10/09/2025
JAGORA (H) YA RUFE TARON MAKON HADIN KAN MUSULMI A ABUJA
*“Duk Wanda Aka Ji Yana Kira Ga Rarraban Kawukan Musulmi, Yana Ma Makiya Aiki Ne.”
*“Al’ummar Musulmi Abu Guda Ne, Kuma Daukakarsu Na Cikin Haduwarsu Ne.”
Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)
A yayin da yake gabatar da jawabin rufe taron Makon Hadin Kan Musulmi, wanda ya gudana a Abuja, a ranar Laraba 17 ga Rabi’ul Awwal, 1447, Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), wanda ya gabatar da jawabi ta hanyar bodiyo daga Iran, ya taya al’umma murnar zagayowar ranar haihuwar Manzon Rahma (S), wanda aka haifa a rana mai k**a ta yau, 17 ga Rabi’ul Auwal, shekara 1500 daidai da s**a gabata a Kidayar Kamariyya.
Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa, ruwayar da ta fi shahara ta haihuwar Manzon Rahma (S) it ace 12 ga watan Rabi’ul Auwal, ruwaya mafi inganci kuma ita ce 17 ga watan. “Don haka mukan dauki tsakanin wadannan ranaku biyun, - 12 zuwa 17 mu yi abinda mukan kira Makon Hadin Kai, wanda akan yi tarurruka daban-daban don a kusanto da juna tsakanin al’ummar Musulmi.”
Sayyid Zakzaky, ya bayyana wannan lokacin a matsayin lokaci mafi dacewa fiye da kowane lokaci a tarihi na bukatar hadin kan Musulmi. Yace: “Domin a wannan lokaci ne makiya addini s**a fito muraran, s**a nuna suna gaba da Manzon Rahma (S) ne, suna gaba da Alkur’ani ne, suna gaba da sakon da ya zo da shi ne, suna gaba da al’ummarsa ce, suna kuma kokari ne su ga sun share wannan al’ummar, sun share wannan sakon a doron kasa.”
Ya cigaba da cewa: “Makiya sun fito da maitarsu balo-balo, hatta kalmomin da da s**an boye, amma yanzu sun fito suna fadi. S**a fadi cewa ba su da makiyi illa Musulmi, kuma za su yi iyakan iyawansu ne su ga sun murkushe su, sun zama ba su da wani tasiri a duniya.”
Jagoran ya yi bayani akan yadda makiya addini daya-bayan-daya suke bi suna kokarin ruguza kasashen Musulmi. “Daga kasashen Musulmi akwai Libya, wanda sun wargazata, da kuma Lebanon wanda yanzu suke kokarin su fada cikinta, da Sudan wanda yanzu aka kai musu matsalar rarraba, da kuma Afganinstan da s**a je s**a yi biji-biji da ita, - da ita ma s**a fara. To kuma suna hankoron Syria da Iraq. Duk sun ayyana cewa sai sun kawar da wadannan kasashe, karshe kuma za su nufi Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Suna ganin in s**a gama da ita, k**ar sun gama da dukkanin al’ummun kenan.”
Ya kara da cewa: “Na’am, akwai Pakistan, da Indonesia, Malaysia, duk suna idanunsu, amma suna ganin wadancan kasashen su s**a fi zama ainihin kasashen da za su mutsittsika. Na ma tsallake muku Yeman, wanda a shekarun baya s**a dira a kanta, s**a dinga kisan ba jib a gani. Duk wannan aikinsu ne.”
Harwayau, Shaikh Zakzaky (H) ya bayyana yadda a daidai wannan lokacin dasisa da makircin da makiya addini s**a dinga yi na rarraba kawukan Musulmi ya fito fili fiye da kowane lokaci a tarihi. “A wannan lokaci ne ya fito balo-balo, ya nuna al’ummar Musulmi ashe akwai wadansu da suna ma makiya ne aiki. Balo-balo s**a fito suna marawa makiyan nan baya. Ba sai na baku misalai ba, wanda duk yake bin abinda ke gudana a duniyar nan, ya san abinda ke faruwa. Aka ga wasu mutane da s**a nuna balo-balo su ba al’ummar Musulmi ta dame su ba, su kujerun mulkinsu ya dame su, kuma su suna ma makiya ne aiki balo-balo.”
Jagora ya kara da bayyana wannan lokaci a matsayin lokacin da makiya s**a farwa al’ummar Musulmi na Palasdinu da kisan da ba a ga irinsa ba a tarihi. Yace: “Da can suna amfani da miyagun mak**ai na harbi da bindiga, s**a zo suna amfani da jiragen sama, s**a zo ba irin nau’in makamin da basu amfani da su akan al’umma wanda basu ji ba, ba su gani ba, maza, da mata da yara, galibansu mata da yara kanana, da ma jarirai.”
Ya bayyana sabon makamin da s**a canza wajen zaluntar Palasdinawa; “Yanzu sun zo da wani irin makami, shi ne a rutsa da mutane, a yunwatar da su, yunwar ta kashe su. Yanzu yunwa din ta zama makami da suke amfani da wajen kashe al’umma, galibansu jarirai wadanda akan haife su ya zama basu iya samun madara. Yanzu an hana mutane abinci, an hana musu magani, an hana musu ruwan sha, an hana musu wutar lantarki, an hana musu kuma mak**ashi k**ar mai da ire-irensu, an haramta musu komai, kuma an rutsa da su ana luguden wuta, kullu-yaumin ana kashe gomomi, har daruruwa ma wani lokacin, kuma galibansu mata da yara.”
Ya nuna takaicinsa akan yadda a sarari hukumomin Yammacin Duniya suke mara wa masu ta’asan bay aba tare da ko jin kunya ba, da kuma yadda ma’aikatansu na cikin al’ummar Musulmi suke nuna halin ko in kula akan lamarin. Yace: “Su da kansu sun fadi cewa, da ace al’ummar Musulmi za su zama al’umma daya, to da tuni sun mallaki wannan duniyar, don za su murkushe su ne gabadansu, saboda haka ba za su taba lamuncewa al’ummar Musulmi su zama abu daya ba.”
A nan ne ya yi kira da babban murya da cewa, mutum ya k**ata ya yi nazarin wa yake ma aiki? Yace: “Mun sha fada, mukan nanata, ba sau daya ba, ba sau biyu ba, cewa, duk wanda aka ji yana kira ga rarraban kawaukan Musulmi, ya yarda ko bai yarda ba, ya sani ko bai sani ba, yana ma makiya aiki ne. Ko ya yarda, ko kar ya yarda. Ko ya sani, ko kar ya sani, yana ma makiya aiki ne. Domin (kira ga rarraban Musulmi) aikin makiya ne, shirinsu ne rarraba din.”
Shaikh Zakzaky ya nuna takaicinsa akan yadda al’umar Musulmi s**a mai da abinda ya dame su shi ne abinda ya raba su, maimakon lura da abinda s**a hada su. Yace, ba mu ce ba abinda ya raba su ba. Inda ya bayyana al’ummar da Manzon Allah (S) ya koma ga Allah (T) ya barta dore akan addini, a matsayin wacce tata bamu gadon wasu abubuwa, daga ciki har da sabani akan shugabanci. Yace: “Ba a samu sabani akan matsayin Allah Ta’ala, da kasancewarsa Shi ne kadai abin bauta ba. Ba a samu sabani akan cewa Manzon nan shi ne Bawan Allah kuma Manzon Allah. Ba wani wanda yake kiranshi da ubangiji, ko dan ubangiji, ko daya daga wanda s**a taru s**a hadu s**a yi ubangiji. Har ma a Tashhud din mu, sai mun ambaci shi bawa ne, kafin mu ce shi Manzo ne. Kullum sai mun ce; ‘Wa ashhadu anna Muhammadan Abduhu wa Rasuluh.’ Saboda haka bamu da sabani kan matsayin Manzon Allah.”
Ya kara da cewa: “Kuma ba mu da sabani akan Alkur’ani. Duk da za ku ji zancen wawayen gari suna cewa akwai wasu masu Alkur’ani daban, amma fi’ilan dai Alkur’ani kwara daya ne, ba kari ba ragi.” Yace: “Amma al’umma ta saba akan fassaran Alkur’ani da kuma ruwayoyi. Don haka aka samu abinda ake ce ma Firka. An samu Firqoqi, an samu Mazhabobi, an samu Dariqoqi. Duk wannan a cikin addinin suke.”
Yace: “Duk lokacin da muke magana akan Firqa, ko Mazhaba, ko Darika, muna magana ne akan Juz’i (wato bangare). Amma in muka zo muna magana akan Musulunci, muna magana ne akan abinda ya dora akan duka wadannan. Shi Musulunci ne a sama. Su wadannan karkashin Musuluncin suke. Duk wanda ka ji yana rigima akan Firqa, to yana rigima akan bangare ne, ya bar tushe, ya bar asali yana magana akan reshe. Haka wanda yake rigima akan Mazhaba ko Darika, shi ma ya bar tushe ne ya koma reshe, don duk wadannan rassa ne… Da ma yanzu da ake yayin kungiyoyi. Dukkansu bangarori ne, ba su ne asasi ba, ba su ne kuma asali ba.”
Shaikh Zakzaky (H) ya jaddada cewa: “Mu muna magana akan asali ne. Sunanmu Musulmi, ba sunanmu wadannan rarrabe-rarrabenba, sunan al’ummarmu Musulmi. Shi ne Allah Ta’ala Yake cewa: “...هُوَ سَمَّاكُمُ الْمُسْلِمِينَ مِن قَبْلُ وَفِي هَٰذَا لِيَكُونَ الرَّسُولُ شَهِيدًا عَلَيْكُمْ وَتَكُونُوا شُهَدَاءَ عَلَى النَّاسِ ۚ...” Wato tun farko ma Shi Allah Ta’ala ne ya ambaci addinin babanku Ibraheem da Musulunci, da kuma a wannan lokacin wannan Manzon, domin ku zama shaida ga sauran al’ummu, kuma Manzo ya zama shaida akanku.”
Jagora yace, “Yanzu ana ta kiraye-kirayen sunannaki, da daukan kowane suna a matsayin shi ne ma addini, ai ta rigima akai, da kuma katangar karfen da aka sa a kwakwalwa, wanda babu katangar sam, ba ta da wujudi sam-sam, amma sai a kirkire ta a raba tsakanin al’umma, har mutum ya rika ganin cewa, wancan tsakaninsa da shi akwai shamaki, ra’ayinsu daban ne, fahimtarsu daban ne, har ma in ta yi k**ari ma sai yace addininsu daban ne. Alhali katanga aka saka masa a kwakwalwarsa, wadda ta fi katangar karfe karfi, saboda ta raba shi da dan uwansa Musulmi, alhalin addininsu guda.”
Yace: “Wannan lokacin da muke ciki, ba mu son ya zama sai makiya ne za su ingiza mu izuwa ga hadin kai, domin shi hadin kan nan a cikin addinin namu ne yake. Umurni ne na Allah Ta’ala; “Ku yi riko da igiyar Allah gabadayanku, kar ku rarraba.” Aka nuna illan rarraba tun a na farko. Sannan shi wannan Manzo (S) ya k**anta al’ummar Musulmi da misalin jiki guda, wanda idan wani bangare nasa ya yi ciwo, duk sauran bangarorin za su amsa da rashin bacci da kuma zazzabi. Idan aka taba wani bangare, duk gabadaya jiki ke amsawa. To haka al’ummar Musulmi suke, tamkar jiki guda ne.”
Shaikh Zakzaky ya bayyana wajabcin al’ummar Musulmi su hada kai su zama abu guda, da kuma haramci da munin rarrabuwa, wanda yace rarraba mummunan abu ne wanda zai kai ga mummunan natija. “Har wadanda ba suna addininmu ba ne, Allah Ya gaya mana cewa a hade suke wajen gaba da mu. “وَالَّذِينَ كَفَرُوا بَعْضُهُمْ أَوْلِيَاءُ بَعْضٍ ۚ إِلَّا تَفْعَلُوهُ تَكُن فِتْنَةٌ فِي الْأَرْضِ وَفَسَادٌ كَبِيرٌ” Yace, ‘Wadanda s**a kafirce tare suke sun damfaru da juna, in ku Muminai ba ku yi irin wannan ba (ku zama sashenku majibinta sashe ne), to za a samu fitina babba a doron kasa, da fasadi. Kuma yanzu abinda yasa duniya ta fada halin da take ciki kenan, saboda wadanda aka dora musu alhakin koyar da sauran al’umma sun raba kansu suna fada.”
Jagora ya bayyana cewa: “Ba mu da alami, wanda zai hada mu gabadayanmu ba tare da rarraba ba k**ar shi Manzon nan (S) da ya zo da addini. Shi ne Qudwa, shi ne abin koyi, shi ya zo da addini, shi ya aikata addini, ya dora mutane akan addinin, to wannan koyarwar na shi kan kansa, shi ne alami. Domin shi ne wanda za a gani a kwafa. Allah Ta'ala yana cewa: “لَّقَدْ كَانَ لَكُمْ فِي رَسُولِ اللَّهِ أُسْوَةٌ حَسَنَةٌ” Muna da kyakkyawan misali ga Manzon Allah (S), abin koyi ne shi wanda za a gani a kwafa. In muka sa Manzon Allah gabadayanmu a matsayin madubi wanda za mu kalla, mu yi koyi da shi, to duk za mu ga mun dunkule mun zama abu guda.”
Yace: “Yana da kyau mu fahimci cewa lallai hadin kan nan wajibinmu ne, kuma lallai shi ne karfinmu, shi ne daukakanmu, dolenmu ne mu yi, kuma bamu son ya zama makiyanmu ne za su tilastamu mu yi, za mu yi ne domin addininmu ne ya umurcemu da mu yi, domin in mun yi ibada ne. Saboda haka kira ga hadin kan al’ummar Musulmi shi ma ibada ne, wanda kuma duk ka ji yana kira zuwa ga rarraban al’ummar Musulmi, shi kuma yana fada da wannan Ibadan ne, yana kokarin ya rusa al’ummar ne.”
Jagora ya bayyana cewa, akwai wadanda duk yadda ake kira ga hadin kai, ba za su daina kira ga rarraba ba, saboda yin hakan sun dauke shi a matsayin kasuwanci ne da suke samu da shi. Yace: “Wadannan mutane ba za su cutar da mu da komai ba. Kamata ya yi wadanda suke kira ga haduwar al’umma din, su su tsaya wajen kira ga al’umma da haduwarta a aikace, ba kawai a zance ba. Domin haduwarmu a matsayinmu na al’ummar Musulmi, shi ne zai fitar da dukkanin al’umma (daga halin da take ciki).”
Jagora ya tabbatar da cewa, insha Allahul Azeem al’ummar Musulmi za su kasance al’umma daya. “Muna shekarun fata ne, ba muna shekarun rashin fata ba ne, muna fata Allah Ta’ala Ya gaggauta bayyanar wanda da bayyanarsa ne za a samu mafita. Domin mun san cewa alkawari ne Ya yi, kuma ba Ya saba alkawari. Lallai addinin nan zai dawo, kuma zai mallaki duniyar nan gabadayanta k**ar yadda ya mallaka”
“Allah Ta'ala Yana cewa:
وَعَدَ اللَّهُ الَّذِينَ آمَنُوا مِنكُمْ وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَيَسْتَخْلِفَنَّهُمْ فِي الْأَرْضِ كَمَا اسْتَخْلَفَ الَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ وَلَيُمَكِّنَنَّ لَهُمْ دِينَهُمُ الَّذِي ارْتَضَىٰ لَهُمْ وَلَيُبَدِّلَنَّهُم مِّن بَعْدِ خَوْفِهِمْ أَمْنًا ۚ يَعْبُدُونَنِي لَا يُشْرِكُونَ بِي شَيْئًا ۚ وَمَن كَفَرَ بَعْدَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْفَاسِقُون.“
Suratun Nuor, 55.
A ranar Juma’a da ta gabata 12 ga Rabi’ul Auwal 1447 ne Harkar Musulunci karkashin Jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ta fara gudanar da taron makon hadin kan Musulmi a garin Abuja. An tsawon kwanakin biyar a jere zuwa 17 ga watan, an saurari jawabai daga Malaman bangarori da darikokin Musulmi daban-daban daga sassan kasar nan, da s**a hada da da darikar Tijjaniyyah, da darikar Kadiriyya, da Ahlus-Sunnah, da kuma mabiya Mazhabar Ahlulbait (AS).
10/September/2025