DG HAUSA

DG HAUSA Gaskiya afadeta yafi abarta DOKIN KARFE TV
(2)

BARKA DA ZUWA WANNAN SASHE NA DG HAUSA DON SAMUN SAHIHAN LABARAI CIKIN GIDA NIGERIA DAMA NA DUNIYAR

ZAKU IYA BIBIYARMU A WHATSAPP CHANEL
https://whatsapp.com/channel/0029Vao3VpsGpLHYlG5TYo0Q

Sama Dá Shékaru 50, Marigayì Sa'adú Zungur Yayi Wànnan Wa'azin A Sigar Wàƙa ~ Matukar a arewa da karuwai,~ yan daudu das...
05/06/2026

Sama Dá Shékaru 50, Marigayì Sa'adú Zungur Yayi Wànnan Wa'azin A Sigar Wàƙa

~ Matukar a arewa da karuwai,
~ yan daudu dasu da magajiya.
~ Da samari masu ruwan kudi,
~ Ga mashaya can a gidan giya.
~ Matukar yayan mu suna bara,
~ T**i da Loko-lokon Nijeriya.
~ Hanyar birni da na kauyuka,
~ Allah baku mu samu abin miya.
~ Sun yafu da fatar bunsuru,
~ Babu mai tanyonsu da dukiya.
~ Babu shakka yan kudu zasu hau,
~ Dokin mulkin Nijeriya.
~ In ko yan kudu sunka hau,
~ Babu sauran dadi, dada kowa zai
sha wuya.
~ A Arewa zumunta ta mutu,
~ Sai karya sai sharholiya.
~ Camfe-camfe da tsibbace
tsibbacen,
~ Malaman karya yan damfara.
~ Sai karya sai kwambon tsiya,
~ Sai hula mai annakiya.
~ Ga gorin asali da na dukiya,
~ Sai kace dan annabi fariya.
~ Jahilci ya ci lakar mu duk,
~ Ya sa mana sarka har wuya.
Ya sa mana ankwa hannuwa,
~ Ya daure kafarmu da tsarkiya.
~ Bakunan mu ya sa takunkumi,
~ Ba zalaka sai sharholiya.
~ Wagga al’umma mai zata yo,
~ A cikin zarafofin duniya.
Kai Bahaushe ba shi da zuciya ,
~ Zaya sha kunya nan duniya “.
~ “Mu dai hakkin mu gaya muku,
~ Ko ku karba ko kuyi dariya.
~ Dariyar ku ta zam kuka gaba,
da nadamar mai kin gaskiya.
~ Gaskiya ba ta neman ado,
ko na zakin muryar zabiya.
~ Karya ce mai launi bakwai,
ga fari da baki ga rawaya.
~ Ga kore ga kuma algashi,
toka-toka da ja sun garwaya”.
~ Marigayi Sa’adu Zungur a cikin
~ waken sa mai suna “Arewa
~ Jamhuriya ko Mulukiya”

Allah Yajiƙan Malam Saadu Zungur

Allah kayimasa Rahama. Amin

Wata sabuwa.Yadda shugaban karamar hukumar Mafara Hon. Yahaya Yari ya haye saman dutse a cikin daji inda 'yan bindiga ke...
05/06/2026

Wata sabuwa.Yadda shugaban karamar hukumar Mafara Hon. Yahaya Yari ya haye saman dutse a cikin daji inda 'yan bindiga ke yawo tare da bayyana cewa ya shirya mutuwa akan al'ummarsa da yake shugabanci.

05/06/2026

Goron juma'a

Munada sabon tsarin subscribe da zai baku damar zama daya daga cikin mu.Da karin samun abubuwan ilimi k**a da koyon abub...
05/06/2026

Munada sabon tsarin subscribe da zai baku damar zama daya daga cikin mu.
Da karin samun abubuwan ilimi k**a da koyon abubuwan k**ar
Vedios editor
Photo editor
Ilimin AI
Da sauran su ta hanyar yin subscribe

Allah Ba Zai Sauko Da Mala’iku Su Magance Mana Matsalolin Arewa Da Najeriya Ba Mu Ne Za Mu Tashi Mu GyaraLokaci ya yi da...
05/06/2026

Allah Ba Zai Sauko Da Mala’iku Su Magance Mana Matsalolin Arewa Da Najeriya Ba Mu Ne Za Mu Tashi Mu Gyara

Lokaci ya yi da ya k**ata mu daina shagaltuwa da tattauna abubuwan da ba su da muhimmanci a rayuwarmu. "Bidiyon tsiraicin Babiana ya fita, G-Freesh ya saki matarsa, Hadiza Gabon ta rame", duk wannan su ta shafa, ba matsaloli ne da ya k**ata mu bari su shagaltar da mu kan halin da Arewa da Najeriya suke ciki ta fuskar tsaro, ilimi, da tattalin arziƙi ba.

Sauyi ba zai zo mana daga sama kai tsaye ba. Allah Ya ba mu hankali, ilimi da ikon ɗaukar mataki domin mu gyara rayuwarmu da al’ummarmu. Don haka, mu ne ya k**ata mu tashi tsaye mu yi ƙoƙarin kawo canji mai amfani.

Ko addinin musulunci da muke ciki sai da wasu s**a sadaukar da rayuwarsu s**a jajirce sannan ya kawo inda yake a yau.

Ya k**ata mu riƙa zaɓen shugabanni bisa nagarta, gaskiya da ƙwarewarsu, ba saboda kuɗi ko wata kyauta da za su ba mu ba. Duk ɗan siyasar da ya ba ka kuɗi ka zaɓe shi, to ya riga ya sayi haƙƙinka, kuma da zarar ya hau mulki zai nemi dawo da abin da ya kashe ne, ba wai ya yi maka hidima ba.

Idan wata matsala ta taso a cikin al’umma, wajibi ne mu nuna damuwa tare da neman a ɗauki matakin da ya dace har sai an samu adalci. Bai k**ata mu shagaltu da abubuwan da ba su da amfani ba yayin da manyan matsalolin da s**a shafi rayuwarmu ke ci gaba da addabar mu.

Babu wanda zai zo daga wani wuri ya gyara mana ƙasa sai mu kanmu. Allah ba zai sauko Ya yi mana komai kai tsaye ba, kuma ba zai aiko da mala’iku su gudanar mana da harkokin ƙasa ba. Al’umma ce ke gina makomarta ta hanyar jajircewa, haɗin kai da ɗaukar alhakin abin da ya shafe ta.

Ko a ƙasashen da s**a ci gaba irin su Amerika, gwamnati tana la’akari da muradin jama’a ne saboda mutane suna tsayawa tsayin daka wajen kare haƙƙoƙinsu da neman abin da ya dace.

Idan mu ma muna son kyakkyawar makoma, dole ne mu kasance masu kishin ƙasa, masu faɗar gaskiya, kuma masu zaɓar shugabanni nagari. Ta haka ne kawai za mu samu ci gaba mai ɗorewa.

- Bashir Abdullahi El-bash
Chairman Arewa Online Publishers Association

Inna lil Laahi wa inna ilaiHi Raaji'un!Allah Ya yi wa Malam Abbakar Pharmacy rasuwa a yau Juma'ah, bayan jinya da ya sha...
05/06/2026

Inna lil Laahi wa inna ilaiHi Raaji'un!

Allah Ya yi wa Malam Abbakar Pharmacy rasuwa a yau Juma'ah, bayan jinya da ya sha fama da ita.

Muna roƙon Allah ya jiƙansa da rahama, ya gafarta masa kurakuransa, ya yalwata masa kabarinsa, ya kuma bai wa iyalansa da masoyansa haƙuri da juriya.

Allah Ya sa Aljannah ce makomarsa tare da iyayenmu da malamanmu da zurriyyarmu da aminanmu da yan'uwanmu.

Sabbin Masu Tsalle Daga Sama Sun Kammala Horo, Sojoji Sun Nuna Gamsuwa Da ƘwarewarsuRundunar Sojin Najeriya ta bukaci sa...
05/06/2026

Sabbin Masu Tsalle Daga Sama Sun Kammala Horo, Sojoji Sun Nuna Gamsuwa Da Ƙwarewarsu

Rundunar Sojin Najeriya ta bukaci sabbin jami’an da s**a kammala horon tsalle daga sama (Paratroopers) da su yi amfani da ƙwarewar da s**a samu wajen ƙarfafa ayyukan tsaro da kuma kare martabar ƙasar nan.

An bayyana hakan ne yayin bikin yaye ɗaliban kwasa-kwasai daban-daban na Airborne da Makarantar Horar da Sojojin Ƙasa ta Najeriya (NASI) ta gudanar a filin saukar laima na Jaji da ke Jihar Kaduna.

Da yake jawabi a wajen bikin, Kwamandan Infantry Corps na Rundunar Sojin Najeriya, Manjo Janar Godwin Michael Mutkut, ya ce horon da jami’an s**a samu zai taimaka wajen inganta ayyukan soji da cimma manufofin tsaro a faɗin ƙasar nan.

Ya jaddada muhimmancin sadaukar da kai, ƙwarewa da bin ƙa’idojin aikin soja, yana mai cewa irin wannan ƙwarewa na da matuƙar muhimmanci wajen tunkarar matsalolin tsaro da Najeriya ke fuskanta da kuma samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

Mutkut ya kuma buƙaci waɗanda s**a kammala horon da su ci gaba da neman ƙarin ilimi da horo na musamman domin bunƙasa kwarewarsu da kuma dacewa da sauye-sauyen da ke faruwa a fannin tsaro.

A nasa jawabin, Kwamandan NASI, Manjo Janar Frank Sunday Etim, ya ce ɗaliban sun samu horo mai kyau wanda ya haɗa da atisayen jiki, koyon dabarun ayyukan sama da kuma horon juriya da shirye-shiryen tunani kafin su samu cancantar zama paratroopers.

Ya bayyana cewa ɗaliban sun nuna ƙwazo, juriya da ƙwarewa a tsawon lokacin horon, yana mai cewa ayyukan tsalle daga sama na buƙatar matuƙar kulawa da bin umarni domin kauce wa haɗurra.

Hakazalika, makarantar ta kuma yaye ɗaliban kwas ɗin tuki da kula da motocin yaƙi masu sulke (APC), inda aka bukace su da su yi amfani da ilimin da s**a samu wajen ƙarfafa ayyukan rundunar tare da koyar da sauran jami’ai a sassan da suke aiki.

Bikin ya samu armashi da tsalle-tsallen nuna ƙwarewa na sabbin paratroopers, sanya musu tambarin Airborne Wings, karrama fitattun ɗalibai da kuma ɗaukar hoton tunawa.

Shugaban Hukumar Hisbah a jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya dawo gida Najeriya daga ƙasar Saudiyya inda ya jag...
04/06/2026

Shugaban Hukumar Hisbah a jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya dawo gida Najeriya daga ƙasar Saudiyya inda ya jagoranci wani rukunin alhazan Hajjin bana.

A wani sako da aka wallafa a shafin malamin na Facebook, Daurawa ya ce : “Alhamdu lillah mun sauko lafiya sai fara shirin auran gata”.

Shugaban mulkin sojin Niger Janar  Abdourahamane Tiani, na ziyarar aiki a kasar Turkiyya
04/06/2026

Shugaban mulkin sojin Niger Janar Abdourahamane Tiani, na ziyarar aiki a kasar Turkiyya

Facebook Subscription ba ƙoƙon bara ba ne.Ainihin manufar Facebook Subscription shi ne mutum ya biya kuɗi domin samun wa...
04/06/2026

Facebook Subscription ba ƙoƙon bara ba ne.

Ainihin manufar Facebook Subscription shi ne mutum ya biya kuɗi domin samun wani ƙarin amfani da wanda bai biya ba ba zai samu ba, k**ar dai yadda mu ke biyan Arewa24 Ondemand don mu samu kallon Dadin Kowa, Kwana Casaʼin, Zabi Biyu, ko biyan YouTube Premium don kar mu ga talla da sauraro ana ci gaba da aiki da sauransu, wanda abu ne mai wahala wanda bai biya kuɗi ba ya samu.

Idan kana da Subscription, ka tambayi kanka:

Me subscriber da ya biya ni kuɗi zai samu?

Shin akwai rubuce-rubuce na musamman da na ke yi masa da in bai biya ba, ba zai samu ba?

Shin akwai bidiyoyi na musamman da in bai biya ba, ba zai samu ba?

Shin akwai group ko community da na tanada masa da in bai biya ba, ba zai samu shiga ba?

Shin akwai ilimi, rahoto ko wata dama da na ke ba shi fiye da sauran mabiya?

Idan amsar waɗannan tambayoyin ita ce a'a, to akwai buƙatar sake tunani.

Duk da cewa akwai wani kaso na mutane da ke biyan kuɗi ko kyauta ga ƴan mata masu girgije-girgijen rufaida, amma kasani mafi yawan mutane ba za su ba ka kuɗi haka kawai ba.

Mutane na biyan kuɗi ne saboda ƙimar abin da suke samu a wajensu.

Shin idan ina samun abin da kake bani ba tare da na biya kuɗi ba, me ya sa zan biya kuɗi?

Idan kana son mutane su yi subscribing ɗinka, ka fara gina abin da zai sa su gamsu da dalilin yin hakan.

Da dama ba wanda ya k**a hannunmu ya ce sai mun yi subscription na manhaja kaza, yau da gobe bukatarka za ta sa ka nema.

Na san mutane da yawa sun fara amfani da chat gpt na free, amma daga baya sai su ce min ai sun yi subscription saboda sun ga akwai ƙarin riba a cikin hakan.

Subscription mai ɗorewa ba ya dogara da tausayi ko soyayya kawai. Ya fi dogara da ƙima, amfani da amincewar mabiya.

A ƙarshe, kafin ka soma neman a baka kuɗi ta Subscription, ka fara tambayar kanka, Idan ni ne mabiyi, shin zan biya kuɗi domin abin da wannan page ɗin ke bayarwa?

Idan amsar ita ce eh, to kana kan hanya mai kyau. Idan kuma a'a, lokaci ya yi da za ka sake shirin kafin soma neman mutane su ba ka kuɗi.

In ba haka ba Facebook Subscription ɗinka ya koma daidai da ƙoƙon bara.

A ƙarshe, abin da ya fi ba ni mamaki shi ne yadda wasu ke neman kuɗin Subscription alhali mafi yawan abubuwan da suke wallafawa ba nasu ba ne, kuma ana iya samun irin su a wasu shafuka kyauta. Idan haka ne, me zai sa mutum ya biya kuɗi?

Allah ya sa mu dace.

Address

Abuja
5,500

Opening Hours

Monday 09:00 - 22:00
Tuesday 09:00 - 22:00
Wednesday 09:00 - 23:00
Thursday 08:51 - 17:50
Friday 05:00 - 13:10
Saturday 05:12 - 12:05
Sunday 08:09 - 15:55

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DG HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DG HAUSA:

Share

Category