Mikiya

Mikiya Mikiya jarida ce mallakin Kamfanin Mikiya Online news LTD dake watsa labarai cikin harshen Hausa. Mikiya Kafar labarai ce cikin harshen hausa a Nageriya
(244)

09/10/2025

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya mayar da karatun manyan Makarantun gabada Sakandari cikin sauki, za a baka bashi ka biya kudin makaranta, sannan duk wata a baka kudin kashewa.

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kamu da Daure Shugaban INEC, Prof. Mahmood YakubuWata babbar kotun tarayya da ke Osogbo, Jihar Osu...
09/10/2025

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kamu da Daure Shugaban INEC, Prof. Mahmood Yakubu

Wata babbar kotun tarayya da ke Osogbo, Jihar Osun, karkashin jagorancin Justice Adefunmilola Demi-Ajayi, ta bayar da umarnin kamu da kuma daure Shugaban Hukumar Zabe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, bisa kin bin hukuncin kotu.

Alkalin ya bayyana cewa dakatar da aiwatar da hukuncin kotu abu ne da bai dace da mutumin da ke rike da mukamin gwamnati ba, don haka ya bayar da umarnin a k**a shi tare da garkame shi nan take.

Wannan hukunci ya jawo cece-kuce a fadin kasar, inda masu lura da al’amuran shari’a ke cewa lamarin na iya haifar da tasiri mai zurfi a cikin tsarin zaben kasar nan.

Najeriya Ta Fice Daga Halin Rugujewar Tattalin Arziki — Sarkin Kano Sanusi IIMai Martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II...
09/10/2025

Najeriya Ta Fice Daga Halin Rugujewar Tattalin Arziki — Sarkin Kano Sanusi II

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II, ya bayyana cewa Najeriya ta kauce daga halin rugujewar tattalin arziki, sak**akon sauye-sauyen da Babban Bankin Ƙasa (CBN) ya aiwatar a cikin watanni kadan da s**a gabata.

Sanusi II, wanda ya kasance tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya, ya bayyana hakan ne yayin wani taron tattaunawa kan tattalin arziki a Abuja, inda ya yaba wa CBN bisa jajircewar da yake nunawa wajen farfaɗo da darajar Naira da daidaita kasuwar kuɗi.

Ya ce matakan gyara da ake aiwatarwa yanzu suna da wahala, amma suna nuni da dawowar kwanciyar hankali da ingantuwar tattalin arzikin ƙasa.

“Najeriya ta sha wahala saboda rashin daidaiton manufofin kuɗi a baya, amma yanzu muna ganin alamar gyara. Idan aka ci gaba da wannan tsari, tattalin arzikin zai farfaɗo sosai,” — in ji Sanusi II.

Da dumi'dumi: 'Yan Bindiga Sun Kai Hari a Jihar Zamfara, Sun Sace Mutane 30Wasu 'yan bindiga sun kai mummunan hari a wan...
09/10/2025

Da dumi'dumi: 'Yan Bindiga Sun Kai Hari a Jihar Zamfara, Sun Sace Mutane 30

Wasu 'yan bindiga sun kai mummunan hari a wani kauye da ke cikin Jihar Zamfara, inda s**a sace akalla mutum 30 daga cikin mazauna yankin.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun kutsa cikin garin ne da daddare, inda s**a bude wuta kan mazauna kafin su yi awon gaba da mata, maza da matasa.

Wani mazaunin yankin ya ce babu jami’an tsaro a lokacin da harin ya faru, lamarin da ya bai wa 'yan bindigar damar gudanar da ta’addancinsu cikin sauki.

Har yanzu ba a samu bayani daga hukumomin tsaro ko gwamnatin jihar Zamfara ba dangane da harin.

Zamfara ta dade tana fama da matsalar 'yan bindiga da ke addabar al’umma tare da sace mutane domin neman kudin fansa.

Babu talauci k**ar Yadda bankin duniya ya bayyana akwai talauci k**ar haka a Nageriya -Shugaba TinubuFadar Shugaban Ƙasa...
09/10/2025

Babu talauci k**ar Yadda bankin duniya ya bayyana akwai talauci k**ar haka a Nageriya -Shugaba Tinubu

Fadar Shugaban Ƙasa karkashin jagorancin shugaba Bola Tinubu ta yi watsi da sabon rahoton tattalin arziƙi da babban mai ba da lamuni na ƙasa da ƙasa na Bankin Duniya da ya fitar, wanda ya ƙiyasta cewa mutane miliyan 139 a Najeriya na rayuwa cikin kangin talauci.

Fadar ta bayyana cewa wannan ƙididdiga ba ta dace da ainihin halin tattalin arziƙin ƙasar ba, tana mai cewa rahoton ya nesanta da gaskiyar abin da ke faruwa a Najeriya.

09/10/2025

Ga Sako na musamman daga Sheikh Prof Ali Isa Pantami..

Tafiyar karramawa ta zama wulakanci: yadda aka sassare matashin Najeriya a Niger — inji Hamid Abdu DutseWani matashi ɗan...
08/10/2025

Tafiyar karramawa ta zama wulakanci: yadda aka sassare matashin Najeriya a Niger — inji Hamid Abdu Dutse

Wani matashi ɗan Najeriya mai suna Suleman Rabi’u wanda ya yi tattaki da keke daga Najeriya zuwa ƙasashen Niger da Burkina Faso, ya gamu da mummunar ƙaddara a hanya bayan da ’yan fashi s**a tare shi a dajin Kankiya, s**a sassare shi tare da dauke masa waya da kuɗaɗensa.

Rahotanni sun nuna cewa, an same shi a daji cikin jini, bayan ya suma sak**akon dukan da aka yi masa da gindin bindiga. Wannan lamari ya tayar da hankali matuƙa, musamman ganin cewa matashin ya fito ne da nufin karrama ƙasashen Afrika ta hanyar wannan tattaki na zaman lafiya da haɗin kai.

Sai dai, a cewar Hamid Abdu Dutse, wannan al’amari ya zama hujja mai ƙarfi da ke nuna yadda ƙasashen irin su Niger ke amfani da furofaganda wajen ɓata sunan Najeriya a idon al’umma.

“Idan har da gaske ne, me yasa mutum zai zaɓi yin barci a daji a kusa da garin Kankiya alhali akwai garuruwa da dama da zai iya kwana a cikinsu cikin aminci?
Sannan, idan manufarsa ita ce tafiya zuwa Niger, me ya sa ya bi ta Jibiya, maimakon Daura wadda ita ce hanyar kai tsaye? Duk wannan yana nuna akwai wata manufa ta furofaganda da aka shirya don zuga jama’a,” in ji Hamid Dutse.

Ya ƙara da cewa, irin waɗannan labaran ana tsara su ne domin ɗauke hankalin jama’ar ƙasashen da suke cikin matsin tattalin arziki, tare da haddasa ƙiyayya ga Najeriya, ƙasar da take da ƙarfi a yankin Afrika ta Yamma.

“Ya k**ata gwamnatin Najeriya ta tashi tsaye ta fuskanci wannan barazana ta furofaganda wadda take neman lalata martabar ƙasarmu. Ya zama wajibi mu ƙara wayar da kan jama’a game da irin wannan dabarar ta ɓata suna,” in ji shi.

A halin yanzu, jama’a da dama suna nuna bakin ciki da fushi kan yadda aka zalunci wannan matashi wanda ya bar gidansa da nufin kawo ɗaukaka ga nahiyar Afrika, amma aka mayar da niyyarsa ta alheri zuwa labarin wulakanci da azabtarwa.

Wasu na ganin cewa, wannan lamari ba wai kawai cin zarafi ba ne, har ma tuhuma ce ta furofaganda da ke neman raba kawunan ƙasashen da ya k**ata su haɗu domin cigaban yankin.

📰 Mikiya Online News Hausa
“Gaskiya ba ta buƙatar ƙawanya.”

“Babu Wani Gwamna da Ya Samar da Zaman Lafiya a cikin karamin lokaci Kamar Uba Sani a duk Yammacin Afrika — Ga Abin da Y...
08/10/2025

“Babu Wani Gwamna da Ya Samar da Zaman Lafiya a cikin karamin lokaci Kamar Uba Sani a duk Yammacin Afrika — Ga Abin da Ya Yi

Kaduna, Cikin ƙanƙanin lokacin mulki, Gwamna Uba Sani ya ɗaga murya kan sabuwar “Tsarin Zaman Lafiya” a jihar Kaduna da ma yankin Yammacin Najeriya baki ɗaya. Yayin da wasu s**a ɗauka wannan maganar babban yabo ne fiye da komai, akwai ayyuka da dama da ke nuna cewa akwai canji — kuma waɗannan ne za mu haskaka maka a wannan babban labari.

Muhimman Abubuwa da Za a Koya a Karkashin Gwamnatin Uba Sani

Gwamnati ta shirya Taron Tattaunawa na Yammacin Arewa kan yadda za a dakile ta’addanci, inda gwamnatin Kaduna ta karɓi bakuncin hukumomi da gwamnonin jihohin yankin.

An rattaba hannu kan yarjejeniyar haɗin kai da The Kukah Centre domin gina tsarin tsaro na al’umma, wanda zai haɗa jami’an tsaro da ƙungiyoyin gari, tare da ba da horo da ƙarfafa basira.

Gwamna ya jaddada cewa ba za a iya magance rashin tsaro da mak**ai kaɗai ba, amma ana buƙatar matakai masu zurfi: ilimi, ayyukan yi, haɗin kai tsakanin al’umma, shugabanni da gwamnati.

Ayyukan gine-gine, hanyoyi, makarantu da asibitoci da farfadowa a cikin sassan jihar sun shiga ajandar gwamnati, domin ƙarfafa rayuwar al’umma ta hanyar samar da bunƙasa tsaro a wuraren da tsaro ke da rauni.

Hukumomin ƙetare sun yaba da cigaban tsaro: Gwamnatin Ingila (UK) ta nuna farin ciki da yadda Kaduna ta sauya matsayin ɗaukaka samun tsaro a cikin karamin lokaci, daga “red” zuwa “amber” a ƙididdigar tafiyar duniya.

Farfadowar harkokin ilimi da kasuwanci a yankuna da aka ce suna fama da rashin tsaro sun nuna cewa al’umma sun fara samun nutsuwa. Misali, Mataimakin Jami’ar Ahmadu Bello ta yaba da ganin yanayi na zaman lafiya a sassan kudu-kaduna.

misali: A ranar 7 ga Maris, 2024, an sace ɗalibai da malamai daga makarantar Kuriga, Kaduna. Bayan wasu kwanaki, sojoji tare da haɗin kai da gwamnati s**a yaƙi lalka, inda aka ce ‘yan ta’adda sun sallami mutane 137 l zargin an sace su.

1. Manufar “Kaduna Peace Model”

Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa tsarin sa na tsaro bai dogara kawai ga aikin soja ba zai haɗa matakan hikima (non-kinetic), tattaunawa, ilimi, ɗaukaka tattalin arziki da shigar da al’umma cikin yanke shawara.
An kuma rubuta cewa wannan tsarin “Kaduna Peace Model” ya fara jan hankali har ga shugaban tsaro na ƙasa Mallam Nuhu Ribadu, inda ya kira jihar Kaduna a matsayin misali ga sauran jihohi.

2. Taron Yammacin Arewa da Hadin Kai

Kaduna ta karɓi bakuncin taron ƙasa da ƙasa da gwamnonin jihohin Arewa-Yamma, hukumomin tsaro da ƙungiyoyin jama'a domin tattaunawa kan Preventing and Countering Violent Extremism (PCVE).
Gwamnan ya yi jawabi inda ya ce dole ne a tashi ƙasa da tsarin da ya rataya da “mak**ai kawai.”

Bincike ya nuna kawo yanzu dai babu wani gwamna da ya bayyana cewa ya iya samar da tsaro cikin karamin lokaci hakan sai gwamna Uba sani na jihar Kaduna.

Sabon Sauyi daga Smile Voice: Sauƙin Kira Tsakanin Ciki da Wajen Ƙasa Kamfanin Smile ya ƙirƙiro sabuwar fasaha mai suna ...
08/10/2025

Sabon Sauyi daga Smile Voice: Sauƙin Kira Tsakanin Ciki da Wajen Ƙasa

Kamfanin Smile ya ƙirƙiro sabuwar fasaha mai suna Smile-Voice E-SIM, domin sauƙaƙa wa ‘yan Najeriya da ke gida da ƙasashen waje yin kiran waya cikin sauƙi da arha.

Abin burgewa shi ne, idan mutum yana Najeriya yana amfani da Smile-Voice, kuma ɗan uwansa ma yana da irin wannan layi, to kiran da za su yi tsakaninsu kyauta ne gaba ɗaya!

Haka kuma, ga ‘yan Najeriya da ke ƙasashen waje, Smile-Voice na basu damar yin kira cikin sauƙi k**ar suna gida — domin suna iya kiran kowanne layin sadarwa irin su MTN, Glo, Etisalat (9mobile), har da Airtel (Zain) cikin farashi mai rahusa.

Smile-Voice E-Sim — haɗin kai tsakanin gida da ƙasashen waje cikin murya ɗaya!

Hukumar Karɓar Haraji ta Jihar Kano ta Shirya Tattara harajin Naira Biliyan N180 a Shekarar 2026.Hukumar Karɓar Haraji t...
08/10/2025

Hukumar Karɓar Haraji ta Jihar Kano ta Shirya Tattara harajin Naira Biliyan N180 a Shekarar 2026.

Hukumar Karɓar Haraji ta Jihar Kano (KIRS) ta bayyana shirin ta na ƙara karɓar kudaden shiga zuwa Naira biliyan 15 a kowane wata daga cikin shekarar 2026, wanda hakan zai kai jimillar Naira biliyan 180 a shekara.

Wannan mataki, a cewar hukumar, yana cikin kokarin gwamnatin jihar na inganta tsarin kula da kuɗaɗen jama’a da kuma ƙarfafa amincewar al’umma da gwamnati.

Hukumar ta ce ana aiwatar da sabbin tsare-tsare da tsarin zamani na tattara haraji da kudaden shiga, tare da wayar da kan ‘yan kasa kan muhimmancin biyan haraji domin ci gaban jihar.

kaso 98% Na ‘Yan Najeriya Za Su Amfana Da Raguwar Haraji Ko Cirewa Gaba ɗaya a Shekarar 2026Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙ...
08/10/2025

kaso 98% Na ‘Yan Najeriya Za Su Amfana Da Raguwar Haraji Ko Cirewa Gaba ɗaya a Shekarar 2026

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Tsarin Kuɗi da Gyaran Haraji (Presidential Committee on Fiscal Policy and Tax Reforms), Dr. Taiwo Oladele, ya bayyana cewa kimanin kashi 98% na ‘yan Najeriya za su amfana da raguwar haraji ko kuma cikakken cire haraji gaba ɗaya a shekarar 2026.

Dr. Oladele ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai, inda ya ce wannan sabon tsarin na daga cikin manufofin gwamnatin Bola Tinubu na sauƙaƙa wa talakawa da ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.

Ya ƙara da cewa, kwamitin na aiki wajen tabbatar da cewa tsarin haraji ya zama mai adalci, sauƙi, da karɓuwa ga kowa, tare da mayar da hankali wajen karawa ƙananan ‘yan kasuwa da ma’aikata damar yin amfani da kuɗin su wajen ci gaban kansu.

Da dumi'dumi: Tinubu Ya Nemi Sabon Bashin Dala Biliyan $2.35 don inganta rayuwar 'yan Nageriya.Shugaban Ƙasa Bola Ahmed ...
08/10/2025

Da dumi'dumi: Tinubu Ya Nemi Sabon Bashin Dala Biliyan $2.35 don inganta rayuwar 'yan Nageriya.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rubuta wasiƙa zuwa Majalisar Wakilai yana neman amincewa da sabon bashin waje na Dala biliyan $2.35 da kuma $500 miliyan na Sovereign Sukuk domin aiwatar da wasu muhimman ayyukan gwamnati a ƙasar.

Wasiƙar, wadda Kakakin Majalisar Wakilai Rt. Hon. Tajudeen Abbas ya karanta a zauren majalisar a yau Laraba, ta bayyana cewa wannan bashin zai taimaka wajen ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa da kuma aiwatar da manyan ayyuka a fannoni k**ar su ababen more rayuwa, mak**ashi, da ilimi.

A cewar shugaban ƙasar, gwamnati na buƙatar waɗannan kuɗaɗe ne domin ci gaba da gudanar da shirin farfaɗo da tattalin arziki da rage tasirin hauhawar farashi ga ‘yan ƙasa.

Majalisar za ta tattauna kan wannan buƙata kafin ta yanke hukunci kan amincewa da neman bashin.

Address

No C320 WorldGate Shopping Center One Man Village Lafia Road N/Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mikiya:

Share