14/04/2026
KO EL'RUFA'I ZAI IYA CIKA SHARUDDAN BELIN DA AKA GINDAYA MASA?
Kotun Trayya dake zaman ta a Jihar Kaduna ta bayar da balin Tsohon Gwamnan Jihar Malam Nasiru El-Rufai.
Belin Na El'Rufa'i N a zuwa ne Bayan Kotun ta Gindaya wasu Sharudda da bukaci ya cika kafin a bashi damar tafiya Gidan ya koma cikin Iyalansa.
Acewar Kotun wajibi ne El'Rufa'i ya jiye Naira miliyan 200 ya kuma kawo mutane biyu da zasu Tsaya Masa.
ta kuma ce tilas ne Daya Daga Cikin Mutanen Ya Mika Takardar Mallakar Fili a ƙasar nan.
kazalika Dayan Kuma Dole Ne Ya Zama Dattijon Da Ake Girmamawa A Jihar Kaduna, Wanda Majalisar Magabatan Jihar Kaduna Ta Amince Da Shi.
Haka kuma Kotun ta ba El'Rufa'I Ko Lauyansa Umurnin su k**a bakinsa kada kuskura su Yi Hira Da 'Yan Jarida Akan duk wani abu da ya shafi Karar Har Sai An Kammala Shari’ar.
Bugu da Kari Kotun ta Bukaci El-Rufai ya rika kai kansa ofishin hukumar ICPC a ranar farko na kowane wata kuma ya mikawa kotu fasfonsa na Tafiye-tafiye.
Ya zuwa Lokacin El'Rufa'i da sauran Mukarabansa na can suna aiki tukuru domin cika wadannan sharudda da kotu ta Gindaya masa.
yayinda aka sake tasa keyarsa zuwa hukumar ta ICPC.