Mikiya

Mikiya Mikiya jarida ce mallakin Kamfanin Mikiya Online news LTD dake watsa labarai cikin harshen Hausa a Najeriya.
(257)

Whatsapp da kira zaku iya samun ma'aikatan mikiya a wannan lamba >08135583932. Mikiya Kafar labarai ce cikin harshen hausa a Nageriya

05/06/2026

Yadda rundunar sojin Najeriya ke samun Nasara a Yaƙi da miyagu.

LABARI NA MUSAMMAN:APC Ta Naɗa Gwamnan Jigawa Namadi,Uzodimma da sauran Wasu Manya a kwamatin Yaƙin Neman Zaben Ekiti Da...
05/06/2026

LABARI NA MUSAMMAN:

APC Ta Naɗa Gwamnan Jigawa Namadi,Uzodimma da sauran Wasu Manya a kwamatin Yaƙin Neman Zaben Ekiti Daga Matakin ƙasa

Jam’iyyar APC (NWC) ta naɗa Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da sauran manyan jigo-jigowar jam’iyyar, a matsayin mambobin Majalisar Yakin Neman Zaben Gwamnan Jihar Ekiti karkashin tutar APC.

Jam’iyyar ta bayyana cewa nada wadannan shugabanni na cikin karramawa kan jajircewarsu, gagarumar gudummawa, da taka rawar gani wajen bunkasa jam’iyyar APC.

05/06/2026

Jawabin Sen Rabi'u Musa Kwankwaso kan Sardauna da Mal Aminu kano...

Fagen Hujja: Shin Amatsayinka na ɗan jam’iyyar APC dake Arewacin Najeriya wanne Ayyuka ka rike Amatsayin hujjar da zaka ...
04/06/2026

Fagen Hujja: Shin Amatsayinka na ɗan jam’iyyar APC dake Arewacin Najeriya wanne Ayyuka ka rike Amatsayin hujjar da zaka sake tallata shugaba Bola tinubu don ganin an sake zaɓen a zaben 2027 mai zuwa?

Gyaran Kundin Tsarin Mulki Domin Kafa ’Yan Sandan Jihohi Ya Kusa Kammaluwa — Fadar Shugaban ƘasaFadar Shugaban Ƙasa ta b...
04/06/2026

Gyaran Kundin Tsarin Mulki Domin Kafa ’Yan Sandan Jihohi Ya Kusa Kammaluwa — Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa aikin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya domin samar da tsarin ’yan sandan jihohi (State Police) ya kusa kammaluwa.

A cewar gwamnatin tarayya, matakin na daga cikin ƙoƙarin da ake yi na ƙarfafa tsaro da bai wa jihohi damar taka rawar gani wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Masu ruwa da tsaki na ganin cewa idan aka aiwatar da tsarin za a inganta tattara bayanan sirri a matakin ƙananan hukumomi da al’umma, za a samu saurin mayar da martani ga matsalolin tsaro, kuma za a rage nauyin da ke kan 'yan sandan Najeriya.

Sai dai, batun kafa ’yan sandan jihohi ya daɗe yana haifar da muhawara a Najeriya. Yayin da masu goyon baya ke ganin zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro, wasu na nuna damuwa cewa ana iya amfani da shi don dalilan siyasa idan ba a samar da isassun matakan kariya a cikin doka ba.

Idan gyaran kundin tsarin mulkin ya samu amincewar hukumomin da s**a dace, zai zama ɗaya daga cikin manyan sauye-sauyen da ake sa ran za su shafi tsarin tsaro a Najeriya.

Kotun Tarayya Ta Umarci Sowore Ya Fara Kare Kansa a Shari'ar Bata Sunan Tinubu...Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta uma...
04/06/2026

Kotun Tarayya Ta Umarci Sowore Ya Fara Kare Kansa a Shari'ar Bata Sunan Tinubu...

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci mawallafin Sahara Reporters kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na African Action Congress (AAC), Omoyele Sowore, da ya fara gabatar da kariyarsa a shari'ar bata suna ta laifi da aka shigar a kansa kan wasu kalamai da ake zargin ya yi game da Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Mai shari'a, Justice Mohammed Umar, ya yi watsi da bukatar lauyan Sowore ta dage sauraron shari'ar har bayan hutun kotu, sannan ya ba da umarnin a ci gaba da shari'ar a kullum bisa tanadin dokar gudanar da shari'o'in laifuka (ACJA). An kuma tsara cewa Sowore zai fara kare kansa a zaman kotu na gaba.

Ana tuhumar Sowore ne a wata shari'a da Department of State Services (DSS) ke jagoranta, bisa zargin yin kalaman ɓatanci a shafukansa na sada zumunta game da Shugaba Tinubu, sai dai shi Sowore ya musanta zarge-zargen da ake masa.

Najeriya da Wasu Ƙasashe 59 Za Su Fuskanci Ƙarin Harajin Shigo da Kaya na Amurka da Kashi 12.5%Gwamnatin Amurka ta sanar...
04/06/2026

Najeriya da Wasu Ƙasashe 59 Za Su Fuskanci Ƙarin Harajin Shigo da Kaya na Amurka da Kashi 12.5%

Gwamnatin Amurka ta sanar da wani sabon shiri na ƙara harajin shigo da kaya (tariff) tsakanin kashi 10 zuwa 12.5 cikin ɗari kan kayayyakin da ke fitowa daga ƙasashe 60, ciki har da Nigeria.

Najeriya na cikin ƙasashen da za su iya fuskantar ƙarin harajin kashi 12.5 idan shirin ya samu amincewa.

Sai dai, wannan ba mataki ne da ya fara aiki kai tsaye ba. USTR ta bayyana cewa za a fara karɓar ra'ayoyin jama'a da masu ruwa da tsaki kafin a yanke hukunci na ƙarshe, tare da gudanar da sauraron ra'ayoyi a watan Yuli.

Masana tattalin arziki na ganin cewa idan aka aiwatar da harajin, zai iya shafar kasuwanci tsakanin Amurka da ƙasashen da abin ya shafa, musamman a bangaren fitar da kayayyaki zuwa kasuwar Amurka.

Bari yau a raba gardama: 'Yan Arewa ku matso ku bayyana mana ra'ayinku kan Sen Rabi'u Musa Kwankwaso da Atiku Abubakar.R...
04/06/2026

Bari yau a raba gardama: 'Yan Arewa ku matso ku bayyana mana ra'ayinku kan Sen Rabi'u Musa Kwankwaso da Atiku Abubakar.

Rubuta mana zaɓinka da hujjojinka a Kwament Section.

Da ɗumi-ɗumi: Kawo yanzu Gwamna Uba Sani Ya kashe Sama da Naira Biliyan 1bn don Tallafin Karatu da Jin Daɗin Ɗaliban jih...
04/06/2026

Da ɗumi-ɗumi: Kawo yanzu Gwamna Uba Sani Ya kashe Sama da Naira Biliyan 1bn don Tallafin Karatu da Jin Daɗin Ɗaliban jihar Kaduna.

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya kashe sama da Naira biliyan 1 wajen tallafin karatu, rancen ɗalibai da sauran shirye-shiryen tallafa wa ilimi cikin shekaru uku da s**a gabata, a wani mataki da gwamnatin ta ce ya sauƙaƙa wa dubban ɗalibai samun ilimi mai zurfi.

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na jihar, Ahmed Maiyaki, ya bayyana hakan yayin tattaunawa da manema labarai a Kaduna. Ya ce ilimi na daga cikin manyan ginshiƙan manufofin gwamnatin Uba Sani na bunƙasa jarin ɗan Adam.

A cewarsa, gwamnatin ta rage kuɗin makaranta da kashi 50 cikin 100 a duk manyan makarantun gwamnati na jihar domin sauƙaƙa wa iyaye da ɗalibai ɗaukar nauyin karatu.

Maiyaki ya ce an kashe Naira miliyan 493.27 wajen tallafin karatu ga ɗalibai 42 da ke karatu a ƙasashen waje a fannoni masu muhimmanci kamar likitanci, kimiyyar kwamfuta, tsaron intanet da injiniya. Haka kuma, an ware Naira miliyan 425.52 domin tallafa wa ɗalibai marasa ƙarfi da ke karatu a manyan makarantu daban-daban na cikin gida.

Baya ga haka, gwamnatin ta ware Naira miliyan 105 domin shirin rancen ɗalibai, yayin da aka sake Naira miliyan 27.25 don taimaka wa waɗanda s**a kammala karatun lauya wajen biyan kuɗin rajista a Makarantar Horar da Lauyoyi ta Najeriya.

Sakataren Hukumar Tallafin Karatu da Lamuni ta Jihar Kaduna, Yahaya Saleh Ibrahim, ya ce sama da ɗalibai 21,106 ne s**a amfana da shirin a cibiyoyin ilimi fiye da 40 a faɗin ƙasar nan.

Ya ƙara da cewa Kaduna ta zama jiha ta farko a Najeriya da ke gudanar da tsarin tallafin karatu da kuma rancen ɗalibai a faɗin jihar, tare da tsarin biyan bashin da ke bai wa masu cin gajiyar shirin damar zaɓar hanyar da ta dace da su.

Ɗaya daga cikin ɗaliban da s**a amfana da shirin, Al’Ameen Abdul Waheed na Jami’ar Jihar Kaduna (KASU), ya yabawa gwamnatin Uba Sani, yana mai cewa tallafin ya rage wa iyayensa nauyin biyan kuɗin makaranta tare da ba shi damar ci gaba da karatu cikin kwanciyar hankali.

Da ɗumi-ɗumi: Daruruwan matasan garin Lawanti sun fice daga jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar PDP domin marawa Professor Isa ...
04/06/2026

Da ɗumi-ɗumi: Daruruwan matasan garin Lawanti sun fice daga jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar PDP domin marawa Professor Isa Ali Pantami baya a zaben 2027.

A yau Alhamis matasan garin Lawanti dake karamar hukumar Akko jihar Gombe s**a gudanar da taro na musamman na jaddada goyon bayansu ga dan takarar Gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar PDP Professor Isa Ali Pantami (Majidadin Daular Usmaniyya) tare da Hon Gidado Lawanti a matsayin dan takarar Majalisar Tarayya mai wakiltar karamar hukumar Akko.

A yayin taron daruruwan matasa ne s**a bayyana ficewarsu daga jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar PDP domin tabbatar da samun ingantattun shugabanni a zabe mai zuwa.

Address

No C320 WorldGate Shopping Center One Man Village Lafia Road N/Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mikiya:

Share