Hausa Daily News

Hausa Daily News Sahihan Labarai

AN DAWO DA 'YAN NAJERIYA 282 DAGA AFIRKA TA KUDU Jirgi na biyar da ke ɗauke da ‘yan Najeriya da aka kwaso daga Afirka ta...
10/07/2026

AN DAWO DA 'YAN NAJERIYA 282 DAGA AFIRKA TA KUDU

Jirgi na biyar da ke ɗauke da ‘yan Najeriya da aka kwaso daga Afirka ta Kudu ya sauka a Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed da ke Legas a yammacin ranar Alhamis.

Jimillar mutane 282 ne s**a dawo da jirgin Air Peace da misalin karfe 7:30 na dare.

Gwamnatin Tarayya na ci gaba da kwashe ‘yan Najeriya da s**a nuna son komawa gida Domin kaucewa hare-haren kin jinin Baki a ƙasar ta Afirka ta Kudu.

SOJOJI SUN K**A MATAR DAKE KAIWA 'YAN BOKO HARAM KAYAN MAYESojoji sun k**a wata Mata ƴar ƙasar Chadi dake kai wa mayaƙan...
10/07/2026

SOJOJI SUN K**A MATAR DAKE KAIWA 'YAN BOKO HARAM KAYAN MAYE

Sojoji sun k**a wata Mata ƴar ƙasar Chadi dake kai wa mayaƙan Boko Haram kayan Maye.

Wata sanarwa da mai magana da yawun sojojin Mohammed Goni ya fitar, ya ce sun yi amfani ne da bayanan sirri wajen bibiyarta, inda a ranar Alhamis 9 ga Yuli s**a k**ata ɗauke da tarin miyagun ƙwayoyi da giya da sauran haramtattun kayayyaki da ake kyautata zaton za ta kai wa ƴan Boko Haram ne.

FAGEN WASANNI!LIONEL MESSI YA FI KOWA ZURA KWALLAYE A GASAR CIN KOFIN DUNIYA!WAYE KUKE GANIN ZAI IYA LASHE TAKALMIN ZINA...
18/06/2026

FAGEN WASANNI!

LIONEL MESSI YA FI KOWA ZURA KWALLAYE A GASAR CIN KOFIN DUNIYA!

WAYE KUKE GANIN ZAI IYA LASHE TAKALMIN ZINARI?

KO EL'RUFA'I ZAI IYA CIKA SHARUDDAN BELIN DA AKA GINDAYA MASA?Kotun Trayya dake zaman ta a Jihar Kaduna ta bayar da bali...
14/04/2026

KO EL'RUFA'I ZAI IYA CIKA SHARUDDAN BELIN DA AKA GINDAYA MASA?

Kotun Trayya dake zaman ta a Jihar Kaduna ta bayar da balin Tsohon Gwamnan Jihar Malam Nasiru El-Rufai.

Belin Na El'Rufa'i N a zuwa ne Bayan Kotun ta Gindaya wasu Sharudda da bukaci ya cika kafin a bashi damar tafiya Gidan ya koma cikin Iyalansa.

Acewar Kotun wajibi ne El'Rufa'i ya jiye Naira miliyan 200 ya kuma kawo mutane biyu da zasu Tsaya Masa.

ta kuma ce tilas ne Daya Daga Cikin Mutanen Ya Mika Takardar Mallakar Fili a ƙasar nan.

kazalika Dayan Kuma Dole Ne Ya Zama Dattijon Da Ake Girmamawa A Jihar Kaduna, Wanda Majalisar Magabatan Jihar Kaduna Ta Amince Da Shi.

Haka kuma Kotun ta ba El'Rufa'I Ko Lauyansa Umurnin su k**a bakinsa kada kuskura su Yi Hira Da 'Yan Jarida Akan duk wani abu da ya shafi Karar Har Sai An Kammala Shari’ar.

Bugu da Kari Kotun ta Bukaci El-Rufai ya rika kai kansa ofishin hukumar ICPC a ranar farko na kowane wata kuma ya mikawa kotu fasfonsa na Tafiye-tafiye.

Ya zuwa Lokacin El'Rufa'i da sauran Mukarabansa na can suna aiki tukuru domin cika wadannan sharudda da kotu ta Gindaya masa.

yayinda aka sake tasa keyarsa zuwa hukumar ta ICPC.

KAKAKIN MAJALISAR JIHAR KEBBI YA RASU.Kakakin Majalisar dokokin jihar Kebbi Alhji Mohammed Usman Zuru  ya rasu.Mai magan...
07/04/2026

KAKAKIN MAJALISAR JIHAR KEBBI YA RASU.

Kakakin Majalisar dokokin jihar Kebbi Alhji Mohammed Usman Zuru ya rasu.

Mai magana da yawun Majalisar Murtala Adamu Diri ne ya tabbatar hakan a cikin sanarwar da ya fitar safiyar ranar talata.

A cewar sanarwar Usman Zuru ya rasu ne a marecen ranar Litinin a birnin Cairo na ƙasar Egypt yayin da yake jinya.

Maragayi dai shi ne ke wakiltar mazaɓar Zuru a Majalisar dokokin jihar Kebbi, kuma yana ɗaya da ga cikin fitattun'yan siyasa a yankin masarautar Zuru, kana Kakakin Majalisar dokokin jihar Kebbi ta 10.
Sanarwar ta ce za'a sanar da lokacin jana'izar sa nan bada jimawa ba.

DANGOTE YA RAGE FARASHIN LITAR MAIMatatar mai ta Dangote  ta sanar da rage farashin man fetur daga naira 1,175 kan kowac...
11/03/2026

DANGOTE YA RAGE FARASHIN LITAR MAI

Matatar mai ta Dangote ta sanar da rage farashin man fetur daga naira 1,175 kan kowace lita zuwa naira 1,075, wanda ke nuna ragin naira 100.

A cikin wata sanarwa da matatar ta wallafa a shafinta na X, ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan saukar farashin danyen mai a kasuwannin duniya, tare da cewa an dauki matakin ne bisa sabon tsarin farashin da kamfanin ya fitar.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa matatar ta rage farashin man dizal zuwa naira 1,430 kan kowace lita daga tsohon farashin naira 1,620.

Matatar ta jaddada kudurinta na taimakawa wajen karfafa tsaron mak**ashi a Najeriya, tare da la’akari da halin tattalin arzikin da al’ummar kasar ke ciki, k**ar yadda wani babban jami’in kamfanin ya bayyana.

Rahotanni sun nuna cewa wannan shi ne karo na farko da aka rage farashin man bayan karin sau uku a jere da aka yi a makonnin baya, wanda ya haddasa tashin farashin man sosai a kasuwa.

Address

Otako Abuja
Abuja

Telephone

+2348124905058

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Daily News:

Shortcuts

Share