Mikiya

Mikiya Mikiya jarida ce mallakin Kamfanin Mikiya Online news LTD dake watsa labarai cikin harshen Hausa a Najeriya.
(253)

Whatsapp da kira zaku iya samun ma'aikatan mikiya a wannan lamba >08135583932. Mikiya Kafar labarai ce cikin harshen hausa a Nageriya

A ranar zaɓe Ku Karɓi Kuɗinsu, Amma Ku tabbata kun zaɓi Wanda Kuke So — Peter Obi Ya Faɗa Wa Magoya BayansaDan takarar s...
07/09/2026

A ranar zaɓe Ku Karɓi Kuɗinsu, Amma Ku tabbata kun zaɓi Wanda Kuke So — Peter Obi Ya Faɗa Wa Magoya Bayansa

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya buƙaci ‘yan Najeriya da kada su bari kuɗin sayen ƙuri’a su rinjayi zaɓinsu a zaɓen 2027.

Obi ya bayyana hakan ne a yayin ziyararsa jihar Kogi ranar Lahadi, inda ya gana da mazauna jihar da magoya bayansa a ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen 2027.

Da yake jawabi ga jama’a, tsohon gwamnan jihar Anambra ya ƙarfafi masu jefa ƙuri’a da su karɓi duk wata kuɗi da ‘yan siyasa s**a ba su, amma su je rumfar zaɓe su zaɓi ɗan takarar da zuciyarsu ta amince da shi.

Peter Obi ya kuma yi gargaɗin cewa ‘yan Najeriya ba za su amince da duk wani yunƙurin maguɗin zaɓen shugaban ƙasa na 2027 ba, yana mai jaddada muhimmancin masu zaɓe su kasance cikin shiri da sanya ido a duk lokacin gudanar da zaɓe.

Kalaman nasa na zuwa ne yayin da harkokin shirye-shiryen siyasa ke ƙara zafafa a faɗin ƙasar, inda manyan jam’iyyun siyasa da ƙungiyoyin adawa ke ƙara ƙaimi wajen neman goyon bayan jama’a kafin zaɓen.

Sai dai wannan furuci ya haifar da muhawara a kafafen sada zumunta, inda wasu ke yabawa da saƙon nasa, yayin da wasu kuma ke tambayar ko ya dace a ƙarfafa mutane su karɓi kuɗin sayen ƙuri’a.

2027: Zan sauke farashin man fetur zuwa Naira N200 kan kowace lita idan na zama shugaban ƙasa — Adebayo ɗan takarar shug...
06/09/2026

2027: Zan sauke farashin man fetur zuwa Naira N200 kan kowace lita idan na zama shugaban ƙasa — Adebayo ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar SDP

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar SDP a zaɓen 2027, Adewole Adebayo, ya yi alƙawarin cewa idan aka zaɓe shi ya zama shugaban ƙasar Najeriya, gwamnatinsa za ta rage farashin fetur zuwa N200 kan kowace lita.

Adebayo ya ce Najeriya na da isassun albarkatun mai da kuma matatun tace mai na cikin gida da za su ba da damar sayar da fetur a farashi mai rahusa, ba tare da komawa tsarin tallafin mai ba.

Ya bayyana cewa matsalar tsadar fetur a Najeriya ta samo asali ne daga rashin inganci, almundahana da kuma yadda ake tafiyar da harkokin man fetur a ƙasar.

A cewarsa, gwamnatinsa za ta gyara tsarin samar da ɗanyen mai, ta ƙarfafa tace mai a cikin gida, tare da rage kuɗaɗen gudanarwa domin tabbatar da cewa farashin fetur ya sauka zuwa N200 kan kowace lita.

Kalaman Adebayo na zuwa ne yayin da batun farashin fetur ke ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan batutuwan da ke jan hankali a siyasar Najeriya gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Maimaita Tsofaffin Zarge-Zarge a kaina Ba Zai Hana Ni kayar da Tinubu zan lashe zaɓen Shugaban Ƙasa Ba — AtikuDan takara...
06/09/2026

Maimaita Tsofaffin Zarge-Zarge a kaina Ba Zai Hana Ni kayar da Tinubu zan lashe zaɓen Shugaban Ƙasa Ba — Atiku

Dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a zaɓen 2027, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa sake fito da tsofaffin zarge-zargen da aka taɓa yi masa ba zai dakatar da shi daga neman shugabancin Najeriya ba.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar ya zargi abokan hamayyarsa da komawa binciko tsofaffin batutuwan da s**a shafe shi, yana mai cewa hakan na faruwa ne saboda ba su da ƙarfin gwiwar fuskantar bincike kan irin tarihin da s**a bari a lokacin da suke mulki.

Atiku ya jaddada cewa duk wani yunƙuri na tayar da tsofaffin zarge-zarge a kansa ba zai karkatar da hankalinsa daga burinsa na tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027 ba.

An wa  Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso kyakkyawar Tarba a Gezawa.An yi wa Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso tarba mai cike da ɗu...
06/09/2026

An wa Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso kyakkyawar Tarba a Gezawa.

An yi wa Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso tarba mai cike da ɗumbin jama'a da nuna ƙauna yayin da ya ratsa don wucewa ta Ƙaramar Hukumar Gezawa da yammacin yau.

📸Hon Saifullahi Hassan

Najeriya Na Bukatar Shugabanni Masu Kishin Ƙasa, Ba Masu kishin Kansu da kansu Ba — TinubuShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinub...
06/09/2026

Najeriya Na Bukatar Shugabanni Masu Kishin Ƙasa, Ba Masu kishin Kansu da kansu Ba — Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa Najeriya na buƙatar shugabanni da 'yan ƙasa masu kishin ƙasa, waɗanda za su fifita muradun jama'a sama da bukatun kansu domin ciyar da ƙasa gaba.

Tinubu ya yi wannan kira ne a Cocin St. Monica Cathedral na Lutheran Church of Christ in Nigeria (LCCN) da ke Jimeta, Yola, yayin bikin godiya da aka shirya domin murnar cika shekaru 70 da haihuwar tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Dr. Boss Mustapha.

A cewarsa, ci gaban Najeriya ba zai tabbata ba sai idan shugabanni da al'umma s**a rungumi gaskiya, kishin ƙasa da hidimtawa jama'a, maimakon fifita muradun kansu.

Shugaban ƙasar ya kuma yabawa Dr. Boss Mustapha bisa gudunmawar da ya bayar wajen bautawa Najeriya a tsawon shekarunsa na hidimar gwamnati, tare da kira ga 'yan Najeriya su haɗa kai domin gina ƙasa mai ci gaba da ɗorewa.

"A Yau Mun Ga Maciya Amana Suna Karɓar Maciya Amana” –Sen Rabi'u kwankwaso ga gwamnatin Jihar kano Jagoran Kwankwasiyya ...
05/09/2026

"A Yau Mun Ga Maciya Amana Suna Karɓar Maciya Amana” –Sen Rabi'u kwankwaso ga gwamnatin Jihar kano

Jagoran Kwankwasiyya kuma ɗan takarar Mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi kakkausar s**a ga jam’iyyar APC yayin da yake karɓar sababbin mambobinta daga Ƙaramar Hukumar Makoda da s**a sauya sheƙa zuwa NDC da Kwankwasiyya a Kano.

A cikin jawabin da ya gabatar, Kwankwaso ya ce abin da ya faru a Kano a yau ranar Asabar ya nuna cewa “Maciya amana suna karɓar Maciya amana.”

Ya ce:
“A yau Asabar mun hangi Maciya amana suna karɓar Maciya amana. Muna farin ciki da ya kasance duk wani shirme ya taru a wuri guda.”

Kwankwaso ya ƙara da cewa al’ummar Jihar Kano ne za su bayar da amsar da ta dace a lokacin zaɓen 2027, inda ya yi ikirarin cewa za su nuna wa waɗanda ya kira maciya amana nauyinsu a akwatin zaɓe.

Ya kuma bayyana cewa zaɓen 2027 ba zai kasance kawai fafatawa tsakanin jam’iyyar NDC da wata jam’iyya ba, illa tsakanin waɗanda ya kira “macuta da azzalumai” da kuma talakawan Najeriya.

Kafin karfe 11 na safe a ranar zaɓe, Amaechi zai umarci magoya bayansa su kaurace wa zaɓe saboda tsoron shan kaye  don k...
05/09/2026

Kafin karfe 11 na safe a ranar zaɓe, Amaechi zai umarci magoya bayansa su kaurace wa zaɓe saboda tsoron shan kaye don ko akwatinsa ba zai iya ci ba ballantana kauyesa na Ubima — Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya sake caccakar tsohon Gwamnan Jihar Rivers, Rotimi Amaechi, inda ya yi hasashen cewa zai umarci magoya bayansa su kaurace wa zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027 tun kafin ƙarfe 11 na safe a ranar zaɓe saboda tsoron shan kaye.

Wike ya bayyana hakan ne yayin da yake raina damar Amaechi a zaɓen 2027, yana mai cewa tsohon gwamnan na iya kasa cin zaɓe har a mazabarsa da ke Ubima, a Jihar Rivers.

“A ranar zaɓe, kafin ƙarfe 11 na safe, Amaechi zai gaya wa mutanensa su kaurace wa zaɓe domin ya san babu yadda zai kayar da mu,” in ji Wike.

Ya ƙara da cewa: “Idan Amaechi ya ci zaɓe a ƙauyensa na Ubima, to sai mu ce ya ci zaɓen gaba ɗaya. Amma ko mazabarsa zai iya ci kuwa?”

Wannan furuci na Wike ya zo ne yayin da rikicin siyasa tsakanin tsoffin abokan tafiyar biyu ke ci gaba da ɗaukar zafi, yayin da kowanne ɓangare ke shirin tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

Kalaman Ministan sun riga sun tayar da kura a tsakanin magoya bayan Wike da Amaechi, lamarin da ke nuna cewa siyasar Jihar Rivers za ta ci gaba da kasancewa mai zafi gabanin zaɓen 2027.

“Kan APC a haɗe Yake a Jihar Katsina Kuma Za Mu Tabbatar da Nasarar Shugaba Tinubu da APC a 2027” — Gwamna RaddaGwamnan ...
05/09/2026

“Kan APC a haɗe Yake a Jihar Katsina Kuma Za Mu Tabbatar da Nasarar Shugaba Tinubu da APC a 2027” — Gwamna Radda

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, Ph.D., CON, ya sake jaddada cewa jam’iyyar APC tana cikin haɗin kai a jihar Katsina, yana mai bayyana cewa jam’iyyar za ta haɗa kai wajen tabbatar da nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima da sauran ‘yan jam’iyyar a Jihar Katsina a zaɓen 2027.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin ƙaddamar da ƙungiyar Tinubu Shettima 2027 (PBAT Door-To-Door) Political Movement, tare da ƙaddamar da ko’odinetocinta na Jihar Katsina.

Ƙungiyar, wadda Shugaban Kamfanin Tantita Security Services, Higher Chief Government Oweizide Tompolo, ya kafa tare da ɗaukar nauyinta, an samar da ita ne domin wayar da kan jama’a da kuma tattara goyon bayan al’umma, domin sake zaɓen Shugaba Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima.

Gwamna Radda ya ce APC tana da ƙarfi kuma tana cikin haɗin kai a Katsina, inda yace zaa ƙarfafa tsarin jam’iyyar daga matakin ƙananan hukumomi 34 zuwa gundumomi 361, domin samun gagarumar nasara ga Tinubu da Shettima a 2027.

Ya kuma buƙaci mambobin ƙungiyar da magoya bayan APC su isar da saƙon jam’iyyar APC zuwa ga al’umma tun daga tushe, su riƙa tattaunawa da jama’a cikin mutunta juna, tare da bayyana manufofi da nasarorin da gwamnatin tarayya da ta jiha s**a samu.

Tun da farko, a jawabinsa na maraba, shugaban ƙungiyar na ƙasa, Comrade Sunday Adenkanbi Asuku, ya bayyana cewa an samar da ƙungiyar ne domin kai saƙon shugaban kasa da jam’iyyar APC kai tsaye ga jama’a, ta hanyar gudanar da tattaunawa da wayar da kan al’umma gida-gida.

A nasa ɓangaren, shugaban kamfanin Tantita Security Services, High Chief Engr. Kestin Ebimorbwei Pondi, wanda ya wakilci wanda ya kafa ƙungiyar, Higher Chief Government Tompolo, ya ce an kafa ƙungiyar ne domin tallafa wa ci gaba da jagorancin gwamnatin Tinubu da jam’iyyar APC.

Ya buƙaci mambobin ƙungiyar su kasance masu zaman lafiya, bin doka da oda da kuma mayar da hankali kan manufar ƙungiyar, tare da yin aiki kafada da kafada da tsarin siyasa da ake da shi domin ƙarfafa goyon bayan jama’a.

A cikin saƙon fatan alheri da ya gabatar, Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Katsina, Dr. Bishir Gambo Saulawa, ya yaba da wannan shiri, tare da tabbatar da cewa jam’iyyar a jihar a shirye take ta yi aiki tare da ƙungiyar da sauran masu ruwa da tsaki wajen ƙarfafa tsarin APC gabanin zaɓen 2027.

Shi ma tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina kuma shugaban shirin Renewed Hope Ambassadors a jihar, Hon. Tukur Ahmed Jikamshi, ya jaddada muhimmancin goyon bayan jama’a daga tushe wajen isar da saƙon nasarorin gwamnatin Shugaba Tinubu da Gwamna Dikko Umaru Radda.

A jawabinsa na godiya, Shugaban ƙungiyar na Jihar Katsina, Dr. Faisal Umar Kaita, ya gode wa jagororin ƙungiyar, Gwamna Radda, shugabannin APC da sauran masu ruwa da tsaki bisa goyon bayan da s**a bayar.

Ya tabbatar da cewa tsarin ƙungiyar na jihar zai yi aiki tukuru wajen ƙarfafa tattara goyon bayan jama’a daga tushe, domin tabbatar da sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Gwamna Dikko Radda da sauran ‘yan jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

Taron ya samu halartar kakakin majalisar dokokin jihar Katsina, Rt. Hon Nasir Yahya Daura, shugabannin APC, jami’an gwamnati, masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa, wakilan matasa da mata, ko’odinetocin ƙungiyar da magoya bayanta daga sassa daban-daban na Jihar Katsina.

An ƙaddamar da tsarin tafiyar ta ƙasa da ƙungiyar a Jihar Katsina, wanda zai jagoranci ayyukanta a ƙananan hukumomi 34 da unguwanni 361 na jihar.

MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government

September 5, 2026.

Da ɗumi-ɗumi: Tsohon janar na soja ya kalubalanci ministan tsaro: Yace dashi ka kawo hujjar cewa el-rufai ya biya ’yan b...
05/09/2026

Da ɗumi-ɗumi: Tsohon janar na soja ya kalubalanci ministan tsaro: Yace dashi ka kawo hujjar cewa el-rufai ya biya ’yan bindiga su kashe mutanen jihar kaduna”

Tsohon Manjo Janar na Rundunar Sojin Najeriya kuma tsohon Babban Kwamandan Runduna ta 1 (GOC 1 Division), Danjuma Hamisu Ali-Keffi, ya yi kakkausar s**a ga Ministan Tsaro, Christopher Musa, kan kalaman da ya yi kwanan nan game da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai.

Ali-Keffi ya bukaci Ministan Tsaron da ya gabatar wa ’yan Najeriya hujjoji masu inganci idan har yana da su da ke nuna cewa El-Rufai ya taba biyan ’yan bindiga domin su kashe mutanen Kaduna. Ya ce irin wannan zargi yana da matuƙar nauyi, don haka bai kamata a yi shi ba tare da cikakkiyar hujja ba.

Tsohon Janar din ya bayyana cewa kalaman Christopher Musa suna nuna alamar siyasa, yana mai cewa bai dace jami’an soja, masu aiki ko wadanda s**a yi ritaya ba, su shiga rikice-rikicen siyasa ko su rika goyon bayan bangaren siyasa.

Ya gargadi manyan hafsoshin soja da su kiyaye mutuncin rundunar soji tare da nisantar duk wani abu da zai iya jefa su cikin takaddamar siyasa, domin hakan na iya rage amincewar jama’a da rundunar.

Ali-Keffi ya jaddada cewa duk wani zargi da ake yi wa mutum, musamman wanda ya shafi rayukan jama’a, dole ne a goyi bayansa da sahihan hujjoji, ba da maganganu kawai ba.

Gwamnatin Tinubu na ci gaba tsare El-rufai na kwanaki 200 amma Yahaya Bello na ci gaba da yawo a bayan kasa –Atiku Abuba...
05/09/2026

Gwamnatin Tinubu na ci gaba tsare El-rufai na kwanaki 200 amma Yahaya Bello na ci gaba da yawo a bayan kasa –Atiku Abubakar

Rundunar tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya yi kakkausar s**a kan ci gaba da tsare tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, wanda ya shafe kwanaki 200 a tsare.

Atiku Abubakar ta bakin Mai magana da yawun Atiku, Paul Ibe, ya ce El-Rufai ba ya neman kariya daga bincike ko shari'a, sai dai yana neman adalci da bin doka ba tare da nuna bambanci ba. Ya zargi gwamnati da tsare El-Rufai saboda dalilan siyasa, yana mai kiran sa "fursunan siyasa."

Paul Ibe ya kuma kwatanta lamarin da na tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, yana cewa duk da shari'ar da yake fuskanta, har yanzu yana gudanar da harkokin siyasa ba tare da tsare shi ba.

Ya yi gargadin cewa bai kamata a yi amfani da hukumomin gwamnati wajen murkushe 'yan adawa gabanin zaɓen 2027 ba.

A gefe guda, El-Rufai na ci gaba da fuskantar tuhume-tuhumen cin hanci da rashawa da wasu zarge-zargen karya doka, waɗanda ya musanta baki ɗaya.

Address

No C320 WorldGate Shopping Center One Man Village Lafia Road N/Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mikiya:

Shortcuts

Share