Sphere News Hausa

Sphere News Hausa The Sphere News Hausa; Your trusted source for News, Entertainment, Awareness, Education, and Governance. Stay informed, stay empowered. Stay informed.

Stay entertained. Stay ahead with The Sphere.

Iran ta ƙera sabon jirgin yaki mara matuki, irin na Amurka Shahed-171 SimorghIran ta sanar da ƙera sabon samfurin jirgin...
04/10/2025

Iran ta ƙera sabon jirgin yaki mara matuki, irin na Amurka Shahed-171 Simorgh

Iran ta sanar da ƙera sabon samfurin jirgin yaki mai saukar ungulu Shahed-171 Simorgh, wanda ke da irin tsarin jirgin Amurka da aka sani da RQ-170 Sentinel, wanda Iran ta k**a a shekarar 2011 ta hanyar jamming da spoofing.

Rahotanni sun bayyana cewa sabon Shahed-171 Simorgh ya samo fasaha daga irin na Amurka, amma an ƙara masa abubuwa guda biyar da ke bambanta shi da asalin kiran RQ-170.

Wadannan sabbin abubuwan sun haɗa da:

1. Sabon tsarin injin mai ƙarancin kuka, domin kauce wa gano shi daga makamin radar.

2.jirgin na dauke da mak**ai masu linzami da bama-bamai.

3. Tsarin tashi da sauka mai cin gashin kansa, wanda ke ba jirgin damar yin aiki ba tare da kulawa kai tsaye ba.

4.Jirgin na da Sabon tsarin leƙen asiri (surveillance system) da ke ɗaukar hotuna da bayanan sirri.

5. Jirgin nada samfurin tsarin Grumman B-2 Spirit bomber na Amurka, wanda ke taimakawa wajen ɓoye shi daga makamin radar.

Warware Gurguwar Fahimta Kan Sauye-sauyen Harajin Kuɗin Shiga Na Gwamnatin Shugaba TinubuRubutawa: Michael ChibuzoFassar...
04/10/2025

Warware Gurguwar Fahimta Kan Sauye-sauyen Harajin Kuɗin Shiga Na Gwamnatin Shugaba Tinubu

Rubutawa: Michael Chibuzo
Fassarawa zuwa Hausa: Aliyu Samba

Yayin da kwanaki ƙididdigaggu s**a rage mu shiga sabuwar Shekara ta 2026, ranar da sabbin dokokin haraji guda biyu za su fara aiki, labaran ƙarya da gurguwar fahimta game da waɗannan dokoki na haraji sun ƙaru sosai a kafafen sada zumunta. Wasu daga ciki suna bayyana ne sak**akon rashin sani, yayin da wasu da yawa kuma wata manufa ce ta siyasa da neman ɓata sunan Gwamnati. A wannan rubutu, zan yi ƙoƙarin warware wannan gurguwar fahimtar game da harajin kuɗin shiga (income tax) a cikin Dokar Haraji ta Najeriya, 2025.

Manyan Jita-jitan Da Aka Fi Ji:

1. Daga ranar 1 ga Janairu, 2026, ‘yan Najeriya za su fara biyan harajin kuɗin shiga mafi tsada.
2. Gwamnati za ta rika cire haraji kai tsaye daga asusun banki na mutum.
3. Gwamnatin Tarayya na neman ƙarin kuɗin shiga ta hanyar kakabawa ‘yan Najeriya haraji mai nauyi.
4. Sabbin dokokin haraji za su hana kasuwanci da haɓakar tattalin arziki.

Zan bisu daki-daki domin warwarewa.

1. SHIN ZA A ƘARA NE, KO KUMA RAGE HARAJIN KUƊIN SHIGA?

Gaskiyar magana ita ce, mafi yawan ‘yan Najeriya za a rage musu haraji sak**akon sabbin tanade-tanaden da ke cikin sabuwar dokar haraji ta 2025, inda aka ware mutanen da ke samun N800,000 ko ƙasa da haka a shekara daga biyan kowanne irin haraji. Ma’ana, ma’aikaci mai karɓar albashin mafi ƙaranci ko ƙasa da haka ba zai biya haraji ba kwata-kwata.

Wasu na iya cewa mafi ƙarancin albashin gwamnati yanzu N70,000 ne a wata (N840,000 a shekara), wanda ya fi N800,000 da aka ware. Haka ne, amma abin lura shi ne, ba duka kuɗin shiga ake kira taxable income ba. Akwai abin da ake kira (Taxable Income), wato abin da ya rage bayan an cire rangwamen da aka amince da shi k**ar:
• Kudin Inshorar Lafiya NHIS (kimanin 5% na albashi)
• Rangwamen haya (20% na haya da bai wuce N500,000 ba)
• Gudunmawar gidauniyar gidaje ta ƙasa NHF (2.5% na albashi)
• Gudunmawar fansho (8% na albashi)
• Inshorar rayuwa, na ka da iyalin ka.

Misali, ma’aikacin da ke karɓar N70,000 a wata (N840,000 a shekara) kuma yake biyan haya N200,000 a shekara, tare da kudin Inshorar lafiya na NHIS, NHF da fansho, zai sami taxable income na N710,800 kacal. Wannan yana cikin iyakar nan da ta ware masu samun N800,000, hakan ya nuna ba zai biya haraji ba.

Ko wanda ke karɓar N80,000 a wata (N960,000 a shekara) zai iya shiga cikin waɗanda aka ware idan an yi amfani da irin waɗannan tsarin. A taƙaice, talakawa da ƙananan ma’aikata sun samu sauƙi, sai masu kuɗi sosai ne za su ɗan biya fiye da da.

2. SHIN ZA A CIRE HARAJI KAI TSAYE DAGA BANKI?

Amsar ita ce A’A! Ba za a rika cire haraji kai tsaye daga asusun bankin mutum ba.

Abin da dokar Haraji ta 2025 ta tanada shi ne, sashe na 29 ya wajabtawa bankuna su rika ba hukumar haraji rahoton masu asusu waɗanda ke da mu’amalar banki har ta fiye da Naira Miliyan 25 a wata ga mutum ɗaya, da Naira Miliyan 100 ga kamfani. Wannan ba yana nufin su cire haraji bane, bayanan ne kawai suke tattarawa don gano masu kuɗi da ke gujewa biyan haraji.

Mutanen da mu’amalarsu ba ta kai Naira Miliyam 25 a wata ba, ba zai shafe su ba kwata-kwata. Kuma a yanzu, fiye da kaso 90% na ‘yan Najeriya ba su da kuɗaɗen da s**a kai wannan adadi a asusun banki.

3. SHIN GWAMNATIN TARAYYA NA NEMAN KUƊI NE TA HARAJI?

Amsar ita ce A’A!

A haƙiƙa, sabbin dokokin an yi su ne domin rage nauyin haraji ga talakawa. Harajin kuɗin shiga da ake magana akai ma, ba na gwamnatin tarayya ba ne kai tsaye. Sashe na 3(2) na dokar haraji ta ƙasa ya bai wa Jihohi ikon karɓar harajin kuɗin shiga daga mutanen da ke zaune a cikin jihohinsu. Gwamnatin Tarayya kawai tana tattara haraji ne daga ma’aikatan soji, ma’aikatun diflomasiyya na ƙasashen waje, da kuma mutanen waje da ke samun kuɗi daga Najeriya.

Saboda haka, jihohi ne suke cin gajiyar harajin kuɗin shiga, ba gwamnatin tarayya ba. Wannan ke nuna cewa ba wai gwamnati na neman karin kuɗi daga talakawa bane, a’a, ana ƙoƙarin kawo sauƙi ne.

4. SHIN SABON DOKAR HARAJI ZAI HANA TATTALIN ARZIKI CI GABA?

A’a, akasin haka ne. Sabbin dokokin suna nufin taimaka wa ƙananan ƴan kasuwa ne da masu ƙaramin karfi.

Misali:
• Dokar haraji ta ƙasa ta ware ƙananan kamfanoni (masu juya kuɗin da bai kai Naira Miliyan 100 ba a shekara) daga biyan harajin riba gaba ɗaya. Wannan ya kai sama da kaso 90 cikin 100 na kamfanoni a Najeriya.
• Manyan kamfanoni kuwa za su ci gaba da biyan kaso 30% na Harajin Kuɗaɗen Shiga na Kamfanoni, amma akwai tanadi a doka cewa za a rage shi zuwa kaso 25% idan Kwamitin Tattalin Arziƙi na ƙasa da Jihohi sun tabbatar hakan ba zai cutar da ribar da ke shiga asusun tarayya ba.

Idan dokokin za su hana ci gaba, za a ƙara Harajin Kuɗaɗen Shiga na Kamfanoni zuwa fiye da kaso 30%,, amma abin da sabuwar doka ta tanada ragewa yake, ba ƙarawa ba.

KAMMALAWA

Daga abin da muka gani, sabbin dokokin haraji, musamman na kuɗin shiga al’amari ne mai sauƙi, domin zai kare talakawa ne, tare da goyon bayan ‘yan kasuwa ƙanana da nufin ƙarfafa ci gaban tattalin arziki.

Jihohi da hukumomin haraji ya k**ata su gudanar da wayar da kai sosai domin mutane su fahimci gaskiyar abin da aka tanada, maimakon su saurari jita-jita marasa tushe.

A ƙarshe, dole ne mu gane cewa biyan haraji nauyi ne na ‘yan ƙasa. Duk wanda ya cancanci biyan haraji bai da hujjar guduwa. Wannan sabuwar doka ma ta sanya masu kuɗi da manyan kamfanoni su kasa gujewa biyan haraji. Idan hakan ya tabbata, zai ƙara wa jama’a ƙarfin gwiwa wajen neman bahasi da gaskiya daga shugabanni kan yadda ake amfani da kuɗaɗen jama’a. Wannan kuwa, a ƙarshe, yana nufin ƙarfafa ci gaban ƙasa ne cikin sauri.

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci A koma Aikin Dere A Hanyar Abuja-Keffi Saboda Yawan CunkosoGwamnatin Tarayya ta bayar da uma...
03/10/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci A koma Aikin Dere A Hanyar Abuja-Keffi Saboda Yawan Cunkoso

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin a fara aikin gyaran hanyar Abuja–Keffi da daddare domin rage cunkoson ababen hawa.

Ministan Ƙasar Ayyuka na Jihohi, Bello Muhammad Goronyo, ya bayar da wannan umarni yayin da yake duba aikin. Ya kuma jaddada cewa za a kammala aikin k**ar yadda aka tsara nan da watan Disamba, 2026.

Trump Ya Umurci Isra’ila Ta Dakatar da Aman Bomabomai A GazaTsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya umurci Isra’ila da ta...
03/10/2025

Trump Ya Umurci Isra’ila Ta Dakatar da Aman Bomabomai A Gaza

Tsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya umurci Isra’ila da ta dakatar da hare-haren bam a Gaza, a yayin da Hamas ta bayyana cewa tana duba shirin sulhu da zai iya kawo ƙarshen kusan shekaru biyu na kisan kiyashi a yankin tare da tabbatar da sakin fursunonin da s**a rage.

A cikin wata sanarwa da Hamas ta fitar, an nuna alamun shirye-shiryen neman zaman lafiya na dindindin. Trump ya ce:

"Ina ganin Hamas ta nuna shirye-shiryen zaman lafiya mai ɗorewa. Isra’ila dole ta dakatar da hare-haren bam a Gaza, domin mu samu damar fitar da fursunoni cikin gaggawa da lafiya... Wannan lamari ne na neman zaman lafiya da aka dade ana nema a Gabas ta Tsakiya."

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya yi kiran waya da Shugaban Amurka Donald Trump bisa roƙonsa:Ya bayyana cewa T...
03/10/2025

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya yi kiran waya da Shugaban Amurka Donald Trump bisa roƙonsa:

Ya bayyana cewa Turkiyya na ƙoƙarin ganin an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, musamman a Gaza, tare da maraba da duk wani shiri da aka yi don cimma wannan buri.

Ya jaddada cewa Ankara ta ƙara hanzarta kokarinta na diflomasiyya domin samar da zaman lafiya, kuma za ta ci gaba da bayar da gudummawa ga hangen nesa na zaman lafiya na duniya.

Ya yi nuni da cewa dakatar da hare-haren Isra’ila muhimmin mataki ne don nasarar duk wani yunkuri na samar da zaman lafiya a yankin.

Sphere News Hausa

03/10/2025

Yadda mota mai dauke da gas din CNG ta k**a da wuta yau a Abuja, a wuse 2, daidai Banex junction

Sphere News Hausa

Gwamna Dauda Lawal ya kaddamar da motocin haya 50 a ZamfaraGwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a ranar Alhamis ya kaddam...
03/10/2025

Gwamna Dauda Lawal ya kaddamar da motocin haya 50 a Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a ranar Alhamis ya kaddamar da sababbin motoci 50 na kujeru 18 ga kamfanin sufuri na jihar, Zamfara Transport Company (ZTC). Gwamnan ya bayyana matakin a matsayin cikar alkawari daga gwamnatinsa da kuma gado mai amfani ga jihar.

A cikin sanarwar da kakakin gwamnan, Sulaiman Idris, ya fitar, an ce motocin na zamani ne masu sanyaya iska, an tanadar musu da kujeru masu taushi, bel ɗin tsaro, tsarin da zai ɗauki mummunan hanya da na’urar GPS don bibiyar motsinsu a ainihin lokaci.

A yayin kaddamarwar, Gwamna Lawal ya ce an jinkirta fara amfani da motocin ne domin kafawa da tabbatar da tsarin gudanarwa, bin diddigi da kula da su yadda ya k**ata. Ya yi nuni da cewa a baya motoci da aka saya da kudin jama’a kan je ga amfanin ‘yan kadan ko kuma su lalace saboda rashin tsari.

Ya ce an horar da ma’aikatan ZTC — daga shugabanni zuwa direbobi, masu gyara da ma’aikatan sayar da tikiti — kan dabarun aiki, dabi’u da yadda za a inganta hidimar sufuri. Gwamnan ya kara da cewa inganta harkar sufuri zai taimaka wajen bunkasa kasuwanci, ilimi, kiwon lafiya da dangantakar zamantakewa, musamman ganin matsayi na Zamfara wajen hada ta da jihohi da dama a arewacin Najeriya.

A karshe, Gwamna Lawal ya yi kira ga jama’a da su yi amfani da motocin tare da kula da su, kada a lalata dukiyar jama’a domin asarar da ake yi ba wa al’umma ce gaba ɗaya.

Sphere News Hausa

Sojoji sun ceto mutum shida da aka yi garkuwa da su a Katsina-Ala, Jihar BenueSojoji sun samu nasarar ceto mutum shida d...
03/10/2025

Sojoji sun ceto mutum shida da aka yi garkuwa da su a Katsina-Ala, Jihar Benue

Sojoji sun samu nasarar ceto mutum shida da s**a hada da wani direba da wani yaro bayan da ‘yan bindiga s**a yi wa motar fasinja kwanton bauna a Katsina-Ala, Jihar Benue.

Lamarin ya faru ne da daren Alhamis lokacin da ‘yan bindiga s**a tare wata motar Toyota Carina II da take tafiya daga Katsina-Ala. Rahotanni sun ce maharan sun tilasta wa fasinjojin sauka daga motar, tare da tursasa musu shiga daji a kusa da tsohon shingen tsaro na Civil Defence da aka bari.

Bayan samun rahoto, dakarun tsaro sun shiga aiki cikin gaggawa, inda s**a bi sahun maharan har s**a ceto dukkan mutanen cikin koshin lafiya ba tare da an cutar da su ba.

Sphere News Hausa

Hukumar Shari’a ta Kano ta dakatar da buɗe sabon masallacin Juma’a a SharaɗaHukumar Shari’a ta jihar Kano ta dakatar da ...
03/10/2025

Hukumar Shari’a ta Kano ta dakatar da buɗe sabon masallacin Juma’a a Sharaɗa

Hukumar Shari’a ta jihar Kano ta dakatar da buɗe sabon masallacin Juma’a da aka gina a gidan marigayi Alhaji Ghali Umar Na’abba, da ke kan titin Sharaɗa kusa da hedikwatar hukumar Hisbah.

A cewar hukumar, dakatarwar ta biyo bayan karya dokokin tantance masallatan Juma’a da sahalewar buɗewa a jihar.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar, mai ɗauke da sa hannun shugaban ta, Sheikh Abbas Abubakar Daneji, ta bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne bisa tanade-tanaden dokar tantance masallatan Juma’a ta shekarar 2003.

Sheikh Daneji ya ce, baya ga rashin bin ka’ida, masallacin ya yi kusa da hedikwatar hukumar Hisbah, inda s**a kasance a katanga ɗaya, abin da ya saba da tsarin da doka ta tanada.

Sanarwar ta ƙara da cewa an tura takardar dakatarwar zuwa ofishin mataimakin babban sufeton ƴansanda mai kula da shiyya ta ɗaya (Zone One), rundunar ƴan sanda ta jihar Kano, fadar mai martaba Sarkin Kano, Ma’aikatar Harkokin Addinai ta jihar, da kuma ofishin hukumar tsaron farin kaya ta ƙasa (DSS), reshen Kano, domin a duba batun.

Sphere News Hausa

Marcus Rashford ya nuna bajinta yayin da Barcaleno ta doke Newcastle da ci 2-1 har gida.Yaya kuka ga wasan?
19/09/2025

Marcus Rashford ya nuna bajinta yayin da Barcaleno ta doke Newcastle da ci 2-1 har gida.

Yaya kuka ga wasan?

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sphere News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share