13/04/2026
Rahotanni na cewa ana zargin gwamnatin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ayyana fiye da fararen hula 200 da s**a mutu a h@rin kasuwar Jilli a matsayin ‘yan ta’.
A cewar majiyoyi, mutanen da s**a rasa rayukansu sun hada da ’yan kasuwa da mazauna yankin, bayan wani h@rin da ake zargin rundunar sojin Najeriya ta kai ta hanyar jefa b@ma-b@mai daga sama a yankin da ke iyakar jihohin Yobe da Borno.
Sai dai ba wannan ne karo na farko da sojojin Najeriya ke kai wa fararen hula wayanda basu san hawa ba, bare dauka h@re-h@re daga bisani su ayyana h@rin a matsayin 'kuskure'
Rahotanni na baya-bayan nan sun nuna cewa fiye da mutane 200 sun rasa rayukansu a h@rin da rundunar sojin Najeriya ta kai a kasuwar Jilli da ke kan iyakar jihohin Yobe da Borno. Mafi yawan waɗanda s**a mutu ’yan kasuwa ne da ke gudanar da harkokinsu a lokacin da aka kai h@rin.
Lamarin ya sake jawo hankalin jama’a kan yawaitar zargin h@re-h@ren kuskure da ke shafar fararen hula a yayin ayyukan soji a yankunan da ake fama da rik!ci, sai dai a wannan lokacin Gwamnatin Tinubu Ta ayyana wayanda h@rin kasuwar Jilli a Jihar Yobe ya rutsa da su a matsayin 'yan ta'
Bincike daga rahotannin kungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da kafafen yaɗa labarai ya nuna cewa:
Cikin shekaru 3 na mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, sojojin Najeriya sun kai h@re-haren b@ma-bamai sama da sau 7 kan fararen hula [Bisa Abin Da Suke Kira Kuskure] daga shekarar 2023 zuwa Shekarar 2026 wanda ya yi sanadiyar mútüwar darurunwan fararen hula tare da raun@ta wasu da dama a jahohin , , , , , , da duk a
Kimanin makonni biyar cif-cif bayan da wani jirgin yaƙin s0jojin Najeriya ya yi aman wúta bisa 'kuskure' kan farar hula a ƙaramar hukumar Maradun ta jihar Zamfara da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 15, sai ga shi ranar Asabar 16 ga watan Fabrairun 2025, an kuma sake samun irin wannan haɗarin wani abu da ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula guda shida.
Ga jerin hare-haren da sojojin Najeriyan s**a kai bisa kuskure a ƙasar:
1) A ranar Jama'a 27 ga watan Janairu shekarar 2023 wani ƙazamin harin jirgin sama sojojin Najeriya ya yi sanadin kashe fararen hula aƙalla 28, a ƙauyen Rukubu na ƙaramar hukumar Doma cikin jahar Nasarawa da ke kan iyaka da jahar Binuwai.
2) A daren ranar Lahadi 3 ga watan Disambar shekarar 2023 wani jirgi maras matuƙi na rundunar sojin Najeriya ya kai hari kan cincirindon fararen hula wanda sun taru ne don bikin Mauludi kamar yadda s**a saba yi shekara-shekara a garin Tudun Biri daga jahar Kaduna wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula sama da 100 tare da raunata wasu da dama.
3) A ranar Laraba 25 ga watan Disamba shekarar 2024 Hare-haren da sojojin Najeriya na sama da na ƙasa s**a kai a wasu ƙauyuka Silame da ke jahar Sokoto sun yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum 15 da raunata wasu da dama.
4) A ranar Asabar 11 ga watan Janairu shekarar 2025 ne wani jirgin yaƙin sojin Najeriya ya yi ɓarin wuta inda ya rutsa da 'yan sa-kai da jama'ar garuruwa da dama da s**a kai ɗauki, domin dakile wani hari da 'yan bindiga s**a kai garin Dangeɓe na yankin ƙaramar hukumar Zurmi a jahar Zamfara.
5) A ranar Lahadi 16 ga watan Fabairun shekarar 2025 Wani jirgin yakin sojojin Najeriya ya yi luguden wuta ya kashe mutum shida tare da raunata wasu a ƙauyen Zakka da ke ƙaramar hukumar Safana na jahar Katsina
6) A farkon shekarar 2026 wani jirgin yaƙin rundunar sojin sama ta Najeriya ya saki wúta kan fararen hula, bisa abin da hukumomin soji s**a bayyana a matsayin kuskure na aiki.
Majiyoyi daga yankin sun ce lamarin ya haifar da firgici da asarar r@yuka/r@unuka (adadin na nan ana tantancewa), yayin da jama’a ke nuna damuwa kan yadda abin ya faru.
A wata sanarwa, rundunar sojin ta ce h@ri ne da aka yi bisa bayanan leƙen asiri, amma daga baya aka fahimci cewa fararen hula ne s**a fada cikin h@rin ba da gangan ba.
Sojojin sun yi alhinin faruwar lamarin tare da alƙawarin bincike mai zurfi domin gano musabbabin kuskuren da kuma ɗaukar matakan da s**a dace.
Hukumomin jiha da na tsaro sun ce ana aiki tare da shugabannin al’umma domin kwantar da hankali, tare da tabbatar da tallafi ga waɗanda abin ya shafa.
Wannan na zuwa ne kwanaki 40 bayan da wani jirgin yaƙin s0jojin Saman Najeriya yayi ruwan wúta akan fararen hula masu kamun kifi a karamar hukumar Kukawa ta jihar Borno bisa abin da s**a kira 'kuskure' wai da tsammanin cewa ko 'yan ta' ne.
Lamarin ya yi sanadiyar asaran rayuka na fararen hula wanda kawo yanzu ba a san adadin su ba, wannan dai ba shine karo na farko da Sojojin Najeriya ke kai wa fararen hula h@re-h@re ba, daga bisani su ayyana h@rin a matsayin 'kuskure'
Masana harkokin tsaro sun daɗe suna s**ar irin sakacin da ake samu a y@ƙi da ƴan B0k0 H@-ram a arewa maso gabas da kuma na 'yan ta-da-ƙayar-baya galibi a arewa maso yamma, da ke ritsawa da rayukan fararen hula wadanda ba su ji ba, ba su gani ba.
Wai shin rashin ƙwarewa ce ko kuma rashin ingancin naurorin da suke amfani da shine ko kuma gaggacine? Kuma wane matakin kuke ganin ya dace a ɗauka wajen hana sake aukuwan hakan? Ku bayyan mana ra'ayoyinku a comment section
📻 Sarauniya Radio — Kafar Al’umma.