Sabuwar Nigeria

Sabuwar Nigeria Domin samun sahihan labarai kan ayyukan da Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa a faɗin Najeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin K**a Dukkan Masu Hannu a Kisan Masu Ibada a MalumfashiGwamnatin Tarayya ta bayyana cew...
22/08/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin K**a Dukkan Masu Hannu a Kisan Masu Ibada a Malumfashi

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta bi diddigin masu hannu a mummunan kisan da aka yi wa masu ibada a karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina, tare da tabbatar da cewa an gurfanar da su a gaban shari’a.

A cikin wata sanarwa, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce wannan ta’addancin da aka aikata kan mutanen da s**a taru domin bauta wa Allah ba zai taɓa wucewa babu hukunci ba.

Ya bayyana cewa jami’an tsaro sun soma ƙoƙarin farauto waɗanda s**a aikata wannan mummunan aiki, tare da tabbatar da cewa an kamo su da hukunta su.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan waɗanda s**a rasu, al’ummar Malumfashi da gwamnatin Katsina, yana addu’ar Allah ya jikansu ya kuma ba iyalan juriyar wannan rashi.

Sanarwar ta kuma bayyana nasarorin da aka samu a yaƙin da ake yi da ta’addanci, inda kwanan nan cibiyar yaki da ta’addanci NCTC ta k**a manyan shugabannin ’yan ta’adda ciki har da Mahmud al-Nigeri, da kuma Mahmud Muhammad Usman (Abu Baraa) na ƙungiyar Ansaru.

Gwamnati ta jaddada cewa duk mai zubar da jinin al’ummabba zai sami mafaka a Najeriya ba, tare da tabbatar da cewa ƙarshen ayyukan ta’addanci a ƙasar ya kusa.

Dakarun Sojin Najeriya Na Tabbatar da Cewa Manoma Na Gudanar da Noma Cikin Kwanciyar Hankali – Hedikwatar TsaroHedkwatar...
22/08/2025

Dakarun Sojin Najeriya Na Tabbatar da Cewa Manoma Na Gudanar da Noma Cikin Kwanciyar Hankali – Hedikwatar Tsaro

Hedkwatar Tsaro ta bayyana cewa dakarun soji a faɗin ƙasar na ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin tabbatar da cewa manoma suna gudanar da ayyukansu ba tare da cikas ba. Daraktan Ayyukan Yaɗa Labarai na Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka a Abuja yayin fitar da rahoton mako na ayyukan tsaro.

Ya ce sojoji tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro da rundunonin haɗaka, sun ƙara tsananta kai sumame ta ƙasa da sama kan ’yan ta’adda, masu tayar da kayar baya, ’yan bindiga da masu fasa bututun mai.

Kangye ya ce irin wannan tsanantawar ya haifar da hallaka ’yan ta’adda da dama, cafke masu taimaka musu, ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, da kuma kwato mak**ai, ababen hawa da kuɗaɗe. A Arewa maso Gabas, sojojin Operation Hadin Kai sun hallaka ’yan Boko Haram da ISWAP da dama tare da cafke wasu da kuma ceto fursunoni a jihohin Borno da Yobe. A Arewa maso Yamma kuwa, sojojin Operation Fasan Yamma sun ceto mutane 60 da aka yi garkuwa da su tare da k**a wasu mutum 14 da ake zargi da taimaka wa ’yan ta’adda.

Haka kuma, a Arewa ta Tsakiya, dakarun Operation Safe Haven da Whirl Stroke sun cafke mashahurin mai aikata laifi Adamu Buba, wanda aka fi sani da “Mai Pankshin,” tare da wasu abokan harkarsa 13 a Jihar Filato da Kaduna. A Kudancin Najeriya, sojojin Operation Delta Safe sun bankado satar mai da darajarta ta kai Naira miliyan 25 tare da rushe haramtattun wurare tace mai. A Kudu maso Gabas kuma, an samu nasarar k**awa da kashe mambobin haramtacciyar ƙungiyar IPOB/ESN tare da ceto mata masu juna biyu da yara daga gidan marayu na bogi a Jihar Imo. Kangye ya tabbatar da cewa dakarun za su ci gaba da wannan ƙoƙari har sai an tabbatar da cikakken zaman lafiya a ƙasar.

Hedikwatar Tsaro ta Ƙasa Ta Ƙaryata Raɗe-Radin Cewa Shugaban Hafsoshin Tsaro Ya Yi Kira da A Ɗauki Makami Don Kare Kai. ...
22/08/2025

Hedikwatar Tsaro ta Ƙasa Ta Ƙaryata Raɗe-Radin Cewa Shugaban Hafsoshin Tsaro Ya Yi Kira da A Ɗauki Makami Don Kare Kai.

* Hedikwatar ta bayyana abin da CDS yake nufi da cewa mutane su koyi dabarun kare kai.

Hedkwatar Tsaro ta ƙaryata rahotannin da suke bayyana cewa Shugaban Hafsoshin Tsaro (CDS), Janar Christopher Musa, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su ɗauki mak**ai. Daraktan Yaɗa Labarai na Tsaro, Birgediya Janar Tukur Gusau, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya ce an juya maganganun CDS a hirar da aka yi da shi a gidan talabijin ranar 20 ga watan Agusta.

Gusau ya bayyana cewa CDS bai yi kira ga ɗaukar mak**ai ba, domin yana sane da dokokin ƙasar da ke hana hakan. A cewarsa, abin da Musa yake nufi shi ne ƙarfafawa ’yan ƙasa su samu ƙwarewar tsira da dabarun kariya, k**ar iya tuƙi don tserewa daga wurin da matsala take, iyo fan kuɓuta daga dulmuyewa a ruwa, taekwondo dan kwatar kai daga bata gari, ko judo da dambe, wanda duk ƙwarewa ce ta rayuwa wadda ke taimakawa wajen kare kai a lokacin hatsari.

Ya ƙara da cewa rundunar sojojin Najeriya tare da sauran hukumomin tsaro na ci gaba da samun nasarori a yaƙi da matsalolin tsaro a sassa daban-daban na ƙasar. Gusau ya tabbatar da cewa wannan ci gaban ya nuna jajircewar gwamnati wajen kare rayuka da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin Najeriya.

Shugaba Tinubu Ya Yi Alkawarin Kammala Ginin Kwalejin Tsaro ta Ƙasa (National Defence College)Shugaban Ƙasa Bola Ahmed T...
22/08/2025

Shugaba Tinubu Ya Yi Alkawarin Kammala Ginin Kwalejin Tsaro ta Ƙasa (National Defence College)

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta kammala ginin Kwalejin Tsaro ta Ƙasa wato National Defence College (NDC) domin inganta horon dabarun tsaro ga Najeriya da ƙasashen abokan hulɗa. Tinubu, wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya wakilta, ya yi wannan jawabi ne a bikin kammala karatun Course 33 na NDC, wanda aka gudanar a Abuja, inda jami’ai 99 daga ƙasashe 19 s**a kammala.

Shugaban ya ce an riga an samu ci gaba wajen gina wurin a Piwoyi, amma akwai sauran aiki da yawa da za a yi. Ya umarci Kwamandan Makarantar da ya yi aiki tare da Ministan Tsaro wajen tsara dabarun inganta ababen more rayuwa, tare da tabbatar da cewa kwalejin ta ƙara haɓaka har ta zama jami’ar koyar da Digiri na biyu a fannin tsaro. Ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatin sa za ta ɗauki ƙarin matakai domin inganta cibiyar.

Tinubu ya taya waɗanda s**a kammala murnar cin nasara, tare da jaddada muhimmancin darussan da s**a koya na jarumtaka, kishin ƙasa da gaskiya. Ya kuma yi kira ga jami’an daga ƙasashen waje da su ci gaba da gina abota da haɗin kai da s**a samu a Najeriya, domin ƙarfafa zumunci da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen su da Najeriya.

Gwamnatin Tarayya Ta Rufe Shafukan Soshiyal Midiya Miliyan 13.5Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta dakatar da shafukan ...
21/08/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Rufe Shafukan Soshiyal Midiya Miliyan 13.5

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta dakatar da shafukan sada zumunta kimanin miliyan 13.5 a Nijeriya saboda suna ɗauke da saƙwannin da ba su dace ba kuma s**a saɓa wa Dokar Aiki Da Intanet da ake kira "2024 Code of Practice".

Hukumar Haɓaka Fasahar Yaɗa Labarai ta Ƙasa (National Information Technology Development Agency, NITDA), ita ce ta ɗauki matakin tare da bayyana cewa shafukan da ta soke ɗin suna kan manyan manhajojin soshiyal midiya da s**a haɗa da TikTok, Facebook, Instagram, da X (wato Twitter a da), ɗauke da saƙwanni wajen miliyan 59 da aka goge.

Hukumar ta ce wannan abu da aka yi yana daga cikin tsauraran matakan sa-ido da gwamnati take ɗauka kan fagen soshiyal midiya na ƙasar nan wanda ke ƙara girma.

Ta ce soshiyal midiya hanyar sadarwa da kasuwanci ce, to amma tana da haɗari wajen yaɗa labaran ƙarya, cin mutuncin jama'a, almundahanar kuɗi, da cin zarafi.

NITDA takan haɗa gwiwa ne da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (Nigerian Communications Commission, NCC) da Hukumar Yaɗa Labarai ta Gidajen Rediyo Da Talbijin (National Broadcasting Commission, NBC) wajen aiwatar da Dokar Aiki Da Intanet ta 2004.

Gwamnatin Tarayya za ta fara daukar ma’aikatan Hukumar Tsaron Daji (Forest Guards) – RibaduMai ba wa shugaban kasa shawa...
21/08/2025

Gwamnatin Tarayya za ta fara daukar ma’aikatan Hukumar Tsaron Daji (Forest Guards) – Ribadu

Mai ba wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce Gwamnatin Tarayya ta fara aiwatar da tsarin daukar ma’aikata karkashin shirin Masu Tsaron Daji (Forest Guards) a matsayin wani bangare na yaki da matsalolin tsaro a karkashin shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Tinubu.

Ribadu ya bayyana haka ne a Abuja a ranar Laraba yayin kaddamar da sababbin motocin aiki 46 da aka raba wa sassan tsaro daban-daban a fadin kasar nan. Ya ce tsarin zai baiwa kowace jiha damar daukar ma’aikata tsakanin 2,000 zuwa 5,000 gwargwadon karfin su.

Ya ce shirin zai taimaka wajen kare al’ummomi, dazuzzuka da albarkatun kasa na Najeriya. Ribadu ya kara da cewa akwai sauye-sauye masu ma’ana da ake samu kullum a fannin tsaro, wadanda koda ba su fito fili ba, ana ganin tasirinsu a rayuwar al’umma.

Gwamnatin Tarayya ta raba kimanin Naira Biliyan 50 ga ƙananan asibitocin Sha-Ka-Tafi a faɗin ƙasar – PateGwamnatin Taray...
21/08/2025

Gwamnatin Tarayya ta raba kimanin Naira Biliyan 50 ga ƙananan asibitocin Sha-Ka-Tafi a faɗin ƙasar – Pate

Gwamnatin Tarayya ta ce ta raba kimanin Naira Biliyan 50 kai tsaye ga cibiyoyin kiwon lafiya na Sha-Ka-Tafi (PHCs) a fadin ƙasar nan ta hanyar Asusun Samar da Kiwon Lafiya na (BHCPF).

Ministan Lafiya Farfesa Muhammad Ali Pate, ne ya bayyana haka a Abuja a ranar Litinin. Ya ce hakan ya samar da ci gaba mai ma’ana wajen inganta tsarin kiwon lafiya a matakin ƙasa.

Farfesa Pate ya kuma ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta kuma saki sama da N20 biliyan don gyara da sabunta cibiyoyin kiwon lafiya 4,362 a jihohin Arewa 19 da Babban Birnin Tarayya (FCT).

Ministan ya kara da cewa, sama da mutane miliyan 37 ne s**a je cibiyoyin kiwon lafiya na Sha-ka-tafi a fadin Najeriya a watanni huɗu na farkon shekarar 2025, wanda ke nuna cewa sabbin matakan gwamnatin Tinubu na tasiri wajen tsare-tsaren kiwon lafiya da samar da bayanan kididdigar wadanda aka duba.

Haka kuma, ya ce shirin inshorar lafiya na gwamnati ya samu ci gaba sosai inda ake sa ran shigar da mutane fiye da na shekara ta 2024 da s**a kai miliyan 2.4 kafin karshen shekara.

Mutane 897 Daga Arewa Maso Gabas ne S**a Amfana da Ragin Kuɗin wankin Ƙoda a Jihar Bauchi. Asibitin koyarwa na Abubakar ...
21/08/2025

Mutane 897 Daga Arewa Maso Gabas ne S**a Amfana da Ragin Kuɗin wankin Ƙoda a Jihar Bauchi.

Asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi (ATBUTH) ya bayyana cewa mutane 897 daga jihohin Arewa maso Gabas sun amfana da wankim Ƙoda a sassauƙan farashin da gwamnatin tarayya ta rage daga Naira 50,000 zuwa Naira 12,000. Jami’in hulɗa da jama’a na asibitin, Malam Usman Koli, ya ce an fara aiwatar da wannan tsari tun daga ranar 8 ga Janairu, 2025, inda aka shigar da duk kayan aiki da magunguna cikin farashin da aka kayyade domin rage wa marasa lafiya da iyalansu nauyin kashe kuɗi.

Koli ya ƙara da cewa ATBUTH Bauchi ta kasance a sahun gaba wajen aiwatar da shirye-shiryen gwamnatin tarayya na Renewed Hope Agenda wajen inganta kiwon lafiya. Tun daga watan Nuwamba, 2024, asibitin ya fara aiwatar da aikin haihuwa ta tiyata (Caesarean Section) kyauta ga mata masu juna biyu, wanda ya haɗa da magani, kulawa bayan haihuwa da kuma jinya ga uwa da jariri. Ya bayyana cewa fiye da mata 1,000 da jariran su sun amfana da shirin.

Haka kuma, ATBUTH na cikin manyan cibiyoyi na farko da s**a kaddamar da Tsarin kasa na Agajin Gaggawa na ‘National Emergency Medical Service and Ambulance System’ a Najeriya. Tuni fiye da marasa lafiya 500 s**a amfana da kulawar gaggawa kyauta har na tsawon sa’o’i 48 tun bayan kaddamar da shirin a Bauchi. Koli ya yabawa gwamnatin tarayya bisa ƙoƙarinta na sauƙaƙa wa al’umma musamman masu ƙaramin ƙarfi, inda ya tabbatar da cewa asibitin zai ci gaba da bayar da gudunmawa wajen kawo sauƙi a harkar lafiya a Arewa maso Gabas da Najeriya baki ɗaya.

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Rijistar Shirin Horas da Matasa 100,000 a Fannin Ilimin Hada-Hadar KuɗiGwamnatin Tarayya ta sa...
20/08/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Rijistar Shirin Horas da Matasa 100,000 a Fannin Ilimin Hada-Hadar Kuɗi

Gwamnatin Tarayya ta sanar da fara rijistar matasa domin shiga cikin shirin koyar da ilimin Hada-Hadar kuɗi kyauta da zai horas da matasa 100,000 a kowace shekara a fannin kasuwancin duniya, ƙirƙirar sana’o’i da zuba jari. Daraktar Sashen Yaɗa Labarai na Ma’aikatar Cigaban Matasa, Omolara Esan ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa a Abuja, inda ta ce an haɗa gwiwa da Investonaire Academy wajen aiwatar da shirin.

Ta bayyana cewa shirin zai taimaka wajen ba matasa dabarun fahimtar manyan fannonin kasuwanci na duniya k**ar harkar kayan masarufi, zinare, hannayen jari da musayar kuɗaɗen kasa da kasa (forex). Haka kuma, za a koyar da su dabarun magance hatsarin afkawa hasara a kasuwanci, yadda za a samar da kundin jarin kasuwanci da hanyoyin haɓaka tattalin arziƙi. Ta ce duk wanda ya kammala za a ba shi takardar shaidar da masana’antu ke amincewa da ita wacce za ta taimaka wajen cigaban haɓakar kasuwanci.

Esan ta ƙara da cewa horon zai gudana ta hanyar tsarin Learning Management System (LMS) da ke haɗa darussa cikin salo na zamani. Haka kuma, za a fara horon kai tsaye a Abuja nan gaba kadan kafin a miƙa shi zuwa sauran jihohi. Ta jaddada cewa shirin kyauta ne, kuma a buɗe yake ga dukkan matasan Najeriya ciki har da ɗalibai, masu bautar ƙasa (NYSC), ‘yan kasuwa, masu neman aiki da ƙwararrun matasa a faɗin ƙasar.

Gwamnatin Tarayya Za Ta Samar da Ƙaramar Tashar Lantarki  ga Makarantun Gaba da Sakandare Nan da 2026Gwamnatin Tarayya t...
20/08/2025

Gwamnatin Tarayya Za Ta Samar da Ƙaramar Tashar Lantarki ga Makarantun Gaba da Sakandare Nan da 2026

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa nan da shekarar 2026, dukkan makarantun gaba da sakandare a ƙasar za su samu Ƙaramar Tashar Lantarki domin samar da isasshen wutar lantarki. Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya bayyana haka a wajen ƙaddamar da sabon ɗakin taro na Olatunji Bello Auditorium da aka gina a Jami’ar Jihar Legas (LASU). Ya ce wannan wani alƙawari ne na Shugaba Bola Ahmed Tinubu ga ɗalibai da jami’o’i a faɗin ƙasa.

Alausa ya bayyana cewa an amince da ƙaramar tasahar lantarkin mai ƙarfin Megawatt 5 domin harabar Epe dake LASU, yayin da TETFund za ta samar da Megawatt 11 domin babbar harabar jami’ar da ke Ojo. Ya ce samun isasshen wutar lantarki zai ba matasa damar ƙara bincike, ƙirƙira da fasaha, wanda zai taimaka wajen bunƙasa ci gaban ƙasa.

Shugaba Tinubu Ya Cire Harajin kashi 5 Da Aka Sanya Kan Kuɗin Waya da Data a NajeriyaShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, y...
20/08/2025

Shugaba Tinubu Ya Cire Harajin kashi 5 Da Aka Sanya Kan Kuɗin Waya da Data a Najeriya

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya cire harajin kashi biyar (5%) da ake ɗora wa kan ayyukan sadarwa da s**a gaɗa da kiran waya da Data a ƙasar nan. Mataimakin Shugaban Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), Dr. Aminu Maida, ne ya tabbatar da hakan, inda ya bayyana cewa sabuwar dokar haraji da Shugaban Ƙasa ya rattaba hannu a kai ta tabbatar da cire wannan nauyi daga kan ‘yan Najeriya.

A cewar Dr. Maida, cire wannan haraji zai rage wa masu amfani da wayar hannu da sauran ayyukan sadarwa nauyin kuɗi, wanda hakan zai taimaka wajen sauƙaƙa rayuwa da kuma rage matsin lamba kan jama’a. Ya ce, wannan mataki ya yi daidai da manufofin gwamnati na sauƙaƙa rayuwar ‘yan ƙasa da kuma bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.

Ya ƙara da cewa, cire harajin zai ƙara ƙarfin amfani da fasahar sadarwa a Najeriya, wanda hakan zai samar da ƙarin damar kasuwanci da kuma ci gaban tattalin arziki. Haka kuma, ya nuna cewa gwamnati za ta ci gaba da duba hanyoyin da za su rage wa jama’a nauyin haraji a fannonin daban-daban.

20/08/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa wurin gabatar da taron cigaban ƙasashen Africa (TICA9) da ake batarwa yau a Birnin Tokyo na ƙasar Japan

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sabuwar Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sabuwar Nigeria:

Share

Category