Mikiya

Mikiya Mikiya jarida ce mallakin Kamfanin Mikiya Online news LTD dake watsa labarai cikin harshen Hausa. Mikiya Kafar labarai ce cikin harshen hausa a Nageriya
(237)

29/07/2025

A daina ɗorawa shugaba Tinubu laifi kan matsalolin Arewa -Gwamna Uba sani

Gwamnan Jihar Kaduna Sen Uba Sani yace “Yawancin mu da muke shugabanni a arewacin Najeriya, ina ganin ya kamata mu fito fili mu dauki laifin matsalar Arewa, ba wanda ya yi magana tsawon shekaru 20 da s**a gabata, idan ba mu dauki kwakkwaran mataki ba, mai yiwuwa wata rana zamu wayi gari ba mu da wani yanki mai suna Arewacin Najeriya, kuma mu daina dora wa Shugaba Tinubu laifi.”

- Gwamna Uba Sani a taron kwana biyu da Sir Ahmadu Bello Memorial Foundation ta shirya

Mun Yanke hukunci Arewa zata marawa Shugaba Bola Tinubu baya domin sake lashe zaɓen 2027 -Gwamna Inuwa Gwamnan jihar Gom...
29/07/2025

Mun Yanke hukunci Arewa zata marawa Shugaba Bola Tinubu baya domin sake lashe zaɓen 2027 -Gwamna Inuwa

Gwamnan jihar Gombe, Yahaya Inuwa, a ranar Talata ya ce Arewa za ta marawa shugaban kasa Bola Tinubu bayan sake cin zaɓe a 2027.

Ya bayyana hakan ne a yayin wani taro na kwanaki biyu da aka gudanar a jihar Kaduna domin tantance ayyukan gwamnatin shugaba Tinubu, musamman yadda ya shafi zamantakewa da tattalin arzikin yankin.

Ya bayyana cewa goyon bayan da aka bai wa Tinubu a lokacin zaben 2023 tuni ya fara samar da sakamako na gaske ta fuskar samar da ababen more rayuwa, tsaro, noma da wutar lantarki.

Taron da Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello ta shirya ya samu halartar Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna, Gwamnan Jihar Gombe, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, Gwamnoni masu ci da kuma wadanda s**a shude, da mai ba Shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, da hafsoshin tsaro, ministoci, da sauran masu rike da mukaman siyasa daga yankin Arewa.

Taron tattaunawa na kwanaki biyu, mai taken “Kimanin alkawurran zabe: inganta hadin gwiwar gwamnati da ‘yan kasa domin hadin kan kasa,” ya samu halartar mahalarta daga jihohin Arewa 19 da kuma Babban Birnin Tarayya.

Da dumi'dumi: Maganganun Omoyele Sowore Ba Abin Mamaki Ba Ne Domin Kwankwaso Ya Bi Ta Kan Kuɗaɗen Mutane A Jihar Kano, C...
29/07/2025

Da dumi'dumi: Maganganun Omoyele Sowore Ba Abin Mamaki Ba Ne Domin Kwankwaso Ya Bi Ta Kan Kuɗaɗen Mutane A Jihar Kano, Cewar Basiru Shuwaki

Tun da farko, Basiru Yusuf Shuwaki ya fara ne da cewa "Ni ina ƙalubalantar Mudugu kan abubuwan da Sawore ya fito ya faɗa a satin nan. Duk mutumin da yake Jihar Kano kuma ya san kansa, ya san irin badaƙakar da aka yi a gwamnatin Rabi'u Musa Kwankwaso. Za a zo a yi abu da sunan aiki amma aikin ba za a yi shi ba. Ko kuma a fara aikin a watsar a kwashe kuɗaɗen". Inji shi.

Basiru wanda ya bayyana haka ta cikin tattaunawarsa da Dokin Ƙarfe TV, ya ba da misali da cewa, "Lokacin da Kwankwaso ya fara aikin gina gadoji, duk gadar da ya fara ba ya iya kammala ta sai gwamnatin Ganduje da ta gaje shi ce ta ƙarasa. Shi da ya gaji Shekaru bai ƙarasa ayyukan da ya tarar an fara ba saboda ba zai samu ko sisi ba". A cewarsa.

"Idan ka ga kuɗaɗen da ake cewa za a sayo magani kwanaki a ƙananan hukumomi, in ka ga kuɗaɗen sun fita hankali. An zo an ƙirƙiri wani abu cewa za a yi tituna na kilo mita biya-biyar a kowace ƙaramar hukuma, har Kwankwaso ya tafi babu ƙaramar hukuma ɗaya a wajen birnin Kano da aka yi wa titin. An fidda kuɗaɗen kuma ba a yi ayyukan ba". In ji shi.

Shuwaki, ya kuma ƙara da cewa, "Ba abin mamaki ba ne dan Sawore ya fito ya ce Kwankwaso ya mallaki manyan gidaje da otel-otel a Abuja da ma wasu ƙasashen ba saboda ya bi ta kan kuɗaɗen mutane. Mu da muke Jihar Kano mun san irin wannan abubuwan za su iya faruwa. Ko yanzu a wannan gwamnati da yake juyawa an zo an yi rabon tallafin Akuyoyi, kowace akuya ɗaya ta tashi ne a ƙalla kan Naira 300,000, kusan kuɗin sa, akuya in dai ba daga Makkah za a kawo ta ba ta ya za ta kai wannan kuɗin". A cewarsa.

Da dumi'dumi : Shugaba Bola Tinubu ya shirya taron Ƙaryata Kwankwaso a jihar Kaduna.Rahotanni na cewa Yanzu haka Gwamnat...
29/07/2025

Da dumi'dumi : Shugaba Bola Tinubu ya shirya taron Ƙaryata Kwankwaso a jihar Kaduna.

Rahotanni na cewa Yanzu haka Gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta fara gudanar da taron kwanaki biyu na 'yan Arewa a jihar Kaduna domin karyata maganar jagoran jam'iyyar NNPP Sen Rabiu Musa Kwankwaso wanda ya ce Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta yi watsi da yankin Arewa kuma tana Inganta kudancin Nageriya a bangaren Rabon Albarkatun arzikin kasa.

Yanzu hakan dai taron yana gidana a jihar Kaduna inda gwamnoni da ministoci suke bayyana irin ayyukan da shugaban kasar bola Tinubu ke gudanarwa a Yankin Arewa.

A kokarin marawa Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, Gwamna Uba Sani ya bi sahun manyan tawagar gwamnati domin tarba...
29/07/2025

A kokarin marawa Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, Gwamna Uba Sani ya bi sahun manyan tawagar gwamnati domin tarbar zakarun WAFCON 2024, Super Falcons na Najeriya, a lokacin da s**a isa Abuja bayan gagarumar nasarar da s**a samu a kasar Morocco.

Gwamna Uba Sani ya yaba da yadda kungiyar ta taka rawar gani, inda ya bayyana ta a matsayin wani abin alfahari ga al’umma. Ya kuma yaba da karimcin da Shugaba Tinubu ya yi na baiwa ’yan wasan kyautar tsabar kudi, gidaje, da karramawar kasa – sako mai karfi ga daukacin ‘yan wasan Najeriya cewa kwazo, sadaukarwa, da jajircewa da gaske na bayar da sakamako mai kyau

Babu wata girgiza, Tabbas Jam'iyyar ADC za ta karbi mulki a 2027 - Atiku Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku A...
28/07/2025

Babu wata girgiza, Tabbas Jam'iyyar ADC za ta karbi mulki a 2027 - Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta hadakar jam’iyyar adawa za ta karbe mulki daga hannun jam’iyyar APC a shekarar 2027.

Atiku, wanda ya koka kan rashin akidar jam’iyyun siyasa a kasar, ya ce jam’iyyar ADC na zuwa ne da akidar da za ta iya magance matsalolin tattalin arzikin kasa da sauran matsalolin da ke addabar kasar.

Ya yi wannan jawabi ne a Ado Ekiti, babban birnin jihar Ekiti yayin kaddamar da majalisar zartaswar ADC ta jihar a karshen mako.

Atiku wanda Farfesa Bayode Fakunle ya wakilta ya ce Najeriya ta sauya a siyasance kuma akwai jam’iyyun siyasa da dama da ba su da akida.

A cewarsa, “An kaddamar da ADC ne kusan makonni uku da s**a wuce, kuma a cikin makonni biyu, ta zama jam’iyya mafi rinjaye a kasar nan, kuma duk wasu jam’iyyu sun riga sun yin kasa

jam’iyya ce mai akida, jama’ar da ke da shirin ceto Nijeriya, domin bai kamata Nijeriya ta zama kasa mai jam’iyya daya ba.

Da dumi'dumi: Barawon Kano Ganduje ya Gina Hotel a Abuja da kuɗin da zai iya Gyara makarantun Jihar Kano -Sowore Ɗan gwa...
28/07/2025

Da dumi'dumi: Barawon Kano Ganduje ya Gina Hotel a Abuja da kuɗin da zai iya Gyara makarantun Jihar Kano -Sowore

Ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowore ya wallafa a shafinsa na Facebook yana mai cewa Ina sane da wani ƙaton otel da tsohon ɓarawon Kano wato Abdullahi Gandollar ya gina. Wannan otel kuwa yana da titin Ƙasa otel in take da daf da Cibiyar Rundunar Sojojin Sama ta Nijeriya da ke Abuja (NAF), kuma girmansa ya kai ya gyara duk makarantu Kano, sai dai kuma suma ɓarayin NNPP ba su da wani bambanci.

Babu wani sauran farfaganda da ya rage.

Da dumi'dumi: Gwamna Uba sani Yace a kaddamar da rabon taki ga manoma a ranar Asabar.Gabanin bikin kaddamar da shirin a ...
28/07/2025

Da dumi'dumi: Gwamna Uba sani Yace a kaddamar da rabon taki ga manoma a ranar Asabar.

Gabanin bikin kaddamar da shirin a hukumance da za a yi a ranar Asabar 2 ga watan Agusta, don rabon tireloli 300 ga manoma dubu ɗari 100,000 na taki kyauta da gwamnatin jihar Kaduna ta shirya, karkashin jagorancin Gwamna Sanata Uba Sani, shugaban kwamitin kuma kwamishinan noma, Hon Malam Murtala Dabo ne ya jagoranci taron na biyu da kwamitin

Idan dai ba a manta ba a shekarar da ta gabata ne gwamnatin jihar ta raba tireloli 500 na takin zamani kyauta ga kananan manoma sama da 120,000 a fadin jihar wanda hakan ya kara habaka harkokin noma sosai.

Taron na gudana ne a dakin taro na sakataren gwamnatin jihar

📷 Abdallah Yunusa Abdallah

Da dumi'dumi: Jam'iyyar SDP ta kori Nasir El-rufa'i na tsawon Shekaru talatin.Kwamitin ayyuka na kasa, na Social Democra...
28/07/2025

Da dumi'dumi: Jam'iyyar SDP ta kori Nasir El-rufa'i na tsawon Shekaru talatin.

Kwamitin ayyuka na kasa, na Social Democratic Party, ya kori tsohon gwamnan Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, daga jam’iyyar.

SDP ta ayyana El-Rufai a matsayin wanda ba zai iya alaƙanta kansa da jam’iyyar ba a kowane matsayi na tsawon shekaru 30 masu zuwa.

Da dumi'dumi: Ga jaddawalin Asibitocin matakin lafiyar farko (Primary Health Care Centres) da Gwamnatin jihar Kano karka...
28/07/2025

Da dumi'dumi: Ga jaddawalin Asibitocin matakin lafiyar farko (Primary Health Care Centres) da Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Engr Abba Kabir Yusuf Za ta gyara guda ɗari biyu da uku 203.

Uwargidar Tsohon Shugaban Kasa A’isha Buhari ta koma gidan Shugaba Buhari na Kaduna. A ranar Lahadi ne mataimakiyar gwam...
27/07/2025

Uwargidar Tsohon Shugaban Kasa A’isha Buhari ta koma gidan Shugaba Buhari na Kaduna.

A ranar Lahadi ne mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe, ta jagoranci tawagar jihar domin tarbar uwargidan tsohon shugaban kasa, A’isha Buhari, yayin da ta dawo Kaduna.

Tare da rakiyar shugabar masu rinjaye na majalisar dokokin jihar Kaduna Rt. Hon. Munira Suleiman Tanimu, da wasu manyan jami’an gwamnati, Dr. Balarabe ne s**a tarbi Misis Buhari da ‘yan uwanta a filin jirgin sama na Kaduna a madadin gwamnatin jihar.

An Tarbi A'isha ne cikin jin dadi da ban girma, wanda ke nuna irin yadda jihar ke ci gaba da mutunta marigayi tsohon shugaban kasa da iyalansa da irin gudunmawar da s**a bayar wajen ci gaban kasa.

Daga bisani mataimakiyar gwamnan ta raka uwargidan Buhari da tawagarta zuwa gidansu dake Kaduna.

Jonathan ne ya fi kowa dacewa ga matsalolin Arewa a zaɓen 2027 – Jigon PDP Umar Sani, jigo a jam’iyyar PDP, ya ce tsohon...
27/07/2025

Jonathan ne ya fi kowa dacewa ga matsalolin Arewa a zaɓen 2027 – Jigon PDP

Umar Sani, jigo a jam’iyyar PDP, ya ce tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kasance mafi kyawun zabi ga arewa idan jam’iyyar adawa ta yanke shawarar tsayar da tikitin takarar shugaban kasa a 2027 zuwa kudu.

A wata hira da aka yi da shi a gidan Talabijin na Trust, Sani, wanda ya kasance babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo, ya ce duk da cewa ba ya adawa da sauya mulki tsakanin yankuna, amma dole ne a gudanar da shi ta hanyar adalci da ayyukan tarihi na kowane yanki a cikin jam’iyyar PDP.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mikiya:

Share