Mikiya

Mikiya Mikiya jarida ce mallakin Kamfanin Mikiya Online news LTD dake watsa labarai cikin harshen Hausa a Najeriya.
(246)

Whatsapp da kira zaku iya samun ma'aikatan mikiya a wannan lamba >08135583932. Mikiya Kafar labarai ce cikin harshen hausa a Nageriya

Bana siyasantar da matsalar tsaro ka daina Anfani da matsalar tsaro kana ɓata min suna -Sen Barau Ya Gargadi Gwamna Abba...
29/11/2025

Bana siyasantar da matsalar tsaro ka daina Anfani da matsalar tsaro kana ɓata min suna -Sen Barau Ya Gargadi Gwamna Abba

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya gargadi Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, da ya daina siyasantar da batun tsaro, inda ya ce ya k**ata gwamnan ya maida hankali kan warware matsalolin da s**a addabi jihar.

Sanata Barau ya maida martani ne bayan gwamnatin Kano ta zarge shi da cewa maganganunsa na iya kawo tarnaki ga kokarin tsaro. Ya ce babu ko sau daya da ya yi kalaman da za su iya tayar da tarzoma, yana kalubalantar gwamnati ta fito da bidiyon da take ikirari akai.

A wata sanarwa da ke dauke da sa hannun mai taimaka masa kan yada labarai, Ismail Mudashir, Sanata Barau ya ce:
“Gwamnati ta karyata aiki, ta koma kirkirar karya don bata suna. A maimakon haka, ya k**ata su hada kai wajen magance barazanar tsaro da ke shiga wasu yankunan Kano.”

Barau ya kuma zargi gwamnatin Kano da kasawa, yana cewa jihar ta yi baya a fannin cigaba saboda rashin ingantaccen jagoranci. Ya ce Kano ta taba zama kusa da Lagos a harkar cigaba amma yanzu an karkata saboda mulkin da bai da tsari.

Sanatan ya lissafa gudunmawar da ya bayar wajen inganta tsaro, ciki har da:

Ba da motocin aiki ga rundunar ’yan sanda a mazabarsa da wasu yankunan jaha

Ba da babura ga dukkan ’yan sanda a Kano ta Arewa

Gina da gyaran ofisoshin ’yan sanda da DSS

Taimakawa wajen kafa makarantu na horas da jami’an tsaro (NSCDC – Gwarzo, Police Commission – Kabo, Immigration – Bichi)

Sanya fitilun tituna na solar a fadin mazabarsa da wasu sassan Kano

Ya ce gwamnatin Kano ta koyi aiki, ta daina bata masa suna.

Rashawa: Naji daɗi da Hukumar EFCC zata Gurfanar da Malami SAN Kan badakalar Tiriliyan 2.15tr -Hon. Khalifa PasaliA yayi...
29/11/2025

Rashawa: Naji daɗi da Hukumar EFCC zata Gurfanar da Malami SAN Kan badakalar Tiriliyan 2.15tr -Hon. Khalifa Pasali

A yayin da ake ci gaba da fama da tsadar rayuwa da rikice-rikicen tsaro a fadin Najeriya, Hon. Khalifa Pasali ya ce dole ne a dage wajen k**a da gurfanar da manyan jami’an gwamnati da ake zargin sun tabka babbar almundahana, musamman wadanda ake alakanta da karkatar da dukiyar kasa sama da tiriliyan ₦2.15, ciki har da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami SAN.

A cewar Khalifa Pasali, a halin da talakawa ke kokawa da yunwa, rashin magani, da tsaro, rashin tausayi ne a ji ana batar da makudan kudaden da za su iya ceton rayuka, inganta ilimi, da karfafa rundunar tsaro. Ya ce dukiyar da ake zargin ta bace za ta iya gina asibitoci, farfado da makarantu, da sanya dubban matasa cikin ayyukan yi.

Pasali ya jaddada cewa ci gaba da k**a manyan da ake zargi da satar dukiyar kasa ba wai siyasa ba ce, aikin gyaran kasa ne. Ya ce idan ba a hukunta masu laifi daga cikin manyan ba, to ba za a taba samun tsoron doka a tsakanin masu rike da madafan iko ba.

A bisa haka, ya yi kira ga EFCC da sauran hukumomin yaki da rashawa da su ci gaba da bincike ba tare da nuna bambanci ba, domin a tabbatar da cewa duk wanda ya tabka laifi zai fuskanci hukunci.

Ya kara da cewa Najeriya ba ta rasa arziki ba, amma an bar ta a hannun mutanen da s**a gina kansu a kan dukiyar jama’a. Saboda haka, matakin k**a irin wadannan manyan zai dawo da martabar kasa, ya karfafa amincin jama’a, kuma ya ba da sako mai karfi cewa lokacin barin talakawa cikin kangin talauci yayin da ake sace tiriliyan-tiriliyan ya wuce.

Ya kammala da cewa: “Talakawa sun gaji da wahala. Idan Najeriya za ta tashi, dole ne mu yaki rashawa daga tushe kuma hakan ya fara da manyan da s**a cinye dukiyar jama’a."

TSARO: Tunda gwamnatin shugaba Bola tinubu ta gaza kare rayukan 'yan Najeriya muna da damar da zamu kira ƙasashen wajen ...
28/11/2025

TSARO: Tunda gwamnatin shugaba Bola tinubu ta gaza kare rayukan 'yan Najeriya muna da damar da zamu kira ƙasashen wajen domin kawo ƙarshen ta’addanci a Najeriya -Obasonjo

Tsohon Shugaban Ƙasa, Chief Olusegun Obasanjo, ya soki gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan yadda ake tafiyar da yaƙi da ta’addanci a Najeriya, yana mai cewa ƙasar nan tana da cikakkiyar ƙarfi da fasaha da za ta bi ta ko’ina ta kawar da ’yan ta’adda—amma rashin ƙuduri da rikice-rikicen siyasa ke hana hakan faruwa.

A cikin jawabin da ya yi cikin zafi, Obasanjo ya tambaya:

“Me yasa muke ba da haƙuri? Me yasa ake tattaunawa da ’yan ta’adda? Najeriya na da damar da za ta bi ta har gida ta shafe su. Idan gwamnati ta kasa kare ’yan ƙasa, to me ya rage?”

Tsohon shugaban ya ce ya zama bayyane yanzu cewa gwamnatin Tinubu “ta kasa samar da cikakken kariya ga al’umma,” don haka ya bayyana goyon bayansa ga shigo da ƙasashen waje domin ba da gudunmawa wajen murƙushe kungiyoyin ta’addanci da ke addabar sassan kasar.

A cewarsa, matsalar tsaro ta kai matakin da ba za a ɓoye gaskiya ba, kuma lokaci ya yi da “duk wanda zai iya taimaka wa Najeriya” ya shiga.

Da dumi'dumi: An gano yadda tsohon ministan shari'a Malami ya sace Kuɗin da S**a Kai Naira Triliyan 2.15Tr An kafa kwami...
28/11/2025

Da dumi'dumi: An gano yadda tsohon ministan shari'a Malami ya sace Kuɗin da S**a Kai Naira Triliyan 2.15Tr An kafa kwamiti bincike -EFCC

Sabbin bayanai da Mikiya ta tattara wanda Jaridar TheCable ta wallafa sun tabbatar da cewa binciken da ake yi wa tsohon Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Malami (SAN), na kara zurfi bayan gano mu’amaloli biyar masu cike da duhu da aka gudanar a lokacin da yake kan karagar mulki.

Rahotanni sun nuna cewa wannan jerin mu’amaloli sun kai dala biliyan 1.436, daidai da naira triliyan 2.154 idan aka maida su zuwa kudin gida naira.

Ga cikakken bayani kan kowacce mu’amala da kuɗin da aka zarga:

Biyan Global Steel — $496m (₦744bn)

Ana tuhumar biyan $496,000,000 ga Global Steel Holdings Ltd kan batun Ajaokuta, duk da cewa kamfanin ya dade da cewa bai neman diyya.
Da naira: ₦744,000,000,000 (₦744bn)

Paris Club Judgment — $419m (₦628.5bn)

Kwamitin bincike na nazarin yadda aka amince da biyan $419,000,000 ga wasu “consultants” da s**a ce sun taimaka wajen dawo da kudin Paris Club ga jihohi.
Da naira: ₦628,500,000,000 (₦628.5bn)

Yarjejeniyar Mambilla da Sunrise — $200m (₦300bn)

Ana binciken amincewar da aka yi na biyan Sunrise Power $200,000,000 a rikicin aikin Mambilla, duk da cewa aikin bai fara ko da matakin farko ba.
Da naira: ₦300,000,000,000 (₦300bn)

Kudin Zambar Abacha — $321m (₦481.5bn)

Akwai zargin maimaita kudin lauya wajen dawo da $321,000,000 na kudin Abacha daga Switzerland batu da ke tayar da kura a ma’aikatar.
Da naira: ₦481,500,000,000 (₦481.5bn)

Sayar da Kadarorin EFCC — Biliyoyin Naira

Sashe mafi duhu cikin zargin shi ne yadda aka sayar da kadarorin da EFCC ta kwato daga manyan mutane.
Ba a bayyana adadin kudaden ba, amma majiyoyi sun ce sun kai biliyoyin naira da ba a san tak**aiman su ba.

Jimilla Mai Tayar da Hankali
Jimillar Dala:

$1,436,000,000
(Dala biliyan 1.436)

Jimillar Naira (ba tare da kadarorin EFCC ba):

₦2,154,000,000,000
(Naira triliyan 2.154)

Tsohon ministan shari'ar dai Abubakar Malami yanzu haka yana neman zama gwamnan jihar Kebbi a zaben 2027.

Rashin Shehu Dahiru daidai Yake da rasa mutane bilyan ɗaya  -Fatima Tabatul. Fatima Tabatul ta wallafa a shafinta na Fac...
28/11/2025

Rashin Shehu Dahiru daidai Yake da rasa mutane bilyan ɗaya -Fatima Tabatul.

Fatima Tabatul ta wallafa a shafinta na Facebook cewa, rashin fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, babban rashi ne da ya yiwa ƙasa ɗummamar nauyi.

A cewarta, “rashin Sheikh Dahiru Usman Bauchi a wannan ƙasa tamkar rashin mutum biliyan ɗaya ne, domin a wannan zamanin samun irinsa sai an tona — astagfirullah.”

Manyan shugabannin Najeriya sun bayyana bayyana cewa irin hazaka, ilimi da hikimar Marigayi Sheikh Dahiru ba kasafai ake samun irinsu ba, lamarin da ya sa rasuwar tasa ta bar gibi mai cike da alhini ga al’umma.

JADMISSION – HANYARKA MAI SAUƘI ZUWA GA SAMUN ADMISSION! Shirin karatu ya fi sauƙi yanzu! Jadmission na kawo maka komai ...
28/11/2025

JADMISSION – HANYARKA MAI SAUƘI ZUWA GA SAMUN ADMISSION!

Shirin karatu ya fi sauƙi yanzu! Jadmission na kawo maka komai a wuri guda — cikin sauri, sauƙi da tabbatacciyar amana.

PIN ɗin Jarabawa?
WAEC, NECO, JAMB ko NABTEB — ka danna, ka samu nan take!

Admission a tabbace?
Muna taimaka maka samun gurbin jami’a cikin sauƙi ba tare da wahala ba.

Tallafin karatu (Scholarships)?
Akwai dama da dama da za ka iya samu cikin sauƙi ta hanyar Jadmission.

Horon JAMB na musamman?
Mun tanadi ingantaccen horo da zai tabbatar ka yi nasara a jarabawar JAMB.

Ka shiga yanzu: 👉 Jadmission.com

Jadmission – Mataki na farko zuwa makomarka!
Ku yi share wa ɗalibai domin dama bata jira!

Da dumi'dumi: Ganduje da Barau ne ke Tunzura 'yan bindiga domin su kai hare haren ta'addanci a jihar kano -Cewar Gwamnat...
28/11/2025

Da dumi'dumi: Ganduje da Barau ne ke Tunzura 'yan bindiga domin su kai hare haren ta'addanci a jihar kano -Cewar Gwamnatin Jihar Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta fito ƙarara tana zargin tsohon gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, da rawar gani wajen tunzura ’yan ta’adda su kai hare-hare a wasu yankunan jihar.

A wani labarin da ta wallafa Nasara radio Najeriya na cewa Majalisar Zartarwar Kano, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta ce akwai alamun wadannan shugabanni na amfani da ’yan ta’adda domin tayar da tarzoma da tada hankalin jama’a a wasu sassan Kano. Ta nemi hukumomin tsaro su gaggauta k**a waɗanda ake zargi domin kare rayuka da dukiyoyi.

Gwamnati ta jaddada cewa ba za ta lamunci duk wani yunkurin tada tarzoma ko amfani da miyagun ’yan bindiga domin cimma siyasa ba, tana mai kira ga jama’a su kasance cikin shiri su kuma taimaka wajen bai wa jami’an tsaro duk wata sahihiyar bayani.

Sanata Ali Ndume ya ce sanatoci na samun albashi fiye da sojojin da ke sadaukar da rayukansu, yana kira ga gwamnati ta g...
28/11/2025

Sanata Ali Ndume ya ce sanatoci na samun albashi fiye da sojojin da ke sadaukar da rayukansu, yana kira ga gwamnati ta gaggauta ƙara albashi da alawus na rundunonin tsaro domin inganta tsaro a ƙasar.

Daga Wajen Jana'izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi.
28/11/2025

Daga Wajen Jana'izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

HOTO: Lokacin da Sen Kashim Shettima ya kwashi Albarka daga marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi.
28/11/2025

HOTO: Lokacin da Sen Kashim Shettima ya kwashi Albarka daga marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Da dumi'dumi: Sodangi Ya fice daga jam’iyyar PDP. fitaccen matashi mai tasiri a harkokin siyasa, Abubakar Sodangi, ya sa...
28/11/2025

Da dumi'dumi: Sodangi Ya fice daga jam’iyyar PDP.

fitaccen matashi mai tasiri a harkokin siyasa, Abubakar Sodangi, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) bayan dogon tunani da tattaunawa da shi da kansa.

A wasikar da ya aikewa shugaban jam’iyyar a Gundumar Bukan Sidi, Sodangi a jihar Nasarawa ya bayyana cewa ya yanke wannan shawara ne saboda “dalilai na kansa,” tare da nuna godiya ga jam’iyyar bisa damar da ta ba shi tun daga matakin farko na siyasa har zuwa yanzu.

Sodangi, wanda ya taba neman zama National Youth Leader na PDP, ya ce tafiyarsa a yanzu za ta ci gaba da karkata ne ga aikin tallafa wa matasa a Najeriya, musamman ta hanyar Nigerian Youth Development Forum, kungiyarsa da ke aikin gina karfin matasa da habaka shigarsu cikin zartaswa.

Ficewarsa na zuwa ne a wani lokaci da PDP ke fama da rikice-rikice da sake fasalin shugabanci a matakai daban-daban, abin da zai iya tsananta yanayin rashin daidaito a jam’iyyar, musamman a jihar Nasarawa inda Sodangi ya fito.

HOTO: Mahalarta jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
28/11/2025

HOTO: Mahalarta jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Address

No C320 WorldGate Shopping Center One Man Village Lafia Road N/Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mikiya:

Share