Rariya

Rariya Rariya jarida ce a harshen Hausa domin kawo labaran cikin gida Nijeriya da ma duniya baki daya da k*m
(372)

Mutanen Arewa Za Su Sake Zabar Tinubu Saboda Ayyukan Da Ya Yi Wa Yankin, Cewar Fa’izu Alfindiki
11/05/2026

Mutanen Arewa Za Su Sake Zabar Tinubu Saboda Ayyukan Da Ya Yi Wa Yankin, Cewar Fa’izu Alfindiki

ZABEN 2027: Ko Wannan Hadin Ya Yi?
11/05/2026

ZABEN 2027: Ko Wannan Hadin Ya Yi?

BABBAR NASARA: Sojojin Nijeriya Sun Haĺĺaka ’Yan Bìdiga 70 A Shiroro Dake Jihar Neja..Sun Musanta Kàśhe Fararen HulaRund...
11/05/2026

BABBAR NASARA: Sojojin Nijeriya Sun Haĺĺaka ’Yan Bìdiga 70 A Shiroro Dake Jihar Neja
..Sun Musanta Kàśhe Fararen Hula

Rundunar Tsaro ta Kasa (DHQ) ta kare harin sararin samaniya da dakarun soji s**a kai a Karamar Huk*mar Shiroro da ke Jihar Neja, inda ta ce harin ya dira ne kai tsaye a sansanonin ’yan bindiga, ba fararen hula ba.

Sanarwar, wadda Daraktan Yada Labarai na Rundunar, Manjo Janar Michael Onoja ya fitar, ta ce an kai harin ne biyo bayan bayanan sirri da aka samu kan taruwar miyagun a kauyen Lukupe ranar 9 ga watan Mayun 2026.

Rundunar ta bayyana cewa dakarun sojin kasa masu sarrafa jiragen yaki marasa matuki (UAV) ne s**a kaddamar da harin tsakanin karfe 11:59 na daren Asabar zuwa karfe 6:00 na safiyar Lahadi, 10 ga watan Mayu.
Wuraren da harin ya shafa sun hada da kauyukan Katerma, Bokko, Kusasu da Kuduru

Sojoji sun bayyana cewa a kauyen Kusasu kadai, an yi nasarar hallaka akalla ’yan bindiga 70, yayin da sauran s**a tsere a kan babura zuwa yankin Zango.

Duk da koke-koken da wasu mazauna yankin ke yi na cewa bama-baman sun fada gidajensu, musamman a unguwar Guradnayi, rundunar tsaron ta ce bayanan da take da su ba su nuna hakan ba.

Rundunar ta ce galibin mazauna wadannan kauyuka tuni s**a kaurace wa gidajensu zuwa garin Sarkin Pawa saboda gudun hare-haren ’yan bindiga, don haka wuraren da aka kai harin sansanonin bata-gari ne kawai.

"Rundunar soji za ta ci gaba da aiki don kakkaba sansanonin ’yan bindiga da nufin dawo da zaman lafiya a yankin Shiroro da sauran sassan jihar." — Maj. Gen. Onoja

A karshe, rundunar ta yi kira ga jama'a da kafafen yada labarai da su guji yada labaran da ba a tantance ba, wadanda za su iya jefa mutane cikin fargaba ko k*ma su kawo cikas ga ayyukan tsaro da ake gudanarwa.

Babu Wani Hari Da Jami'anmul S**a Kai Kan Farar Hula A Neja, Inji Rundunar Sojojin Nijeriya
11/05/2026

Babu Wani Hari Da Jami'anmul S**a Kai Kan Farar Hula A Neja, Inji Rundunar Sojojin Nijeriya

11/05/2026

Mutum Biyar Ba Farko Su Duba 'Comment Section'

Yadda Huk*mar Alhazai Ta Jihar Kano, Ta Gudanar Da Bitar Aikin Hajji A Sansanin Maniyata Dake Kano, Domin Kara Wayar Da ...
11/05/2026

Yadda Huk*mar Alhazai Ta Jihar Kano, Ta Gudanar Da Bitar Aikin Hajji A Sansanin Maniyata Dake Kano, Domin Kara Wayar Da Mahajjatan Kan Yadda Za Su Gudanar Da Hajji A Ilmance

Gwamnatin Jihar Katsina A Karkashin Jagorancin Gwamna Dikko Raɗɗa Ta Bayar Da Sama Da Naira Biliyan Uku Domin Tabbatar D...
11/05/2026

Gwamnatin Jihar Katsina A Karkashin Jagorancin Gwamna Dikko Raɗɗa Ta Bayar Da Sama Da Naira Biliyan Uku Domin Tabbatar Da Cewa Jihar Ba Ta Rasa Adadin Kujerun Aikin Hajjin Da Aka Ware Mata Ba, Tare Da Aiwatar Da Wasu Muhimman Tsare-tsare Da S**a Baiwa Jihar Damar Samun Kujerun Maniyyata 2,035.

11/05/2026

Gwamna Abba Kabir Adalin Shugaba Ne, Inji Dan Takarar Majalissar Tarayya Na Gwarzo/Kabo A Jam’iyyar APC, Hon Fahad Dankabo

Nijeriya Da Maroko Za Su Kulla Yarjejeniya A Fannin Makamashi, Noma Da Kuma Harkokin CinikayyaAlaƙar diplomasiyya tsakan...
10/05/2026

Nijeriya Da Maroko Za Su Kulla Yarjejeniya A Fannin Makamashi, Noma Da Kuma Harkokin Cinikayya

Alaƙar diplomasiyya tsakanin kasashen Najeriya da Maroko ta kara nuna ƙarfafa, inda kasashen biyu s**a kulla yarjejeniyar karfafa dangantaka a fannonin makamashi, noma, da k*ma harkokin cinikayya.

Wannan sanarwa ta fito ne bayan wata tattaunawa da aka yi tsakanin Ministar Harkokin Wajen Najeriya, Bianca Ojukwu, da takwaranta na kasar Maroko, Nasser Bourita.

Babban kashin bayan tattaunawar shi ne aikin ginin bututun iskar gas na Najeriya da Maroko (African Atlantic Gas Pipeline). Ministocin biyu sun bayyana wannan gagarumin aiki a matsayin "mai canza alkiblar tattalin arziki" wanda zai samar da tsaro a fannin makamashi da k*ma dunkulewar yankin Afirka ta Yamma baki daya.

Ma’aikatar Harkokin Wajen ta tabbatar da cewa tuni kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) da takwaransa na kasar Maroko (ONHYM) s**a kammala binciken fasaha na aikin. Ana sa ran Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Sarki Mohammed VI za su sanya hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin a rubuce kafin karshen rubu'i na hudu na wannan shekara.

Baya ga batun iskar gas, kasashen biyu sun tattauna hanyoyin hadin gwiwa wajen sarrafawa da rarraba takin zamani. Wannan mataki na da nufin tabbatar da wadatar abinci ba kawai a kasashen biyu ba, har ma da sauran sassan nahiyar Afirka.

Domin farfado da tsoffin yarjejeniyoyin da aka kulla tun zamanin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2018, Najeriya na shirin karbar bakuncin taron hadin gwiwa na kasashen biyu (Bilateral Joint Commission) karo na biyu.
Haka zalika, ministocin sun jaddada bukatar sake kafa Majalisar Kasuwanci ta Najeriya da Maroko. Sun bayyana cewa yarjejeniyar cinikayya ta bai-daya ta nahiyar Afirka (AfCFTA) da k*ma shirin kauce wa biyan haraji ninki biyu, za su bude sabbin kofofin bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu.

10/05/2026

A Cikin Irin Ayyukan Raya Kasa Da Shugaba Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Yake Aiwatarwa A Jihar Jigawa, Wanda Tafiyar Siyasar Tinubu Rumfa-Rumfa Ke Gabatarwa A Karƙashin Jagorancin Shugabanta, Alhaji Mahmud Abdullahi Sheriff

Ku Tabbata Kun Zaɓi Jam'iyyar APC Tun Daga Sama Har Ƙasa A Yayin Zaɓen 2027, Saƙon Gwamna Abba Ga KanawaKanawa me za ku ...
10/05/2026

Ku Tabbata Kun Zaɓi Jam'iyyar APC Tun Daga Sama Har Ƙasa A Yayin Zaɓen 2027, Saƙon Gwamna Abba Ga Kanawa

Kanawa me za ku ce?
......................TALLA..........
‎Ku sauke manhajar AREWA TOPUP domin siyan Data akan farashi mai sauki da rahusa.

Kamfanin AREWA TOPUP yana rab0n kudi ₦150,000 ga mutum 10 na farko masu yawan amfani dashi a duk karshen wata.

Wanda yazo na fark0 zai sami kyàútàr̃ ₦50,000, wanda yazo na biyu ₦30,000, na uku ₦20,000, na hudu ₦15,000, sannan na biyar ₦10,000. Daga mutum na 6 zuwa na 10, kowane mutum zai sami ₦5,000. Daga mutum na 10 zuwa na 20, suna mayar dasu cikin jerin Top Users wadanda za'a ragewa farashin DATA.

Indai kana sayar da DATA wacce ta kai ta ₦10,000 za ka iya kasancewa daya daga cikin wadanda za su mori wannan garabasa ta "Top Users"

‎Ku sauke app din AREWA TOPUP yanzu ku more wannan garabasa.

Play store.
👇👇👇👇👇👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.toparewanet.app

App store.
👇👇👇👇👇👇
https://apps.apple.com/ng/app/arewa-topup-cheap-data/id6758279366

Address

Abuja

Telephone

+2347045480959

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rariya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share