29/11/2025
Bana siyasantar da matsalar tsaro ka daina Anfani da matsalar tsaro kana ɓata min suna -Sen Barau Ya Gargadi Gwamna Abba
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya gargadi Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, da ya daina siyasantar da batun tsaro, inda ya ce ya k**ata gwamnan ya maida hankali kan warware matsalolin da s**a addabi jihar.
Sanata Barau ya maida martani ne bayan gwamnatin Kano ta zarge shi da cewa maganganunsa na iya kawo tarnaki ga kokarin tsaro. Ya ce babu ko sau daya da ya yi kalaman da za su iya tayar da tarzoma, yana kalubalantar gwamnati ta fito da bidiyon da take ikirari akai.
A wata sanarwa da ke dauke da sa hannun mai taimaka masa kan yada labarai, Ismail Mudashir, Sanata Barau ya ce:
“Gwamnati ta karyata aiki, ta koma kirkirar karya don bata suna. A maimakon haka, ya k**ata su hada kai wajen magance barazanar tsaro da ke shiga wasu yankunan Kano.”
Barau ya kuma zargi gwamnatin Kano da kasawa, yana cewa jihar ta yi baya a fannin cigaba saboda rashin ingantaccen jagoranci. Ya ce Kano ta taba zama kusa da Lagos a harkar cigaba amma yanzu an karkata saboda mulkin da bai da tsari.
Sanatan ya lissafa gudunmawar da ya bayar wajen inganta tsaro, ciki har da:
Ba da motocin aiki ga rundunar ’yan sanda a mazabarsa da wasu yankunan jaha
Ba da babura ga dukkan ’yan sanda a Kano ta Arewa
Gina da gyaran ofisoshin ’yan sanda da DSS
Taimakawa wajen kafa makarantu na horas da jami’an tsaro (NSCDC – Gwarzo, Police Commission – Kabo, Immigration – Bichi)
Sanya fitilun tituna na solar a fadin mazabarsa da wasu sassan Kano
Ya ce gwamnatin Kano ta koyi aiki, ta daina bata masa suna.