Maibiredi Tv

Maibiredi Tv Domin kawo maku rahotanni akan al'amurran yau da kullum.
(1)

za ku iya kiranmu a +2348069807496 ko ku biyo mu a Whatsapp Channel ta wannan rariyar liƙau: https://whatsapp.com/channel/0029VanmLGu2Jl86PakU7U3G

Ba a taba Gwamnan da ya yi abin azo-a-gani kan Matsalar Tsaron Zamfara Kamar Dauda ba-Sanusi LalanKarin bayani https://y...
12/06/2025

Ba a taba Gwamnan da ya yi abin azo-a-gani kan Matsalar Tsaron Zamfara Kamar Dauda ba-Sanusi Lalan

Karin bayani https://youtu.be/AK1AxKXSUTI

Tv

Duk matsin ds Yan Nigeria s**a samu kansu a Mulkin Dimukaradiya ya fi Mulkin Soja- Activist Muhammad Lawal Gusau https:/...
12/06/2025

Duk matsin ds Yan Nigeria s**a samu kansu a Mulkin Dimukaradiya ya fi Mulkin Soja- Activist Muhammad Lawal Gusau

https://youtu.be/J_xsaViS0Ac

Tv

HOTUNA: Yadda faɗuwar jirgin saman Indiya ta kacace wasu gine-gine.Jirgin ya faɗo ne a kan hanyarsa ta zuwa Landan jim k...
12/06/2025

HOTUNA: Yadda faɗuwar jirgin saman Indiya ta kacace wasu gine-gine.

Jirgin ya faɗo ne a kan hanyarsa ta zuwa Landan jim kaɗan bayan ya tashi daga birnin Ahmedabad.

June 12: Matawalle ya yaba wa Shugaba Tinubu a matsayin gwarzon sabuntawa da inganta dimokradiyyaMinistan kasa a ma'aika...
12/06/2025

June 12: Matawalle ya yaba wa Shugaba Tinubu a matsayin gwarzon sabuntawa da inganta dimokradiyya

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Mohammed Matawalle, ya yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin fitila mai haskakawa da inganta sabuwar dimokradiyya, yana masa kallon jagora mai hangen nesa da kishin sauya halin da kasar ke ciki.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis domin bikin Ranar Dimokradiyya, Matawalle ya jinjina wa rawar da Shugaba Tinubu yake takawa wajen ci gaban dimokradiyya a Nijeriya.

Ya bayyana gwagwarmayar da Shugaba Tinubu ya dade yana yi don kafuwar dimokradiyya da kuma zabensa a matsayin shugaban kasa na biyar tun bayan dawowar mulkin farar hula, a matsayin alamar ni’ima daga Allah da kuma kwarin guiwa a siyasa.

"Gwagwarmayarka don dawo da mulkin dimokradiyya a Nijeriya da kuma yadda ka kai ga zama shugaban kasa na nuna cewa akwai albarka ta Ubangiji a bisa hangen nesanka da juriya," in ji Matawalle.

Ya kara da cewa tarihi zai tuna da Shugaba Tinubu bisa irin kudurinsa da matsayinsa na daukar manyan matakai, wadanda ke mayar da Nijeriya kan turbar samun kima a nahiyar Afrika.

Yayin da Nijeriya ke cika shekara 26 da mulkin dimokradiyya ba tare da katsewa ba, Matawalle ya jaddada irin nasarorin da Shugaba Tinubu ya samu karkashin tsare-tsaren Renewed Hope, musamman a fannin tsaro.

Ya yaba wa himmar gwamnatin wajen yaki da matsalar tsaro ta hanyar Renewed Hope Legacy Project, wanda ya ce yana hada manyan hanyoyin tattalin arziki a tsakanin shiyyoyi shida na kasar.

“A bangaren tsaro, ka kawo amfanin dimokradiyya ta hanyar daidaito da ayyuka masu tarihi — inda mutane yanzu ke iya yin tafiya daga Abuja zuwa Kaduna, Zamfara da Katsina ba tare da tsoron sace su ba, sabanin yadda aka saba a mulkoki da s**a gabata,” in ji shi.

“Daidaituwar ku don kawar da matsalar tsaro a Nijeriya na zama tubalin gina cigaban tattalin arziki da hadin kan kasa mai dorewa.”

Ministan ya kuma yaba da yadda hadin kai ke karuwa tsakanin bangarorin gwamnati na zartarwa, majalisa da shari’a, yana danganta hakan da irin salon shugabanci na Shugaba Tinubu.

A cewar Matawalle, wannan gwamnati ta kawo sabon zamani na sabunta dimokradiyya, inda hukumomi ke aiki tare don gina kasa, ba tare da la’akari da kabila, addini ko matsayin rayuwa ba.

Najeriya Ba Za Ta Zama Ƙasa Mai Jam’iyya Ɗaya Ba – Shugaba TinubuShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa ba zai ...
12/06/2025

Najeriya Ba Za Ta Zama Ƙasa Mai Jam’iyya Ɗaya Ba – Shugaba Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa ba zai bari Najeriya ta koma ƙasa mai jam’iyya ɗaya ba a zamaninsa.

Yayin da yake jawabi ga zaman haɗaka a Majalisar Tarayya a ranar Alhamis domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Shugaba Tinubu ya kore raɗe-raɗin da ƴan jam’iyyun adawa ke yi na iƙirarin mayar da Najeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya.

Yayin da yake bada amsa kan tsoron yan adawa na yadda ake tururwae dawowa jam’iyyar APC, Shugaba Tinubu ya ce jam’iyyar APC za ta aikata “babban kuskuren siyasa” idan ta hana ’yan jam’iyyun adawa shigowa cikin jam’iyyar.

Ya ce, “Najeriya ba za ta zama ƙasa mai jam’iyya ɗaya ba. Wannan ba zai faru ba. Amma za mu aikata laifin siyasa idan muka rufe ƙofofin ga waɗanda ke son shiga APC.”

Idan ba a manta ba, manyan yan adawar Gwamnatin Shugaba Tinubu sun cika kafafen yaɗa labarai da cewa ana ƙoƙarin mayar da Najeriya ƙasa mai jam’iyya daya, lamarin da Gwamnatin ta bayyana a matsayin ruɗewar yan adawa duba da yadda suke rasa mabiya suna dawowa jam’iyyar APC.

A kwana-kwanan nan an samu dawowar Gwamnoni masu ci, Yan Majalisun Dokoki da Majalisar Dattawa daga sassa daba daban na ƙasar zuwa Jam’iyyar APC daga wasu jam’iyyun adawa dake ƙasar.

12/06/2025

Yadda Shugàban Karamar Hukumar Karim Lamido Dake Jihar Taraba Ya Durkusa Yana Roko Al'ummar Garin Da Su Yi Hakuri Su Daina Rìķicin Kabilancì

Wata gamayyar kungiya a jihar Zamfara ta kare Matawalle, ta ce faifan bidiyon da ke yawo yunkurin bata masa suna neWata ...
12/06/2025

Wata gamayyar kungiya a jihar Zamfara ta kare Matawalle, ta ce faifan bidiyon da ke yawo yunkurin bata masa suna ne

Wata gamayyar kungiya mai son ganin an yi shugabanci na adalci ta fito karara tana kare tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Hon. Bello Matawalle, inda ta musanta bidiyon da ke yawo a kafafen sada zumunta, tana bayyana shi a matsayin na yaudara da ke da “rashin nasaba ta gaskiya”, tana kiran lamarin a matsayin yunkurin siyasar bata suna.

A cikin wata sanarwa da Shugaban Kungiyar, Kabir Ibrahim Bukuyum, ya fitar ranar Laraba, ya ce masu kira da a sauke Matawalle daga mukaminsa na watsi da irin rawar da ya taka kwanan nan a matakin kasa, da kuma gudunmuwarsa wajen dakile rikice-rikice a jihar Zamfara.

Matawalle, wanda ke aiki a karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na taka rawar gani wajen karfafa kokarin sojoji na yaki da ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda musamman a yankin Arewa maso Yamma.

Ya taka muhimmiyar rawa wajen tsara manyan ayyukan tsaro, hada kai tsakanin jami’an soja da na leken asiri na cikin gida, da kuma taimakawa wajen tura dakaru na musamman zuwa wuraren da ake fama da rikici.

“A karkashin jagorancinsa, an rushe da dama daga maboyar ‘yan ta’adda a jihohin Zamfara, Katsina da Kaduna, tare da kubutar da daruruwan mutane da aka yi garkuwa da su a hare-haren da ake ci gaba da kai wa.”

“Dabararsa ta tsunduma kai tsaye cikin lamarin — daga ziyarar filin daga zuwa tarurruka da manyan hafsoshin tsaro na shiyya — ya kawo sabon kuzari a kokarin yaki da ‘yan ta’adda.”

“A lokacin da yake Gwamnan Jihar Zamfara daga 2019 zuwa 2023, Matawalle ya karbi jihar da ke fama da rikici. Amma ta hanyar shirye-shiryen samar da zaman lafiya, tallafa wa jami’an tsaro da kayan aiki, da kuma kafa rundunar tsaro ta jihar, ya samu nasarori masu yawa.”

“Haka kuma ya hada kai da sarakunan gargajiya domin samar da aminci tsakanin al’umma — matakin da aka yaba da shi wajen inganta tattara bayanan sirri da hadin kai daga jama’a.”

“Baya ga amfani da mak**ai da dakaru, Matawalle ya fi mayar da hankali kan hanyoyin warware matsalar tsaro ta dogon lokaci. Gwamnatinsa ta zuba jari a fannin ilimi, inganta matasa da ci gaban fasaha domin magance tushen matsalolin da ke haifar da tashin hankali a yankunan karkara.”

Bukuyum ya ce ikirarin da ke cikin bidiyon da ke yawo — wanda ke nuna cewa wai Matawalle na zargin al’umma da haddasa rashin tsaro — na karkata daga gaskiyar abin da ya fada da irin salon shugabancinsa.

Kungiyar ta bayyana cewa kalmar da Ministan ya fada cewa “Allah kawai zai iya taimakawa yanzu” kalma ce da ke nuni da bukatar hadin kan kowa, ba fassarar faduwar gwiwa ba.

“A kowace kasa mai da’a,” in ji Bukuyum, “ana auna ministoci bisa aikin da s**a yi, ba a kan bidiyo da aka kitsa domin bata suna ba.”

A cewarsa, idan za a yi hukunci bisa wannan mizanin, to tarihin aiki da nasarorin da Matawalle ya samu a Zamfara da ma fadin Nijeriya sun isa su kare shi daga duk wani yunkurin bata masa suna.

12/06/2025

From Federal ministry of information & national orientation

12/06/2025

Ƙaramin Sani Ƙuƙumine Saƙo Zuwa Wannan Kiristan Allah Yabaka Ikon Karɓar Gaskiya

� New to streaming or looking to level up? Check out StreamYard and get $10 discount! �

DA ƊUMI-ƊUMI:🔥 Soji sun kāshe shugaban ƴan ta’adda Auta da wasu da dama a wani samame a ZamfaraDakarun Operation Forest ...
12/06/2025

DA ƊUMI-ƊUMI:🔥 Soji sun kāshe shugaban ƴan ta’adda Auta da wasu da dama a wani samame a Zamfara

Dakarun Operation Forest Yaƙi (OPFY) sun samu gagarumar nasara a ci gaba da ayyukan yaki da ta’addanci a Jihar Zamfara, inda s**a káshe sanannen shugaban ‘yan ta’adda mai suna Auta, tare da wasu daga cikin yaransa a wani samame na musamman da s**a kai.

Bayanan sirri da aka samu sun shaida wa Zagazola Mak**a cewa wannan samame ya gudana ne a ranar 10 ga Yuni, a yankin Ƙunchin Kalgo da ke cikin Gundumar Ƙunchin Kalgo, Karamar Hukumar Tsafe - A wajen samamen, an hallaka wasu manyan ‘yan ta’adda da aka tantance sunayensu da Abdul Jamilu da Salisu, tare da Auta.

Dakarun sun fafata da ‘yan ta’addan cikin zafafan harbe-harbe, inda s**a samu galaba s**a kuma kashe su. Sai dai har yanzu ba a gano inda wani shugaban ‘yan ta’adda mai suna Babaye da wani abokin aikinsa da ba a tantance ba suke ba, duk da cewa rahotanni daga yankin na nuna cewa su ma wata kila sun mutu a harin da aka kai.

A wani cigaba a lamarin, Sale Ado Madele, wanda aka fi sani da Sarki kuma ɗan fari ga sanannen jagoran ‘yan ta’adda Ado Alieru, ya tsere daga harin ta hanyar fakewa a gonaki. Shaidu daga yankin sun bayyana cewa tserewarsa ta samu ne a lokacin da manoma ke aiki a gonakinsu, lamarin da ya ba shi damar sulalewa ba tare da an k**a shi ba.

Karin bayanai daga majiyoyi na sirri sun nuna cewa ‘yan ta’addan da ke aiki a yankin Ƙunchin Kalgo sun hada kai da magoya bayansu domin gudanar da bincike kan inda Babaye da sauran da ba a gano su ba s**a shiga. Majiyoyin cikin gari sun bayyana cewa akwai tashin hankali sosai a tsakanin ‘yan ta’addan, sak**akon yawan asarar da suke fuskanta a ‘yan kwanakin nan.

Wannan samame ya zo ne kwana guda bayan wata nasarar farmaki da dakarun soji s**a kai a ranar 9 ga Yuni, a wani gidan mai da ke Danjibga, inda aka kashe kimanin ‘yan ta’adda goma da ake zargi da shirin kai hari, ƙarƙashin jagorancin wani Dogo Sule da aka kashe. Daya daga cikin gawarwakin, an ce an binne shi ne a makabartar Danjibga, ƙarƙashin jagorancin wani Alhaji Hamza MKO, wanda Dogo Sule ya tuntuba domin gudanar da jana’izarsa.

Ana samun Karuwar masu yunkurin kashe kan su a Jihar Zamfara.Jiya ma wani ma'aikacin Gidan Yari (Correctional Service of...
12/06/2025

Ana samun Karuwar masu yunkurin kashe kan su a Jihar Zamfara.
Jiya ma wani ma'aikacin Gidan Yari (Correctional Service officer) Mai Babban mukami na CCA wato Chief Correctional Assistant Abdullahi Nura dake aiki a Gidan Yari na Gusau yayi yunkurin kashe kanshi amma cikin taimakon Allah an ceto shi Bai mutu ba.

Wani bayani daga Gidan Yarin Mai dauke da SA hannun Mai magana da hukumar Gidan Yarin ASC1 Mustapha Abubakar yace da safiyar jiya Laraba Sai da Abdullahi Nura yaje Wurin aiki, Sai Kuma ya fita ya hau kabu kabu aka kaishi Dam din Baga na Hanyar Wanke, kawai sai yayi Tuma ya fada a cikin Ruwan. Nan take Dan Kabu-Kabun yayi gudu ya shaidawa ma'aikatan Wurin inda s**a kokari matuka s**a ceto shi.

KO da aka fito da shi Yana sanye da Uniform din shi waton Kayan aiki da I.D Card din shi sai aka kai shi Asibiti inda yanzu haka yake karbar Magani.

Har yanzu ba a San Dalilin Shi ba.

A.B.Kaura

Danfulani ya jagoranci taron manyan jami’an hukumar NAIC don taimaka wa manufar 'Renewed Hope Agenda' ta Shugaba TinubuA...
12/06/2025

Danfulani ya jagoranci taron manyan jami’an hukumar NAIC don taimaka wa manufar 'Renewed Hope Agenda' ta Shugaba Tinubu

A wani yunkuri na sake daidaita harkokin Hukumar Inshorar aikin Noma ta Nijeriya NAIC da manufar "Renewed Hope Agenda" na Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, Manajan Daraktar hukumar Alhaji Yazid Shehu Umar Danfulani, ya jagoranci wani muhimmin taro da manyan jami’an hukumar.

An gudanar da taron ne a hedikwatar NAIC da ke Abuja, inda aka tattauna hanyoyin da za a bi wajen bunkasa hukumar da kuma kara tasirinta a cikin bangaren noma na kasar.

Shugaban hukumar gudanarwar hukumar NAIC, Dr Aliyu Bello, shi ma ya halarci taron, inda ya gana da tawagar manyan jami'an gudanarwa na hukumar.

Tawagar ta hada da Mr Abubakar Umar Jarengo, Daraktan Ayyuka; Prince Babaranti Ayandayo Rasheed, Daraktan Gudanarwa da Kudi; da kuma Mrs Florence Onwuanuokwu, Babbar Manaja mai kula da inshora.

Bisa bayanan da aka fitar, babban abin da aka mayar da hankali a kansa a yayin taron shi ne yadda za a inganta yadda hukumar NAIC ke gudanar da ayyukanta, kara yawan manoman da ke amfani da inshora, da kuma tallafa wa kokarin Gwamnatin Tarayya na sauya fasalin harkokin noma a Nijeriya.

Danfulani ya sake jaddada kudirin hukumar na cika aikinta yadda ya k**ata, inda ya ce NAIC dole ne ta zama ginshiki a yunkurin Nijeriya na cimma isasshen abinci da ingancin tattalin arziki.

Shi ma shugaban hukumar gudanarwar NAIC, Dr Bello, ya yaba da hangen nesa da jajircewar manyan jami’an gudanarwar, tare da nuna kwarin guiwa cewa za su iya aiwatar da sauye-sauyen da s**a dace da muradun kasa.

An kammala taron da sabon alkawari na bin hanyoyin kirkire-kirkire, gaskiya da rikon amana, da kuma kara hada kai da masu ruwa da tsaki domin daga martabar NAIC zuwa mataki mafi girma.

Address

Oranti Plaza Eastern Bypass Opposite Salbas (MAIGORO) Filling Station Gusau
Abuja
632101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Maibiredi Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Maibiredi Tv:

Share

Category