Maibiredi Tv

Maibiredi Tv Domin kawo maku rahotanni akan al'amurran yau da kullum.
(2)

za ku iya kiranmu a +2348069807496 ko ku biyo mu a Whatsapp Channel ta wannan rariyar liƙau: https://whatsapp.com/channel/0029VanmLGu2Jl86PakU7U3G

Nijeriya na buƙatar haɗin kai yanzu fiye da kowane lokaci – Ministan Yaɗa LabaraiMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ...
11/08/2026

Nijeriya na buƙatar haɗin kai yanzu fiye da kowane lokaci – Ministan Yaɗa Labarai
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga 'yan Nijeriya da su ɗaukaka tunanin su sama da bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa, su haɗa kai wajen yaƙi da rashin tsaro da sauran ƙalubalen da ke fuskantar ƙasar.

Idris ya yi wannan kiran ne a ranar Talata, a wajen taron ƙasa da ƙasa mai taken “Bambance-bambance da Zaman Lafiyar Al'umma: Haɗin Gwiwa don Kyakkyawar Makoma,” wanda ƙungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS) ta shirya tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (Muslim World League) a Abuja.

Ministan ya ce bambance-bambancen mutanen da s**a halarci taron ya nuna cewa akwai fahimtar juna cewa tsaro, zaman lafiya da wadata a Nijeriya sun dogara ne da yadda 'yan ƙasa za su yi aiki tare ba tare da la'akari da bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa ba.

Idris ya ce: “Dukkan mu muna buƙatar mu haɗa kai, mu yi tunani a matsayin 'yan Nijeriya, mu yi tunani a matsayin 'yan'adam, kuma mu yi aiki tare ba tare da la'akari da bambance-bambancen mu ba, domin mu kasance tsintsiya maɗaurin ki ɗaya.”

Ya jaddada cewa rarrabuwar kawuna bisa addini da ƙabila za ta ƙara dagula yaƙi da rashin tsaro, yana mai kira ga 'yan Nijeriya da su yi watsi da tashin hankali, rashin haƙuri da ƙoƙarin amfani da bambance-bambancen ƙasar nan wajen raba kan al'umma.

“Babu lokacin bambance-bambance. Idan a yayin yaƙin da muke yi da rashin tsaro muka bari bambance-bambancen addini s**a shiga, hakan zai ƙara dagula matsalar. Buƙatar da muke da ita ta haɗa kan mu a matsayin al'umma ɗaya na da matuƙar muhimmanci,” inji shi.

Idris ya fayyace cewa ba Gwamnatin Tarayya ce ta shirya taron ba, sai dai ya ce gwamnati tana maraba da shirye-shiryen da ke inganta tattaunawa tsakanin mabiya addinai, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

“Idan muna son ci gaba da tafiya zuwa ga wadata, dole ne dukkan mu mu yi tunani da aiki tare, mu kuma haɗa kai a matsayin al'umma ɗaya,” inji ministan.

Ya ce yawan al'ummar Nijeriya, muhimmancin ta da kuma tasirin ta na nufin zaman lafiya da kwanciyar hankalin ƙasar na da matuƙar tasiri ga Afirka da ma sauran sassan duniya.

“Nijeriya ƙasa ce mai matuƙar muhimmanci. Ƙasa ce mai mutane sama da miliyan 230. Zaman lafiya da kwanciyar hankali a nan na nufin zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk faɗin Afirka, har ma da duniya baki ɗaya,” inji shi.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a taron, ya isar da saƙon aniyar Shugaban Ƙasa ta tabbatar da ingantaccen tsaro mai ɗorewa, haɗin kan ƙasa da haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa, yana mai cewa Nijeriya za ta ci gaba da aiki tare da abokan hulɗar ta na ƙasa da ƙasa wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Babban Sakataren Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya kuma Shugaban Ƙungiyar Malaman Musulunci ta Duniya, Sheikh Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa, ya buƙaci 'yan Nijeriya da su kare haƙƙin ɗan'adam da s**a yi tarayya a cikin ta, tare da yin watsi da ƙoƙarin amfani da addini, ƙabila ko talauci wajen raba kan ƙasa.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa'ad Abubakar III, ya yi kira da a ci gaba da tattaunawa, tsare gaskiya da ƙara ƙaimi wajen aiwatar da hanyoyin magance ƙalubalen Nijeriya, tare da kira ga 'yan Nijeriya da su sake gina amana da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin mabiya addinai.

A nasa jawabin, Shugaban jam'iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya buƙaci 'yan Nijeriya da su ɗauki bambance-bambancen ƙasar a matsayin tushen ƙarfi maimakon rarrabuwar kai, yana mai cewa duk da cewa 'yan Nijeriya suna gudanar da ibada ta hanyoyi daban-daban, suna da buri da ƙalubale iri ɗaya.

Shugaban JIBWIS na Ƙasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau, ya yi kira da a ƙara haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, ƙungiyoyin addini da al'ummomi wajen yaƙi da rashin tsaro, tare da ƙara zuba jari a fannin ilimi da bunƙasa ƙwarewa domin rage yiwuwar matasa su rungumi tsattsauran ra'ayi ko kuma a ɗauke su aikin laifi.

Daga cikin waɗanda s**a halarci taron akwai Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu; Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani; Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi; Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum; Ministan Bunƙasa Kiwo, Idi Mukhtar Maiha; Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa'ad Abubakar III; Shugaban APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda; Sheikh Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa; Shugaban JIBWIS na Ƙasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau; Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Nijeriya (NSCIA), da sauran manyan jami'an gwamnati, shugabannin addinai da na gargajiya, jami'an diflomasiyya, wakilan ƙungiyoyin fararen hula da sauran manyan baƙi.

11/08/2026

“President Bola Ahmed Tinubu is manifesting his good intentions for the people of the Southeast.”

— Senator Engr. David Nweze Umahi, CON, FNSE, FNATE
Honourable Minister of Works
❤️👌👍👏

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da Kotun Laifukan Talla domin ƙarfafa tsarin gudanar da harkar tallaGwamnatin Tarayya ta ƙ...
11/08/2026

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da Kotun Laifukan Talla domin ƙarfafa tsarin gudanar da harkar talla

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da sabuwar Kotun Laifukan Talla, a wani mataki na ƙarfafa tsari da sa ido kan harkar talla, inganta ƙwarewa da tabbatar da bin ƙa'ida a masana'antar talla da sadarwar kasuwanci a Nijeriya.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Talata a wurin ƙaddamar da kotun a Abuja, yana mai bayyana kafa kotun a matsayin wani muhimmin mataki wajen gina masana'antar talla mai ƙwarewa da ɗaukar nauyi.

Ya ce: “Mu gina masana'antar talla da za ta yi fice wajen ƙirƙire-ƙirƙire, ta samu amincewar jama'a kuma ta kiyaye ɗaukar nauyi."

Ministan ya ce Dokar Majalisar Kula da Harkokin Talla ta Nijeriya (ARCON) mai lamba 23 ta shekarar 2022 ta faɗaɗa ikon hukumar na tsarawa da sa ido kan harkar talla, tare da tanadar da kafa kotun domin sauraron laifukan da s**a shafi dokar da kuma ƙa'idoji da dokokin da s**a shafi harkar talla.

Ya buƙaci sabuwar kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Cecilia M. A. Olatoregun, da ta gudanar da ayyukant ta cikin gaskiya, 'yanci da adalci.

A cewar sa, “Duk wata shari'a da aka gabatar a gaban ku, ku duba ta bisa hujjojin da ke cikin ta, ba tare da tsoro ko nuna son kai ba, ko ƙauna ko ƙiyayya. Dole kotun ta kasance, kuma a gan ta a matsayin hukuma mai adalci da rashin nuna son kai."

Idris ya taya shugabar da sauran membobin kotun murna, tare da tabbatar masu da ci gaba da goyon bayan ma'aikatar ga ARCON da ƙoƙarin gina masana'antar talla da za ta iya yin gogayya a duniya.

Tun da farko, Darakta-Janar na ARCON, Dakta Olalekan Olumuyiwa Fadolapo, ya bayyana ƙaddamar da kotun a matsayin wani babban mataki wajen ƙarfafa tsari da bin ƙa'idoji a masana'antar talla.

“Kotun Laifukan Talla wata babbar dama ce ga masana'antar talla ta Nijeriya. Ita ce irin ta ta farko a duniya, domin Nijeriya ta ɗauki matakin hangen nesa, ba wai kawai wajen kafa dokoki kan harkar talla ba, har ma da samar da tsare-tsare da tsarin gudanarwa,” inji Fadolapo.

Shugabar Kotun Laifukan Talla, Mai Shari'a Cecilia M. A. Olatoregun, ta yi alƙawarin cewa sabuwar kotun za ta gudanar da ayyukan ta cikin gaskiya, adalci da ƙwarewa.

“Babban abin alfahari ne a kira mu domin yi wa ƙasar mu hidima, kuma mun ɗauki wannan nauyi da muhimmanci sosai. An buƙace mu da yin aiki cikin gaskiya, kuma wannan shi ne abin da za mu yi,” inji ta.

Membobin kotun sun haɗa da Musa Ahmed Attah, SAN; Merga Tyowanan Kachina, Esq.; Dakta Ken Onyeali Ikpe, FRPA; da Hajiya Sa’a Ibrahim, RPA.

Daga cikin waɗanda s**a halarci taron akwai Babbar Sakatare ta Ma'aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Binyerem Ukaire; Darakta mai kula da Sadarwar Jama'a da Wayar da Kai na Ƙasa, Henshaw Ogubike; Daraktan Hulɗa da Jama'a da Ƙa'idojin Gudanarwa, Dakta Suleiman Haruna; da Mataimaki na Musamman kan Harkokin Gudanarwa ga Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Sunday Baba, da sauran manyan baƙi.

Allah Ya Yi Wa Tsohon Ɗan Wasan Barkwanci, Sani Tumbuleƙe Rasuwa
11/08/2026

Allah Ya Yi Wa Tsohon Ɗan Wasan Barkwanci, Sani Tumbuleƙe Rasuwa

11/08/2026

Live streaming of Aliyu Ibrahim

11/08/2026

Al'ummar Gwaram da ke ƙaramar hukumar Talata Mafara na cigaba da zanga-zanga sak**akon musgunawa da s**a ce Askarawa (Yan Maiduguri) na yi masu in sun shigo garin Jangebe

DSS ta saki kafintan da aka k**a bisa zargin hannu a sace daliban Oyo sanan ta bashi diyyar Naira miliyan 3Hukumar tsaro...
11/08/2026

DSS ta saki kafintan da aka k**a bisa zargin hannu a sace daliban Oyo sanan ta bashi diyyar Naira miliyan 3

Hukumar tsaro ta farin kaya ta Najeriya (DSS) ta saki wani kafinta mai suna Mustapha Marwana, bayan bincike ya tabbatar da cewa ba shi da hannu a satar ɗalibai da malamai da aka yi a jihar Oyo.

Marwana, wanda aka haifa a Katsina, an k**a shi ne bisa zargin yana da alaƙa da harin da ’yan ta’addan Ansaru s**a kai wasu makarantu a Oriire, inda aka sace ɗalibai 39 da malamai bakwai.

Bayan gudanar da cikakken bincike, wani kwamiti na DSS ya gano cewa babu wata hujja da ke nuna Marwana ɗan ƙungiyar Ansaru ne ko kuma yana da hannu wajen tallafa mata ko gudanar da ayyukanta.

Saboda haka, Darakta-Janar na DSS, Tosin Ajayi, ya bayar da umarnin a sake shi tare da ba shi Naira miliyan 3 a matsayin tallafin diyya domin taimaka masa wajen komawa rayuwarsa da sana’arsa.

An saki Marwana ga lauyansa, Oghene Forgive, wanda ya yaba da matakin DSS na tabbatar da rashin laifin wanda yake karewa.

Harin na Oriire ya faru ne a ranar 15 ga Mayu, inda aka sace mutane 46, sannan aka kashe biyu daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su kafin a kuɓutar da sauran a ranar 10 ga Yuli ta hanyar wani samame na sojoji.

Lawal Woos Investors to Zamfara, Highlights Opportunities in Mining, Agriculture, EnergyZamfara State Governor, Dauda La...
11/08/2026

Lawal Woos Investors to Zamfara, Highlights Opportunities in Mining, Agriculture, Energy

Zamfara State Governor, Dauda Lawal, has called on local and foreign investors to take advantage of the vast investment opportunities available in the state, particularly in mining, agriculture, renewable energy and information technology.

According to a statement signed by the Director-General of Media and Communications to the Governor, Mal. Nuhu Salihu Anka, Lawal made the call while participating in a high-level Nigeria-Canada summit focused on leveraging digital technology for economic growth and sustainable development.

The governor, who was among the prominent speakers at the summit, used the occasion to showcase Zamfara’s investment potential and encourage businesses and investment groups to explore opportunities across various sectors of the state’s economy.

Lawal identified the state’s mineral resources as a major area with potential to drive industrial development and create employment, stressing the need for increased exploration, value addition and investment in the sector.

He also highlighted agriculture and agro-processing as key investment opportunities, citing Zamfara’s vast arable land and the potential to strengthen agricultural production, processing and supply chains linking farmers to markets.

On energy, the governor said the state had significant potential for solar and other clean-energy solutions that could expand electricity access while supporting industries, businesses and communities.

He further described information and communication technology as an important pillar of the state’s economic development strategy, noting its potential to create jobs and open new opportunities for young people.

Lawal said participation in international economic platforms such as the Nigeria-Canada summit provided Zamfara with an opportunity to present its investment prospects to global investors and explore partnerships capable of accelerating the state’s economic development.

He assured potential investors that his administration would continue to strengthen policies and create an enabling environment to attract investment and facilitate ease of doing business in Zamfara.

11/08/2026

Al'ummar Gwaram da ke ƙaramar hukumar Talata Mafara na cigaba da zanga-zanga sak**akon musgunawa da s**a ce Askarawa (Yan Maiduguri) na yi masu in sun shigo garin Jangebe

Za mu kawo maku cikakkiyar hirarmu da su akan abin da ya sa su Zangar-zangar

11/08/2026

Duk Tsohon Dan APC yana da kurji da yadda gwamna Dauda Lawal ke nunawa Ɓangaren Matawalle da Yari ba kowa ne ba- Anas Abdullahi Kaura jigo a APC

Address

Oranti Plaza Eastern Bypass Opposite Salbas (MAIGORO) Filling Station Gusau
Gusau
632101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Maibiredi Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Maibiredi Tv:

Shortcuts

Share

Category