05/09/2026
“Kan APC a haɗe Yake a Jihar Katsina Kuma Za Mu Tabbatar da Nasarar Shugaba Tinubu da APC a 2027” — Gwamna Radda
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, Ph.D., CON, ya sake jaddada cewa jam’iyyar APC tana cikin haɗin kai a jihar Katsina, yana mai bayyana cewa jam’iyyar za ta haɗa kai wajen tabbatar da nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima da sauran ‘yan jam’iyyar a Jihar Katsina a zaɓen 2027.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin ƙaddamar da ƙungiyar Tinubu Shettima 2027 (PBAT Door-To-Door) Political Movement, tare da ƙaddamar da ko’odinetocinta na Jihar Katsina.
Ƙungiyar, wadda Shugaban Kamfanin Tantita Security Services, Higher Chief Government Oweizide Tompolo, ya kafa tare da ɗaukar nauyinta, an samar da ita ne domin wayar da kan jama’a da kuma tattara goyon bayan al’umma, domin sake zaɓen Shugaba Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima.
Gwamna Radda ya ce APC tana da ƙarfi kuma tana cikin haɗin kai a Katsina, inda yace zaa ƙarfafa tsarin jam’iyyar daga matakin ƙananan hukumomi 34 zuwa gundumomi 361, domin samun gagarumar nasara ga Tinubu da Shettima a 2027.
Ya kuma buƙaci mambobin ƙungiyar da magoya bayan APC su isar da saƙon jam’iyyar APC zuwa ga al’umma tun daga tushe, su riƙa tattaunawa da jama’a cikin mutunta juna, tare da bayyana manufofi da nasarorin da gwamnatin tarayya da ta jiha s**a samu.
Tun da farko, a jawabinsa na maraba, shugaban ƙungiyar na ƙasa, Comrade Sunday Adenkanbi Asuku, ya bayyana cewa an samar da ƙungiyar ne domin kai saƙon shugaban kasa da jam’iyyar APC kai tsaye ga jama’a, ta hanyar gudanar da tattaunawa da wayar da kan al’umma gida-gida.
A nasa ɓangaren, shugaban kamfanin Tantita Security Services, High Chief Engr. Kestin Ebimorbwei Pondi, wanda ya wakilci wanda ya kafa ƙungiyar, Higher Chief Government Tompolo, ya ce an kafa ƙungiyar ne domin tallafa wa ci gaba da jagorancin gwamnatin Tinubu da jam’iyyar APC.
Ya buƙaci mambobin ƙungiyar su kasance masu zaman lafiya, bin doka da oda da kuma mayar da hankali kan manufar ƙungiyar, tare da yin aiki kafada da kafada da tsarin siyasa da ake da shi domin ƙarfafa goyon bayan jama’a.
A cikin saƙon fatan alheri da ya gabatar, Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Katsina, Dr. Bishir Gambo Saulawa, ya yaba da wannan shiri, tare da tabbatar da cewa jam’iyyar a jihar a shirye take ta yi aiki tare da ƙungiyar da sauran masu ruwa da tsaki wajen ƙarfafa tsarin APC gabanin zaɓen 2027.
Shi ma tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina kuma shugaban shirin Renewed Hope Ambassadors a jihar, Hon. Tukur Ahmed Jikamshi, ya jaddada muhimmancin goyon bayan jama’a daga tushe wajen isar da saƙon nasarorin gwamnatin Shugaba Tinubu da Gwamna Dikko Umaru Radda.
A jawabinsa na godiya, Shugaban ƙungiyar na Jihar Katsina, Dr. Faisal Umar Kaita, ya gode wa jagororin ƙungiyar, Gwamna Radda, shugabannin APC da sauran masu ruwa da tsaki bisa goyon bayan da s**a bayar.
Ya tabbatar da cewa tsarin ƙungiyar na jihar zai yi aiki tukuru wajen ƙarfafa tattara goyon bayan jama’a daga tushe, domin tabbatar da sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Gwamna Dikko Radda da sauran ‘yan jam’iyyar APC a zaɓen 2027.
Taron ya samu halartar kakakin majalisar dokokin jihar Katsina, Rt. Hon Nasir Yahya Daura, shugabannin APC, jami’an gwamnati, masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa, wakilan matasa da mata, ko’odinetocin ƙungiyar da magoya bayanta daga sassa daban-daban na Jihar Katsina.
An ƙaddamar da tsarin tafiyar ta ƙasa da ƙungiyar a Jihar Katsina, wanda zai jagoranci ayyukanta a ƙananan hukumomi 34 da unguwanni 361 na jihar.
MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government
September 5, 2026.