11/01/2026
AZAWON tana ƙarfafa batun Zakka da Waƙafi don cigaban al'umma
Daga Mukhtar A. Halliru, da Buhari Lawal
Shugaban haɗakar ƙungiyoyin Zakka da Waƙafi naa Ƙasa wato Association of Zakat and Waqf Operators in Nigeria, (AZAWON) Malam Muhammad Lawal Maidoki, Sadaukin Sakkwato ya yi kira ga al'ummar Musulmi da hukumomi su tabbatar da sun cire haƙƙin daga dukiyarsu, domin samun tsira duniya da lahira.
Shaihun malamin ya bayyana haka ne yayin ƙaddamar da Gidauniyar Zakka da Waƙafi ta Karamar Hukumar Mulki ta Kubau, watau
Kubau Waqf Foundation, Gundumar Pambeguwa, a Ƙaramar hukumar Kubau ta Jihar Kaduna.
A cikin jawabinsa, Sadaukin Sakkwato, Muhammad Lawal Maidoki ya gabatar da ƙasida mai taken, 'Tasirin Zakka Da Waƙafi Wajen Samar Da Cigaban Tattalin Arziƙin Al'umma', inda ya nanata buƙatar kafa irin waɗannan ƙungiyoyi a dukkan matakai, daga jiha, masarautu, Al'ummomi da kuma na ɗaiɗaikun jama'a, domin taimakon masu rauni da samar da zaman lafiya.
Ya kuma yi bayanin nau'ikan Waƙafi daban-daban da s**a shafi Waƙafin iyali, Waƙafin tallafin karatu, Waƙafin itatuwa da sauransu.
A yayin taron ƙungiyar masu sayar da masara da sauran 'yan kasuwar yankin sun yi abin a zo a gani, domin an ƙaddamar da asusun tara kuɗaɗe ga Gidauniyar Waƙafi ta Kubau, inda aka yi nasarar tara sama da Naira miliyan Goma, domin soma ayyukan waƙafin. Gidauniyar ta kuma tara wasu kuɗaɗen da su ma yawansu ya kai Miliyan goma wanda 'yan kasuwar s**a bada bashi zuwa shekara daya a yi kasuwanci da su kafin a mayar masu da kuɗin, sai a barwa Gidauniyar ribar don aiwatar da ayukkan alkhairi da su.
A jawabin maraba, wanda shugaban Gidauniyar Alhaji Ibrahim Musa ya yi godiya da yabawa gudunmawar da kowa ya bayar don samun nasarar wannan aikin alheri.
Shima a jawabinsa shugaban Lafiya Waqf Movement, Alhaji Balarabe ya bada tarihin kafuwarsa yana mai cewa yanzu haka yana da rassa a jihohi huɗu da ƙananan hukumomi huɗu a Jihar Kaduna wanda Kuma sanadiyar Lafiya Waqf ɗin ne aka samu damar kafa Dandalin Waƙafi na Kubau.
Babbar manufar, a cewarsa shi ne wayar da kan al'ummah akan mihimmancin yin Waƙafi da buƙatar komai ƙanƙantarsa akwai ɗimbin lada a nan duniya da gobe ƙiyama.
Wakilin Masautar Zazzau kuma Hakimin Anchau, Alhaji Tanimu Haruna da Alhaji Sufiyanu Umar Usman ƙarfen Dawakin Zazzau kuma Hakimin Pambeguwa sun yi godiya ga Malam Muhammad Lawal Maidoki, ga baƙi da sauran al'ummar da s**a halarshi taron kaddamarwar.
Sun bayyana cewa su Sardaunan Sakkwato Sa Ahmadu Bello ne s**a kafa garin Pambegua Kuma gidansa dake garin anmaidashi cibiyar yada addinin musulunci.
Daga cikin tawagar ta AZAWON akwai shugaban dandalin wakafi na Kaduna Malam Abdullahi Salisu Halidu, satarensa Malam Yanusa Bawa da sauran tawagarsu, akwai shugabar kungiyar Zakat ta mata a Sakkwato Malama Amina Musa Sakaba da mataimakiyarta Malama Fatima Bintu Musa, Hajiya Hauwau Ahmad da Mukhtar A. Haliru, Muhammad Lawal Maidoki sai Kuma Buhari Lawal Baban Maheer da sauransu.
Tun farko a jawabin maraba shugaban dandalin Alh Ibrahim Musa ya yi godiya ga mahalarta da roƙon Allah Ya albarkaci tsare-tsaren wannan dandali.