Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky

Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky Shafin Cibiyar Wallafa Da Yada Ayyukan Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

SANARWA: Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)AN GA JINJIRIN WATAN SAFAR بسم الله الرحمن الرحيم وصلى الله على سيدنا م...
25/07/2025

SANARWA:

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

AN GA JINJIRIN WATAN SAFAR

بسم الله الرحمن الرحيم

وصلى الله على سيدنا محمد وآله الطيبين الطاهرين

Ya zuwa yanzu haka mun sami tabbacin ganin jinjirin watan Safar a Yabo da Sanyinna duk a Jihar Sakkwato da kuma Talata Mafara a Jihar Zamfara.

Don haka gobe Asabat ta zama 1 ga watan Safar 1447, in sha Allah.

Kada a manta da addu'o'i ma'thurai na watan Safar mai yawan nahisa. Allah Ta'ala ya kiyaye mu sharrukan da ke cikin kwanakin watan; Ya sadar da mu alheran da ke cikinsa.

Allah ya ba mu sa'a.

Wassalam


Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky


29/Muharram/1447
25/07/2025

25/07/2025

Video:

Sallah Da rakiyar Jana'izar su Shahid Ahmad, Hamid da Mahmud, 'ya'yan Shaikh Ibraheem Zakzaky da sojojin Nijeriya s**a kashe a ranar 25 ga watan Yulin 2014 a Zaria.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky
Www.cibiyarwallafa.org

Yau Juma'a 25/7/2025 yan uwa Musulmi almajiran Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) s**a gudanar da taron Zikira don tunaw...
25/07/2025

Yau Juma'a 25/7/2025 yan uwa Musulmi almajiran Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) s**a gudanar da taron Zikira don tunawa da Waki'ar Quds ta shekarar 2014 a garin Zaria.

Taron ya gudana ne a makabartan Shahidai da ke Darur Rahma, inda aka gabatar da addu'oi, jawabai, wakoki da faretin girmama Shahidan, su 33 da sojojin Nijeriya s**a kashe a lokacin mulkin Goodluck Ebele Jonathan.

Za a cigaba da tarurruka a wurare daban-daban don tunawa da Shahidan har zuwa ranar Lahadi.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky


25/07/2025

Video|

Waki'ar Quds ta shekarar 2014 a Zaria.

- Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky



ABUBUWAN DA S**A FARU A WAƘI'AR 25th JULY, 2014 A TAƘAICEDaga cikin Jawabin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na tunawa da waƙ...
25/07/2025

ABUBUWAN DA S**A FARU A WAƘI'AR 25th JULY, 2014 A TAƘAICE

Daga cikin Jawabin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) na tunawa da waƙi'ar Shekaru Goma wanda ya gabatar bara.

“A irin wannan Tadhamuni da muke yi a daidai wannan lokaci duk shekara a ƙarshen watan Ramadan, (wannan ina gaya muku yanzu dayake mun wuce Ramadan ɗin) shekaru goma da s**a wuce sai ya faɗo a (25th July) don haka muke tunawa da shahidanmu na wannan rana, kwatsam ana cikin wannan kawai sai s**a bayyana s**a buɗe wuta, s**a kashe mana mutane kimanin mutum da muka tabbatar talatin da huɗu (34), mun san da talatin da biyu mutanenmu ne (har mun yi Jana'izarsu), to akwai kuma wani wanda yake shi Kirista ne ɗan Ƙabilar Igbo, mai suna “Jealous Anyewu”, wanda yana da 'Workshop' akan hanyar wurin, lokacin da ya ga ana buɗe wuta sai yaje ya yi magana da Sojojin, yace “Me ya sa ku ke buɗe ma waɗannan mutanen wuta? Yau shekara da shekaru suna yin wannan abin, kuma na san suna abinsu lafiya lau”.

“To bayan ya yi maganar ya dawo sai s**a bishi wajen 'Workshop' ɗin nasa kawai sai s**a je s**a buɗe masa wuta (nan take s**a kashe shi), to shi ne muka sanar talatin da uku, to sai daga baya kuma muka samu labarin akwai wani Yaro ma ana ce masa Abubakar a cikin gari, a unguwar Alƙali, shima ashe an kashe shi, yana koyon aikin kafinta a Sabon Gari, lokacin ana buɗe wuta sai Maigidansa yace gwara ka koma gida (akan hanyar komawa gidan ashe an harbe shi), to amma mu ba mu sani ba sai daga baya, daga baya ne s**a zo s**a ce ai akwai wani Yaro ma, amma sun ɗauke shi sun je sun yi jana'izarsa a cikin gari ɗin, to sai muka sanar cewa sun kashe mutane talatin da huɗu kenan.

“To, bayan nan sun yi yunƙurin za su ci gaba da kisa ɗin, domin talatin da huɗun nan da nake cewa, ba kawai ranar Juma'ar ne kawai aka kashe ba, akwai waɗanda aka kashe ranar Asabat, don ranar Asabat sun nufi Husainniyah kuma sun buɗe wuta, sun kashe waɗansu ƙarin mutane, sannan kuma ranar Asabat ɗin sun yi niyyar su tafi Gyallesu inda muke, to amma lokacin an riga an kira taron Ƴan Jaridu na ƙasa-da-ƙasa, wanda har Ƴan Jaridun ƙasashen waje sun zo, kuma Gyallesu ta cika maƙil da Mutane, don sun ɗauka za a yi Jana'izar Yarana guda uku da aka kashe, (su tun ranar Juma'a aka kashe su), to don haka ƴan'uwa da abokan arziki duk sun hallara da safe a ranar Asabat (sun ɗauka ranar ne za a yi Jana'iza ɗin), amma sai muka ce a'a ranar za mu Jana'izar wasu daga cikin Shahidan ne, su na su Yaranmu sai daga baya.

“Bisa gaskiya ma a lokacin Mahmud ne kawai yake tare da mu, wanda aka kashe shi ranar Juma'a kuma yana hannunmu, don an zo dashi gida ma bai cika ba, daga baya akan hanyar zuwa da shi Asibiti ya cika, a Husainiyya kenan tunda ba hanyar zuwa Asibiti Sojoji sun doɗe hanyoyin, to a nan ya cika. Amma su Ahmad dama sun tafi da su barikin soja ne sai daga baya muka samu labarin ashe sun kashe su, amma sun kai jikkunansu Asibiti bayan da s**a kashe ɗin, don har Hamid lokacin da aka kai su ma yana numfashi, (bai gama cikawa ba) don da s**a lura yana numfashi a mota sun caccaka masa wuƙa a kansa, amma duk da haka dai yana numfashin har ya zuwa lokacin da aka kai su Asibitin, s**a sa shi a 'Emergency' (wajen gaggawa kenan), daga baya ya cika.

“To, su a bisa gaskiya ba a kawo su ba sai ma ranar Asabat da yamma, koda s**a zo mutane suna tsammanin za mu yi jana'izar a lokacin, sai muka ce ai lokacin ma ba a kawo su ba, (sai bayan Isha'i aka kawo su) to amma ranar Asabat ɗin da yamma, mun yi Jana'izar wasu daga ciki, sai kuma ranar Lahadi ma muka sake Jana'izar wasu, su kuma su Ahmad aka yi Jana'izarsu su uku ranar Litinin.

“To, lokacin mun samu goyon baya zan ce ko Tadhamuni? Ainihin daga mutane daban-daban, Nahiyoyi daban-daban a nan ƙasar da waje, ta hanyar aiko da takardu na wasiƙun jaje da kuma waɗanda s**a riƙa zuwa da kansu, mun samu wannan aka yi ta tayi kwana da kwanaki, har muka ga abin ya yi nisa har an yi Arba'in, akwai lokacin da muka yi Arba'in. Arba'in ɗin su ya dace kuma da lokacin daidai da ainihin ranar haihuwar Imam Ridah (11 ga watan Zulqadah kenan), to lokacin muka yi Arba'in ɗin su, sai ta zama daidai lokacin da muka yi Arba'in ɗin su ya dace da ainihin haihuwar Imam Ridah har wasu sun zo daga Jamhuriyar Musulunci (Iran) akan sun zo saboda sanya Tutar Imam Ridah ne amma kuma sun samu Arba'in ɗin Shuhada ɗin.

“To, har bayan Arba'in mutane suna ta zuwa yi mana ta'aziyya, har ma akwai hotuna da ya nuna cewa waɗannan sun zo, waɗannan sun zo, har ana rana ta sittin mutane ba su daina zuwa ba, har ma muna ga da abin ya yi tsawo sai muka fara sauran harkokinmu, (zuwa karatuttukanmu) amma duk da haka mutane sun yi ta zuwa. An nuna mana goyon baya da kuma jaje ba kaɗan ba, wanda wala'alla ɗabi'ar mutanen ƙasar nan na cewa idan su a wurinsu shugaba Musulmi ne k**ar komai lafiya lau ne, ƙila domin lokacin Jonathan ne aka yi, don an yi mana a lokacin Ƴar'Aduwa a 2009, shi kuma lokacin da aka kashe su mutum biyu, Abdulrahman Isah, da Isah Muhammad, shima a ranar Qudus ɗin ne, to lokacin shi mutane ba su cika damuwa ba, amma lokacin Jonathan sai s**a nuna damuwa, musamman ma kashe Ƴaƴana uku.

“To sun ta nuna mana jaje kam, kusan kowa sai da ya yi jaje, har shima Shugaban kasa ɗin sai da ya bugo waya shi ma ya yi jaje, kodayake ya yi kalma irin yadda suke cewa a Ingilishin Nijeriya yake cewa 'Sorry' nake cewa to ai ba haɗari bane, da gangan ne Sojoji masu mak**ai ne s**a yi harbin, sai yace ai abin da yake nufi tunda ba za a iya dawo da ransu ba abin da zamu tabbatar shi ne mu tabbatar irin wannan bai auku ba, nace eh na ji, amma tunda yake Soja ne ya yi harbin, kuma da gangan ya yi ba kuskure bane, saboda haka ba yadda za a yi indai akwai doka a ƙasar nan ba zai yiwu ace ainihin k**ar haɗari ne ba, da mutuwa ne na haɗari to da sai ace wani abu, amma an kashe su ne da gangan, sai ma da aka ce musu “kune Ƴaƴan El-Zakzaky?” Su ka ce eh, su ka ce “to za mu kashe ku ne”, kuma fi'ilan abin da s**a yi kenan, to me ya rage kuma? Kuma ba wai sun sa uniform ɗin Soja bane, su Sojoji ne, kuma barikin Soja aka kai su, to amma dai duk da haka dai ya nace shi dai 'Sorry' dai irin wannan ba zai sake aukuwa ba, to shi kenan dai sai nace na gode da ta'aziyyar da aka yi mana, duk da na san cewa in ka ga abu an yi maka shiru kasan cewa wanda s**a sa ne s**a yi abin su.

“To sun so su ma su kawo hari a ranar Asabat, amma ganin Gyallesu ta cika maƙil da nutane, a lokacin Ƴan Jaridar ƙasa-da-ƙasa, da kuma wanda s**a zo suna tsammanin za a yi jana'iza ne a lokacin, sai ya zamana har sun kamo hanya amma sai s**a koma, ganin cewa in s**a zo Gyallesu sai dai in za su yi abin da ake ce ma kisan kiyashi ne, don mutane sun cika unguwar maƙil, to kuma ina jin sun samu masaniya cewa lallai indai ba za su zo su kashe dubban mutane ba (don abin da s**a so su yi kenan), to dai shi kenan, amma sun kashe mutane a Husainiyyah.

“To wannan abin da ya faru, na san ba ya ɓata ma mutane bane, don duk lokacin da wannan ya zo mukan ta tattaunawa dangane da abubuwan da s**a faru, waɗansu su bada ainihin labarin abin da ya faru ta nasu bangaren, musamman ɓangaren waɗanda abin ya rutsa da su kuma s**a rayu, su faɗi abin da s**a gani da abin da s**a ji wanda abin ya faru da su, an yi Interview da mutane daban-daban, an kuma sajjala, kuma duk shekara akan ƙara yi, a yi ta tattaunawa da mutane daban-daban, to wannan in za a tattara shi babban littafi ne, ko yanzu in mutum yana da sha'awar ya gani akwai shi an zuzzuba a Shafukanmu, ko a hotunan ABS, ko na YouTube, ko na waɗansu dai zai gansu duk an zuzzuba tattaunawa da mutanen da abin ya shafa daban-daban da yadda s**a ji abin, da yadda s**a ga abin, to wannan yana nan sajjale.

“To kuma duk shekara mukan yi tarurruka, akan yi lakcoci da kuma symposium da kuma abubuwa tamsiliyya, ga su nan abubuwa dai bukukuwan tun daga ranar 25 ɗin har waɗansu kwanaki, yakan zama musamman ma dayake akan ɗauki ƙarshen mako, k**ar yau 25 ɗin ta faɗo Alhamis ne, to amma kuma jibi Asabat duk akwai za a yi wannan bikin, za a yi gobe Juma'a ma, za kuma a yi ranar Asabat haka har zuwa Lahadi da safe, haka za a yi ta yi har ya zama sai wata shekara kuma, to waɗannan dai duk a cikin tunawa da abin da ya faru a waƙi'a ɗin ne.”

—Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a cikin jawabinsa na tunawa da waƙi'ar 25th, July Shekaru Goma.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky
https://www.cibiyarwallafa.org


29 Muharram 1447
25th July, 2025

“Mu dai abinda muka sani, shaidawa da "La'ilaha illallah Muhammadur Rasulallah" shi ya maishe ka Musulmi, ba wani Kalmar...
18/07/2025

“Mu dai abinda muka sani, shaidawa da "La'ilaha illallah Muhammadur Rasulallah" shi ya maishe ka Musulmi, ba wani Kalmar Shahada ta daban. Amma Na'am, mun san cewa akwai Sunnan da Amerika ta kirkira, su ne masu kai h@re-hare da sunan addini, su ne su Boko Har@m, su ISIS, su waye da waye din nan, duk Amerika s**a yi su, suke kai h@re-hare da sunan Ahlussunnah. To sai kuma s**a ƙirƙiri wasu Shi'a.

“Su waɗannan Sunnan suna cewa Shi'a na zagin Sahabbai, suna auren Mutu'a. Su kuma wadannan Shi'an da Ingila ta kirkira kuma, su kuma sai suna zagin Sahabban. Wato abinda wadannan suke cewa ana yi, su kuma shi suke yi, har ma suna da Kalmar Shahadar wai shiga Shi'a. Har ma wasu da s**a zo nan, sai ake cewa ka shiga Shi'a ne?

“To mu kuma a iyakan saninmu ba a shiga Shi'a, in dama can kai Musulmi ne shikenan an gama. Abinda muke cewa shi ne, Annabi (S) ya ce, bayansa ga wadansu mutane a bi su. Mu abinda muka sani kenan. Saboda haka ba wani abu ne sabo ba. A'a, Annabi (S) ya yi wasiyya ya ce a bi wadannan mutanen (Ahlulbaiti (AS)? Eh. To shi ne kawai. Me s**a koyar? Ga koyarwar nasu. Shikenan zance ya kare (kai Shi'a ne in ka bi wasiyyar Annabi (S) din). Amma shiganka addini, furta La'ilaha ilallahu Muhammadur Rasulullah, shi kenan.

“Duk wanda ya ce, La'ilaha ilallahu Muhammadur Rasulullah, Musulmi ne, kuma ɗan uwanmu ne, ko da ya kafirta mu, mu ba za mu kafirta shi ba. Shi ya dauki laifin kafirta mu din, amma mu ba za mu ce mashi Kafiri ba, sai dai mu ce Jahilci ne ya kai shi ga hakan.”

— Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H).


Cibiyar Wallafa







18/07/2025

Bayyana Mutuwar Buhari A Watan Yuli:BITAN ABUBUWAN DA S**A FARU A WATAN YULI, 2019Daga Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Za...
14/07/2025

Bayyana Mutuwar Buhari A Watan Yuli:

BITAN ABUBUWAN DA S**A FARU A WATAN YULI, 2019

Daga Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky (H)

A yayin da aka bayyana mutuwar tsohon shugaban ƙasar Nijeriya, Janar Buhari a ranar 13 ga watan Yulin 2025, CIBIYAR WALLAFA DA YAƊA AYYUKAN SHAIKH ZAKZAKY (H) ta yi bitan wasu ta'addanci da gwamnatinsa ta yi ga 'yan uwa Musulmi almajiran Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), a irin wannan watan na Yuli a shekarar 2019, kimanin shekaru shida kenan da s**a gabata.

Bayan kisan ta'addanci da Buhari ya sa sojoji s**a aiwatar akan yan uwa Musulmi a Zaria a Disambar 2015, almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky sun rika Muzaharori don kira gare shi da ya saki Malaminsu, wanda yake tsare da shi tare da matarsa tun bayan harin da aka kai masa.

A wannan Muzaharorin kira a sake Malam Zakzaky din, Buhari ya rika ba jami'an tsaronsa umurnin kashe yan uwa Musulmi, inda s**a kashe mutane kusan 200 a Abuja, Kaduna, Kano da sauran biranen Nijeriya.

* 9 Yuli, 2019:

A ranar 9/7/2019 (6/11/1440H) ‘yan uwa almajiran Shaikh Zakzaky (H) s**a gudanar da gagarumar Muzaharar kira a saki Shaikh Ibraheem Zakzaky a gaban Majalisar Tarayya da ke Abuja.

Jami'an tsaron 'Yan sanda, bisa umurnin Janar Buhari, sun dira a kan 'yan uwan da harbi da harsasai masu rai, inda s**a Shahadantar da mutum biyu; Shahid Jafar Mika'il Lafia, da Shahid Mahmud Umar Sakafa, tare da jikkata da dama.

Yan sanda sun kuma k**a mutum 40 waɗanda sai bayan lokaci mai tsawo sannan kotu ta ba da belinsu.

* 11th Yuli, 2019:

Kwanaki biyu bayan wancan harin ta'addancin, a ranar 11 Juli, 2019 (da ta dace da 8 Zulka’adah, 1440H) jami'an tsaron Buhari s**a ƙara afkawar da Waki'o'i a Abuja da Kaduna. Inda yan sanda s**a dirarwa ‘yan uwa masu Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky a daidai Sakatariyan Gwamnatin Tarayya a Abuja, s**a jikkata da dama, s**a k**a ƙwarorin yan uwa.

A garin Kaduna kuwa a wannan ranar, 'yan sandan sun bude wuta ne sosai akan masu Muzaharar, inda s**a kashe yan uwa biyu; Shahid Ahmad Nasir Maraban Jos, da Shahid Abubakar Aliyu Badikko.

* 16th Yuli, 2019:

Bayan wancan harin da kwanaki biyar, a ranar 16/7/2019, gamayyar 'yan sanda da 'yan iskan gari s**a afkawa 'yan uwa masu Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky a Bypass, cikin garin Kaduna, s**a raunata mutum biyu, ɗaya a kafa, ɗaya harbi a kirji. Daga baya Allah Ya wa ɗaya daga wadanda raunata din mai suna Shahid Nura Lawal (Markaz) cikawa.

* 22nd Yuli, 2019:

Kwanaki shida bayan wannan kisan, a ranar wata Litinin 22/7/2019 da ta dace da 19 ga Zulka'ada 1440H, gamayyar jami'an 'yan sanda, Mopol, da DSS, bisa umurnin shugaban ƙasa Janar Buhari, s**a dira a kan 'yan uwa masu Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky a daidai Federal Sectariat, Abuja, inda s**a yi harbin ba ji ba gani, s**a kashe mutane fiye da 10.

Mutane shida aka iya samun gawarwakin su nan take, 'yan uwa s**a yi musu Jana'iza a kashe-garin ranar, aka bizne 5 daga cikinsu a makabarta Shahidai da ke Darur Rahma, sune;
Shahid Hamisu Ibrahim Magaji,
Shahid Husaini Yahya Soba,
Shahid Ali Haidar Ibrahim Rinji (An bizne shi a Rinji ne)
Shahid Dahiru Tudun Wada Kaduna,
Shahid Abubakar Isma'il Yola,
Shahida Batula Muhammad Dakwa Suleja.

A wannan ranar ta 22/7/2019, 'yan sanda sun kashe Mataimakin Kwamishinan 'yan sanda tare da wani dan Jaridar gidan Channels TV da bindiga, a ƙoƙarinsu na yin sharri ga 'yan uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H).

Sannan kuma sun k**a 'yan uwa maza kimanin 55 da mata shida, wanda s**a tsare su a Kurkukun Kuje da na Suleja, bayan sun tsare su a Hedikwatar SARS a Abuja, sai bayan shekaru shida, bai wuce wata guda da kotu ta wanke 'yan uwan daga tuhumomin da ake musu, ta sake su ba.

A wannan harin ta'addancin, jami'an tsaron Buhari sun je har asibiti a Gwagwalada, inda s**a sace marasa lafiya da gawarwakin wasu daga 'yan uwan da s**a harba s**a tafi da su. Wannan yasa aka kai ƙarar su kotu, akan kotun ta sa su bayar da gawarwakin da s**a sace. Kuma a wannan watan July din 2020, shekara guda kenan bayan sace sun, kotu ta tabbatar da hakan da 'yan sanda s**a yi ya sabawa ka'ida. Kuma ta yanke hukunci su maidawa 'yan uwa gawarwakin, sannan su biya diyyar naira miliyan 15 na gawarwakin da s**a sace.

* 26 Yuli, 2019:
Buhari Ya Haramta Harkar Musulunci:

Kwanaki hudu bayan wannan waki’ar, a ranar 26 Yuli, 2019 (daidai da 23 Zulka’adah, 1440H) sai gwamnatin Buhari ta fitar da sanarwar ta ayyana Harkar Musulunci a matsayin kungiyar Ta'addanci, kuma ta haramta ta a fadin tarayyar Nijeriya. Ko da yake gwamnatin ta sanar da hakan a manyan jaridun kasa ne a ranar 27/7/2019.

Ko da yake sun bayyana haramta wata ƙungiya ce mai suna IMN, amma a nufinsu Harkar Musulunci s**a haramta, don su samu lasisin cigaba da kashe 'yan uwa Musulmi bisa hujjar zalunci da haramcin da ko a dokar ƙasa har yau bai tabbata ba, b***e kuma a dokar Allah Ta'ala, Mahaliccin sammai da ƙasan da Ya tsara dokoki na gaskiya ga bayi.

* Tambaya:

Da me kuka fi tuna zaluncin tsohon shugaban ƙasa, Janar Buhari?

14/7/2025 (18 Almuharram 1447).



09/07/2025

Video| Babban darasin da za mu koya daga Waki'ar Ashura.

— Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) a ranar 9 ga Almuharram 1447, a gidansa da ke Abuja.


Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky





13/Al-Muharram/1447

WANI DARASIN DA WAKI’AR KARBALA KE KOYARWADaga bakin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)“Darasin da ke tattare da waƙi’ar...
08/07/2025

WANI DARASIN DA WAKI’AR KARBALA KE KOYARWA

Daga bakin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

“Darasin da ke tattare da waƙi’ar Karbala yana da yawan gaske, sai dai mu ɗauki wani janibi, saboda muna ɗan tunatar da junan mu ne kaɗan, mu bar wani janibin. A wannan lokaci namu, muna buqatar mu ɗauki darasin da ya auku a Karbala, wajen tunkarar zaluncin zamanin mu, domin ba ma’ana ga jin (tarihi) kawai, ka sha tarihi ka koka, shi kenan tarihi ya wuce, ba abinda ake nufi kenan ba, ana nufin kai ma ka lura ta ina ya shafe ka? Labari ake ba ka don ka ji kawai ko kuwa ya shafe ka?

“Mun san cewa; Imam Husaini (AS) ya sadaukar da ransa ne don ya ceci addinin nan, kuma ta nan ne ya nuna mana cewa ga inda addini yake, da ba don abinda ya yi ba, da ainihin mutane za su ɗauka inda sarauta take, a nan ne addini yake, mai mulki shi ke da addini, kuma shi ne za a bi, za a koma ‘Almulku Liman Qahara ne’, (Constitution ɗin Jahiliyya), in kai ka ke da iko, to kai za a bi, kuma kai ne addini.

“Wannan Manɗiƙin amawa kenan, har da malamansu, ko kwanakin nan ba ku ji suna wannan manɗiƙin a soshiyal midiya ba? (Suna cewa); “Idan wasu s**a fito s**a yi zanga-zanga, sun fita daga ɗa’ar Amir kenan, kuma in mutum ya fita daga ɗa’ar Amir ya halaka”. To kun ga manɗiƙinsu ne, da ainihin za a zauna ne akan wannan manɗiƙin, wanda yake cewa; duk wanda ake ce masa shugaba, to wajibin ka ne ka bi shi, in kuma ba ka bi shi ba, ka saba ma Allah.

“A wancan karon ina yi wa ‘yan’uwa bayani, nake cewa; ai kun ga Allah Ta’ala yana cewa; “Wa’aɗi’ullaha Wa’aɗi’ur Rasula Wa’ulul Amri Minkum”, sai s**a ce; ‘Ulul-Amri’, sune shuwagabanni, a bi Allah, a bi Manzo, a bi shuwagabanni?”. Sai muka ce; Eh, eh, eh, amma kuma Allah Ta’ala ya ce; “Ya Ayyuhallaziyna Amanut-taqullaha Wakuunu Ma’as-sadiqin”.

“To ina tambaya, su waɗannan shuwagabannin naku su ne sadiqin? Za su yi shiru. s**an ce; kai lallai wannan ko ya faɗi gaskiya ma sai dai sau ɗaya a cikin (magana) dubu, mugun maƙaryaci ne, na ce; to, ai ka ga Allah ya ce; “Kuunu Ma’as Sadiqina”, wane ne Assadiq? Sai ka ce; Alhaji wane, kai Alhaji wane akwai gaskiya, a ce Alhaji wane ne yake da gaskiya? To bari in kawo maka ƙaryarsa guda ɗari, sai ka ce; a’a, ba shi ba ne kenan, to wane kuma, sai ka ce shi ma ba ya ce kaza ba, kuma ƙarya ne? Sai ka ce; Eh haka fa.

“To wane ne mai gaskiya? Ai ka ga kaine ba ka san shi ba, da ba ka san Ulul-Amri ba, shi ya sa ba ka san Sadiqina ɗin ba. Ba yadda za a yi Allah Ta’ala ya ce maka; “Kuunu Ma’a haza”, wannan haza ɗin kuma ya batar da kai, ba yadda za a yi a ce maka; ka bi Ulul-Amri, Ulul-Amrin kuma su bayar da kai. Ku ba ku san su waye Ulul-Amri ɗin ba, wannan Ulul-Amri ɗin ne aka yanka a Karbala, Ulul-Amri ɗin ne ku ka yayyanka kafin yankan Karbala, ku ka kashe Ali, ku ka kashe Hassan, ku ka kashe Husaini. Ɗaya bayan ɗaya kuma ku ka riƙa kashe su, sune Ulul-Amri ɗin da aka ce a bi ɗin, sune kuma sadiqina ɗin.

“Na ga wani ɗan clip na wata ‘yar Tunusiya tana magana (abin ya ba ni sha’awa), ake tambayar ta; “Yanzu kina nufin ke kin zama Shi’a?” Ta ce; “Eh, kuma ni ban karanta Shi’a a littafin Shi’a ba, duk a littafin Sunna na gani, ashe ana ɓoye mana gaskiya ne, kuma gaskiyar na nan a ciki”, sai wannan mai tambayar nata yake ce mata; “To ba kuna cewa ainihin Limamanku Ma’asumai ne ba?” Ta ce; “Eh haka ne”, sai ya ce; “To ki gaya min wane ne Ma’asumin Limaminku a cikin shuwagabannin ƙasashen nan na yanzu?” Sai ta ce; “To ai ba ka gane ba ne, Ma’asuman su ne A’imma, (Imam Mahdi) ake nufi, shi ne Limamin shiriyar”. (Duk bayanan) suna nan a littafansu, ta ce; ita wallahi duk a littafin Ahlus-sunna ta gani, kuma haka ɗin ne, yana nan amma dai ba su faɗa ne, amma sun sani, yana nan a cikin littafinsu, ga waɗanda aka ce a bi, an ƙi a bi ne.

“To ainihin ba don sadaukarwar Imam Husaini (AS) ba, da a ce misali bai sadaukar ba, sai ya bi Sarki, shi kenan, da biyayya ga Sarki ya zama hujja, (kuma da) addini ya mutu murus. Da in ka ga abu ba daidai ba, in ka ce wannan ba daidai ba ne, za a ce; “A’a, ka fi Husaini ne? Da ya ga uwarbari me ya yi? Ya bi Sarki ne, saboda haka Sarakuna ake bi”. To sai ya zama yanzu tunda aka ba shi zaɓi tsakanin ko ya bi Sarki, ko kansa, sai ya ce ga kan, (ya miƙa kan aka cire)”.

—Ɓangaren Jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a ranar Ashura (10/Muharram/1446—2024) a Abuja

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky (H)




12/Muharram/1447
8th/July/2025

“Mutum ya tsaya ƙyam tsakani da Allah, ƙyam-ƙyam-ƙyam saboda Allah, ko me zai faru ya faru. Sadaukarwa saboda Allah, sab...
07/07/2025

“Mutum ya tsaya ƙyam tsakani da Allah, ƙyam-ƙyam-ƙyam saboda Allah, ko me zai faru ya faru. Sadaukarwa saboda Allah, saboda Allah, saboda Allah. Mu ɗauka ma kawukanmu wani alƙawari guda; mu ɗauka ma Imam Husaini (AS) alkawarin cewa abin nan da ya fito dominsa, za mu cigaba daga inda ya tsaya har ya zuwa bayyanar wanda da bayyanarsa ne za a samu mafita insha Allah, Allah Ya gaggauta bayyanarsa.”

— Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) yayin ganawa da ƴan'uwa ranar Asabar 9 ga Muharram 1447, a gidansa da ke Abuja.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky




11/Muharram/1447
7th/July/2025

“Duk wanda kuka gan shi yanzu yana mara ma azzalumai baya, in a wancan lokacin yake, wa zai mara ma? Azzalumai. Wanda ka...
07/07/2025

“Duk wanda kuka gan shi yanzu yana mara ma azzalumai baya, in a wancan lokacin yake, wa zai mara ma? Azzalumai. Wanda ka ga ya dake akan sai dai ko a kashe shi, amma ba zai bar tafarkin Allah ba, to irin shi ne zai bi Imam Husaini da ace ya zo a lokacinsa."

— Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) yayin ganawa da ƴan'uwa ranar Asabar 9 ga Muharram 1447, a gidansa da ke Abuja.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky




11/Muharram/1447
7th/July/2025

Ƙarin Hotunan Zaman Juyayin Ashura da Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar a gidansa, jiya Asabar 9 ga Almuharr...
06/07/2025

Ƙarin Hotunan Zaman Juyayin Ashura da Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar a gidansa, jiya Asabar 9 ga Almuharram 1447.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky
Www.cibiyarwallafa.org
#

Address

Fct Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky:

Share