Hausa Daily Times

  • Home
  • Hausa Daily Times

Hausa Daily Times Hausa Daily Times ingantacciyar majiyar yaɗa sahihan labarai ce da shirye-shirye a harshen Hausa.

Ku na tunanin labarin rayuwar Ummi Nuhu ne ya ratsa Hadiza Gabon ya sa ita ma ta yi ƙwalla yayin hirarsu cikin shirinta ...
25/07/2025

Ku na tunanin labarin rayuwar Ummi Nuhu ne ya ratsa Hadiza Gabon ya sa ita ma ta yi ƙwalla yayin hirarsu cikin shirinta na “Gabon Talk Show”?

Mutanen garin Hamdullahi da ke gundumar Panda a Karamar Hukumar Albasu ta jihar Kano su na namen gwamna Kano Abba Kabir ...
25/07/2025

Mutanen garin Hamdullahi da ke gundumar Panda a Karamar Hukumar Albasu ta jihar Kano su na namen gwamna Kano Abba Kabir Yusuf da ya kai musu ɗaukin gaggawa sakamakon yadda zaizayar ƙasa ke neman cinye makarantar ɗaya tilo da su ke da ita ta sakandare a garin, wato “Government Arabic Secondary School” wadda a yanzu haka zaizayar ke neman laƙumewa, kasancewar babbar hanyar ruwa na garin na jikin makarantar.

📸 Muhammad Salees, Hamdullahi

An gyara harabar inda aka binne tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a cikin gidansa tare da sake kewaye inda kabarinsa...
25/07/2025

An gyara harabar inda aka binne tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a cikin gidansa tare da sake kewaye inda kabarinsa ya ke a daidai lokacin da jama'a ke ci gaba da tururuwa zuwa gidan domin yin ta'aziyya tare da yi masa addu'a.

Gawakin mutum 27 da aka kashe a wani hari a garin Riyom na jihar Plateau a ranar Talata da ta gabata kenan yayin da aka ...
25/07/2025

Gawakin mutum 27 da aka kashe a wani hari a garin Riyom na jihar Plateau a ranar Talata da ta gabata kenan yayin da aka ɗauko su daga matuware zuwa garin domin yi musu bizina a yau Jumma'a.

Me ku ke gani a matsayin babbar hanyar magance matsalar kashe-kashen da ke faruwa a jihohin Benue da Plateau?

📸TVC News

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello yayin da ya ke motsa jiki a safiyar yau kamar yadda ya saba yi tare da yaɗawa kai...
25/07/2025

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello yayin da ya ke motsa jiki a safiyar yau kamar yadda ya saba yi tare da yaɗawa kai tsaye a shafukansa na dandalin sada zumunta.

Yadda Kwamishinan Sufurin jihar Kano ya yi belin wani ƙasurgumin dillalin miyagun ƙwayoyi daga hannun kotuWasu takardu d...
25/07/2025

Yadda Kwamishinan Sufurin jihar Kano ya yi belin wani ƙasurgumin dillalin miyagun ƙwayoyi daga hannun kotu

Wasu takardu daga babbar kotun tarayya da ke jihar Kano sun ka nuna yadda Kwamishinan Sufuri na jihar, Hon. Ibrahim Namadi, ya yi belin wani da ake zargin dallancin miyagun ƙwayoyi ne, Sulaiman Aminu Ɗanwawu daga hannun kotu.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito ana zargin Ɗanwawu shi ne ƙasurgumin dillalin miyagun ƙwayoyi da ya fi kowa a jihar Kano.

📸Daily Nigerian

Allah ya jiƙan Sarkin Katsinan Gusau. Ya kyautata na ƴan baya.
25/07/2025

Allah ya jiƙan Sarkin Katsinan Gusau. Ya kyautata na ƴan baya.

Rania Abdussamad kenan, ƴar hamshaƙin ɗan kasuwa Abdussamad Isyaka Rabiu (BUA) yayin da mahaifin ya halarci bikin kammal...
25/07/2025

Rania Abdussamad kenan, ƴar hamshaƙin ɗan kasuwa Abdussamad Isyaka Rabiu (BUA) yayin da mahaifin ya halarci bikin kammala karatun jami'a da ta yi a fannin Injiniyanci daga jami'ar Sussex na ƙasar Birtaniya.

Mai Martaba Sarkin Awe kenan daga jihar Nassarawa yayin da ya kai ziyarar ta'aziyyar rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhamm...
25/07/2025

Mai Martaba Sarkin Awe kenan daga jihar Nassarawa yayin da ya kai ziyarar ta'aziyyar rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a gidansa na Daura, inda ya samu tarba da ga babban ɗansa namiji Yusuf Buhari da wasu ƴan uwan marigayin.

📸 Buhari Sallau

Jigo a APC a jihar Kebbi ya fice daga jam'iyyar zuwa sabuwar tafiyaMarafan Zuru Dr. Sule-Iko Sadeeq Sami ya sanar da fic...
25/07/2025

Jigo a APC a jihar Kebbi ya fice daga jam'iyyar zuwa sabuwar tafiya

Marafan Zuru Dr. Sule-Iko Sadeeq Sami ya sanar da ficewa daga jam'iyyar APC tare da bayyana shiga tafiyar haɗaka ta su Abubakar Malami.

Dama tun can a san shi a matsayin makusancin tsohon Ministan na Shari'a, kuma hakan ne ma ya sa tun farkon fara kafa sabuwar tafiya ake ganinsu tare a duk wurin wani taro da za ayi.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un Mun samu labarin rasuwar Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau Alhaji Dr. Ibrahim Bello ...
25/07/2025

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un

Mun samu labarin rasuwar Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau Alhaji Dr. Ibrahim Bello a wani asibiti da ke Abuja bayan ɗan gajeriyar rashin lafiya jiya da dare.

Allah ya gafarta masa.

25/07/2025

Tsoffin ƴan sanda kenan a Abuja yayin da su ke mayar wa rundunar ƴan sanda ruwa da lemon da ta kawo domin a raba musu a ranar da su ka gudanar da zanga-zanga kan fanshonsu.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Daily Times posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Daily Times:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share