Hausa Daily Times

Hausa Daily Times Hausa Daily Times ingantacciyar majiyar yaɗa sahihan labarai ce da shirye-shirye a harshen Hausa.

Yau a ke zaɓen Shugaban Ƙasa a Jamhuriyar Kamaru (Cameroon). Wa ku ke fatan ya lashe zaɓen?
12/10/2025

Yau a ke zaɓen Shugaban Ƙasa a Jamhuriyar Kamaru (Cameroon).

Wa ku ke fatan ya lashe zaɓen?

Wata ƙungiyar lauyoyi ta gano sabon shugaban INEC Amupitan lauyan APC neGamayyar lauyoyi sama da 1,000 a ƙarƙashin inuwa...
12/10/2025

Wata ƙungiyar lauyoyi ta gano sabon shugaban INEC Amupitan lauyan APC ne

Gamayyar lauyoyi sama da 1,000 a ƙarƙashin inuwar ƙungiyar masu fafutukar kafa dokoki (ALDRAP) sun yi ƙira ga majalisar dattawa da ta ƙi amincewa da naɗin Farfesa Joash Ojo Amupitan, a matsayin sabon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC).

Lauyoyin, a wata wasiƙa su ka aike wa shugaban kwamitin majalisar dattawa kan al’amuran zaɓe, Sanata Simon Lalong, sun yi zargin cewa Farfesa Amupitan bai cancanci muƙamin ba saboda rawar da ya taka a baya a matsayin babban lauyan jam’iyyar APC a shari'ar zaɓen Shugaban Ƙasa na 2023 a kotun ƙoli.

Ƙungiyar ta buƙaci Majalisar da ta martaba doka domin maimaita abin da ta yi a 2021 lokacin da ta ƙi amincewa da sunan Lauretta Onochie a matsayin Kwamishiyar zaɓe ta hukumar ta INEC kan kasancewarta a jam'iyyar APC, shi ma batun Farfesa Amupitan ya yi daidai da wancan matakin na soke naɗinta.

Cikin wannan dare madugun adawan Najeriya Atiku Abubakar ya yi zama da jiga-jigan jam’iyyar ADC na jihar Adamawa waɗanda...
11/10/2025

Cikin wannan dare madugun adawan Najeriya Atiku Abubakar ya yi zama da jiga-jigan jam’iyyar ADC na jihar Adamawa waɗanda su ka haɗa da tsohon gwamnan jihar Muhammad Umar Bindow Jibrilla, tsohon Sanatan Adamawa ta Arewa Sanata Cliff Ishaku Abbo, tsohuwar ƴar takarar gwamnan jihar Sanata Aishatu Ɗahiru Binani da dai sauransu. A cewar Atikun a wani jawabi da aka wallafa a shafinsa na Facebook, sun tattauna tare da yanke shawarar ci gaba da haɗa kansu domin samun nasara a zaɓe mai zuwa.

Bayan yin kiciɓis da juna a taron Majalisar Ɗinkin Duniya a Amurka, Mai Martaba Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sunusi na II...
11/10/2025

Bayan yin kiciɓis da juna a taron Majalisar Ɗinkin Duniya a Amurka, Mai Martaba Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sunusi na II ya sake cin karo da tshon Mataimakin Shugaban Ƙasa Farfesa Yemi Osinbajo a birnin Addis Ababa na ƙasar Ethiopia a kan hanyar kowannensu na zuwa wata ƙasa.

Jaruma Nafisa Abdullahi na ci gaba da shaƙatawarta a ƙasar Austaraliya.
11/10/2025

Jaruma Nafisa Abdullahi na ci gaba da shaƙatawarta a ƙasar Austaraliya.

11/10/2025

Ko kun san aikin babban titin Abuja zuwa Kaduna mai nisan kilomita 140, da kuma Kaduna zuwa Kano mai nisan kilomita 280 da Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke yi a yanzu haka na ci gaba da gudana gadani?

Magoya bayan ƴan adawa sun yi fito-na-fito da jami’an tsaro a titunan birnin Abidjan na ƙasar Cote d’Ivoire, gabanin zaɓ...
11/10/2025

Magoya bayan ƴan adawa sun yi fito-na-fito da jami’an tsaro a titunan birnin Abidjan na ƙasar Cote d’Ivoire, gabanin zaɓen shugaban ƙasar da ke tafe, a wani yunƙuri na yin tir da matakin da gwamatin ƙasar ta ɗauka na haramta wa jagororin ƴan adawa Tidjane Thiam da Laurent Gbagbo tsayawa takara tare da zargin an shirya maguɗi a zaɓen.

Fitan Jarman Kontagora kuma tsohon ɗan takaran gwamnan jihar Neja a zaɓen 2015 da 2019 Umar Muhammad Nasko a wurin bikin...
11/10/2025

Fitan Jarman Kontagora kuma tsohon ɗan takaran gwamnan jihar Neja a zaɓen 2015 da 2019 Umar Muhammad Nasko a wurin bikin naɗin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Malam Namadi Sambo a matsayin sabon Sardaunan Zazzau wanda ya gudana a yau Asabar a fadar Sarkin Zazzau da ke garin Zaria a jihar Kaduna.

Jerin sunayen waɗanda Gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi wa afuwa da sassauci kan hukuncin da aka zartar musu. Shugaba Bola ...
11/10/2025

Jerin sunayen waɗanda Gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi wa afuwa da sassauci kan hukuncin da aka zartar musu.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa manyan fursunoni da tsofaffin fursunoni guda 175 afuwa da sassauci, ciki har da marigayi Major Janar Mamman Jiya Vatsa, marigayi Ken Saro-Wiwa, “Ogoni Nine”, tare da Maryam Sanda da wasu da dama.

Kwamitin bada shawara kan afuwar shugaban ƙasa, ƙarƙashin jagorancin Ministan Shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi ne ya bada shawarar yin afuwa ga tsofaffin fursunoni 15 (11 daga cikinsu sun riga sun rasu), da bayar da sassauci ga fursunoni 82, tare da rage wa’adi ga fursunoni 65. Haka kuma, an mayar da hukuncin kisa ga fursunoni bakwai zuwa daurin rai-da-rai.

Prince Fagbemi ya gabatar da wannan rahoto a taron Council of State ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Cikakken Sunayen Waɗanda S**a Amfana da Afuwa da Sassauci

Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa
1. Nweke Francis Chibueze (44) – daurin rai-da-rai saboda kwayar Co***ne.
2. Dr Nwogu Peters (67) – hukuncin shekara 17 saboda zamba tun 2013.
3. Mrs Anastasia Daniel Nwaoba (63) – ta rigaya ta kammala zaman gidan yari saboda zamba.
4. Barr. Hussaini Alhaji Umar (58) – an yanke masa tara N150M a shari’ar ICPC a 2023.
5. Ayinla Saadu Alanamu (63) – an yanke masa shekara 7 saboda cin hanci a 2019.
6. Hon. Farouk M. Lawan (62) – an yanke masa shekara 5 saboda rashawa a 2021.

Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa Bayan Mutuwarsu

7. Sir Herbert Macaulay – an hana shi muk**an siyasa a 1913 saboda zargin karkatar da kuɗi ta hannun Turawan mulkin mallaka.
8. Major Janar Mamman Jiya Vatsa – an kashe shi a 1986 saboda zargin juyin mulki.

Ogoni Nine
9. Ken Saro-Wiwa
10. Saturday Dobee
11. Nordu Eawa
12. Daniel Gbooko
13. Paul Levera
14. Felix Nuate
15. Baribor Bera
16. Barinem Kiobel
17. John Kpuine

An kuma yi girmamawa ta musamman ga waɗanda aka kashe a wannan rikici:
• Chief Albert Badey
• Chief Edward Kobaru
• Chief Samuel Orage
• Chief Theophilus Orage

Sassauci da Rage Hukunci

Da dama daga cikin waɗanda s**a amfana sun nuna nadama, sun koyi sabbin sana’o’i a gidan yari, ko kuma sun nuna halin kirki. Sun haɗa da:
• Maryam Sanda (37) – an yanke mata hukuncin kisa a 2020 saboda kisan mijinta; yanzu ta amfana daga sassauci bisa nadama da kyakkyawar halinta a gidan yari da kuma bukatar kare yaranta biyu.
• Farfesa Magaji Garba – an yanke masa hukuncin shekara 7 saboda zamba a 2021, an rage shi zuwa shekara 4.
• Major S.A. Akubo – an yanke masa hukuncin rai-da-rai saboda cire mak**ai ba bisa ƙa’ida ba, yanzu an rage zuwa shekara 20.
• Haka kuma fursunoni da dama da aka k**a da laifukan miyagun ƙwayoyi, kisan kai, satar jama’a da cin hanci sun ci gajiyar rage hukunci ko sauyi daga kisa zuwa daurin rai-da-rai.

Waɗanda Aka Sauya daga Hukuncin Kisa Zuwa Rai-Da-Rai

Fursunoni bakwai, ciki har da waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa saboda kisan kai, fashi da makami da miyagun ƙwayoyi, duk sun amfana daga wannan sassauci, an mayar da hukuncinsu zuwa daurin rai-da-rai saboda nuna nadama da ɗabi’a mai kyau.

Wani mummunan hatsari kenan da ya faru da misalin ƙarfe 5 na asubahin yau Asabar a yankin Ikoyi da ke jihar Legos, inda ...
11/10/2025

Wani mummunan hatsari kenan da ya faru da misalin ƙarfe 5 na asubahin yau Asabar a yankin Ikoyi da ke jihar Legos, inda aka garzaya da direban motar zuwa asibiti rai a hanun Allah a sak**akon mummunan raunuka da ya ji.

📸 Linda Ikeji Blog

Labari da Ɗumi-ƊuminsaMaryam Sanda da kotu ta yanke wa hukuncin kisa bisa samunta da laifin kashe mijinta Bilyaminu Hall...
11/10/2025

Labari da Ɗumi-Ɗuminsa

Maryam Sanda da kotu ta yanke wa hukuncin kisa bisa samunta da laifin kashe mijinta Bilyaminu Halliru Bello na daga cikin mutum 175 da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa afuwa.

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf yayin da ya tsaya domin gaisawa da wata yarinya a lokacin da ya kai ziyarar duba ayy...
11/10/2025

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf yayin da ya tsaya domin gaisawa da wata yarinya a lokacin da ya kai ziyarar duba ayyukan da gwamnatinsa ke gudanarwa.

Address

Mambila Street
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Daily Times posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Daily Times:

Share