Hausa Daily Times

Hausa Daily Times Hausa Daily Times ingantacciyar majiyar yaɗa sahihan labarai ce da shirye-shirye a harshen Hausa.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un: Matashi ɗan shekara 25 ya kashe ubansa don ya gaji abin da ya taraAn k**a wannan ma...
12/01/2026

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un: Matashi ɗan shekara 25 ya kashe ubansa don ya gaji abin da ya tara

An k**a wannan matashi mai shekara 25, Abubakar Muhammad Buba, a yankin Chanchaga na Minna a jihar Neja, bisa zargin biyan abokinsa mai suna Aliyu Muhammad kuɗi har naira 110,000 don ya kashe mahaifinsa, Alhaji Muhammad Buba, domin ya gaji dukiyarsa.

Rahotanni sun ce an kai wa mahaifin, mai shekara 52, hari aka soke shi da wuƙa har lahira a gidansa da ke yankin Korokpan na Karamar Hukumar Paikoro da ke jihar, a ranar 13 ga Oktoba.

Majiyar Hausa Daily Times ta ce Abubakar ya fara biyan ₦50,000 ga abokin nasa a matsayin rabin kudin aiki, kafin daga bisani ya cika masa ₦60,000 bayan ya sayar da wasu kadarorin mahaifinsa.

Yanzu haka ana ci gaba da neman Aliyu Muhammad, wanda ake zargin shi ne ya aikata kisan wanda ya gudu.

Kalma ɗaya ga wannan matashi da ya kashe ubansa don ya gaji dukiyarsa....

📸Sargacious Bello Lukman

Yadda manyan ƴan siyasa daga manyan jam'iyyun Najeriya su ka halarci taron bikin cika shekaru 60 na tsohon gwamnan jihar...
12/01/2026

Yadda manyan ƴan siyasa daga manyan jam'iyyun Najeriya su ka halarci taron bikin cika shekaru 60 na tsohon gwamnan jihar Sokoto Sanata Aminu Waziri Tambuwal ba tare da la'akari da banbancin siyasa da jam'iyyun da ke tsakaninsu ba da kuma yaƙin zaɓen da ke gabansu a 2027. Bikin ya guda ne a Abuja a ranar Asabar.

Faɗa mana sunan wanɗanda ku ka gani a wurin bikin kuma ku ka yi mamaki- da kuma waɗanda ya k**ata a gani amma ba ku gansu a wurin ba

Amaryar Jarumi Adam A. Zango kuma tsohuwar Jaruma a fina-finan Hausa yayin da ita ma ke baza kafasiti a cikin sabuwar mo...
12/01/2026

Amaryar Jarumi Adam A. Zango kuma tsohuwar Jaruma a fina-finan Hausa yayin da ita ma ke baza kafasiti a cikin sabuwar motar mijinta wadda kaf Kannywood babu wani mai irin ta.

Tinubu ya isa Abu Dhabi don taron ADSW 2026Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na ƙasar Haɗaɗɗiyar D...
11/01/2026

Tinubu ya isa Abu Dhabi don taron ADSW 2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a daren Lahadi, domin halartar taron Abu Dhabi Sustainability Week (ADSW) na 2026, wanda zai fara a yau Litinin.

Jirgin Shugaban Ƙasan ya sauka a Sashen Shugaban Ƙasa na Filin Jirgin Sama na Zayed da misalin ƙarfe 11:30 na dare agogon Dubai. Ministan Harkokin Wajen UAE, Sheikh Shakhboot Nahyan Al Nahyan, tare da Jakadan UAE a Nijeriya, Salem Saeed Al-Shamsi, da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Amb. Yusuf Maitama Tuggar, da kuma jami’an ofishin jakadancin Najeriya a Abu Dhabi ne s**a tarbe shi.

Haka kuma, wasu ministoci da s**a haɗa da Ministan Kasafi da Tsare-tsare, Atiku Bagudu, Ministan Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, Dr. Jumoke Oduwole, da Darakta-Janar na Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa (NIA), Amb. Muhammed Muhammed, sun tarbe Shugaban Ƙasan a otal ɗinsa.

Kafin isowarsa Abu Dhabi, Shugaba Tinubu ya shafe wani ɓangare na hutun ƙarshen shekara a Turai, inda ya yi muhimman tattaunawa da Shugaban Rwanda, Paul Kagame, da Shugaban Faransa, Emmanuel Macron.

Taron ADSW 2026, mai taken “The Nexus of Next, All Systems Go”, dandali ne na duniya da ke haɗa shugabanni, masu tsara manufofi, masu zuba jari da ƙwararru domin tattaunawa da ɗaukar matakai kan ci gaba mai dorewa, yaƙi da sauyin yanayi, sauya tsarin mak**ashi da bunƙasa tattalin arziki da ya haɗa kowa da kowa.

Ziyarar ta ƙara jaddada kyakkyawar alaƙar diflomasiyya da tattalin arziki tsakanin Najeriya da UAE, tare da nuna matsayar Najeriya a matsayin ƙasa mai taka rawa a tattaunawar duniya kan ci gaba mai dorewa.

Jarumarku Rabi'atu Sulaiman wato (Nadiya a cikin shirin Manyan Mata) yayin ziyara da ta kai Birnin Cairo na ƙasar Egypt.
11/01/2026

Jarumarku Rabi'atu Sulaiman wato (Nadiya a cikin shirin Manyan Mata) yayin ziyara da ta kai Birnin Cairo na ƙasar Egypt.

11/01/2026

Fitaccen Malamin nan Sheikh Abubakar Imam Gana ƙarƙashin gidauniyarsa ta taimaka wa marasa ƙarfi da gajiyayyu ya ƙaddamar da wani gagarimin shirin duba marasa lafiya kyauta a garin Jos na jihar Filato, inda ya gayato wasu ƙwararrun likitoci s**a duba lafiyar jama'a Musulmai da Krista tare da basu magunguna kyauta.

An gudanar da duba lafiyar ne a makarantar malamin da ke Sabon Garin Narabi.

Ga abin da Malamin da wasu da su ka amfana ke cewa....

Yanzu haka gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf na jagorantar bikin yaye ɗalibai 2,260 daga makarantun koyar da sana'o'i ...
11/01/2026

Yanzu haka gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf na jagorantar bikin yaye ɗalibai 2,260 daga makarantun koyar da sana'o'i na gwamnatin jihar.

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa Ƴan Kwankwasiyya ƴan kasuwar waya a Kano sun fara cire hotunan gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da k...
11/01/2026

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa

Ƴan Kwankwasiyya ƴan kasuwar waya a Kano sun fara cire hotunan gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da ke cikin ofisoshi da shagunansu su na yagewa sak**akon ficewa daga gidan jagoransu Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da gwamnan ke shirin yi zuwa APC.

Ku ne ganin sun yi daidai ko kuma kuskure ne yin hakan?

AZAWON tana ƙarfafa batun Zakka da Waƙafi don cigaban al'ummaDaga Mukhtar A. Halliru, da Buhari Lawal Shugaban haɗakar ƙ...
11/01/2026

AZAWON tana ƙarfafa batun Zakka da Waƙafi don cigaban al'umma

Daga Mukhtar A. Halliru, da Buhari Lawal

Shugaban haɗakar ƙungiyoyin Zakka da Waƙafi naa Ƙasa wato Association of Zakat and Waqf Operators in Nigeria, (AZAWON) Malam Muhammad Lawal Maidoki, Sadaukin Sakkwato ya yi kira ga al'ummar Musulmi da hukumomi su tabbatar da sun cire haƙƙin daga dukiyarsu, domin samun tsira duniya da lahira.

Shaihun malamin ya bayyana haka ne yayin ƙaddamar da Gidauniyar Zakka da Waƙafi ta Karamar Hukumar Mulki ta Kubau, watau
Kubau Waqf Foundation, Gundumar Pambeguwa, a Ƙaramar hukumar Kubau ta Jihar Kaduna.

A cikin jawabinsa, Sadaukin Sakkwato, Muhammad Lawal Maidoki ya gabatar da ƙasida mai taken, 'Tasirin Zakka Da Waƙafi Wajen Samar Da Cigaban Tattalin Arziƙin Al'umma', inda ya nanata buƙatar kafa irin waɗannan ƙungiyoyi a dukkan matakai, daga jiha, masarautu, Al'ummomi da kuma na ɗaiɗaikun jama'a, domin taimakon masu rauni da samar da zaman lafiya.

Ya kuma yi bayanin nau'ikan Waƙafi daban-daban da s**a shafi Waƙafin iyali, Waƙafin tallafin karatu, Waƙafin itatuwa da sauransu.

A yayin taron ƙungiyar masu sayar da masara da sauran 'yan kasuwar yankin sun yi abin a zo a gani, domin an ƙaddamar da asusun tara kuɗaɗe ga Gidauniyar Waƙafi ta Kubau, inda aka yi nasarar tara sama da Naira miliyan Goma, domin soma ayyukan waƙafin. Gidauniyar ta kuma tara wasu kuɗaɗen da su ma yawansu ya kai Miliyan goma wanda 'yan kasuwar s**a bada bashi zuwa shekara daya a yi kasuwanci da su kafin a mayar masu da kuɗin, sai a barwa Gidauniyar ribar don aiwatar da ayukkan alkhairi da su.

A jawabin maraba, wanda shugaban Gidauniyar Alhaji Ibrahim Musa ya yi godiya da yabawa gudunmawar da kowa ya bayar don samun nasarar wannan aikin alheri.

Shima a jawabinsa shugaban Lafiya Waqf Movement, Alhaji Balarabe ya bada tarihin kafuwarsa yana mai cewa yanzu haka yana da rassa a jihohi huɗu da ƙananan hukumomi huɗu a Jihar Kaduna wanda Kuma sanadiyar Lafiya Waqf ɗin ne aka samu damar kafa Dandalin Waƙafi na Kubau.

Babbar manufar, a cewarsa shi ne wayar da kan al'ummah akan mihimmancin yin Waƙafi da buƙatar komai ƙanƙantarsa akwai ɗimbin lada a nan duniya da gobe ƙiyama.

Wakilin Masautar Zazzau kuma Hakimin Anchau, Alhaji Tanimu Haruna da Alhaji Sufiyanu Umar Usman ƙarfen Dawakin Zazzau kuma Hakimin Pambeguwa sun yi godiya ga Malam Muhammad Lawal Maidoki, ga baƙi da sauran al'ummar da s**a halarshi taron kaddamarwar.

Sun bayyana cewa su Sardaunan Sakkwato Sa Ahmadu Bello ne s**a kafa garin Pambegua Kuma gidansa dake garin anmaidashi cibiyar yada addinin musulunci.

Daga cikin tawagar ta AZAWON akwai shugaban dandalin wakafi na Kaduna Malam Abdullahi Salisu Halidu, satarensa Malam Yanusa Bawa da sauran tawagarsu, akwai shugabar kungiyar Zakat ta mata a Sakkwato Malama Amina Musa Sakaba da mataimakiyarta Malama Fatima Bintu Musa, Hajiya Hauwau Ahmad da Mukhtar A. Haliru, Muhammad Lawal Maidoki sai Kuma Buhari Lawal Baban Maheer da sauransu.

Tun farko a jawabin maraba shugaban dandalin Alh Ibrahim Musa ya yi godiya ga mahalarta da roƙon Allah Ya albarkaci tsare-tsaren wannan dandali.

Mahaifiyar Jarumi Adam A. Zango yayin da ta shiga sabuwar motar da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya ɗanta kya...
11/01/2026

Mahaifiyar Jarumi Adam A. Zango yayin da ta shiga sabuwar motar da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya ɗanta kyauta domin yi masa addu'a tare da danya alkhairi.

Jiya kenan wurin ɗaurin auren ɗan yayan Jarumin Kannywood Malam Ibrahim Mandawari mai suna Murtala Muhammad Mandawari wa...
11/01/2026

Jiya kenan wurin ɗaurin auren ɗan yayan Jarumin Kannywood Malam Ibrahim Mandawari mai suna Murtala Muhammad Mandawari wanda aka ɗaura a Kano.

Allah ya basu zaman lafiya.

📸 Ibrahim Mandawari

Kara'iMai Martaba Sarkin Daura Alhaji Dr. Umar Faruk Umar tare da tsaleliyar amaryarsa a birnin Paris na ƙasar Farasa a ...
11/01/2026

Kara'i

Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Dr. Umar Faruk Umar tare da tsaleliyar amaryarsa a birnin Paris na ƙasar Farasa a ziyarar shaƙatawa da su ka kai.

Ko kun ga laifin Mai Martaba Sarki?

Allah ya ƙara wa Sarki lafiya da nisan kwana.

Address

Mambila Street
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Daily Times posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Daily Times:

Share