Sashen Hausa Muryar Najeriya, Abuja

Sashen Hausa Muryar Najeriya, Abuja VON-HAUSA (MURYAR NAJERIYA) YA FADADA MU'AMULLA DA MASU SAURARO KAI TSAYE DOMIN BAYYANA RA'AYOYINKU

SANATA KWANKWASO YA BAYYANA ANIYAR KOMAWA APC BISA SHARADIDaga Yusuf Bala a KanoTsohon dantakarar shugabancin Najeriya a...
20/09/2025

SANATA KWANKWASO YA BAYYANA ANIYAR KOMAWA APC BISA SHARADI

Daga Yusuf Bala a Kano

Tsohon dantakarar shugabancin Najeriya a karkashin Inuwar jam'iyyar NNPP Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana aniyar komawa jam'iyyar APC bisa sharadi.

A cewar Kwankwaso za su koma APC ne kawai idan an basu tabbaci na abin da za su samu a matsayin jam'iyya.

Yace jam'iyyar NNPP ta taka muhimmiyar rawa a zaben shugaban kasa don haka mika kanta ga wata jam'iyyar ba zai zamo sakaka ba.

Gwamnan Kano Ya Ɗauki Karin Malaman Makaranta Sama Da Dubu HuduDaga Yusuf Bala a Kano Gwamnan Jihar Kano Arewa maso Yamm...
19/09/2025

Gwamnan Kano Ya Ɗauki Karin Malaman Makaranta Sama Da Dubu Hudu

Daga Yusuf Bala a Kano

Gwamnan Jihar Kano Arewa maso Yammacin Najeriya , Abba Kabir Yusif, ya ɗauki karin malamai 4,315 aiki daga cikin tsaffin malaman da ke aikin sa kai na BESDA domin zama cikakkun ma’aikata a bangaren malinta.


Gwamnan ya bayyana haka a lokacin da yake kaddamar da aikin rabon takardun daukar aikin a dakin taro na Sani Abacha da ke Kofar Mata inda ya shawarce su da su kasance masu kishin aiki, gaskiya, da kuma baiwa dalibansu tarbiyya ta gari.

Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa ta ɗauki malamai 5,500 a shekarar 2023, sai a shekarar 2024 ya ɗauki Malamai 5,632, yanzu kuma ya dauki 4,000 a watan Mayu 2025, dukkansu daga cikin masu aikin koyarwa na sa kai na BESDA.

A cewar Gwamnan, “Wannan tsari alama ce ta jajircewar gwamnatinmu wajen gyara harkar ilimi a jihar Kano, kuma don ƙarfafa tsarin ina sanar da ɗaukar karin malamai 2,616, da kaddamar da shirin bada lamunin ababen hawa na Naira milyan 200, tare da amincewa da rabon babura 444 da kwamfutoci 300 domin inganta kula da makarantu”.

Haka kuma, ya bayar da umarnin sake buɗe makarantar kwana ta Shehu Minjibir wacce za ta fara da ɗalibai 180, da ɗaukaka darajar wata makaranta a karamar hukumar Ungogo zuwa makarantar kwana, sannan ya amince da ɗaukar masu gadi 17,000 a makarantun da ke fadin jihar.



Gwamna Yusuf dai ya jaddada cewa gyare-gyaren ilimi da gwamnatinsa ke aiwatarwa sun fara haifar da ɗa mai ido, la’akari da nasarar da Ɗaliban Kano s**a samu a sakamakon jarrabawar NECO ta 2025

Taron dai ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan harkokin ilimi da s**a hadar da wakilan hukumar ilimin bai daya UBEC da na kungiyoyi da ke aikin tallafar Ilimi da wakilan sarakunanan Kano da Karaye da dai sauransu.

Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Saki Kudi Don Inganta Ilimi.Binta Aliyu Birnin Kebbi.A wani muhimmin mataki da zai kawo sauyi a...
18/09/2025

Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Saki Kudi Don Inganta Ilimi.

Binta Aliyu Birnin Kebbi.

A wani muhimmin mataki da zai kawo sauyi a harkar ilimi a Jihar Kebbi, gwamnatin jihar, karkashin jagorancin Kwamared Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), ta amince da sakin makudan kudade domin gudanar da wasu muhimman ayyuka a fannin ilimi mai zurfi.

Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi na Jihar Kebbi, Hon. Isah Abubakar Tunga, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar. Ya ce an amince da kudaden ne domin tabbatar da cewa dalibai da makarantun gaba da sakandare na jihar sun samu ingantattun kayan aiki da kyakkyawan yanayi na karatu.

Daga cikin ayyukan da za a aiwatar akwai: Gyaran dakunan kwanan dalibai a Kwalejin Kiwon Lafiya da Fasaha da ke Jega da yyukan gyaran za su shafi dakunan Abdulsalam Nagimbana, Bush House, da Emir Haruna Rasheed, inda za a kashe N230,205,981.96, siyan kayan aiki na zamani domin fara karatu a sabuwar Kwalejin Ungozoma da ke Zauro, Birnin Kebbi.

"Za a sayi kayan aiki na bangaren Library, Physical Sciences da Microbiology Laboratory da kudin N251,525,065.00.

"Biyan kudin makaranta na daliban Jihar Kebbi da ke karatu a manyan makarantun cikin Najeriya domin zangon karatu na 2024/2025.

"Wannan ya kai kimanin N695,936,660.00.
Kwamishinan ya ce wannan mataki wani babbar shaida ce ta yadda Gwamna Nasir Idris ke jajirce wajen inganta rayuwar matasa ta hanyar ilimi. Ya kara da cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin cewa duk wani dan jihar Kebbi ya samu damar karatu cikin sauki da walwala.

A cewarsa, “Ilimi jari ne na dogon lokaci, kuma shine ginshikin ci gaban kowace al'umma. Don haka, duk wani yunkuri na bunkasa wannan fanni ya cancanci yabo da goyon baya.”

A karshe, Hon. Isah Abubakar Tunga ya roki dalibai da al’ummar jihar da su ci gaba da yi wa gwamnati addu’a, tare da bayar da hadin kai domin ci gaba da samun nasarori a fannin ilimi da sauran bangarori na rayuwa.

RENEWED HOPE:  ASIBITIN AMINU KANO YA RABAUTA  DA AIKIN SAMAR DA LANTARKI MAI AMFANI DA HASKEN RANA NA BILIYOYIN KUDADEY...
18/09/2025

RENEWED HOPE: ASIBITIN AMINU KANO YA RABAUTA DA AIKIN SAMAR DA LANTARKI MAI AMFANI DA HASKEN RANA NA BILIYOYIN KUDADE

Yusuf Bala daga Kano

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da aikin samar da wutar lantarki Mai amfani da hasken rana mai karfin megawatt bakwai a Asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH), kasa da awa 48 bayan rikicin wuta tsakanin asibitin da kamfanin rarraba wutar Kano (KEDCO).

Shugaban kwamitin kasafin kudi na Majalisar Wakilai, Hon. Abubakar Kabir Bichi, wanda ke wakiltar mazabar Bichi, shi ne ya kawo aikin da darajarsa ta kai sama da naira biliyan 12.

A cewar Bichi wannan bangare ne na shirin Renewed Hope na Shugaba Bola Tinubu na samar wa dukkan manyan makarantu da asibitocin koyarwa wutar hasken rana a fadin kasar.

Bichi ya bayyana cewa asibitin AKTH kadai ya samu ayyukan da kudinsu ya kai sama da naira biliyan 26 a bana, tare da shirin saka irin wannan tsarin a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK), ADUSTECH Wudil, da asibitocin Murtala da Nasarawa.

Shugaban Asibitin AKTH, Farfesa Abdulrahman Sheshe, ya bayyana cewa asibitin na kashe sama da naira miliyan 150 duk wata wajen biyan wutar lantarki haka nan yakna kashe sama da miliyan 30 na dizal. yana mai cewa aikin zai rage kudaden kashewa da kashi 30 cikin 100 tare da tabbatar da ci gaba da samun wuta ba tare da yankewa ba.

KANO TA DOKE JIHOHIN NAJERIYA A SAKAMAKON NECOYusuf Bala daga KanoShugaban hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire t...
18/09/2025

KANO TA DOKE JIHOHIN NAJERIYA A SAKAMAKON NECO

Yusuf Bala daga Kano

Shugaban hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta NECO, Farfesa Ibrahim Wushishi ne ya bayyana haka a garin Minna babban birnin jihar Neja yayin da yake sanar da sakamakon jarrabawar ta wannan shekara ta 2025.

Farfesa Wushishi ya ce dalibai 68,159 ne s**a samu kiredit biyar da s**a haɗa da Turanci da lissafi daga jihar Kano Arewa maso Yammacin Najeriya.

Sai jihar Lagos da ke biye mata da dalibai 67,007, a inda jihar Oyo ta zo ta uku da dalibai 48,742.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce wannan nasara ta samo asali ne daga matakan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dauka wajen farfaɗo da ilimi, da s**a hadar da ware kaso 31% na kasafin kuɗin jihar ga bangaren ilimi da ɗaukar malamai da gyaran makarantu, da samar da kayan koyo da kayarwa kyauta.

Sanarwar ta Kara da cewa nasarar ta biyo bayan jajircewar gwamnatin jihar Kano wajen inganta ilimin 'ya'ya mata da rage yawan yaran da basa zuwa makarantar da gyara makarantu da kuma inganta walwalar malamai.

Gwamna Abba Abba Kabir Yusuf ya bayyana farin cikinsa bisa wannan nasara, yana mai cewa kwalliya ta biyan kuɗin sabulu.

Wannan nasara na zuwa duk da irin rahotanni da wasu kungiyoyi na kasa da kasa irinsu UNICEF ke fitarwa na koma bayan ilimi a jihohi na Arewa n Najeriya.

17/09/2025

KUNGIYAR AMATA TA YI SABBIN SHUGABANNI A KANO

Babbar Hadaddiyar Kungiyar Kula da Jin Fadin 'Yankasuwa da Masu Sana'a ta Kasa (AMATA) reshen Jihar Kano Arewa maso Yammacin Najeriya ta gudanar da zabe tare da tabbatar davsabbin Shugabanninta.

Daga Kano Yusuf Bala ya hada mana wannan rahoto.

Alhaji Aliko Dangote, shugaban Kamfanin albarkatun Mai na Dangote yace bin dogon layi a gidajen Mai ya zama Tarihi, abin...
16/09/2025

Alhaji Aliko Dangote, shugaban Kamfanin albarkatun Mai na Dangote yace bin dogon layi a gidajen Mai ya zama Tarihi, abin da ke zuwa yayin da kamfaninsa ke cika shekara da fara aikin da yake fitar da gangar mai 650.000 duk rana.

Da yake bikin a Legas Dangote yace 'yan Najeriya na ganin 'sabon babi" inda farashin Mai ke ci gaba da sauka daga kusan 1,100 zuwa kusan 841 a wasu jihohi da dama na Najeriya.

Yace motocinsa masu amfani da CNG gas 4,000 za su fara aiki inda za a samar wa mutane 24,000 aikin yi.

Dangote ya yi alkawari na fadada aikin Kamfanin ta yadda zai rika fitar da mai ganga 700,000 a duk rana inda ya kuma bukaci doka yin aikinta na ba da kariya ga masana'antu na cikin gida da ma sake mayar da hankali wajen samar da ayyuka da walwala da bunkasa masana'antu.


SOKOTO INEC TA YI TATTAKIN FADAKARWA KAN KATIN ZABE Hadiza Haliru Muhammad Sokoto A cigaba da shirye- shiryen tabbatar d...
16/09/2025

SOKOTO INEC TA YI TATTAKIN FADAKARWA KAN KATIN ZABE

Hadiza Haliru Muhammad Sokoto

A cigaba da shirye- shiryen tabbatar da cikakken gudanar da zabe mai inganci, a Najeriya Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta INEC reshen jihar Sakoto ta gudanar da wani gangamin tattakin wayar da kan al'umma a fadin jihar.

Wannan tattakin ya mayar da hankali kan karfafa fahimtar al'umma game da muhimmanci mallakar katin zabe ( PVC) da kuma bukatar sabunta bayanai ga wasu sassa na masu zabe., tattakin nada zimmar wayar da kan al'umma game da muhimmanci mallakar katin zabe ( PVC).

Sakataren sashen mulki na INEC a jihar Sokoto Aliyu Bello ya bayyana makasudin tattakin tare da kira ga sauran jama'a da s**ayi katin zabe tun wancan lokacin da su je hukumar su karbi katinsu, ya kuma ce wadanda ke da bukatar sauya kati domin wasu dalillai ko na canza wurin zama ko.lalacewar kati da kuma wadanda basu taba yin katin ba suna da damar zuwa domin samun yin katin zabe.

Abdullahi Sale wanda jami'i ne a hukumar ya bayyana tattakin da cewa zai zagaya kwaryar birnin na Sokito domin kira tare da ilmantarwa ga sanin muhimmanci yin katin zabe

Hukumar ta nuna tsayin daka da jajircewa wajen ganin cewa duk dan kasa ya samu damar yin rajista da jefa kuri'a a lokacin zabe, wannan tattakin wani bangare ne na kokarin tabbatar da cewa tsarin dimukaradiyya ya inganta a Najeriya ta hanyar karfafa shigar al'umma cikin harkokin zabe.

Titinin Sokoto–Badagry Zai Ƙarfafa Kasuwanci a Yammacin Afirka...MinistaDaga Binta Aliyu, Birnin KebbiKaramin Ministan A...
13/09/2025

Titinin Sokoto–Badagry Zai Ƙarfafa Kasuwanci a Yammacin Afirka...Minista

Daga Binta Aliyu, Birnin Kebbi

Karamin Ministan Ayyuka, Muhammad Bello Goronyo, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa jajircewarsa wajen inganta ababen more rayuwa a ƙasar nan, duk da ƙalubalen tattalin arziki da ake fuskanta.

Goronyo ya bayyana hakan ne yayin da yake duba aikin t**in tare da Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, a jihohin Kebbi da Sokoto a ranar Juma’a. Ya bayyana cewa aikin gina babban t**in Sokoto–Badagry Superhighway na daga cikin manyan shaidun yadda gwamnatin ke mai da hankali wajen cigaban kasa.

Ya bayyana cewa t**in, wanda zai ratsa jihohin Sokoto, Kebbi da Neja, zai taimaka matuka wajen bunkasa tattalin arziki da harkokin kasuwanci, musamman a yankin Sokoto da Kebbi, kafin ya kai ƙarshen sa a Badagry, Jihar Legas.
"Wannan aiki ba na Jihohin Sokoto, Kebbi ko Neja kadai ba ne.
Aikin kasa ne, domin yana haɗa sassa daban-daban na ƙasa kafin ya kai Badagry a Legas," in ji Goronyo.

Ministan ya jaddada muhimmancin aikin musamman dangane da dangantakar sa da Kasuwar Duniya ta Illela, inda aikin zai fara. Ya ce,
“Wannan t**i zai bude sabbin damammakin kasuwanci a wannan yankin da ya kai fiye da kilomita 1,000, yana haɗa Najeriya da Nijar, Mali da sauran ƙasashen makwabta.”

Goronyo ya bayyana aikin a matsayin “mai sauya tarihi”, inda ya bukaci al’ummomin da aikin zai shafa da su yaba wa gwamnatin tarayya bisa wannan ƙoƙari.
"Ina kira ga al’umma da su fahimci muhimmancin aikin da ake yi, kuma su nuna godiya ga Shugaba Tinubu bisa kulawa da wannan yanki," in ji shi.

“Ba wai muna yin kamfen ba ne. Idan an kammala wannan aiki, babu bukatar mu dawo da kamfen, domin Shugaban kasa ya riga ya nuna ƙauna da kulawa ga al’ummarsa.”

A ƙarshe, Goronyo ya yaba da jajircewar Minista Dave Umahi wajen aiwatar da Manufar “Sabon Fatan” Shugaban Kasa, musamman a ɓangaren ayyukan more rayuwa.

12/09/2025

YARAN DA AKA HAIFA A HADE A KANO SUN SAMU TARBAR GWAMNA YUSUF BAYAN AIKIN RABA SU A SAUDIYA

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya karbi yaran nan Jarirai biyu da aka haife su a hade a Kano sama da shekaru biyu da s**a gabata wadanda aka raba su a kasar Saudiya karkashin kulawar Sarki Abdulaziz na Saudiyya.

Yaran dai sun iso jihar ta Kano tare da mahaifansu cikin koshin lafiya kamar yadda zaa ji karin bayani a rahoton wakilinmu a Kano Yusuf

11/09/2025

Gangamin Makaranta AlKur’ani mai girma sun Gudanar da Addu’a ga Shugaba Tinubu da Barau da Atah a Kano

Makarantan na AlKur'ani mai girma sun hadu a unguwar Kurna a karamar hukumar Fagge da ke Kano don gudanar da addu'oi gabanin faran ayyukan kungiyar TBA a Kano Arewa masoYammacin Najeriya.

Daga Kano Yusuf Bala ya hada mana wannan rahoto

Address

VON Corporate Headquarters Plot 1386 Oda Crescent, Off Aminu Kano Crescent, Wuse II
Abuja
PMB5089,WUSEPOSTOFFICEABUJA.

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sashen Hausa Muryar Najeriya, Abuja posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sashen Hausa Muryar Najeriya, Abuja:

Share