Rariya

Rariya Rariya jarida ce a harshen Hausa domin kawo labaran cikin gida Nijeriya da ma duniya baki daya da k*m
(385)

Jonathan Ya Samu Sarautar 'Jigon Bauchi'
11/08/2026

Jonathan Ya Samu Sarautar 'Jigon Bauchi'

Haɗin Kai Nijeriya Take Buƙata A Yanzu Fiye Da Kowane Lokaci, Inji Ministan Yaɗa LabaraiMinistan Yaɗa Labarai da Wayar d...
11/08/2026

Haɗin Kai Nijeriya Take Buƙata A Yanzu Fiye Da Kowane Lokaci, Inji Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga 'yan Nijeriya da su ɗaukaka tunanin su sama da bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa, su haɗa kai wajen yaƙi da rashin tsaro da sauran ƙalubalen da ke fuskantar ƙasar.

Idris ya yi wannan kiran ne a ranar Talata, a wajen taron ƙasa da ƙasa mai taken “Bambance-bambance da Zaman Lafiyar Al'umma: Haɗin Gwiwa don Kyakkyawar Makoma,” wanda ƙungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS) ta shirya tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (Muslim World League) a Abuja.

Ministan ya ce bambance-bambancen mutanen da s**a halarci taron ya nuna cewa akwai fahimtar juna cewa tsaro, zaman lafiya da wadata a Nijeriya sun dogara ne da yadda 'yan ƙasa za su yi aiki tare ba tare da la'akari da bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa ba.

Idris ya ce: “Dukkan mu muna buƙatar mu haɗa kai, mu yi tunani a matsayin 'yan Nijeriya, mu yi tunani a matsayin 'yan'adam, k*ma mu yi aiki tare ba tare da la'akari da bambance-bambancen mu ba, domin mu kasance tsintsiya maɗaurin ki ɗaya.”

Ya jaddada cewa rarrabuwar kawuna bisa addini da ƙabila za ta ƙara dagula yaƙi da rashin tsaro, yana mai kira ga 'yan Nijeriya da su yi watsi da tashin hankali, rashin haƙuri da ƙoƙarin amfani da bambance-bambancen ƙasar nan wajen raba kan al'umma.

“Babu lokacin bambance-bambance. Idan a yayin yaƙin da muke yi da rashin tsaro muka bari bambance-bambancen addini s**a shiga, hakan zai ƙara dagula matsalar. Buƙatar da muke da ita ta haɗa kan mu a matsayin al'umma ɗaya na da matuƙar muhimmanci,” inji shi.

Idris ya fayyace cewa ba Gwamnatin Tarayya ce ta shirya taron ba, sai dai ya ce gwamnati tana maraba da shirye-shiryen da ke inganta tattaunawa tsakanin mabiya addinai, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

“Idan muna son ci gaba da tafiya zuwa ga wadata, dole ne dukkan mu mu yi tunani da aiki tare, mu k*ma haɗa kai a matsayin al'umma ɗaya,” inji ministan.

Ya ce yawan al'ummar Nijeriya, muhimmancin ta da k*ma tasirin ta na nufin zaman lafiya da kwanciyar hankalin ƙasar na da matuƙar tasiri ga Afirka da ma sauran sassan duniya.

“Nijeriya ƙasa ce mai matuƙar muhimmanci. Ƙasa ce mai mutane sama da miliyan 230. Zaman lafiya da kwanciyar hankali a nan na nufin zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk faɗin Afirka, har ma da duniya baki ɗaya,” inji shi.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a taron, ya isar da saƙon aniyar Shugaban Ƙasa ta tabbatar da ingantaccen tsaro mai ɗorewa, haɗin kan ƙasa da haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa, yana mai cewa Nijeriya za ta ci gaba da aiki tare da abokan hulɗar ta na ƙasa da ƙasa wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Babban Sakataren Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya k*ma Shugaban Ƙungiyar Malaman Musulunci ta Duniya, Sheikh Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa, ya buƙaci 'yan Nijeriya da su kare haƙƙin ɗan'adam da s**a yi tarayya a cikin ta, tare da yin watsi da ƙoƙarin amfani da addini, ƙabila ko talauci wajen raba kan ƙasa.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa'ad Abubakar III, ya yi kira da a ci gaba da tattaunawa, tsare gaskiya da ƙara ƙaimi wajen aiwatar da hanyoyin magance ƙalubalen Nijeriya, tare da kira ga 'yan Nijeriya da su sake gina amana da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin mabiya addinai.

A nasa jawabin, Shugaban jam'iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya buƙaci 'yan Nijeriya da su ɗauki bambance-bambancen ƙasar a matsayin tushen ƙarfi maimakon rarrabuwar kai, yana mai cewa duk da cewa 'yan Nijeriya suna gudanar da ibada ta hanyoyi daban-daban, suna da buri da ƙalubale iri ɗaya.

Shugaban JIBWIS na Ƙasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau, ya yi kira da a ƙara haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, ƙungiyoyin addini da al'ummomi wajen yaƙi da rashin tsaro, tare da ƙara zuba jari a fannin ilimi da bunƙasa ƙwarewa domin rage yiwuwar matasa su rungumi tsattsauran ra'ayi ko k*ma a ɗauke su aikin laifi.

Daga cikin waɗanda s**a halarci taron akwai Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu; Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani; Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi; Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum; Ministan Bunƙasa Kiwo, Idi Mukhtar Maiha; Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa'ad Abubakar III; Shugaban APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda; Sheikh Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa; Shugaban JIBWIS na Ƙasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau; Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Nijeriya (NSCIA), da sauran manyan jami'an gwamnati, shugabannin addinai da na gargajiya, jami'an diflomasiyya, wakilan ƙungiyoyin fararen hula da sauran manyan baƙi.

Hajiya Amal Muhammad, Ita Ce Mace Ta Farko Da Ta Zama Farfesa A Sashen Nazarin Harshen Larabci A Jami'ar Maiduguri, Jiha...
11/08/2026

Hajiya Amal Muhammad, Ita Ce Mace Ta Farko Da Ta Zama Farfesa A Sashen Nazarin Harshen Larabci A Jami'ar Maiduguri, Jihar Borno

Wace Irin Fata Za Ku Yi Mata?

Daga Jamilu Dabawa

Sukar Da Ake Yi Min Saboda Kalmar Muslim-Muslim Ba Ya Damuna, Saboda Dama Na Riga Na Siya Kuma Na Biya, Kuma Har Yau Kan...
11/08/2026

Sukar Da Ake Yi Min Saboda Kalmar Muslim-Muslim Ba Ya Damuna, Saboda Dama Na Riga Na Siya Kuma Na Biya, Kuma Har Yau Kan Wannan Kalmar Ta Muslim-Muslim Babu Ranar Nadama, Kuma Ni Ba Tinubu Nake Tallatawa Ba, Musulunci Nake Tallatawa, Inji Sheik Sani Yahaya Jingir

Duk Mai Faɗa Da Izala Ya Yi Wa Kansa, Domin Izala Ta Yi Masa Fintinkau, Sannan Muna Tare Da Sheik Sani Yahaya Jingir Kan...
11/08/2026

Duk Mai Faɗa Da Izala Ya Yi Wa Kansa, Domin Izala Ta Yi Masa Fintinkau, Sannan Muna Tare Da Sheik Sani Yahaya Jingir Kan Furucinsa Na Muslim-Muslim Tiket Ɗari Bisa Ɗari, Inji Sheik Ibrahim Sheik Alhassan Saeed Adam Jos

Wani Sashe Na Taron Ƙungiyar Tripple R A Jihar Jigawa
11/08/2026

Wani Sashe Na Taron Ƙungiyar Tripple R A Jihar Jigawa

Allah Ya Yi Wa Tsohon Ɗan Wasan Barkwanci, Sani Tumbuleƙe Rasuwa
11/08/2026

Allah Ya Yi Wa Tsohon Ɗan Wasan Barkwanci, Sani Tumbuleƙe Rasuwa

An Zargin Shugaban Ƙaramar Huk*mar Kabo Dake Kano Da Hannu A Tsare Matashi Aliyu Muhammad HarunaAna zargin Shugaban Kara...
11/08/2026

An Zargin Shugaban Ƙaramar Huk*mar Kabo Dake Kano Da Hannu A Tsare Matashi Aliyu Muhammad Haruna

Ana zargin Shugaban Karamar Huk*mar Kabo ta Jihar Kano, Hon. Lawan Najume Kabo, da hannu wajen k**a da tsare wani matashi mai suna Aliyu Muhammad Haruna, wanda aka fi sani da Babagana, bisa zargin ya bayyana ra’ayinsa kan wasu batutuwan siyasa.

An bayyana hakan ne cikin wata takardar ƙorafi mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Agusta, 2026, wadda aka miƙa wa Sufeto-Janar na Rundunar ’Yan Sandan Najeriya a Hedikwatar ’Yan Sanda da ke Louis Edet House, Abuja.

Takardar ta ƙunshi ƙorafi kan k**awa da tsarewa ba bisa ka’idar doka ba, da k*ma zargin amfani da ikon ’yan sanda ba daidai ba wajen k**a matashin.
‎A cikin ƙorafin, lauyoyin Aliyu Muhammad Haruna sun bayyana cewa:

“Mu ne lauyoyin Mr. Aliyu Muhammad Haruna (Babagana), k*ma bisa umarninsa, mun rubuto wannan wasiƙa domin sanar da ku halin da ya dabaibaye k**awa da tsare shi da jami’an ’yan sanda da ke aiki a Sashen ’Yan Sandan Kabo.”

A cewar takardar, lauyoyin sun yi zargin cewa k**awa da tsare Babagana ya faru ne bisa umarni ko sa hannun Shugaban Karamar Huk*mar Kabo, Hon. Lawan Najume Kabo.

‎LauyoyinLauyoyin sun k*ma nemi a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa domin gano halaccin k**awa da tsarewar, yanayin da ya kai ga jami’an ’yan sanda ɗaukar matakin, da k*ma rawar da Shugaban Karamar Huk*mar ya taka a cikin lamarin.

Takardar ta bayyana Babagana a matsayin ɗan Najeriya, ɗalibi k*ma ɗan asalin Jihar Kano, tare da cewa, bisa bayanan lauyoyinsa, ba shi da wani tarihin aikata laifi da ya shafi wannan ƙorafi.

A ranar 3 ga Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 1:00 na rana, jami’an ’yan sanda da ke aiki a Sashen ’Yan Sandan Kabo sun je gidan Babagana da ke Gidan Alh. Haruna, Kabo, inda s**a k**a shi tare da kai shi ofishin ’yan sanda.

A cewar Babagana, jami’an sun ɗauki matakin ne bisa umarni ko sa hannun Hon. Lawan Najume Kabo, Shugaban Karamar Huk*mar Kabo.

Takardar ta ƙara da cewa Babagana ya taɓa samun rashin jituwa da Shugaban Karamar Huk*mar kan wasu batutuwan siyasa da k*ma yadda ake gudanar da harkokin ƙaramar huk*mar.

Kafin k**a shi, Babagana ya kasance yana bayyana ra’ayoyinsa da rashin amincewarsa da wasu manufofi ko matakan gudanarwa da s**a shafi Shugaban Karamar Huk*mar.

‎A halin yanzu, lauyoyin matashin suna neman a gudanar da bincike domin tabbatar da ainihin dalilin k**awa da tsare shi, da k*ma gano ko an yi amfani da ikon ’yan sanda ba bisa ka’ida ba.

Wane Ne Gwaninka Cikin Ƴan Ƙwallon Da Suke Saka Lamba 7?
11/08/2026

Wane Ne Gwaninka Cikin Ƴan Ƙwallon Da Suke Saka Lamba 7?

Ɗan Wasan Katsina United, Uzor Ya Rasu Ana Tsaka Da Wasa
11/08/2026

Ɗan Wasan Katsina United, Uzor Ya Rasu Ana Tsaka Da Wasa

Address

Abuja

Telephone

+2347045480959

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rariya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share