Hausa Daily News

Hausa Daily News Sahihan Labarai

KO EL'RUFA'I ZAI IYA CIKA SHARUDDAN BELIN DA AKA GINDAYA MASA?Kotun Trayya dake zaman ta a Jihar Kaduna ta bayar da bali...
14/04/2026

KO EL'RUFA'I ZAI IYA CIKA SHARUDDAN BELIN DA AKA GINDAYA MASA?

Kotun Trayya dake zaman ta a Jihar Kaduna ta bayar da balin Tsohon Gwamnan Jihar Malam Nasiru El-Rufai.

Belin Na El'Rufa'i N a zuwa ne Bayan Kotun ta Gindaya wasu Sharudda da bukaci ya cika kafin a bashi damar tafiya Gidan ya koma cikin Iyalansa.

Acewar Kotun wajibi ne El'Rufa'i ya jiye Naira miliyan 200 ya kuma kawo mutane biyu da zasu Tsaya Masa.

ta kuma ce tilas ne Daya Daga Cikin Mutanen Ya Mika Takardar Mallakar Fili a ƙasar nan.

kazalika Dayan Kuma Dole Ne Ya Zama Dattijon Da Ake Girmamawa A Jihar Kaduna, Wanda Majalisar Magabatan Jihar Kaduna Ta Amince Da Shi.

Haka kuma Kotun ta ba El'Rufa'I Ko Lauyansa Umurnin su k**a bakinsa kada kuskura su Yi Hira Da 'Yan Jarida Akan duk wani abu da ya shafi Karar Har Sai An Kammala Shari’ar.

Bugu da Kari Kotun ta Bukaci El-Rufai ya rika kai kansa ofishin hukumar ICPC a ranar farko na kowane wata kuma ya mikawa kotu fasfonsa na Tafiye-tafiye.

Ya zuwa Lokacin El'Rufa'i da sauran Mukarabansa na can suna aiki tukuru domin cika wadannan sharudda da kotu ta Gindaya masa.

yayinda aka sake tasa keyarsa zuwa hukumar ta ICPC.

KAKAKIN MAJALISAR JIHAR KEBBI YA RASU.Kakakin Majalisar dokokin jihar Kebbi Alhji Mohammed Usman Zuru  ya rasu.Mai magan...
07/04/2026

KAKAKIN MAJALISAR JIHAR KEBBI YA RASU.

Kakakin Majalisar dokokin jihar Kebbi Alhji Mohammed Usman Zuru ya rasu.

Mai magana da yawun Majalisar Murtala Adamu Diri ne ya tabbatar hakan a cikin sanarwar da ya fitar safiyar ranar talata.

A cewar sanarwar Usman Zuru ya rasu ne a marecen ranar Litinin a birnin Cairo na ƙasar Egypt yayin da yake jinya.

Maragayi dai shi ne ke wakiltar mazaɓar Zuru a Majalisar dokokin jihar Kebbi, kuma yana ɗaya da ga cikin fitattun'yan siyasa a yankin masarautar Zuru, kana Kakakin Majalisar dokokin jihar Kebbi ta 10.
Sanarwar ta ce za'a sanar da lokacin jana'izar sa nan bada jimawa ba.

DANGOTE YA RAGE FARASHIN LITAR MAIMatatar mai ta Dangote  ta sanar da rage farashin man fetur daga naira 1,175 kan kowac...
11/03/2026

DANGOTE YA RAGE FARASHIN LITAR MAI

Matatar mai ta Dangote ta sanar da rage farashin man fetur daga naira 1,175 kan kowace lita zuwa naira 1,075, wanda ke nuna ragin naira 100.

A cikin wata sanarwa da matatar ta wallafa a shafinta na X, ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan saukar farashin danyen mai a kasuwannin duniya, tare da cewa an dauki matakin ne bisa sabon tsarin farashin da kamfanin ya fitar.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa matatar ta rage farashin man dizal zuwa naira 1,430 kan kowace lita daga tsohon farashin naira 1,620.

Matatar ta jaddada kudurinta na taimakawa wajen karfafa tsaron mak**ashi a Najeriya, tare da la’akari da halin tattalin arzikin da al’ummar kasar ke ciki, k**ar yadda wani babban jami’in kamfanin ya bayyana.

Rahotanni sun nuna cewa wannan shi ne karo na farko da aka rage farashin man bayan karin sau uku a jere da aka yi a makonnin baya, wanda ya haddasa tashin farashin man sosai a kasuwa.

Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDPƊan Majalisar Tarayya mai Wakiltar Sabon Gari Daga Jihar Kaduna, Sadiq...
13/10/2025

Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP

Ɗan Majalisar Tarayya mai Wakiltar Sabon Gari Daga Jihar Kaduna, Sadiq Ango Abdullahi, ya fice daga Jam’iyyarsa ta PDP.

Honorabul Abdullahi wanda shi ne Mataimakin Shugaban Kwamishinan Hukumar Kula da Hanyoyi (FERMA) ya alaƙanta ficewarsa da rikicin cikin gida da rabuwar kai da ya ki ci ya ƙi cinyewa a jam’iyyar.

A ranar Litinin ya aike da wasikar ta ficewa ga Shugaban PDP na Mazabar Hanwa da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, yana mai cewa rikicin ya hana shi taɓukawa matsayin zaɓaɓɓen ɗan Majalisar Tarayya.

Ya cewa saboda haka yana dacewar ficewarsa daga jam’iyyar ba tare da la’akari da siyasa ba, domin amfanin ɗauƙacin al’ummar mazabar.

Ya yaba wa jam’iyyar bisa damar da kuma gudummawar da ta ba shi domin hidimta wa al’umma.

Sheikh Abubakar da aka fi sani da Lawan Triumph ya nemi afuwar wadanda s**a yi wa kalamansa kuskuren fahimta. Sheikh Law...
13/10/2025

Sheikh Abubakar da aka fi sani da Lawan Triumph ya nemi afuwar wadanda s**a yi wa kalamansa kuskuren fahimta.

Sheikh Lawan Triumph ya bayyana hakan a gaban Kwamitin Shura da gwamnatin Kano a Najeriya ta kafa domin bincike kan zargin yin wasu kalaman batanci ga Ma’aiki da kuma salon yadda yake wa’azi.

Kwamitin Shura na Jihar Kano, ya yi ganawar sirri da Malam Lawan Abubakar Triumph a ofishin DSS, kan zarginsa da ɓatanci...
13/10/2025

Kwamitin Shura na Jihar Kano, ya yi ganawar sirri da Malam Lawan Abubakar Triumph a ofishin DSS, kan zarginsa da ɓatanci ga Annabi Muhammad (SAW).

Bayan Kwamitin Shura, Wazirin Kano, Shehu Gidado, da daraktan DSS da wasu manyan malamai sun halarci zaman da aka fara da misalin ƙarfe 11:39 na safe, inda malamin ya yi ƙarin haske kan maganganun da ake zarginsa da su.

Babu batun maye gurbin ministan kudi don ya na samun sauki i: Fadar Shugaban Ƙasa Ministan Kudi kuma Ministan da ke da a...
13/10/2025

Babu batun maye gurbin ministan kudi don ya na samun sauki i: Fadar Shugaban Ƙasa

Ministan Kudi kuma Ministan da ke da alhakin Tsare-tsaren Tattalin Arzikin Ƙasa, Mista Wale Edun, yana jinya a gidansa da ke Abuja bayan ya kamu da rashin lafiya, kuma babu wani shiri daga Shugaba Bola Tinubu na maye gurbinsa, k**ar yadda majiyoyi da dama daga Fadar Shugaban Ƙasa s**a tabbatar wa jaridar The PUNCH a ranar Lahadi.

Wani babban jami’in gwamnati da ya nemi a sakaya sunansa saboda ba shi da izinin yin magana da manema labarai, ya karyata jita-jitar da ke cewa ministan ya kamu da ciwon barin jiki ko kuma an kai shi kasashen waje domin jinya.

Ya ce, “Eh, gaskiya ba shi da lafiya. Ciwon yana da ɗan tsanani, amma ba shanyewar barin jiki ba ne.”

Majiyar ta ƙara da cewa, “A halin yanzu yana gidansa. Ba a kai shi ko’ina ba.

“Tabbas, idan likitoci s**a ce ya k**ata a tafi neman ƙarin kulawa a wani wuri, zai iya tafiya. Amma ba gaskiya ba ne cewa ya kamu da cutar barin jiki. Ba shi da wannan, shi ya sa muka bayyana cewa yana rashin lafiya kawai.”

Wani jami’i na daban ma ya tabbatar da cewa Edun na samun kulawar likitoci a Najeriya, kuma zai iya zuwa ƙasashen waje idan bukatar hakan ta taso.

“Likitocin Najeriya ne ke duba shi yanzu. Har yanzu suna bibiyar lafiyarsa. Idan har za a bukaci kulawa ta musamman a ƙasashen waje, zai iya tafiya, amma a yanzu yana gida,” in ji shi. “Babu wani shiri na maye gurbinsa.”

Mai Ba wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin yada labarai Mista Bayo Onanuga, ya tabbatar cewa Ministan yana karɓar magani a cikin ƙasar.

Ya ce, “Eh, gaskiya ba shi da lafiya. Wale Edun yana da shekaru kusan 69. Ya kamu da rashin lafiya ne kwatsam. Yanzu haka yana nan a Najeriya. Yana samun sauƙi. Yana nan kusa.” in ji Onanuga ga wakilinmu Punch.

ƘARIN ƘANANAN HUKUMOMIN KATSINA UKU SUN YI SULHU DA ƳANBINDIGAƘananan hukumomin Malumfashi da Funtua da Bakori sun bi sa...
13/10/2025

ƘARIN ƘANANAN HUKUMOMIN KATSINA UKU SUN YI SULHU DA ƳANBINDIGA

Ƙananan hukumomin Malumfashi da Funtua da Bakori sun bi sahun wasu takwarorinsu da s**a yi sulhu da ƴanbindigar a jihar da ke fama da matsalar tsaro.

Jihar Katsina na daga cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya da ke fama da matsalar ƴanbindiga masu kai hare-hare a ƙauyuka da garuruwan jihar da kashe mutane da sace wasu domin neman kuɗin fansa.

An gudanar da zaman sulhun ne a garin Kakumi da ke yankin ƙaramar hukumar Bakori, k**ar yadda Jaridar Daily Trust ta bayyana.

Taron sulhun ya samu halartar shugabannin alumomin yankunan da wakilan ƴanbindigar.

A baya-bayan nan ana ta samun ƙaruwar ƙananan hukumomin Katsina a ke rungumar sulhu a wani mataki na magance matsalar tsaron jihar.

Afuwar Tinubu Za Ta Buɗe Hanyar Ci Gaba Da Aikata Miyagun Laifuka — AtikuTsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar...
13/10/2025

Afuwar Tinubu Za Ta Buɗe Hanyar Ci Gaba Da Aikata Miyagun Laifuka — Atiku

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan yadda shugaba Bola Tinubu ya yi wa wasu mutane afuwa, ciki har da waɗanda s**a aikata manyan laifuka.

A cikin saƙon da Atiku ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ana yin afuwa ne ga waɗanda aka yi wa rashin adalci ko waɗanda s**a nema gafara bayan sun shafe wani lokaci a gidan yari.

Ya ce a wannan karon an yi wa masu safarar ƙwayoyi, masu garkuwa da mutane, masu kisan kai, da kuma masu cin hanci da rashawa afuwa.

Atiku, ya ce abin mamaki ne yadda gwamnati ke yafewa irin waɗannan mutane, a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsaro da lalacewar tarbiyya, musamman tsakanin matasa masu shan miyagun ƙwayoyi.

Ya ce bincike ya nuna cewa kashi 29 na waɗanda aka yi wa afuwa suna da alaƙa da hakrar miyagun ƙwayoyi, yayin da Najeriya ke ƙoƙarin wanke sunanta a idon duniya kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi.

Atiku, ya ce maimakon wannan afuwa ta zama darasi ga masu laifi, ta zama hanyar durƙusa da ɓangaren shari’a da jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu wajen k**awa da hukunta masu aikata laifuka.

Ya ƙara da cewa idan gwamnati ta fara yafe wa masu laifi, hakan zai rage ƙimar shugabanci kuma ya ƙarfafa wa masu aikata laifuka su ci gaba da aikata su.

Atiku ya jaddada cewa Najeriya tana buƙatar shugabanci na gari wanda zai tabbatar da adalci a shari’a, ba tare da nuna bambanci ba.

Yajin Aikin ASUU: Gwamnatin Tarayya Tace Ba Aiki Ba Albashi Gwamnatin Tarayya, ta gargaɗi Ƙungiyar Malaman Kami’o’i ta Ƙ...
13/10/2025

Yajin Aikin ASUU: Gwamnatin Tarayya Tace Ba Aiki Ba Albashi

Gwamnatin Tarayya, ta gargaɗi Ƙungiyar Malaman Kami’o’i ta Ƙasa (ASUU), cewa za ta aiwatar da dokar “babu aiki, babu albashi” idan malaman s**a ci gaba da yajin aikin da ka iya zai kawo cikas ga harkokin karatu.

A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta fitar da yammacin ranar Lahadi, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, da Ƙaramar Ministan Ilimi, Suwaiba Sa’id Ahmed, sun ce gwamnati tana da niyyar magance ƙorafe-ƙorafen ASUU ta hanyar tattaunawa cikin lumana.

“Gwamnati ta nuna gaskiya, haƙuri da kyakkyawar niyya a tattaunawarta da ƙungiyar,” in ji sanarwar.

Ministocin sun bayyana cewa yawancin buƙatun ASUU, k**ar ƙarin kuɗin koyarwa da inganta yanayin aiki an riga an biya musu.

Sauran matsalolin kuma suna ƙarƙashin kulawar kwamitocin gudanarwar jami’o’i, waɗanda gwamnati ta sake kafawa don su kula da batutuwan da s**a rage.

Sai dai duk da waɗannan matakan, ASUU ta zaɓi shiga yajin aiki.

Ministocin sun ce wannan mataki bai nuna haɗin kai ko adalci ga ɗalibai da jama’a ba.

Sun ƙara da cewa: “Gwamnati ta yi tsayin daka wajen tabbatar da zaman lafiya da daidaita karatu a jami’o’i.

“Amma sun yi gargaɗi cewa, dokar “babu aiki, babu albashi” tana nan daram a tsarin dokokin ƙwadago na Najeriya, kuma gwamnati za ta yi amfani da ita idan aka katse harkokin karatu.

Gwamnati ta roƙi ASUU da ta sake tunani tare da dawowa teburin sulhu, inda ta ce ƙofarta a buɗe ta ke don tattaunawa da yin sulhu.

SOJA YA HARBE MATARSA, YA KASHE KANSA A JIHAR NEJAWani soja mai muƙamin Las Kofur ya ɗirka wa matarsa harbi har lahira s...
13/10/2025

SOJA YA HARBE MATARSA, YA KASHE KANSA A JIHAR NEJA

Wani soja mai muƙamin Las Kofur ya ɗirka wa matarsa harbi har lahira sannan ya kashe kansa a Jihar Neja.

Las Kofur Akenleye Femi da ke aiki a Bataliya ta 221, ya yi wannan aika-aika ne a Barikin Sojoji na Wawa da ke Ƙaramar Hukumar Borgu a Jihar Neja.

Muƙaddashin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Soja ta 22 da ke Ilorin, Kyaftin Stephen Nwankwo, ne ya tabbatar da lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce abin ya faru ne a ranar 11 ga Oktoba, 2025.

Ya ce mutuwar sojan da matarsa ta haifar da tashin hankali a cikin sansanin soja, inda mazauna wurin s**a shiga ɗimuwa da mamaki kan abin da zai iya jawo irin wannan lamari.

“An gano gawar Last Kofur Femi da matarsa ne a cikin dakinsu da ke Block 15, Room 24 na Corporals and Below Quarters a Wawa Cantonment,” in ji Kyaftin Nwankwo.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa sojan yana kan aiki a cikin sansanin kafin ya nemi izinin zuwa gida domin wasu bukatun kansa, sai daga bisani aka gano gawarsu a gida.

Kyaftin Nwankwo ya ce an ajiye gawar mamatan domin ci gaba da bincike, kuma rundunar sojan na aiki tukuru don gano musabbabin lamarin.

Rundunar Soja ta Najeriya ta bayyana matuƙar baƙin cikinta kan wannan abin takaici, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalai, abokai da abokan aikin mamatan.

Kwamandan Rundunar, Birgediya Janar Ezra Barkins, ya sha alwashin gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru, tare da ɗaukar matakan da za su hana faruwar irin haka a nan gaba.

Address

Otako Abuja
Abuja

Telephone

+2348124905058

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Daily News:

Share