

A wata sanarwa, rundunar sojin ta ce h@ri ne da aka yi bisa bayanan leƙen asiri, amma daga baya aka fahimci cewa fararen hula ne s**a fada cikin h@rin ba da gangan ba.

Sojojin sun yi alhinin faruwar lamarin tare da alƙawarin bincike mai zurfi domin gano musabbabin kuskuren da kuma ɗaukar matakan da s**a dace.

Hukumomin jiha da na tsaro sun ce ana aiki tare da shugabannin al’umma domin kwantar da hankali, tare da tabbatar da tallafi ga waɗanda abin ya shafa.

Wannan na zuwa ne kwanaki 40 bayan da wani jirgin yaƙin s0jojin Saman Najeriya yayi ruwan wúta akan fararen hula masu kamun kifi a karamar hukumar Kukawa ta jihar Borno bisa abin da s**a kira 'kuskure' wai da tsammanin cewa ko 'yan ta' ne.

Lamarin ya yi sanadiyar asaran rayuka na fararen hula wanda kawo yanzu ba a san adadin su ba, wannan dai ba shine karo na farko da Sojojin Najeriya ke kai wa fararen hula h@re-h@re ba, daga bisani su ayyana h@rin a matsayin 'kuskure'

Masana harkokin tsaro sun daɗe suna s**ar irin sakacin da ake samu a y@ƙi da ƴan B0k0 H@-ram a arewa maso gabas da kuma na 'yan ta-da-ƙayar-baya galibi a arewa maso yamma, da ke ritsawa da rayukan fararen hula wadanda ba su ji ba, ba su gani ba.

Wai shin rashin ƙwarewa ce ko kuma rashin ingancin naurorin da suke amfani da shine ko kuma gaggacine? Kuma wane matakin kuke ganin ya dace a ɗauka wajen hana sake aukuwan hakan? Ku bayyan mana ra'ayoyinku a comment section



📻 Sarauniya Radio — Kafar Al’umma.

Gwamnatin mulkin soja a ƙasar Nijar ta sanar da haramta wa’azi da kuma sauraron karatun wasu malamai da ake kira ‘yan Qa...
13/04/2026

Gwamnatin mulkin soja a ƙasar Nijar ta sanar da haramta wa’azi da kuma sauraron karatun wasu malamai da ake kira ‘yan Qala-ƙato, a wani mataki da ta ce na da nufin kare tsaro da hana yaɗuwar saƙonnin da za su iya tayar da hankali.

A cikin wata sanarwa da hukumomi s**a fitar, sun bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne domin takaita kalaman da ka iya haddasa r!kici ko rarrabuwar kawuna a tsakanin al’umma, musamman a wannan lokaci da ƙasar ke fuskantar ƙalubalen tsaro.

‘Yan Qala-ƙato dai wasu mutane wayanda basu yarda da koyarwar Annabi Muhammad (S.A.W) da suke kiran kansu da ‘yan kur'ani zalla.

Rahotanni sun nuna cewa dokar ta shafi wa’azi a masallatai da kuma shirye-shiryen addini a kafafen yada labarai, inda aka gargadi masu karya dokar da su fuskanci hukunci mai tsauri.

Sai dai wannan mataki ya janyo muhawara, inda wasu ke ganin hakan zai taimaka wajen rage tsattsauran ra’ayi, yayin da wasu ke kallon sa a matsayin takura wa ‘yancin addini da faɗin albarkacin baki.

Masu sharhi na cewa wannan na daga cikin matakan da gwamnatin soja ke ɗauka tun bayan hawanta kan mulki, domin ƙarfafa iko da kuma daidaita al’amuran tsaro a ƙasar.

Ana sa ran matakin zai ci gaba da janyo martani daga al’umma da kuma ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam.

Sarauniya Radio - Kafar Al'ummar

Address

Sanusi Dantata House, Plot 274, Central Business District
Abuja
8411

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sarauniya Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sarauniya Radio:

Share

Category