12/06/2025
Wata gamayyar kungiya a jihar Zamfara ta kare Matawalle, ta ce faifan bidiyon da ke yawo yunkurin bata masa suna ne
Wata gamayyar kungiya mai son ganin an yi shugabanci na adalci ta fito karara tana kare tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Hon. Bello Matawalle, inda ta musanta bidiyon da ke yawo a kafafen sada zumunta, tana bayyana shi a matsayin na yaudara da ke da “rashin nasaba ta gaskiya”, tana kiran lamarin a matsayin yunkurin siyasar bata suna.
A cikin wata sanarwa da Shugaban Kungiyar, Kabir Ibrahim Bukuyum, ya fitar ranar Laraba, ya ce masu kira da a sauke Matawalle daga mukaminsa na watsi da irin rawar da ya taka kwanan nan a matakin kasa, da kuma gudunmuwarsa wajen dakile rikice-rikice a jihar Zamfara.
Matawalle, wanda ke aiki a karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na taka rawar gani wajen karfafa kokarin sojoji na yaki da ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda musamman a yankin Arewa maso Yamma.
Ya taka muhimmiyar rawa wajen tsara manyan ayyukan tsaro, hada kai tsakanin jami’an soja da na leken asiri na cikin gida, da kuma taimakawa wajen tura dakaru na musamman zuwa wuraren da ake fama da rikici.
“A karkashin jagorancinsa, an rushe da dama daga maboyar ‘yan ta’adda a jihohin Zamfara, Katsina da Kaduna, tare da kubutar da daruruwan mutane da aka yi garkuwa da su a hare-haren da ake ci gaba da kai wa.”
“Dabararsa ta tsunduma kai tsaye cikin lamarin — daga ziyarar filin daga zuwa tarurruka da manyan hafsoshin tsaro na shiyya — ya kawo sabon kuzari a kokarin yaki da ‘yan ta’adda.”
“A lokacin da yake Gwamnan Jihar Zamfara daga 2019 zuwa 2023, Matawalle ya karbi jihar da ke fama da rikici. Amma ta hanyar shirye-shiryen samar da zaman lafiya, tallafa wa jami’an tsaro da kayan aiki, da kuma kafa rundunar tsaro ta jihar, ya samu nasarori masu yawa.”
“Haka kuma ya hada kai da sarakunan gargajiya domin samar da aminci tsakanin al’umma — matakin da aka yaba da shi wajen inganta tattara bayanan sirri da hadin kai daga jama’a.”
“Baya ga amfani da mak**ai da dakaru, Matawalle ya fi mayar da hankali kan hanyoyin warware matsalar tsaro ta dogon lokaci. Gwamnatinsa ta zuba jari a fannin ilimi, inganta matasa da ci gaban fasaha domin magance tushen matsalolin da ke haifar da tashin hankali a yankunan karkara.”
Bukuyum ya ce ikirarin da ke cikin bidiyon da ke yawo — wanda ke nuna cewa wai Matawalle na zargin al’umma da haddasa rashin tsaro — na karkata daga gaskiyar abin da ya fada da irin salon shugabancinsa.
Kungiyar ta bayyana cewa kalmar da Ministan ya fada cewa “Allah kawai zai iya taimakawa yanzu” kalma ce da ke nuni da bukatar hadin kan kowa, ba fassarar faduwar gwiwa ba.
“A kowace kasa mai da’a,” in ji Bukuyum, “ana auna ministoci bisa aikin da s**a yi, ba a kan bidiyo da aka kitsa domin bata suna ba.”
A cewarsa, idan za a yi hukunci bisa wannan mizanin, to tarihin aiki da nasarorin da Matawalle ya samu a Zamfara da ma fadin Nijeriya sun isa su kare shi daga duk wani yunkurin bata masa suna.