Hausa Daily Times

Hausa Daily Times Hausa Daily Times ingantacciyar majiyar yaɗa sahihan labarai ce da shirye-shirye a harshen Hausa.

Hotunan Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima daga wurin taron sauyin yanayi na COP30 yayin da ya ke tattaunawa da Ma...
06/11/2025

Hotunan Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima daga wurin taron sauyin yanayi na COP30 yayin da ya ke tattaunawa da Mataimakin Shugaban Ƙasar Brazil da ake gudanar da taron tare da sauran shuwagabannin duniya.

Irin haka ya taɓa faruwa da ku?
06/11/2025

Irin haka ya taɓa faruwa da ku?

06/11/2025

Jawabin Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai Mohammed Idris, a yayin taron manema labarai kan matakin ƙasar Amurka na sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargi da tauye ƴancin addini.

Yayin da ya cika shekaru 70 a duniya, tsohon gwamnan jihar Kano kuma jigo a jam'iyyar PDP Malam Ibrahim Shekarau ya ce z...
06/11/2025

Yayin da ya cika shekaru 70 a duniya, tsohon gwamnan jihar Kano kuma jigo a jam'iyyar PDP Malam Ibrahim Shekarau ya ce zai ci gaba da kasancewa a cikin siyasa har ƙarshen rayuwarsa.

Wani fata ku ke yi masa?

Jawo hankalin duniya ga shirin inganta karatun allo da tsangayu Daga Mukhtar A. Halliru Tambuwal, SakkwatoAn kammala duk...
05/11/2025

Jawo hankalin duniya ga shirin inganta karatun allo da tsangayu

Daga Mukhtar A. Halliru Tambuwal, Sakkwato

An kammala dukkan shirye-shirye domin gudanar da babban taron ƙasa da ƙasa wanda ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen Afirka ta Yamma ta ECOWAS da haɗin gwiwar ƙungiyar Tarayyar Ƙasashen Afirka ta AU s**a shirya, domin raya ilimin makarantun allo da tsangayu.

Jam'iyyatu Ansaruddeen Attijjaniya da haɗin gwiwar ECOWAS da AU ne s**a tsara taron domin kawo sauyi a harkokin zaman lafiya da tsaro, bunƙasa ilimin makarantun tsangaya da almajiranci.

An tsara cewa taron zai mayar da hankali ne wajen tattauna batun gudummawar ilimin almajiranci da ƙalubalensa, hanyoyin inganta tsarin karatun allo da almajiranci a Afirka ta Yamma, da duba darussa daga Nijeriya. Za kuma a duba batun amfani da hanyoyin Zakka da Waqafi wajen inganta ilimi da tattalin arziƙi a Afirka.

Taron wanda zai gudana gobe Alhamis 4 ga watan Nuwamba, 2025 a Babban Ɗakin Taro na ECOWAS da ke Abuja zai haɗo kan masu ruwa da tsaki a harkar ilimin addinin Musulunci, hafizai, alarammomi, masu makarantun tsangaya da na allo. Harwayau, akwai manyan jami'an gwamnati, jami'an tsaro, ƴan kasuwa, da masu masana'antu daga sassa daban-daban na Afirka.

Ana kuma sa rai da halartar wakilan ƙasashen larabawa da jakadun ƙasashen Libiya, Mauritania, Chadi, Kamaru, Masar, da Morocco har ma da Turkiyya da sauran su.

Daga cikin manyan bakin akwai Ministar Ilimi ta Nijeriya, Farfesa Suwaiba Ahmed da za ta wakilci uwargidan Shugaban ƙasa Sanata Oluremi Tinubu, da Babban Mashawarcin Ministan Ilimi Kan Harkokin Almajirai da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta, Hon. Kakaba Shehu Balarabe, Barden Makarantun Allo da Tsangayu na Ƙasar Hausa.

Sauran sun haɗa da Dr Muhammad Ibn Chambas Shugaban Hukumar ECOWAS, kuma Babban Wakilin AU game da yaƙi da bazuwar ƙananan makamai a Afirka. Shi ne kuma zai zama shugaba na biyu na wannan babban taro.

05/11/2025

Kai Tsaye daga wurin buɗe bikin kwallayya na Africa da ke gudana a Abuja.

“Birnin New York zai ci gaba da zama birni na baƙin haure, Birnin da baƙin haure su ka gina, Birnin da baƙin haure su ka...
05/11/2025

“Birnin New York zai ci gaba da zama birni na baƙin haure,

Birnin da baƙin haure su ka gina,

Birnin da baƙin haure su ka bunƙasa,

A yanzu kuma baƙin haure ke jagoranta”.

Saƙon zaɓaɓɓen Magajin Garin birnin New York na ƙasar Amurka Zohran Mamdani ga shugaban ƙasar Donald Trump a cikin jawabinsa na karɓan nasara da ya yi.

Birgediya Janar Sama'ila Uba ya zama Kakakin hedikwatar tsaron Najeriya bayan ya karɓa daga hannun Birgediya Janar Tukur...
05/11/2025

Birgediya Janar Sama'ila Uba ya zama Kakakin hedikwatar tsaron Najeriya bayan ya karɓa daga hannun Birgediya Janar Tukur Ismail Gusau wanda ya kammala shekaru aikinsa a gidan soja.

Sabon Kakakin hedkwatar tsaron ɗan asalin jihar Kano ne daga Ƙaramar Hukumar Nasarawa da cikin birnin Kano.

Zohran Kwame Mamdani, musulmi kuma haifaffen ƙasar Uganda da ke Africa amma iyayensa ƴan asalin ƙasar India ne ya lashe ...
05/11/2025

Zohran Kwame Mamdani, musulmi kuma haifaffen ƙasar Uganda da ke Africa amma iyayensa ƴan asalin ƙasar India ne ya lashe zaɓen Magajin Garin birnin New York na ƙasar Amurka bayan fafatawa da ɗan takaran Donald Trump Andrew Cuomo.

Laftanar Janar Ibrahim Abdulsalami Gwazawa kenan, Badakkaren soja daga yankin Zuru na jihar Kebbi yayin da Babban Hafsan...
05/11/2025

Laftanar Janar Ibrahim Abdulsalami Gwazawa kenan, Badakkaren soja daga yankin Zuru na jihar Kebbi yayin da Babban Hafsan Hafsoshin Tsaron Najeriya ke maƙala masa alamar ƙarin girma na ƙarshe gare shi daga Manjo Janar zuwa Laftanar Janar gabanin ritayarsa bayan kammala shekaru 35 a gidan soja.

Bikin wanda ya gudana a shalkwatantar tsaron ƙasa da ke Abuja a jiya Talata, ya samu halartar dukkan manyan Hafsoshin Tsaron Sojin sama, ƙasa, da na ruwa gami da shugaban hukumar leƙen asirin soji.

Fitattun jarumai mata na Kannywood biyu, Maryam Booth da Fati Abdullahi Washa yayin yawon bude ido a birnin Paris na kas...
04/11/2025

Fitattun jarumai mata na Kannywood biyu, Maryam Booth da Fati Abdullahi Washa yayin yawon bude ido a birnin Paris na kasar Faransa.

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya tafi ƙasar Brazil domin halartar taron sauyin yanayi na Majalisar Ɗinkin Dun...
04/11/2025

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya tafi ƙasar Brazil domin halartar taron sauyin yanayi na Majalisar Ɗinkin Duniya COP 30.

Address

Mambila Street
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Daily Times posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Daily Times:

Share