Fityanu media Press

Fityanu media Press FITYANU PRESS 💙🤍
LABARAN TIJJANIYYA❤️

24/08/2026

Sanarwar Live

🔴 MUNA LIVE YANZU!

📍 Zawiyyar Maulana Sheikh Modibbo Jailani Yola (RTA)

📖 Kai tsaye daga wajen Maulidin Maulana Sheikh Modibbo Jailani Yola (RTA).

🤲 Muna gayyatar dukkan ’yan uwa Musulmi da masoya zuwa wannan Live Broadcast domin kasancewa tare da mu wajen bibiyar wannan babban taro na tunawa da Maulana Sheikh Modibbo Jailani Yola (RTA).

📲 Ku kasance tare da mu kai tsaye a shafin Facebook na Fityanu Media Press.

❤️ Ku yi Share domin sauran ’yan uwa su samu damar kallo.

✨ Fityanu Media Press — Muryar Al’umma, Kai Tsaye Zuwa Gare Ku.

🔴 SANARWA TA MUSAMMAN | LIVE 🔴Muna sanar da daukacin al’umma cewa yau, insha Allah, za mu kasance LIVE kai tsaye a shafi...
24/08/2026

🔴 SANARWA TA MUSAMMAN | LIVE 🔴

Muna sanar da daukacin al’umma cewa yau, insha Allah, za mu kasance LIVE kai tsaye a shafinmu na Facebook mai suna Fityanu Media Press, domin haska muku Maulidin Zawiyyar Maulana Sheikh Modibbo Jailani Yola (RTA). ❤️🕌

Za ku samu damar bibiyar yadda ake gudanar da wannan gagarumin taro kai tsaye, tare da muhimman abubuwan da za su gudana a wajen Maulidin.

📍 Ku shiga shafin: Fityanu Media Press
🔴 LIVE Daren yau Insha Allah

Ku kasance tare da mu, ku gayyaci ‘yan uwa da abokan arziki domin su ma su kalli wannan gagarumin taro.

Fityanu Media Press — Muryar Fityanul Islam.

E-sign
Aliyu Samaila
State media and publicity

19/08/2026

State Director na Jihar Adamawa Ya Bada Umarnin Fitowar Rundunar Agaji a Ranar Zagayen Maulidi

Mai Girma State Director na Rundunar Agaji ta Fityanul Islam Reshen Jihar Adamawa, Brigadier General Alh. Saidu Modibbo Buba Alkali, ya bayar da umarnin cewa dukkan membobin Rundunar Agaji su fito cikin cikakken kayan aiki (uniform) a ranar zagayen Maulidin 12 ga watan Rabi’ul Awwal.

Wannan umarni ya zo ne biyo bayan dogon nazari, shawarwari da duba yanayin yadda ake gudanar da zagayen Maulidi, musamman domin tabbatar da tsaro, tsari da kuma kare mutunci da martabar al’umma.

A yayin zagayen, Rundunar Agaji za ta mayar da hankali wajen taimakawa da kare al’umma, tabbatar da tsari da kuma hana duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiya. Haka kuma, za a yi ƙoƙarin raba maza da mata a wuraren da ake samun cudanya, domin rage cakuduwar da ba ta dace ba da kuma tabbatar da bin ƙa’idojin taron.

Wannan mataki ya kuma zo ne bisa la’akari da abin da ya faru a shekarar da ta gabata, inda State Director ya dakatar da fitowar ’yan Agaji a zagayen Maulidi saboda wasu dalilai na tsaro da kuma bukatar kare daraja, mutunci da martabar Rundunar Agaji ta Fityanul Islam.

A wannan shekarar kuwa, bayan sake duba al’amura tare da tuntubar masu ruwa da tsaki, an ga dacewar Rundunar Agaji ta fito cikin cikakken tsari, domin taka rawar da ta dace wajen tabbatar da tsaro, zaman lafiya, ladabi da tsari yayin gudanar da zagayen.

Mai Girma State Director ya jaddada cewa fitowar Rundunar Agaji ba ta nufin tsoma baki ko takura wa mahalarta ba ce, illa dai domin hidimtawa al’umma, kare su, tabbatar da tsari da kuma taimakawa wajen gudanar da taron cikin nasara.

Ya kuma yi kira ga dukkan membobin Rundunar Agaji da su kasance masu ladabi, haƙuri, biyayya ga umarni, mutunta al’umma da kiyaye martabar uniform da kungiyar, domin su zama abin koyi ga sauran mahalarta.

E-sign
Aliyu Samaila
State media and publicity

Cikin hotuna yanda Rundunar Agaji ta Fityanul Islam Adamawa Ta Tattauna da Daraktocin Ƙananan Hukumomin Central Zone Kan...
19/08/2026

Cikin hotuna yanda Rundunar Agaji ta Fityanul Islam Adamawa Ta Tattauna da Daraktocin Ƙananan Hukumomin Central Zone Kan Tsaron Zagayen Maulidi

A yau, Rundunar Agaji ta Fityanul Islam, Reshen Jihar Adamawa, ta gudanar da wata muhimmiyar ganawa da Daraktocin Ƙananan Hukumomin Central Zone na Jihar Adamawa, domin samun maslaha da fahimtar juna tare da tsara yadda za a gudanar da zagayen Maulidin ranar 12 ga watan Rabi’ul Awwal cikin tsari, zaman lafiya da bin ƙa’idojin addini.

Ganawar ta mayar da hankali ne kan yadda za a samar da cikakken tsari wajen gudanar da zagayen, musamman ganin cewa a shekarun baya an samu wasu bata-gari da ke shiga cikin masu wannan ziyarar, inda wasu daga cikinsu ke bayyana da tufafin da ba su dace da taron addini ba tare da aikata wasu abubuwa da s**a saɓa wa ƙa’idojin Shari’a da kuma tarbiyyar Musulunci.

Saboda haka, a wannan shekarar, Rundunar Agaji ta Fityanul Islam ta yi ingantaccen shiri na musamman, tare da haɗin gwiwar jami’an tsaron gwamnati, domin tabbatar da tsaro, kare mutuncin taron, da kuma dakile duk wani yunƙuri na kawo rashin tsari ko aikata abubuwan da s**a saɓa wa dokokin ƙasa da koyarwar Musulunci.

Haka kuma, ganawar ta kasance wata dama ta ƙarfafa haɗin kai tsakanin Rundunar Agaji ta Fityanul Islam da Daraktocin Ƙananan Hukumomi, domin tabbatar da cewa dukkan masu ruwa da tsaki za su yi aiki tare wajen samun nasarar wannan gagarumin taro.

Rundunar ta jaddada cewa manufar wannan shiri ba wai hana mutane shiga cikin zagayen Maulidi ba ce, sai dai tabbatar da tsari, tsaro, kyawawan ɗabi’u da mutunta dokokin addini da na ƙasa, tare da kare martabar wannan rana mai albarka.

A ƙarshe, Rundunar Agaji ta Fityanul Islam, Reshen Jihar Adamawa, ta yi kira ga dukkan mahalarta da masu son shiga cikin zagayen da su kasance masu bin doka, mutunta juna da kuma guje wa duk wani hali da zai iya kawo rashin zaman lafiya ko ɓata martabar taron.

Da haɗin kan al’umma, shugabannin Fityanul Islam, Daraktocin Ƙananan Hukumomi da jami’an tsaro, ana sa ran gudanar da zagayen Maulidin na ranar 12 ga Rabi’ul Awwal cikin tsari, aminci da zaman lafiya, in Allah Ya yarda.

E-sign
Aliyu samaila
State media and publicity

Rundunar Agaji ta Fityanul Islam Adamawa Ta Tattauna da Kwamitin Shirya Maulidin Gidan Malam Sheikh Modibbo Jailani Yola...
19/08/2026

Rundunar Agaji ta Fityanul Islam Adamawa Ta Tattauna da Kwamitin Shirya Maulidin Gidan Malam Sheikh Modibbo Jailani Yola

A yau, Rundunar Agaji ta Fityanul Islam, Reshen Jihar Adamawa, ta gudanar da wata ganawa mai muhimmanci da ɗaya daga cikin shugabannin kwamitin shirya Maulidin Gidan Malam Sheikh Modibbo Jailani Yola, domin tattauna yadda za a gudanar da taron Maulidin cikin tsari, zaman lafiya da ingantaccen tsaro.

A yayin ganawar, shugabannin Rundunar Agajin sun bayyana bukatarsu ta ganin an bai wa ’yan Agajin Fityanul Islam na Jihar Adamawa damar shiga cikin wasu daga cikin kwamitocin da za su taka muhimmiyar rawa wajen shirya Maulidin, musamman Kwamitin Tsaro da lafiya (Security Committee and health) da sauran kwamitocin da s**a dace.

Wannan bukata ta samo asali ne daga yadda Rundunar Agaji ta Fityanul Islam ke da ƙwarewa da gogewa wajen gudanar da ayyukan agaji, kula da taron jama’a, tabbatar da tsari da taimakawa wajen samar da yanayi mai kyau a manyan taruka.

A nasa bangaren, ɗaya daga cikin shugabannin kwamitin shirya Maulidin ya tabbatar wa shugabannin Rundunar Agajin cewa zai yi ƙoƙari wajen zama tare da sauran shugabannin kwamitocin shirya Maulidin, domin isar da sakon Rundunar Agajin da kuma duba yiwuwar shigar da ’yan Agajin Fityanul Islam cikin kwamitocin da s**a dace.

Haka kuma, yayin ganawar, an gabatar da wasu korafe-korafe da abubuwan da s**a faru a baya da s**a shafi mu’amala da kuma yadda aka gudanar da wasu al’amura. An saurari waɗannan korafe-korafe, inda aka ba da tabbacin cewa za a yi ƙoƙarin ganin irin waɗannan abubuwa ba su sake faruwa ba, tare da samar da kyakkyawar fahimta da haɗin kai tsakanin Rundunar Agaji ta Fityanul Islam da kwamitocin shirya Maulidin.

Ganawar ta kasance cikin yanayi na fahimtar juna, mutunta juna da kuma neman haɗin kai, domin cimma manufa guda samun nasarar Maulidin da gudanar da shi cikin tsari, zaman lafiya, tsaro da haɗin kan al’umma.

Rundunar Agaji ta Fityanul Islam, Reshen Jihar Adamawa, na ƙara jaddada shirinta na bayar da cikakken haɗin kai da gudummawa wajen ganin an gudanar da wannan babban taro cikin nasara da kwanciyar hankali.

E-signed
Aliyu Samaila
State Media and publicity

SANARWA KAN TARON ƘASA (NATIONAL SEMINAR)Ana sanar da dukkan Manyan Shugabanni da Mambobin First Aid Group Fityanul Isla...
05/08/2026

SANARWA KAN TARON ƘASA (NATIONAL SEMINAR)

Ana sanar da dukkan Manyan Shugabanni da Mambobin First Aid Group Fityanul Islam of Nigeria cewa za a gudanar da Taron Ƙasa (National Seminar) kamar haka:

Ranar Isowa: Jumma'a, 21 ga Agusta, 2026
Kaduna State Nigeria.

Ana buƙatar dukkan mahalarta su iso a ranar Jumma'a domin yin rajista (Registration) da tantancewa (Accreditation) kafin fara taron.

Kasancewarku a wannan taro na da matuƙar muhimmanci, domin za a tattauna muhimman batutuwan da s**a shafi ci gaban ƙungiyarmu, ƙarfafa haɗin kai, inganta tsare-tsaren aiki, da kuma shirye-shiryen ayyukanmu na gaba.

Saboda haka, ana kira ga dukkan mambobi da su fara yin dukkan shirye-shiryen da s**a dace domin halartar wannan muhimmin taro.

Za a sanar da cikakken bayani kan wurin taro da lokacin fara taron nan gaba.

Muna roƙon kowa da ya taimaka wajen yaɗa wannan sanarwa tare da ƙarfafa sauran mambobi su halarta domin samun cikakkiyar nasarar taron.

Allah Ya ba mu ikon halarta Ameen, Ya sanya albarka da nasara a cikin wannan taro. Amin.

Mungode.

Signed🖊️
Alh. Mohammed Kabir Makkah
Assistant National Director General, Information

FITYANU MEDIA PRESS

SANARWAR NEMAN TAIMAKO (FISABILILLAHI)Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh.Wata daga cikin membobin Kungiyar Ag...
03/08/2026

SANARWAR NEMAN TAIMAKO (FISABILILLAHI)

Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh.

Wata daga cikin membobin Kungiyar Agaji ta Fityanul Islam, Yola North LGA, wacce aka fi sani da Maman Goshi, tana neman taimakon ‘yan uwa mambobin kungiyar da kuma daukacin al’ummar Musulmi.

Ta shafe lokaci mai tsawo tana fama da jinyar ɗan uwanta wanda rashin lafiyarsa ta yi tsanani, lamarin da ya jefa iyalansu cikin mawuyacin hali har s**a rasa mafi yawan abin da suke da shi wajen neman lafiya.

A halin yanzu, suna neman taimakon Fisabilillahi domin su samu damar kammala biyan kuɗin aikin likita da kuma ci gaba da jinyarsa.

Mai Girma State Director na Fityanul Islam, Adamawa State Command, Brigadier General Alh. Saidu Modibbo Buba Alkali, yana kira ga duk mai hali da Allah Ya h**e masa da ya taimaka gwargwadon ikonsa. Ko da kaɗan ne, yana da matuƙar amfani, kuma Allah Madaukakin Sarki ba Ya taɓa barin ladan mai aikata alheri.

Account Details:
Account Name: Aisha Dauda
Account Number: 2363601452
Bank: Zenith Bank

Lambar Waya: 07044812281

Allah Ya saka wa duk wanda ya taimaka da alheri, Ya ba mara lafiyar lafiya cikin gaggawa, Ya sauƙaƙa wa iyalansa wannan jarabawa, kuma Ya ninka wa masu taimako lada a duniya da Lahira. Ameen.

E-sign
Aliyu Samaila
State media and publicity

AN KADDAMAR DA KWAMITIN WA’AZI NA YOLA SOUTHA yau, Alhamis, 30 ga Yuli, 2026, an gudanar da bikin ƙaddamar da Kwamitin W...
30/07/2026

AN KADDAMAR DA KWAMITIN WA’AZI NA YOLA SOUTH

A yau, Alhamis, 30 ga Yuli, 2026, an gudanar da bikin ƙaddamar da Kwamitin Wa’azi na Yola South na Fityanul Islam a Sakatariyar Jiha ta Fityanul Islam da ke Yola.

An gudanar da wannan ƙaddamarwa ne domin ƙarfafa ayyukan da’awa, yaɗa koyarwar addinin Musulunci, da kuma bunƙasa ayyukan wa’azi a tsakanin al’umma.

A yayin taron, an tunatar da mambobin kwamitin irin nauyin da aka ɗora musu na isar da saƙon addinin Musulunci cikin hikima, haƙuri da gaskiya, tare da kiyaye manufofi da ƙa’idojin Fityanul Islam.

Haka kuma, an yi kira gare su da su kasance masu haɗin kai, jajircewa da riƙon amana wajen sauke nauyin da aka ɗora musu domin ci gaban addini da ƙungiya baki ɗaya.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ba su ikon sauke wannan nauyi yadda ya dace, Ya sanya albarka a cikin ayyukansu, Ya kuma sanya su zama sanadin ƙara yaɗuwar addinin Musulunci. Amin.

Allah Ya ba da nasara.

E-sign
Aliyu Samaila
State media and publicity

SANARWA ZUWA GA DUKKAN MEMBOBIN FIRST AID GROUP FITYANUL ISLAM OF NIGERIA JIHAR ADAMAWAAssalamu Alaikum Warahmatullahi W...
30/07/2026

SANARWA ZUWA GA DUKKAN MEMBOBIN FIRST AID GROUP FITYANUL ISLAM OF NIGERIA JIHAR ADAMAWA

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh.

Office of the State Director, First Aid Group Fityanul Islam Adamawa State yana sanar da daukacin membobin ƙungiyar a faɗin jihar cewa har yanzu ana ci gaba da karɓar rajistar Babban Taron Horaswa na Ƙasa (National Seminar 2026).

Ana sanar da ku cewa za a rufe rajistar a ranar 14 ga watan Agusta, 2026. Saboda haka, ana kira ga dukkan membobi da su gaggauta kammala rajistarsu kafin wa’adin ya cika domin gujewa rasa damar halartar wannan muhimmin taro na ƙasa.

Wannan babban taron horaswa ne da ake sa ran dubban ’yan agaji na Fityanul Islam daga sassa daban-daban na Najeriya za su halarta. Kasancewarka a wannan taro wata babbar dama ce ta ƙara ilimi, ƙwarewa, musayar gogewa da kuma ƙarfafa haɗin kai tsakanin membobin ƙungiyar.

Kuɗaɗen Rajista:
• Kuɗin Rajista (Registration Fee): ₦10,000
• Kuɗin Fom (Form Fee): ₦500

Lura: Kowane memba zai tanadi kuɗin zirga-zirgarsa zuwa Kaduna da kuma dawowa.

Ba sai kana riƙe da wani mukami ba kafin ka halarta. Matuƙar kai memba ne na First Aid Group Fityanul Islam, kana da cikakkiyar damar yin rajista da halartar wannan babban taro na ƙasa.

Domin yin rajista ko samun ƙarin bayani, a tuntube mu ta wannan lambar:

📞 0803 493 1748

Ana karɓar kira (Call) da kuma saƙonnin WhatsApp a wannan lamba.

Muna ƙarfafa dukkan membobin First Aid Group Fityanul Islam a Jihar Adamawa da su yi amfani da wannan dama ta musamman kafin ranar rufe rajista.

Allah Ya ba mu ikon halarta tare da cin gajiyar wannan babban taro, Ya sanya albarka a cikinsa. Amin.

E-sign
Aliyu Samaila
Head of State media and publicity

Rundunar Agajin Fityanul Islam reshen Jihar Adamawa, ta hannun Kwamitin Ladabtarwa wato Disciplinary Committee karkashin...
05/07/2026

Rundunar Agajin Fityanul Islam reshen Jihar Adamawa, ta hannun Kwamitin Ladabtarwa wato Disciplinary Committee karkashin jagorancin State Discipline Lieutenant Colonel Ibrahim Adamu, tare da mukarrabansa, na ci gaba da gudanar da ziyarar gani da ido da s**a fara a fadin jihar.

Wannan ziyara na daga cikin shirin da kwamitin ya kuduri aniyar gudanarwa domin ziyartar dukkan kananan hukumomi 21 na Jihar Adamawa, da nufin tabbatar da cewa ana bin doka, oda, da ka’idojin Rundunar Agajin Fityanul Islam yadda ya kamata.

Ya zuwa yanzu, kwamitin ya kammala zagayen Central Zone, tare da ziyartar wasu kananan hukumomi da ke Southern Zone. A ci gaba da wannan aiki, yanzu sun shiga Northern Zone, inda s**a fara da Song Local Government Area (LGA).

A yayin ziyarar, kwamitin na duba yadda ake gudanar da ayyukan runduna, bin dokoki da ka’idoji, da kuma ba da shawarwari da umarni domin kara inganta aiki, tabbatar da da’a, hadin kai, da gudanar da ayyukan agaji cikin tsari.

Shugabannin kwamitin sun jaddada cewa wannan shiri zai ci gaba har sai an zagaya dukkan kananan hukumomi 21 da ke Jihar Adamawa, domin tabbatar da cewa ana tafiyar da harkokin rundunar bisa doka, oda, da manufar kungiyar Fityanul Islam.

Allah Ya ba da ikon kammala wannan aiki cikin nasara, Ya kara hada kan al’ummar Fityanul Islam, Amin.

E-sign
Aliyu Samaila
Head of state media and publicity

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fityanu media Press posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share