Mikiya

Mikiya Mikiya jarida ce mallakin Kamfanin Mikiya Online news LTD dake watsa labarai cikin harshen Hausa a Najeriya.
(256)

Whatsapp da kira zaku iya samun ma'aikatan mikiya a wannan lamba >08135583932. Mikiya Kafar labarai ce cikin harshen hausa a Nageriya

Da ɗumi-ɗumi: A cikin awa 4 kacal an tara naira milyan N45.7m domin sayen fom ɗin takarar El-Rufai a 2027Ƙungiyar magoya...
08/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: A cikin awa 4 kacal an tara naira milyan N45.7m domin sayen fom ɗin takarar El-Rufai a 2027

Ƙungiyar magoya bayan tsohon gwamnan jihar Kaduna, , ta bayyana cewa ta samu nasarar tara kuɗi har Naira miliyan 45 da dubu 750 cikin sa’o’i huɗu kacal domin sayen fom ɗin nuna sha’awa da tsayawa takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC a zaɓen 2027.

Ƙungiyar ta bayyana wannan mataki a matsayin babban nuna goyon baya da haɗin kai daga magoya bayan El-Rufai, tana mai cewa wannan ba tara kuɗi ba ne kawai, illa wata alama ce da ke nuna yadda jama’a s**a rungumi tafiyar siyasar tasa.

A cewar ƙungiyar, “Wannan murya ce daga dubban magoya baya masu cewa da zuciya ɗaya: Mallam, muna tare da kai.”

Ƙungiyar ta kuma gode wa duk waɗanda s**a bayar da gudummawa, tana mai cewa wannan goyon baya ya nuna cewa har yanzu tafiyar siyasar El-Rufai na ƙara samun karɓuwa a faɗin ƙasar nan.

“The Movement is Rising” — in ji sanarwar da aka fitar tare da jaddada cewa tarihi na ci gaba da sauyawa ta hannun jama’a.

Gwamnan Jihar Filato, Barista Caleb Mutfwang, Na Shirin Yin Babban Kuskure — Kuma Wannan Kuskuren Zai Iya Hana Shi Sake ...
08/05/2026

Gwamnan Jihar Filato, Barista Caleb Mutfwang, Na Shirin Yin Babban Kuskure — Kuma Wannan Kuskuren Zai Iya Hana Shi Sake Lashe Zaɓe –Hon Khalifa Pasali

Matashin ɗan takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya ƙarƙashin jam’iyyar APC, Khalifa Pasali, ya jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta bayan ya wallafa wani saƙo mai ƙarfi a shafinsa na Facebook dangane da Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang.

A cikin wallafar, Khalifa Pasali ya bayyana cewa Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang yana dab da yin wani “babban kuskure,” inda ya yi gargaɗin cewa irin wannan mataki na iya shafar damar gwamnan wajen sake cin zaɓe a nan gaba. Sai dai matashin ɗan siyasar bai bayyana cikakken bayani ko irin kuskuren da yake nufi ba.

A cewar Pasali, idan har gwamnan bai yi abin da ya kira “abin da ya dace” ba, akwai yiwuwar ya fito fili ya bayyana ƙarin bayanai nan gaba kaɗan. Wannan furuci nasa ya haifar da tattaunawa tsakanin masu bibiyar harkokin siyasa da magoya baya a faɗin Jihar Filato.

Duk da wannan gargaɗi, Khalifa Pasali ya bayyana cewa har yanzu yana da matuƙar girmamawa da kulawa ga gwamnan da kuma jihar baki ɗaya. Ya ƙara da cewa kullum yana yi wa Gwamna Mutfwang addu’a dare da rana, tare da yi wa Jihar Filato addu’ar zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaba.

Pasali ya kuma jaddada cewa kalamansa ba daga ƙiyayya ko wata manufa ta kashin kai s**a fito ba, sai dai daga abin da ya bayyana a matsayin damuwa ta gaskiya kan makomar jihar da shugabancinta.

Har yanzu wannan furuci na ci gaba da jawo ra’ayoyi mabambanta daga magoya bayan jam’iyyun siyasa daban-daban, yayin da mutane da dama ke jiran ƙarin bayani daga matashin ɗan siyasar dangane da zarge-zargen nasa.

08/05/2026

Yadda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu Ya Shimfiɗa Hanya Daga Ajingi Ta Jihar Kano Ta Wuce Jihar Jigawa Ta Shiga Garuruwan Jahun Da Kafin-Hausa.

Da ɗumi-ɗumi: Za'a sake ɗauke shari’ar Jam'iyyar ADC tsakanin Sen Devid Mark da Nafi’u Bala zuwa wata kotun.A yau ne bab...
08/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: Za'a sake ɗauke shari’ar Jam'iyyar ADC tsakanin Sen Devid Mark da Nafi’u Bala zuwa wata kotun.

A yau ne babbar kotun tarayya tayi zaman farko tun bayan da Kotun kolin Najeriya ta bayar da umarnin komawa kotun don ci gaba shari’ar acan.

Sai da a wata wasika da bangaren Nafi’u Bala s**a shigar Gaban kotun sun bukaci a sake dauke shari’ar daga gaban kotun tarayya Kotu ta 8 zuwa kotu ta uku 3 lamarin da bangaren Sen Devid Mark s**a ƙalubalanta suna cewa komawa da shari’ar zuwa kotu ta 3 suna da tabbacin alkalanci dake wurin ba za suyi masu adalci.

Yanzu dai kotu zata duba wannan bukata a zama na gaba.

Me zaku ce

Da ɗumi-ɗumi: An kashe mata masu juna biyu da wasu 13 a sabon harin Filato.Wasu mahara sun kashe mutum 13 ciki har da ma...
08/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: An kashe mata masu juna biyu da wasu 13 a sabon harin Filato.

Wasu mahara sun kashe mutum 13 ciki har da mata masu juna biyu a wani sabon hari da s**a kai a jihar Filato, lamarin da ya sake tada hankalin al’umma.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun afka wa yankin ne cikin dare inda s**a riƙa harbe-harbe ba tare da tausayi ba, abin da ya yi sanadin salwantar rayuka tare da jikkata wasu.

Harin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan yadda kashe-kashe da hare-hare ke ƙaruwa a wasu sassan jihar Filato.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan harin ba.

Da ɗumi-ɗumi: Gwamna Uba Sani Ya Ba da Umarnin Samar wa Alhazan Kaduna Ingantaccen Kulawa a Hajjin Bana.Gwamnan Jihar Ka...
08/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: Gwamna Uba Sani Ya Ba da Umarnin Samar wa Alhazan Kaduna Ingantaccen Kulawa a Hajjin Bana.

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya umarci a tabbatar da cewa an kula da alhazan jihar yadda ya kamata kafin tafiya, yayin gudanar da aikin Hajji da kuma bayan dawowarsu daga ƙasar Saudiyya.

Daraktan Ayyuka na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna, Alhaji Abubakar Usman Yusuf, ya bayyana cewa ma’aikata da shugabannin hukumar za su aiwatar da wannan umarni yadda ya kamata ba tare da gazawa ba.

A cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan, Malam Ibraheem Musa ya fitar, Daraktan ya ce an kammala duk shirye-shiryen da s**a dace domin tabbatar da jin daɗin alhazan jihar.

Ya bayyana cewa Gwamna Uba Sani ya sake fasalin sansanin wucin gadi na alhazai da ke Mando tare da inganta shi da kayayyakin more rayuwa na zamani domin gudanar da aikin Hajji cikin sauƙi da tsari.

A cewarsa, sansanin yanzu yana da kayayyakin more rayuwa irin na otel mai taurari biyar, tare da raba bangarori na maza da mata masu niyyar aikin Hajji, dakuna masu kyau da kuma ingantattun wuraren tsafta.

Haka kuma ya ce an samar da cibiyar ICT ta zamani, babban zaure na zamani da ofisoshi a sansanin Hajjin, inda ya ce har ma hukumar na iya gudanar da ayyukanta daga wurin domin sauƙaƙa jigilar alhazai zuwa filin jirgin sama.

Daraktan ya ƙara da cewa an yi kwalta a harabar sansanin, an ƙara tsaro, sannan an ware wani yanki a matsayin cibiyar kasuwanci domin alhazai su samu damar yin sayayya ba tare da fita waje ba.

Ya kuma bayyana cewa sansanin da ke Mando a ƙaramar hukumar Igabi na da wutar lantarki mai ɗorewa, lamarin da zai taimaka wajen gudanar da ayyukan Hajjin bana cikin nasara.

Alhaji Abubakar ya gode wa Gwamna Uba Sani bisa bai wa hukumar motocin CNG, yana mai cewa hakan zai taimaka sosai wajen jigilar alhazai zuwa filin jirgin sama cikin sauƙi.

Haka kuma ya ce an kammala duk shirye-shiryen da s**a dace a ƙasar Saudiyya domin tabbatar da jin daɗin alhazan Kaduna yayin gudanar da aikin Hajji.

Daraktan ya yabawa Gwamna Uba Sani kan nasarorin da hukumar ke samu tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, wanda ya ce ya haifar da ingantuwar ayyukan Hajji a jihar.

Ya tuna cewa a shekarar 2023 an karrama Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Kaduna saboda samar da ingantattun masaukai ga alhazai.

Sannan a shekarar 2024, ƙungiyar Independent Hajj Reporters ta yabawa jihar Kaduna bisa nasarar kwashe dukkan alhazanta zuwa Makkah kwanaki goma kafin rufe Filin Jirgin Sama na King AbdulAzeez International Airport.

Kazalika, ya ce hukumar ta samu yabo kan yadda ta gudanar da aikin “Hadaya” cikin gaskiya da riƙon amana, lamarin da ya sa aka mayar wa alhazai dala 50 kowannensu.
Allah Ya ba alhazan Najeriya sauƙin ibada tare da dawowa lafiya.

“Ba Za Mu Zuba Ido Ana Wulakanta ‘Yan Kasarmu Ba” — Bianca Ojukwu Ta Faɗa wa Afirka Ta KuduMinistar harkokin wajen Niger...
08/05/2026

“Ba Za Mu Zuba Ido Ana Wulakanta ‘Yan Kasarmu Ba” — Bianca Ojukwu Ta Faɗa wa Afirka Ta Kudu

Ministar harkokin wajen Nigeria, Bianca Ojukwu, ta bayyana cewa Najeriya ba za ta ci gaba da kallon yadda ake cin zarafi da wulakanta ‘yan ƙasarta a South Africa ba.

Ta bayyana hakan ne yayin tattaunawa kan alaƙar ƙasashen biyu da kuma matsalolin da wasu ‘yan Najeriya ke fuskanta a Afirka ta Kudu.

Ojukwu ta jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da kare martaba da haƙƙin ‘yan Najeriya a duk inda suke a duniya, tare da neman a mutunta su kamar yadda ake mutunta sauran ‘yan ƙasa.

Kalaman nata na zuwa ne yayin da ake yawan samun koke-koke kan cin zarafi, hare-hare da matsalolin da wasu ‘yan Najeriya ke fuskanta a Afirka ta Kudu a lokuta daban-daban.

Da Dumi Dumi: Dangote Ya Rage Farashin Mai Zuwa N1,200..Dangote Refinery Ta Rage Farashin Fetur da N75, Ya Koma N1,200 K...
08/05/2026

Da Dumi Dumi: Dangote Ya Rage Farashin Mai Zuwa N1,200..

Dangote Refinery Ta Rage Farashin Fetur da N75, Ya Koma N1,200 Kan Lita

Wannan ragin na zuwa ne bayan sauye-sauyen farashin mai da aka samu a baya, wanda ya jawo muhawara a tsakanin masu amfani da mai da ‘yan kasuwa.

Masana sun bayyana cewa rage farashin na iya taimakawa wajen sauƙaƙa matsin farashin sufuri da wasu kayayyaki, idan ‘yan kasuwa s**a saukar da farashi.

Ana sa ran wannan sauyi zai yi tasiri a kasuwar man fetur a Najeriya, yayin da jama’a ke fatan ƙarin sauƙi a farashin makamashi.

Da ɗumi-ɗumi: Aan tayar da ƙura a yobe: masu neman takarar gwamna a apc sun yi bore kan zaɓen ɗan takarar maslaha.Ƴan ta...
08/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: Aan tayar da ƙura a yobe: masu neman takarar gwamna a apc sun yi bore kan zaɓen ɗan takarar maslaha.

Ƴan takarar kujerar gwamnan jihar Yobe a jam’iyyar APC sun bayyana rashin amincewarsu da abin da s**a kira ayyana wani ɗan takara a matsayin wanda aka cimma matsaya a kansa domin tsayawa takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar.

A cikin wata sanarwa da s**a fitar bayan taronsu da aka gudanar a Abuja ranar 7 ga Mayu, 2026, masu neman takarar sun ce wannan mataki bai yi daidai da tanade-tanaden Dokar Zaɓe ta 2026 da kuma kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC ba, saboda haka ba za su amince da shi ba.

Sun jaddada cewa dole ne a bi dukkan ƙa’idojin da s**a shafi zaɓen ‘dan takara ta hanyar sasanci domin tabbatar da fitowar ɗan takara nagari kuma abin karɓa ga jam’iyyar APC a jihar Yobe.

Masu neman takarar sun kuma bayyana cewa idan ba a cimma matsaya ta sasanci ba, to wajibi ne a gudanar da zaɓen fidda gwani kai tsaye cikin adalci, gaskiya da sahihanci kamar yadda ƙa’idodin APC s**a tanada.

Haka kuma, sun zargi shugaban APC na jihar Yobe da nuna son kai a fili, lamarin da s**a ce ya sa s**a rasa amincewa da cewa zai iya jagorantar zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci.

Saboda haka, sun buƙaci a cire shugaban jam’iyyar APC na jihar Yobe daga duk wani aiki da ya shafi gudanarwa ko sa ido kan zaɓen fidda gwani na gwamna a jihar.

A ƙarshe, masu neman takarar sun sake bayyana cikakken goyon bayansu ga shugabancin APC na ƙasa tare da marawa shugaban ƙasa, baya domin sake tsayawa takara da nasara a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

An fitar da wannan sanarwa ne a Abuja ranar 7 ga Mayu, 2026.

07/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: DR. Tariq Abubakar ya bayyana Aniyarsa na tsaya takarar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Yole ta Arewa, Yola Ta Kudu da Girei.

Abdul Samad Bua Ya Zama Na Biyu Mafi Arziki a AfirkaShugaban BUA Group, Abdul Samad Rabiu, ya zama mutum na biyu mafi ar...
07/05/2026

Abdul Samad Bua Ya Zama Na Biyu Mafi Arziki a Afirka

Shugaban BUA Group, Abdul Samad Rabiu, ya zama mutum na biyu mafi arziki a nahiyar Africa, bisa sabbin rahotannin masu bibiyar attajirai a duniya.

Rabiu, wanda ya shahara a bangarorin siminti, s**ari da sauran masana’antu, ya ci gaba da faɗaɗa kasuwancinsa a Najeriya da wasu sassan Afirka.

Wannan matsayi na nuna ƙara ƙarfin manyan ‘yan kasuwar Najeriya a tattalin arzikin nahiyar, musamman a fannoni kamar masana’antu, gine-gine da abinci.

Masana sun bayyana cewa ci gaban kamfanonin BUA ya taimaka wajen samar da ayyukan yi, bunƙasa masana’antu da ƙarfafa tattalin arzikin Najeriya.

Address

No C320 WorldGate Shopping Center One Man Village Lafia Road N/Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mikiya:

Share