11/05/2026
BABBAR NASARA: Sojojin Nijeriya Sun Haĺĺaka ’Yan Bìdiga 70 A Shiroro Dake Jihar Neja
..Sun Musanta Kàśhe Fararen Hula
Rundunar Tsaro ta Kasa (DHQ) ta kare harin sararin samaniya da dakarun soji s**a kai a Karamar Huk*mar Shiroro da ke Jihar Neja, inda ta ce harin ya dira ne kai tsaye a sansanonin ’yan bindiga, ba fararen hula ba.
Sanarwar, wadda Daraktan Yada Labarai na Rundunar, Manjo Janar Michael Onoja ya fitar, ta ce an kai harin ne biyo bayan bayanan sirri da aka samu kan taruwar miyagun a kauyen Lukupe ranar 9 ga watan Mayun 2026.
Rundunar ta bayyana cewa dakarun sojin kasa masu sarrafa jiragen yaki marasa matuki (UAV) ne s**a kaddamar da harin tsakanin karfe 11:59 na daren Asabar zuwa karfe 6:00 na safiyar Lahadi, 10 ga watan Mayu.
Wuraren da harin ya shafa sun hada da kauyukan Katerma, Bokko, Kusasu da Kuduru
Sojoji sun bayyana cewa a kauyen Kusasu kadai, an yi nasarar hallaka akalla ’yan bindiga 70, yayin da sauran s**a tsere a kan babura zuwa yankin Zango.
Duk da koke-koken da wasu mazauna yankin ke yi na cewa bama-baman sun fada gidajensu, musamman a unguwar Guradnayi, rundunar tsaron ta ce bayanan da take da su ba su nuna hakan ba.
Rundunar ta ce galibin mazauna wadannan kauyuka tuni s**a kaurace wa gidajensu zuwa garin Sarkin Pawa saboda gudun hare-haren ’yan bindiga, don haka wuraren da aka kai harin sansanonin bata-gari ne kawai.
"Rundunar soji za ta ci gaba da aiki don kakkaba sansanonin ’yan bindiga da nufin dawo da zaman lafiya a yankin Shiroro da sauran sassan jihar." — Maj. Gen. Onoja
A karshe, rundunar ta yi kira ga jama'a da kafafen yada labarai da su guji yada labaran da ba a tantance ba, wadanda za su iya jefa mutane cikin fargaba ko k*ma su kawo cikas ga ayyukan tsaro da ake gudanarwa.