25/07/2025
ABUBUWAN DA S**A FARU A WAƘI'AR 25th JULY, 2014 A TAƘAICE
Daga cikin Jawabin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na tunawa da waƙi'ar Shekaru Goma wanda ya gabatar bara.
“A irin wannan Tadhamuni da muke yi a daidai wannan lokaci duk shekara a ƙarshen watan Ramadan, (wannan ina gaya muku yanzu dayake mun wuce Ramadan ɗin) shekaru goma da s**a wuce sai ya faɗo a (25th July) don haka muke tunawa da shahidanmu na wannan rana, kwatsam ana cikin wannan kawai sai s**a bayyana s**a buɗe wuta, s**a kashe mana mutane kimanin mutum da muka tabbatar talatin da huɗu (34), mun san da talatin da biyu mutanenmu ne (har mun yi Jana'izarsu), to akwai kuma wani wanda yake shi Kirista ne ɗan Ƙabilar Igbo, mai suna “Jealous Anyewu”, wanda yana da 'Workshop' akan hanyar wurin, lokacin da ya ga ana buɗe wuta sai yaje ya yi magana da Sojojin, yace “Me ya sa ku ke buɗe ma waɗannan mutanen wuta? Yau shekara da shekaru suna yin wannan abin, kuma na san suna abinsu lafiya lau”.
“To bayan ya yi maganar ya dawo sai s**a bishi wajen 'Workshop' ɗin nasa kawai sai s**a je s**a buɗe masa wuta (nan take s**a kashe shi), to shi ne muka sanar talatin da uku, to sai daga baya kuma muka samu labarin akwai wani Yaro ma ana ce masa Abubakar a cikin gari, a unguwar Alƙali, shima ashe an kashe shi, yana koyon aikin kafinta a Sabon Gari, lokacin ana buɗe wuta sai Maigidansa yace gwara ka koma gida (akan hanyar komawa gidan ashe an harbe shi), to amma mu ba mu sani ba sai daga baya, daga baya ne s**a zo s**a ce ai akwai wani Yaro ma, amma sun ɗauke shi sun je sun yi jana'izarsa a cikin gari ɗin, to sai muka sanar cewa sun kashe mutane talatin da huɗu kenan.
“To, bayan nan sun yi yunƙurin za su ci gaba da kisa ɗin, domin talatin da huɗun nan da nake cewa, ba kawai ranar Juma'ar ne kawai aka kashe ba, akwai waɗanda aka kashe ranar Asabat, don ranar Asabat sun nufi Husainniyah kuma sun buɗe wuta, sun kashe waɗansu ƙarin mutane, sannan kuma ranar Asabat ɗin sun yi niyyar su tafi Gyallesu inda muke, to amma lokacin an riga an kira taron Ƴan Jaridu na ƙasa-da-ƙasa, wanda har Ƴan Jaridun ƙasashen waje sun zo, kuma Gyallesu ta cika maƙil da Mutane, don sun ɗauka za a yi Jana'izar Yarana guda uku da aka kashe, (su tun ranar Juma'a aka kashe su), to don haka ƴan'uwa da abokan arziki duk sun hallara da safe a ranar Asabat (sun ɗauka ranar ne za a yi Jana'iza ɗin), amma sai muka ce a'a ranar za mu Jana'izar wasu daga cikin Shahidan ne, su na su Yaranmu sai daga baya.
“Bisa gaskiya ma a lokacin Mahmud ne kawai yake tare da mu, wanda aka kashe shi ranar Juma'a kuma yana hannunmu, don an zo dashi gida ma bai cika ba, daga baya akan hanyar zuwa da shi Asibiti ya cika, a Husainiyya kenan tunda ba hanyar zuwa Asibiti Sojoji sun doɗe hanyoyin, to a nan ya cika. Amma su Ahmad dama sun tafi da su barikin soja ne sai daga baya muka samu labarin ashe sun kashe su, amma sun kai jikkunansu Asibiti bayan da s**a kashe ɗin, don har Hamid lokacin da aka kai su ma yana numfashi, (bai gama cikawa ba) don da s**a lura yana numfashi a mota sun caccaka masa wuƙa a kansa, amma duk da haka dai yana numfashin har ya zuwa lokacin da aka kai su Asibitin, s**a sa shi a 'Emergency' (wajen gaggawa kenan), daga baya ya cika.
“To, su a bisa gaskiya ba a kawo su ba sai ma ranar Asabat da yamma, koda s**a zo mutane suna tsammanin za mu yi jana'izar a lokacin, sai muka ce ai lokacin ma ba a kawo su ba, (sai bayan Isha'i aka kawo su) to amma ranar Asabat ɗin da yamma, mun yi Jana'izar wasu daga ciki, sai kuma ranar Lahadi ma muka sake Jana'izar wasu, su kuma su Ahmad aka yi Jana'izarsu su uku ranar Litinin.
“To, lokacin mun samu goyon baya zan ce ko Tadhamuni? Ainihin daga mutane daban-daban, Nahiyoyi daban-daban a nan ƙasar da waje, ta hanyar aiko da takardu na wasiƙun jaje da kuma waɗanda s**a riƙa zuwa da kansu, mun samu wannan aka yi ta tayi kwana da kwanaki, har muka ga abin ya yi nisa har an yi Arba'in, akwai lokacin da muka yi Arba'in. Arba'in ɗin su ya dace kuma da lokacin daidai da ainihin ranar haihuwar Imam Ridah (11 ga watan Zulqadah kenan), to lokacin muka yi Arba'in ɗin su, sai ta zama daidai lokacin da muka yi Arba'in ɗin su ya dace da ainihin haihuwar Imam Ridah har wasu sun zo daga Jamhuriyar Musulunci (Iran) akan sun zo saboda sanya Tutar Imam Ridah ne amma kuma sun samu Arba'in ɗin Shuhada ɗin.
“To, har bayan Arba'in mutane suna ta zuwa yi mana ta'aziyya, har ma akwai hotuna da ya nuna cewa waɗannan sun zo, waɗannan sun zo, har ana rana ta sittin mutane ba su daina zuwa ba, har ma muna ga da abin ya yi tsawo sai muka fara sauran harkokinmu, (zuwa karatuttukanmu) amma duk da haka mutane sun yi ta zuwa. An nuna mana goyon baya da kuma jaje ba kaɗan ba, wanda wala'alla ɗabi'ar mutanen ƙasar nan na cewa idan su a wurinsu shugaba Musulmi ne k**ar komai lafiya lau ne, ƙila domin lokacin Jonathan ne aka yi, don an yi mana a lokacin Ƴar'Aduwa a 2009, shi kuma lokacin da aka kashe su mutum biyu, Abdulrahman Isah, da Isah Muhammad, shima a ranar Qudus ɗin ne, to lokacin shi mutane ba su cika damuwa ba, amma lokacin Jonathan sai s**a nuna damuwa, musamman ma kashe Ƴaƴana uku.
“To sun ta nuna mana jaje kam, kusan kowa sai da ya yi jaje, har shima Shugaban kasa ɗin sai da ya bugo waya shi ma ya yi jaje, kodayake ya yi kalma irin yadda suke cewa a Ingilishin Nijeriya yake cewa 'Sorry' nake cewa to ai ba haɗari bane, da gangan ne Sojoji masu mak**ai ne s**a yi harbin, sai yace ai abin da yake nufi tunda ba za a iya dawo da ransu ba abin da zamu tabbatar shi ne mu tabbatar irin wannan bai auku ba, nace eh na ji, amma tunda yake Soja ne ya yi harbin, kuma da gangan ya yi ba kuskure bane, saboda haka ba yadda za a yi indai akwai doka a ƙasar nan ba zai yiwu ace ainihin k**ar haɗari ne ba, da mutuwa ne na haɗari to da sai ace wani abu, amma an kashe su ne da gangan, sai ma da aka ce musu “kune Ƴaƴan El-Zakzaky?” Su ka ce eh, su ka ce “to za mu kashe ku ne”, kuma fi'ilan abin da s**a yi kenan, to me ya rage kuma? Kuma ba wai sun sa uniform ɗin Soja bane, su Sojoji ne, kuma barikin Soja aka kai su, to amma dai duk da haka dai ya nace shi dai 'Sorry' dai irin wannan ba zai sake aukuwa ba, to shi kenan dai sai nace na gode da ta'aziyyar da aka yi mana, duk da na san cewa in ka ga abu an yi maka shiru kasan cewa wanda s**a sa ne s**a yi abin su.
“To sun so su ma su kawo hari a ranar Asabat, amma ganin Gyallesu ta cika maƙil da nutane, a lokacin Ƴan Jaridar ƙasa-da-ƙasa, da kuma wanda s**a zo suna tsammanin za a yi jana'iza ne a lokacin, sai ya zamana har sun kamo hanya amma sai s**a koma, ganin cewa in s**a zo Gyallesu sai dai in za su yi abin da ake ce ma kisan kiyashi ne, don mutane sun cika unguwar maƙil, to kuma ina jin sun samu masaniya cewa lallai indai ba za su zo su kashe dubban mutane ba (don abin da s**a so su yi kenan), to dai shi kenan, amma sun kashe mutane a Husainiyyah.
“To wannan abin da ya faru, na san ba ya ɓata ma mutane bane, don duk lokacin da wannan ya zo mukan ta tattaunawa dangane da abubuwan da s**a faru, waɗansu su bada ainihin labarin abin da ya faru ta nasu bangaren, musamman ɓangaren waɗanda abin ya rutsa da su kuma s**a rayu, su faɗi abin da s**a gani da abin da s**a ji wanda abin ya faru da su, an yi Interview da mutane daban-daban, an kuma sajjala, kuma duk shekara akan ƙara yi, a yi ta tattaunawa da mutane daban-daban, to wannan in za a tattara shi babban littafi ne, ko yanzu in mutum yana da sha'awar ya gani akwai shi an zuzzuba a Shafukanmu, ko a hotunan ABS, ko na YouTube, ko na waɗansu dai zai gansu duk an zuzzuba tattaunawa da mutanen da abin ya shafa daban-daban da yadda s**a ji abin, da yadda s**a ga abin, to wannan yana nan sajjale.
“To kuma duk shekara mukan yi tarurruka, akan yi lakcoci da kuma symposium da kuma abubuwa tamsiliyya, ga su nan abubuwa dai bukukuwan tun daga ranar 25 ɗin har waɗansu kwanaki, yakan zama musamman ma dayake akan ɗauki ƙarshen mako, k**ar yau 25 ɗin ta faɗo Alhamis ne, to amma kuma jibi Asabat duk akwai za a yi wannan bikin, za a yi gobe Juma'a ma, za kuma a yi ranar Asabat haka har zuwa Lahadi da safe, haka za a yi ta yi har ya zama sai wata shekara kuma, to waɗannan dai duk a cikin tunawa da abin da ya faru a waƙi'a ɗin ne.”
—Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a cikin jawabinsa na tunawa da waƙi'ar 25th, July Shekaru Goma.
— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky
https://www.cibiyarwallafa.org
29 Muharram 1447
25th July, 2025