08/05/2026
Da ɗumi-ɗumi: Gwamna Uba Sani Ya Ba da Umarnin Samar wa Alhazan Kaduna Ingantaccen Kulawa a Hajjin Bana.
Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya umarci a tabbatar da cewa an kula da alhazan jihar yadda ya kamata kafin tafiya, yayin gudanar da aikin Hajji da kuma bayan dawowarsu daga ƙasar Saudiyya.
Daraktan Ayyuka na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna, Alhaji Abubakar Usman Yusuf, ya bayyana cewa ma’aikata da shugabannin hukumar za su aiwatar da wannan umarni yadda ya kamata ba tare da gazawa ba.
A cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan, Malam Ibraheem Musa ya fitar, Daraktan ya ce an kammala duk shirye-shiryen da s**a dace domin tabbatar da jin daɗin alhazan jihar.
Ya bayyana cewa Gwamna Uba Sani ya sake fasalin sansanin wucin gadi na alhazai da ke Mando tare da inganta shi da kayayyakin more rayuwa na zamani domin gudanar da aikin Hajji cikin sauƙi da tsari.
A cewarsa, sansanin yanzu yana da kayayyakin more rayuwa irin na otel mai taurari biyar, tare da raba bangarori na maza da mata masu niyyar aikin Hajji, dakuna masu kyau da kuma ingantattun wuraren tsafta.
Haka kuma ya ce an samar da cibiyar ICT ta zamani, babban zaure na zamani da ofisoshi a sansanin Hajjin, inda ya ce har ma hukumar na iya gudanar da ayyukanta daga wurin domin sauƙaƙa jigilar alhazai zuwa filin jirgin sama.
Daraktan ya ƙara da cewa an yi kwalta a harabar sansanin, an ƙara tsaro, sannan an ware wani yanki a matsayin cibiyar kasuwanci domin alhazai su samu damar yin sayayya ba tare da fita waje ba.
Ya kuma bayyana cewa sansanin da ke Mando a ƙaramar hukumar Igabi na da wutar lantarki mai ɗorewa, lamarin da zai taimaka wajen gudanar da ayyukan Hajjin bana cikin nasara.
Alhaji Abubakar ya gode wa Gwamna Uba Sani bisa bai wa hukumar motocin CNG, yana mai cewa hakan zai taimaka sosai wajen jigilar alhazai zuwa filin jirgin sama cikin sauƙi.
Haka kuma ya ce an kammala duk shirye-shiryen da s**a dace a ƙasar Saudiyya domin tabbatar da jin daɗin alhazan Kaduna yayin gudanar da aikin Hajji.
Daraktan ya yabawa Gwamna Uba Sani kan nasarorin da hukumar ke samu tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, wanda ya ce ya haifar da ingantuwar ayyukan Hajji a jihar.
Ya tuna cewa a shekarar 2023 an karrama Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Kaduna saboda samar da ingantattun masaukai ga alhazai.
Sannan a shekarar 2024, ƙungiyar Independent Hajj Reporters ta yabawa jihar Kaduna bisa nasarar kwashe dukkan alhazanta zuwa Makkah kwanaki goma kafin rufe Filin Jirgin Sama na King AbdulAzeez International Airport.
Kazalika, ya ce hukumar ta samu yabo kan yadda ta gudanar da aikin “Hadaya” cikin gaskiya da riƙon amana, lamarin da ya sa aka mayar wa alhazai dala 50 kowannensu.
Allah Ya ba alhazan Najeriya sauƙin ibada tare da dawowa lafiya.