
07/08/2025
Da misalin karfe 6:00 na safe, wani rukuni na ‘yan sanda a karkashin jagorancin wani CSP (Chief Superintendent of Police) daga sashen sa-ido na Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (IGP Monitoring Unit), sun farke kofar dakin da aka tsare dan gwagwarmaya kuma dan jarida Omoyele Sowore a hedikwatar sashen leken asiri na ‘yan sanda (FID) da ke Abuja.
Rahotanni sun bayyana cewa a yayin wannan mamaya, ‘yan sandan sun karya hannun damansa, sannan s**a dauke shi zuwa wani wurin da ba a bayyana ba.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a san halin da yake ciki ba, Kamar Yadda Shafi sa dan Jaridar Mai Dauke da Omoyele Sowore su bayyana,kuma ba a samu wata sanarwa daga rundunar ‘yan sanda ta Najeriya dangane da wannan lamari ba.
Wannan lamari ya kara dagula lamarin tsare Sowore, wanda kungiyoyin kare hakkin bil’adama da masu lura da harkokin siyasa a duniya ke ganin a matsayin tsare-tsaren siyasa da rashin adalci.