10/07/2026
AN DAWO DA 'YAN NAJERIYA 282 DAGA AFIRKA TA KUDU
Jirgi na biyar da ke ɗauke da ‘yan Najeriya da aka kwaso daga Afirka ta Kudu ya sauka a Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed da ke Legas a yammacin ranar Alhamis.
Jimillar mutane 282 ne s**a dawo da jirgin Air Peace da misalin karfe 7:30 na dare.
Gwamnatin Tarayya na ci gaba da kwashe ‘yan Najeriya da s**a nuna son komawa gida Domin kaucewa hare-haren kin jinin Baki a ƙasar ta Afirka ta Kudu.