Mikiya

Mikiya Mikiya jarida ce mallakin Kamfanin Mikiya Online news LTD dake watsa labarai cikin harshen Hausa a Najeriya.
(251)

Whatsapp da kira zaku iya samun ma'aikatan mikiya a wannan lamba >08135583932. Mikiya Kafar labarai ce cikin harshen hausa a Nageriya

Da ɗumi-ɗumi: Ban damu ba don ɗana ya shiga Apc damuwata kawai yadd jam’iyyar APC ta saka 'yan Najeriya cikin Bala'in Ta...
15/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Ban damu ba don ɗana ya shiga Apc damuwata kawai yadd jam’iyyar APC ta saka 'yan Najeriya cikin Bala'in Talauci –Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma jagoran jam’iyyar adawa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa matakin da ɗansa Abba Abubakar ya ɗauka na shiga jam’iyyar APC shawara ce ta kansa gaba ɗaya, ba tare da wani tilas ko matsin lamba daga gare shi ba.

Atiku ya ce a tsarin dimokuraɗiyya, irin waɗannan zaɓi ba abin mamaki ba ne, ko da kuwa siyasa da zumunci sun haɗu. Ya jaddada cewa shi a matsayinsa na ɗan dimokuraɗiyya, ba ya tilasta wa ’ya’yansa ra’ayi ko zaɓin siyasa, haka nan kuma ba zai tilasta wa ’yan Najeriya ba.

Sai dai Atiku ya nuna cewa abin da ya fi damunsa shi ne mulkin APC, wanda ya ce ya jefa ’yan Najeriya cikin matsanancin wahalar tattalin arziƙi da zamantakewa.

A cewarsa, talauci, tsadar rayuwa da rashin kyakkyawan shugabanci sun addabi jama’a.
Ya ƙara da cewa har yanzu yana tsayin daka tare da sauran ’yan kishin ƙasa masu ra’ayi ɗaya, domin maido da kyakkyawan shugabanci da kuma gabatar wa ’yan Najeriya madadin shugabanci nagari da zai kawo sauƙi, fata da cigaba.

“Dimokuraɗiyya ba tilas ba ce, amma APC ta kasa ba ta cika alkawari ga talaka ba,” in ji Atiku.

Da ɗumi-ɗumi: Ɗan Atiku Abubakar ya fice dag jam’iyyar PDP Ya koma jam’iyyar APCAbubakar Atiku Abubakar (Abba), ɗan tsoh...
15/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Ɗan Atiku Abubakar ya fice dag jam’iyyar PDP Ya koma jam’iyyar APC

Abubakar Atiku Abubakar (Abba), ɗan tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, ya fice daga PDP zuwa APC.

An karɓe shi a Majalisar Ƙasa ta Tarayya Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin sen Barau Jibrin ne ya karɓe shi

Abba ya bayyana cikakken goyon bayansa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin zaɓen 2027, tare da umartar ƙungiyarsa Haske Atiku da su koma APC, inda aka sake raɗa mata suna zuwa Haske Bola Tinubu Organisation.

Kuna ganin Wannan mataki na iya sauya yanayin siyasa gabanin 2027.

Da ɗumi-ɗumi: Ana matsa lamba ga shugaba Tinubu da ya ɗauki Mataimaki kirista domin adalci ga addini, Bishop Kukah, Doga...
15/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Ana matsa lamba ga shugaba Tinubu da ya ɗauki Mataimaki kirista domin adalci ga addini, Bishop Kukah, Dogara da Janar Christopher na cikin waɗanda ake hasashen Tinubu zai iya ɗauka Mataimaki a 2027

A yayin da siyasar zaɓen 2027 ke ƙara ɗaukar zafi, rahotanni na nuni da cewa ana ƙara matsin lamba kan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya tabbatar da daidaiton addini a tikitin APC — wato Musulmi da Kirista.

Majiyoyi daga jaridar Daily Sun sun bayyana cewa wasu masu karfi na cikin gida da ma daga ƙasashen waje, musamman Amurka, na son a sauya tsarin tikitin domin samun karɓuwa da haɗin kan ƙasa kafin zaɓen 2027.

Sunayen da ake ta jita-jita
A cikin mutanen da ake hasashen Tinubu zai iya ɗauka a matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa, an fi ambaton:

Matthew Hassan Kukah – Bishop ɗin Katolika na Sokoto, wanda ake ganin zai kawo daidaiton addini idan har ya amince da shiga siyasa.

Yakubu Dogara – Tsohon Shugaban Majalisar Wakilai, gogagge a harkar siyasa da mulki.

Christopher Musa – Babban Hafsan Tsaro, Janar mai kwarewa kan batun tsaro da zaman lafiya.

Rahotanni sun ce duk waɗannan sunaye na fitowa ne musamman saboda kiraye-kirayen sauya Mataimakin Shugaban Ƙasa na yanzu, Kashim Shettima, domin a samu tikitin Musulmi-Kirista.

Har yanzu jita-jita
Duk da haka, babu wata sanarwa a hukumance daga fadar shugaban ƙasa ko jam’iyyar APC. Masu lura da siyasa na cewa har yanzu magana ce ta jita-jita, kuma lokaci ne kaɗai zai nuna inda lamarin zai dosa.

15/01/2026

Ga masu samun matsala da kuma masu neman sauƙi ga dama ta samu a Comment Section 👇

Da ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Kano ta nemi Taimakon Yarabawa domin samar da tsaro a jihar kanoGwamnatin Jihar Kano ta yi kira ...
15/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Kano ta nemi Taimakon Yarabawa domin samar da tsaro a jihar kano

Gwamnatin Jihar Kano ta yi kira ga al’ummar Yarabawa da ke zaune a jihar da su haɗa kai da hukumomi domin ƙarfafa tsaro da bunƙasa zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Kiran ya fito ne daga bakin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, yayin wata ganawa da shugabannin al’ummar Yarabawa a Kano, ƙarƙashin ƙungiyar ’yan yankin Kudu maso Yamma da ke zaune a Kano, ƙarƙashin jagorancin Sarkin Yarabawa a Kano, Ambasada Murtala Alimi Otisese.

Waiya ya bayyana cewa ganawar na daga cikin jerin tattaunawa da gwamnati ke yi da sassa daban-daban na ƙasar nan domin tara goyon baya ga ƙoƙarin Gwamna Abba Kabir Yusuf na dawo da zaman lafiya da magance ƙalubalen tsaro a jihar.

15/01/2026

"A matsayinmu na ƴan Arewa za mu ci gaba da yabon shugaban ƙasa Tinubu da gode masa kan aikin t**i da yake mana daga Adamawa zuwa Fufore zuwa bodar Najeriya da Kamaru, da aikin t**in Mina zuwa Tagina zuwa Kwantagora, da aikin gina asibiti, tituna da makarantu a ƙauyen Tudun Biri, da sauran ayyukan da yake mana".

In Ji Hon. Nuhu Abdullahi, yayin da yake gabatar da jawabi a taron wayar da kai kan ayyukan shugaban ƙasa Tinubu a Arewa, karo na huɗu, wanda aka gabatar jiya a Jihar Kano.

Da ɗumi-ɗumi: Gwamnatin shugaba Bola Tinubu Ta dakatar da fara aiwatar da sabuwar dokar haraji.Gwamnatin Tarayyar Najeri...
15/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Gwamnatin shugaba Bola Tinubu Ta dakatar da fara aiwatar da sabuwar dokar haraji.

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta dakatar da fara aiwatar da sabuwar dokar haraji da aka shirya ta fara aiki daga 1 ga Janairu, biyo bayan wasu rashin tabbas da matsaloli da s**a taso a matakan ƙarshe na dokar.

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Tsarin Haraji, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa akwai buƙatar ƙarin nazari da tantancewa kafin a fara aiki da dokar, inda ya umarci dukkan hukumomin haraji da su dakatar da duk wani shiri da ya shafi aiwatar da ita.

Rahotanni sun nuna cewa dokar ta fuskanci s**a daga sassa daban-daban, musamman kan zargin cewa an yi mata sauye-sauye bayan Majalisar Dokoki ta amince da ita, tare da gano wasu matsaloli a cikin tanade-tanadenta.

Sai dai Oyedele ya ce yawancin caccakar da ake yi wa dokar sakamakon yaɗa labaran ƙarya ne, yana mai cewa hakan ya janyo wa Najeriya asarar Naira tiriliyan 4.6 a rana guda a watan Nuwamban da ya gabata.

Ana sa ran gwamnati za ta sake fitowa da cikakken bayani bayan kammala wannan ƙarin nazari.

Da ɗumi-ɗumi: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya nemi Taimakon Nasir Ja'oji domin Ya wuce masa gana wurin ganawa da shugabannin ...
15/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya nemi Taimakon Nasir Ja'oji domin Ya wuce masa gana wurin ganawa da shugabannin jam’iyar APC

Rahoton Jaridar Daily Nigerian na cewa Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, na ci gaba da shirin komawa jam’iyyar APC ta hanyar ganawa da manyan jiga-jiganta a Abuja.

Rahoton ya nuna cewa a ranar Talata, gwamnan ya gana da Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗi na Majalisar Wakilai, Abba Bichi, inda ya shaida masa aniyarsa ta shiga APC tare da neman mara masa baya domin shimfiɗa hanya.

Haka kuma a ranar Laraba, gwamnan ya gana da Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan ƙasa da Jagoranci, Nasir Ja’oji, inda ya roƙe shi da ya kira Shugaban APC na Jihar Kano, Abdullahi Abbas, domin a shirya ganawa kai tsaye da gwamnan.

Wannan sabon motsi na nuna cewa siyasar Kano na dab da shiga sabon babi—idanu na kan abin da zai biyo baya.

Da ɗumi-ɗumi: Shugaba Tinubu zai kashe Biliyan 1.9bn a Fadar Shugaban Ƙasa A*o Rock domin zuba man janareto a 2026.Rahot...
15/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Shugaba Tinubu zai kashe Biliyan 1.9bn a Fadar Shugaban Ƙasa A*o Rock domin zuba man janareto a 2026.

Rahoton binciken SaharaReporters kan takardun kasafin kuɗin Najeriya na shekarar 2026 ya nuna cewa an ware N1.989 biliyan domin sayen man janareto a A*o Rock Villa, ƙarƙashin sashen “State House Headquarters.”

Bayan haka, an kuma tanadi N17 miliyan don mai kula da aikin janareto a cikin wannan kasafin, duk da korafe-korafen jama’a kan tsadar rayuwa da buƙatar rage ɓarnar kuɗaɗen gwamnati.

Masu sharhi na ganin wannan tanadi na ƙara tayar da muhawara kan dalilin dogaro da janareto a manyan cibiyoyin gwamnati, musamman a daidai lokacin da ake kira a ƙara saka jari a hanyoyin wutar lantarki masu ɗorewa.

Tambaya ita ce: Shin ya dace a wannan lokaci a kashe biliyoyi kan janareto, alhali ’yan ƙasa na fama da tsadar rayuwa?
Ku faɗi ra’ayinku a sharhi.

Da ɗumi-ɗumi: Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fara tuntubar manyan APC a Kano bayan ganawarsa da Tinubu ta ci tura a Faransa....
15/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fara tuntubar manyan APC a Kano bayan ganawarsa da Tinubu ta ci tura a Faransa.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya fara gudanar da jerin ganawa a asirce da wasu manyan shugabannin jam’iyyar APC a Kano, yayin da rahotanni ke nuna cewa shirin ganawarsa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a Faransa ya faskara a minti na ƙarshe.

Majiyoyi daga Daily Nigerian sun bayyana cewa an soke tafiyar ne ko dai saboda matsalar biza, ko kuma rashin samun amincewar Shugaban Ƙasa don ganawa da shi. Wannan lamari ya ƙara tayar da ƙura a siyasar Kano, musamman duba da rade-radin cewa gwamnan na shirin ficewa daga NNPP zuwa APC.

Rahoton ya ce makon da ya gabata, Gwamna Yusuf ya yi wata ganawa ta sirri da uban gidansa na siyasa, Rabiu Musa Kwankwaso, a gidansa da ke Miller Road, Kano, domin rage zafin martanin da ya biyo bayan jita-jitar sauya sheƙa. A ganawar, gwamnan ya shaida masa cewa ba zai ɗauki matakin barin NNPP ba har sai ya gana da Shugaban Ƙasa, tare da gabatar masa da sharuddan Kwankwaso na shiga APC.

Sai dai da yake lokaci na tafiyar APC na ƙara ƙurewa, kuma ganawar da Shugaban Ƙasa ta gaza tabbata, majiyoyi na cewa gwamnan na iya sanar da ficewarsa daga NNPP kowane lokaci daga yanzu.

Rahotanni sun kuma tabbatar da cewa Gwamna Yusuf ya gana da Abba Bichi, shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Kasafin Kuɗi, da kuma Nasir Ja’oji, Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Harkokin Ƙasa da Jagoranci, inda ya nemi su share masa fage da shugabannin APC na Kano.

A gefe guda kuma, manyan jiga-jigan APC na Kano sun yi wani dogon taro a Abuja a gidan Abdullahi Ganduje, inda s**a tattauna batun shigowar gwamnan jam’iyyar. Duk da cewa an fara shirin yi masa rijista a matsayin mamba na farko, jinkirin da gwamnan ke yi ya sa s**a dakatar da shirin na ɗan lokaci.

Majiyoyi sun ce da zarar gwamnan ya ji an shirya ci gaba ba tare da shi ba, sai ya gaggauta tuntuɓarsu yana roƙon a ɗan dakata, yana mai jaddada aniyarsa ta shiga APC.

Ƙoƙarin jin ta bakin mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature-Dawakin Tofa, bai yi nasara ba, domin bai amsa kira ko saƙon da aka tura masa ba.

Tambayar da ke yawo yanzu: Shin Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa zuwa APC nan ba da jimawa ba, ko kuwa siyasar Kano na dab da sake juyawa?

15/01/2026

Sen Rabi'u kwankwaso Yace duk wanda ya haɗu da 'yan bangaren gidan gwamnatin Abba Kabir Yusuf Yace dasu Giv me Dash Money domin sun karɓi Bilyoyi suna sayen gidaje da gidan Gona.

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya samu gurbin karatun shari’a a jami’ar KanoMai Martaba Sarkin Kano, Dr. Muhammadu Sa...
15/01/2026

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya samu gurbin karatun shari’a a jami’ar Kano

Mai Martaba Sarkin Kano, Dr. Muhammadu Sanusi II, ya samu shiga ta musamman (special admission) domin karantar Law (LL.B) a Northwest University, Kano, inda zai fara daga mataki na 200.

Majiyoyi sun bayyana cewa an amince da shigar Sarkin ne bisa la’akari da kwarewarsa da gogewarsa a harkokin ilimi, shugabanci da shari’a, abin da ke kara nuna jajircewarsa wajen neman ilimi ko da a matsayinsa na Sarki.

Wannan mataki na Sarki Sanusi ya janyo yabo daga al’umma, inda da dama ke ganin hakan a matsayin darasi ga matasa kan muhimmancin ilimi a kowane matsayi.

Address

No C320 WorldGate Shopping Center One Man Village Lafia Road N/Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mikiya:

Share