DG HAUSA

DG HAUSA BARKA DA ZUWA WANNAN SASHE NA DG HAUSA Gaskiya afadeta yafi abarta DOKIN KARFE TV

Na yi takaicin rashin musuluntar Michael Jackson- "In ji Jermaine (Yayan Michael jackson)A Wata Hira Da BBC a Ranar 23 G...
05/07/2025

Na yi takaicin rashin musuluntar Michael Jackson-
"In ji Jermaine (Yayan Michael jackson)

A Wata Hira Da BBC a Ranar 23 Ga Watan Yuni 2010 Yau Shekaru (14)

A wata hira ta musamman da yayi da BBC, Jermaine Jackson, ya ce da Michael Jackson ya shiga musulunci, da bai samu kansa a wancan hali ba, abinda har ya yi sanadiyyar rasuwar sa.

"Yace kodayaushe nakan yi takaicin cewa ban samu damar ceto rayuwar sa ba".

Ga dai yadda hirar tasa da BBC ta kasance:

BBC: To ko menene dalilinka?

Jermaine: Idan da Michael Jackson ya shiga musulunci, da tuni yana raye. Saboda idan kana da yakini a kan abinda kake aikatawa da kuma wadanda suke kewaye da kai, to lallai rayuwarka za ta inganta, domin Allah zai taimake ka.

Ya kara da cewa yana karanta litattafai da dama, na sayo masa wasu daga Saudi Arabiya da kuma Bahrain. Ni ne na fara kai shi Bahrain saboda ina so ya bar Amurka domin rayuwar Amurka na jefa shi cikin mawuyacin hali.

BBC: Sai dai bai so ya shiga musuluncin ba ko kuwa?

Jermaine: Ba wai ba ya so ya shiga musulunci bane. Duka masu gadinsa musulmai ne saboda ya amince da musulunci, kuma ganin wadannan mutane tare da shi zai taimaka Allah ya bashi kariya ko don saboda su.

BBC: Shin ko ka yarda da zargin da aka yi masa na cin zarafin yara?

Jermaine: Ai kotu ta wanke shi game duk wadannan zarge-zargen. Yaron da ake magana a kansa Jordan Chandler ya ce bai taba taba shi ba. Abinda ya sa kuma mahaifinsa ya kashe kansa.

Kuma da wannan ne kafafen yada labarai s**a yi ta zuzuta lamarin suna s**ar dan uwana a kan abinda bai aikata ba, kuma har yanzu wasu ba su amince da hakan ba.

Ya ce kaunar da aka nunawa dan uwana lokacin da ya rasu, ita ya k**ata a nuna masa lokacin da yake raye. Hukumar bincike ta FBI a Amurka ta bincike shi har na tsawon shekaru 17, amma ba ta same shi da wani laifi ba.

Sai daga baya s**a zo suna yabonsa, a gani na irin wannan yabon ya k**ata su nuna masa tun yana raye, kuma da hakan ya karfafa masa zuciya.

BBC: To ko yaya rayuwa take bayan mutuwa

Marigayi Sheik Dakta Idris Abdul-Aziz Dutsen Tanshi Ya Bar Baya Da Dumbin AlheriWasu daga cikin 'ya'yan Marigayi Sheikh ...
04/07/2025

Marigayi Sheik Dakta Idris Abdul-Aziz Dutsen Tanshi Ya Bar Baya Da Dumbin Alheri

Wasu daga cikin 'ya'yan Marigayi Sheikh Dr Idris Abdul-Aziz Bauchi (Limamin jaddada Tauhidi na Afirka) guda biyar sun kammala karatun jami'ah a Kasar Indiya.

Malam Idris ya tura 'ya'yansa maza da mata Kasar India domin su yi ilimi a fannoni na kiwon lafiyar mutane su dawo su cike wa al'ummar Musulmi gurbi.

Malam Idris ya gina Asibiti da kudin aljihunsa, ya kawo tsarin da mace Likita zata duba 'yar uwarta mace, a lokacin da ya gina asibitin ya nemi mace Likita tazo tayi aiki zai ninka mata albashi ya rasa, shine ya tura 'yar cikinsa taje tayi karatun.

Malam yau baya raye Allah Ya cika masa burinsa, ku duba fannoni na ilimin kiwon lafiya masu tsada da yaransa s**a karanta a India, kuma sun kammala da sak**ako mai kyau, gasu k**ar haka:
👇
(1) Abdullahi Idris Abdul-Aziz ya karanta Physiotherapy

(2) Abdul-Aziz Idris Abdul-Aziz ya karanta Doctor of Pharmacy

(3) Muhammad Idris Abdul-Aziz ya karanta Medical Laboratory Technology

(4) Khadijah Idris Abdul-Aziz ta karanta Nursing

(5) Fatima Idris Abdul-Aziz ta karanta Radiology Imaging Technology

Idan ban manta ba akwai wanda ya kammala karatun MBBS, kunga asibiti guda ya hadu da Likitoci

Marigayi Malam Idris Abdul-Aziz rayuwarsa ta yi albarka, ya cike wa Musulunci gurbin da s**a rasa, tabbas ba mu yi nadamar kasancewa tare da shi ba a lokacin da aka tsangwamemu saboda shi.

Yaa Allah Ka jikansa da rahama, Ka hada fuskokinmu da shi a cikin Aljannah Madaukakiya.

Daga Datti Assalafiy

TEKNOLOGIA: Nawa zaku iya sayen wannan motar da aka kirkiro mai daukar mutum daya Sunan motar dai "Fiat Panda" kuma ana ...
04/07/2025

TEKNOLOGIA: Nawa zaku iya sayen wannan motar da aka kirkiro mai daukar mutum daya

Sunan motar dai "Fiat Panda" kuma ana cajin ta...

Kuyi mata kudi...

Gwamnonin jihohin Kano da Jigawa da kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II sun daura aniyar aikin Umara bayan kammala jana...
02/07/2025

Gwamnonin jihohin Kano da Jigawa da kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II sun daura aniyar aikin Umara bayan kammala jana'izar marigayi Aminu Alhassan Dantata

Ina Mai Janye Kalaman Da Na Yi Kan 'Yan Fim Din Hausa, Saboda Na Yi Su Ne Kan Kuskure, Sannan Kada A Yi Zaton Rarara Ne ...
02/07/2025

Ina Mai Janye Kalaman Da Na Yi Kan 'Yan Fim Din Hausa, Saboda Na Yi Su Ne Kan Kuskure, Sannan Kada A Yi Zaton Rarara Ne Ya Sa Ni Na Furta Wadannan Kalaman, Cewar Al-Hikima

01/07/2025

A safiyar Yau Talata akesa Ran gudanar da jana'izar Alhaji Aminu Dantata

A Senegal ana can ana cigaba da gudanar da gasar sarauniyar kyau ta Tumaki, kawo yanzu dai ba'akai ga fidda wacce tafi k...
01/07/2025

A Senegal ana can ana cigaba da gudanar da gasar sarauniyar kyau ta Tumaki, kawo yanzu dai ba'akai ga fidda wacce tafi kowacce kyau ba.

YANZU YANZU: Mai girma Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf tare da Mai Martaba Sarkin Kano Sunusi Lamiɗo Sunusi, Sheikh Aminu ...
30/06/2025

YANZU YANZU: Mai girma Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf tare da Mai Martaba Sarkin Kano Sunusi Lamiɗo Sunusi, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da sauran al'umma sun k**a hanya zuwa ƙasa mai tsarki domin halartar jana'izar Alh Aminu Ɗantata a yau Litinin.

Wasu majiyoyi daga fadar shugaban Najeriya sun tabbatar wa BBC cewa Ganduje ya ajiye muƙamin ne bayan da fadar shugaban ...
27/06/2025

Wasu majiyoyi daga fadar shugaban Najeriya sun tabbatar wa BBC cewa Ganduje ya ajiye muƙamin ne bayan da fadar shugaban ƙasa ta umarce shi da yin hakan.

YANZU-YANZU: Sheikh Ɗahiru Bauchi Ya Cika Shekaru 101 a Duniya!!Fitaccen malamin addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Ɗa...
27/06/2025

YANZU-YANZU: Sheikh Ɗahiru Bauchi Ya Cika Shekaru 101 a Duniya!!

Fitaccen malamin addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi, ya cika shekaru 101 da haihuwa. An haife shi a shekarar 1924, kuma ya shahara wajen wa’azi, tafsiri da yada ilimin addini a faɗin ƙasa da wajen kasar Najeriya,

Yana daga cikin manyan jagororin Darikar Tijjaniyya, kuma yana da dimbin mabiya.

Al’ummar Musulmi da dama na taya shi murna tare da fatan Allah ya ƙara masa lafiya da nisan kwana.

Wane darasi kuka ɗauka a rayuwarsa?

YANZU-YANZU:Gungun Yahudawa Ƴan asalin kasar Iran, sun yi taron addu'a tare da yin Tir da ayyukan Natenyahu. Taron addu'...
27/06/2025

YANZU-YANZU:Gungun Yahudawa Ƴan asalin kasar Iran, sun yi taron addu'a tare da yin Tir da ayyukan Natenyahu.

Taron addu'ar ta gudana ne a Haikalin Abrishami da ke Tehran domin nuna goyon baya ga Ayatollah Ali Khamenei da Rundunonin Tsaron ƙasar Iran.

HOTO📸 News Agency

Wannan wani wurin ibadah ne a ƙasar India 🇮🇳 Kowane abun bauta an saka hotonsa da addininsaSai dai, shi Allah gagari gas...
27/06/2025

Wannan wani wurin ibadah ne a ƙasar India 🇮🇳

Kowane abun bauta an saka hotonsa da addininsa

Sai dai, shi Allah gagari gasa ne kuma gagari misali

Ba’a iya tunanin Allah, ko zanashi, ko sassaƙashi

Tsarki ya tabbata ga Allah

Mai kowa-mai komai

Mabuwayi mai girma 🥹
____________________________

DG HAUSA

Address

Abuja
5,500

Opening Hours

Monday 09:00 - 22:00
Tuesday 09:00 - 22:00
Wednesday 09:00 - 23:00
Thursday 08:51 - 17:50
Friday 05:00 - 13:10
Saturday 05:12 - 12:05
Sunday 08:09 - 15:55

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DG HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DG HAUSA:

Share

Category