Rariya

Rariya Rariya jarida ce a harshen Hausa domin kawo labaran cikin gida Nijeriya da ma duniya baki daya da k*m
(343)

Kashim Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Taron Majalisar Dinkin Duniya A Birnin New YorkMataimakin Shugaban Ƙ...
20/09/2025

Kashim Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Taron Majalisar Dinkin Duniya A Birnin New York

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, zai jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 da za a gudanar a birnin New York, da ke Amurka, daga ranar Litinin 22 ga Satumba zuwa Lahadi 28 ga watan.

Wannan na zuwa ne bisa umarnin Shugaba Bola Tinubu, k**ar yadda mai taimaka masa na musamman kan yaɗa labarai, Stanley Nkwocha, ya bayyana a wata sanarwa a Abuja.

A cewar sanarwar, Shettima zai halarci taron murnar cika shekara 80 da kafuwar Majalisar Ɗinkin Duniya a ranar Litinin 22 ga Satumba, sannan daga ranar Talata 23 zuwa Lahadi 28 zai shiga tattaunawar manyan shugabanni a zauren babban taro.

Haka k*ma, a ranar Laraba 24 ga Satumba ne zai gabatar da jawabin ƙasa na Najeriya tsakanin ƙarfe 3 zuwa 9 na dare agogon New York.

Bugu da ƙari, Shettima zai shiga taro na musamman kan sauyin yanayi da Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya zai jagoranta a ranar 24 ga Satumba, inda Najeriya za ta sanar da sabbin manufofin ta bisa yarjejeniyar Paris.

Haka k*ma zai halarci taron manyan shugabanni kan samar da gidaje masu araha da shugaban Kenya zai shirya.

Bayan kammala taron Majalisar, Shettima zai zarce Frankfurt a ƙasar Jamus domin ganawa da jami’an Deutche Bank kafin ya dawo gida Najeriya.

20/09/2025

Rahoto Na Musamman Kan Yadda Tallafin Bashin Karatu Na NELFUND Ke Taimakawa Dalibai Masu Karamin Kàrfi A Manyan Makarantun Nijeriya

Har Yanzu Ina Kan Neman Mijin Aure Jama'a, Cewar Faizat Mahmood Eggi
20/09/2025

Har Yanzu Ina Kan Neman Mijin Aure Jama'a, Cewar Faizat Mahmood Eggi

An Sake Yin Zaman Sulhu Ďa Ýan Bìndiga A Kananan Huk*momin Sabuwa, Dandume Da Faskari Dake Jihar Katsina A Yau AsabarDag...
20/09/2025

An Sake Yin Zaman Sulhu Ďa Ýan Bìndiga A Kananan Huk*momin Sabuwa, Dandume Da Faskari Dake Jihar Katsina A Yau Asabar

Daga Mukhtar Lawan Liver Gwarzo

Me Ya Sa Har Yau (Dr) Rarara Bai Yi Wa Kashim Shettima Waka Ba?Daga Ali Abba Aji GetznerDa zanga Rarara ido da ido zan s...
20/09/2025

Me Ya Sa Har Yau (Dr) Rarara Bai Yi Wa Kashim Shettima Waka Ba?

Daga Ali Abba Aji Getzner

Da zanga Rarara ido da ido zan so yi masa wata tambaya a matsayina na matsoyin Alangubro Kashim Shetima.


Tambayar ita ce:

Rarara ya yi wa 'yan siyasa daga matakin sama har zuwa kasa, k**ar shugaban kasa, matar shugaban kasa, yaron shugaba kasa.

A bar ma maganar wadannan sun girma, ya yi wa gwamnoni zuwa kasa har matan gwamnoni.

Amma ban taba ganin Rarara ya yi wa Kashim Shettima waka ba, ko a cikin waka bai taba k**a sunan sa ba a matsayin sa na 002 a Nijeriya.

Ko me dalili.

Zan so na yi masa wannan tambayar na ji amsar da zai ba ni, kar na yi masa hukunci da zuciya ta ko abin da muke zarginsa.

SIYASA DA KULAWA: Cikin iKon Allah Yau Hon Hassan Shakara Ya Aurar Da Wasu Daga Cikin Mabiyansa, Sannan Ya Jagorance Su ...
20/09/2025

SIYASA DA KULAWA: Cikin iKon Allah Yau Hon Hassan Shakara Ya Aurar Da Wasu Daga Cikin Mabiyansa, Sannan Ya Jagorance Su Zuwa Wajen Yin Walima Sanye Da Tufafi Iri Daya

Wannan yana cikin irin kulawar da ake so mai gidan Siyasa yana yiwa masoyinsa.

Daga Safiyanu Musa Birkandy

Sak**akon Rayuwar Dàmfara Da  Sowore  Ya Dade Yana Yi Ne Da Sunan Ķàŕyar Kare 'Ýañci  Ita Çe Ke Bibiyar Sa, inji Hadimin...
20/09/2025

Sak**akon Rayuwar Dàmfara Da Sowore Ya Dade Yana Yi Ne Da Sunan Ķàŕyar Kare 'Ýañci Ita Çe Ke Bibiyar Sa, inji Hadimin Wike

Babban Mataimaki na Musamman kan Huldar Jama’a da Kafafen Sada Zumunta ga Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, Lere Olayinka, ya ce ɗan gwagwarmayar da ya ɗora wa kansa suna k*ma mai gidan Jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore, yana tsoron “innuwar zambarsa,” inda ya bayyana zargin da ya yi cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Minista Wike suna shirin kashe shi a matsayin “wani wasa da kwakwalwa da yake yi domin ci gaba da rayuwar zamba.”

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Olayinka ya ce ya k**ata Sowore ya fuskanci shari’arsa ta laifi, ya k*ma shirya kawo hukuncin kotun da ya nuna cewa an taɓa yanke wa Shugaba Tinubu hukunci, idan har yana so ya kare maganarsa marar tushe.

Kakakin Ministan ya ƙara da cewa:
“Mutum irin Sowore, wanda ya karɓi sama da dala miliyan uku a 2019 domin sayar da takarar gwamna na jam’iyyar African Action Congress (AAC) a Jihar Rivers, sannan jam’iyyar ta dakatar da shi kan rashawa, dole ne ya san cewa yana da tarin waɗanda ya ci amana waɗanda za su iya bibiyar shi.”

Olayinka ya tuna cewa a shekarar 2020, Sowore ya fuskanci zargi daga Oluwatosin Adeniji kan yin amfani da sunanta ya nemi tallafin kuɗin ba tare da saninta ba sannan ya ci gaba da amfani da kuɗin.

“Daga 2016 zuwa 2019, Sowore ya karɓi sama da dala miliyan 1.3 daga MacArthur Foundation, k*ma yana karɓar miliyoyin daloli daga wasu masu tallafi daga ƙasashen waje wai don horar da ’yan jarida a Najeriya, amma bai taɓa yin horon ba.

“Hakanan an san shi da amfani da shafin sa na Sahara Reporters wajen yi wa mutane barazana da neman kuɗaɗe ta hanyar garkuwa da suna, alhali ma’aikatansa suna rayuwa cikin talauci.”

Olayinka ya ce idan akwai wani barazana ga rayuwar Sowore, to daga cikin waɗanda ya taɓa zalunta ko ya ci zarafinsu ne. “Ya k**ata ya bar Shugaba Tinubu da Minista Wike a gefe daga cikin sak**akon rayuwar zambarsa.”

Ya ƙara da cewa:
“Duk hayaniyar da yake yi game da Wike cikin sa’o’i 48 da s**a wuce, tamkar ƙoƙarin ƙarshe ne na doki mai mutuwa. Ya san illolin da ke tattare da tuhumar da ake yi masa. Shi ya sa yake wasa da kwakwalan jama'a , yana nuna kansa a matsayin wanda ake zalunta domin ci gaba da zambarsa.”

Kan batun mallakar gidaje a Amurka, Olayinka ya tambaya:
“Shin Ministan ya taɓa musanta cewa matarsa tana da kadarori a Amurka? Laifi ne a mallaki kadarori ta hanyar gadon iyali ko saye? Wannan shi ne kariyarsa ga wallafa ƙarya tsantsa da kiran Shugaban ƙasa da mai laifi?

“Shin wannan ne kariyarsa ga karɓar dala miliyan uku domin sayar da tikitin gwamna na jam’iyyarsa, sannan ya yi shiru lokacin da aka kashe mutane a Jihar Rivers a 2019 domin tilasta wa jama’a dan takarar da aka biya shi kansa?

“Shin wannan ne kariyarsa ga yin Yahoo Yahoo da karɓar miliyoyin daloli daga masu bada tallafi na ƙasashen waje a ƙarƙashin karya?”

Olayinka ya kammala da cewa:
“K**ar yadda na sha faɗi, Sowore zai iya ci gaba da boyewa ƙarƙashin suna na ‘Cashtivist’ na ɗan lokaci, amma da sannu zai kai ƙarshen dabarun zambarsa.”

Dan Arewa Daga Jihar Jigawa, Ismail Muhammad Adam Ya Zama Na Uku A Gasar Fasaha Mafi Girma A AfirkaGasar Digital for All...
20/09/2025

Dan Arewa Daga Jihar Jigawa, Ismail Muhammad Adam Ya Zama Na Uku A Gasar Fasaha Mafi Girma A Afirka

Gasar Digital for All Challenge, wacce ita ce gasar koyon fasaha mafi girma a Afirka, an shirya ta ne ta hannun Tech4Dev tare da haɗin gwiwar Foreign, Commonwealth & Development Office (FCDO), NITDA da k*ma UK-international development Tech Hub. Gasar ta sake samun wani babban ci gaba inda Ismail Muhammad Adam, wanda ya wakilci yankin Arewa maso Yamma, ya fito a matsayin na uku (2nd Runner-Up) a rukuni na matasa (Youth Intermediate Category).

Rukunin, wanda shi ne mafi girma daga cikin rukunan gasar, an tsara shi ne domin gwada ƙwarewar mahalarta a fannin fasaha da k*ma yadda za su iya amfani da ita a aikace.

A matsayin ladan nasarar da ya samu, Ismail Muhammad Adam ya karɓi kudin ₦10,000,000 tare da samun takardar shaidar ƙwararren mai haɓaka manhajar kwamfuta (Certified Software Developer), wanda ke nuna babban ci gaba a rayuwar aikinsa.

Yayin da yake wakiltar Jihar Jigawa, shi ne kaɗai ɗan takara da jami’an gwamnatin jiha s**a raka, abin da ya ƙara tabbatar da jajircewar Gwamnatin Jihar Jigawa wajen bunƙasa ilimin fasaha da ƙarfafa matasa. Sabon Daraktan Huk*mar ICT da Tattalin Arzikin Dijital ta Jihar Jigawa ya bayar da muhimmin tallafi ta hanyar kasancewa tare da shi har zuwa ƙarshen gasar.

Manchester United Ta Yi Wa Chelsea Ci 2-1
20/09/2025

Manchester United Ta Yi Wa Chelsea Ci 2-1

(Dr.) Tare Da Mai Dakinsa, Hajiya Aisha Humaira .************* SASHEN TALLA**********************Kuyi Download din Appli...
20/09/2025

(Dr.) Tare Da Mai Dakinsa, Hajiya Aisha Humaira

.
************* SASHEN TALLA**********************

Kuyi Download din Application din ABBA PANTAMI DATA ta wannan link din a PlayStore da k*ma AppStore
👇👇
Ga link din PlayStore
https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.com.abbapantamidata.app

Ga link din AppStore
https://apps.apple.com/us/app/abba-pantami-data-ltd/id6744061271

Mai bukatan karin bayani, ya tuntubi daya daga cikin customer care ta WhatsApp;
09138275183
08126081967
07046868000
07061347599.

BINCIKE: Sanata Ibrahim Bomai Ya Fi Kowane Sanata A Jihar Yobe Jinkai Da Gudanar Da Ayyuka Ga Al'ummarsaDaga Sani Tanbal...
20/09/2025

BINCIKE: Sanata Ibrahim Bomai Ya Fi Kowane Sanata A Jihar Yobe Jinkai Da Gudanar Da Ayyuka Ga Al'ummarsa

Daga Sani Tanbala Drogba (PKM)

Sanata Ibrahim Mohammed Bomai ya taɓa zama Shugaban Kwamitin Sadarwa a Majalisar Dattawa, k*ma yanzu haka shi ne Shugaban Kwamitin Babban Birnin Tarayya (FCTA), Abuja.

Muna kira ga matasan Jihar Yobe da su kalli irin gagarumin ayyukan da Sanata Ibrahim Mohammed Bomai ya gudanar. Ayyukansa sun shafi kowa da kowa ba tare da wariya ba, domin ya shimfiɗa ci gaba a lungu da sako. Wannan ya tabbatar da cewa shi ɗan kowa ne, mai kishin jama’a.

Saboda haka, muna kira ga jama’a su tashi tsaye wajen mara masa baya domin ya jagoranci Jihar Yobe a matsayin Gwamna a 2027 Insha Allah.

Sanata Bomai mutum ne mai taimakon al’umma. Babu babba, babu ƙarami a wurinsa. Ya tallafa wa mata, ya taimaka wa masu ƙaramin ƙarfi, ya k*ma ba matasa damar yin karatu har zuwa ƙasashen waje. Mutum ne mai kula da jama’a. Muna kira ga maza da mata, dattawa da matasa, da duk masu amfani da kafafen sada zumunta da su tashi tsaye wajen goyon bayansa.

Muhimman Ayyukan da ya gudanar a Yobe ta Kudu sun haɗa da shimfidar hanyoyi a wurare guda 28, ciki har da:

Sabon Garin Nangere

Fika Gari

Damagum

Unguwar Jaji ×3

Jujin Osi

Layin Alkali Kalli

Layin Chairman Salisu Muktari

Arikeme – Gadan Talakawa

Bomai Road (Fanfo Mai Baki Biyu) ×4

Bayan Access Back

Masallacin Yarbawa

Layin Dipper Life ×2

Layin Bayan Masallacin Yarbawa

Tandari

Misau Road

Layin Batayya

Layin Baba Gimba – Unguwar Jaji

Bayan Gidan Marayu Low-Cost

Ngelzerma

Layin Yan Kuka – Bakin Kasuwa

Asibitin Kutare

Garin Gadaka

Sabon Garin Nangere zuwa Tsohon Garin Nangere

Damagum – Fadar Mai Martaba

Fika – Hanyar Asibiti

Lailai Ikira (GRA)

Bayan Dogon Karfe

Army Barrack Potisk*m

Jimilla: 28 wurare.

Sauran Ayyuka da ya gudanar sun haɗa da:

Raba motocin alfarma

Raba gidaje

Rabawa al’umma transformers na wutar lantarki

Gina sabbin asibitoci

Rabawa matasa jari domin dogaro da kai

Madallah! Allah ya saka da alheri Sanata Ibrahim Mohammed Bomai, Turakin Fika.

20/09/2025

ABIN TAUSAYI: Wata Mahaifiya Ta Roki Gwamna Zulum Da Ya Taimaka Ya Saki Danta Da Ya Sa 'Yan Sanda S**a K**a Shi

An gurfanar da Babagana a kotun Magistrate dake Maiiduguri, indda bayan an bada belin sa tare da sharadin kawo Mai Unguwa a matsayin wanda zai tsaya masa.

Amma a gefe daya k*ma gwamnatin jihar Borno ta gargadi masu Unguwanni akan cewa duk wanda ya tsaya matsa a bakin aikinsa.

Yanzu haka yana gidan Yari, wanda hakan ya sa mahaifiyar Yaron kuka da neman agajin Gwamna akan ya fitar mata da danta.

Ana zargin Babagana da tofa albarkacin bakinsa, akan shiri da suke yi akan 'ýan siyasa saboda ta ki damawa da su.

Address

Abuja

Telephone

+2347045480959

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rariya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share