Sabuwar Nigeria

Sabuwar Nigeria Domin samun sahihan labarai kan ayyukan da Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa a faɗin Najeriya

Gwamnatin Tarayya da Tarayyar Turai sun kaddamar da shirin ilimi da ƙarfafawa matasa a Arewacin NajeriyaGwamnatin Tarayy...
15/10/2025

Gwamnatin Tarayya da Tarayyar Turai sun kaddamar da shirin ilimi da ƙarfafawa matasa a Arewacin Najeriya

Gwamnatin Tarayyar Najeriya tare da Tarayyar Turai (EU) sun kaddamar da sabon shiri na ilimi da ƙarfafawa matasa mai darajar Yuro miliyan 40 domin inganta harkar ilimi a yankin Arewa maso Yamma na ƙasar.

An gudanar da kaddamarwar ne a Abuja, inda babban sakataren ma’aikatar ilimi ta tarayya, Abel Olumuyiwa Enitan, wanda Dr. Ejeh Usman ya wakilta, ya bayyana shirin a matsayin ginshikin manufar Renewed Hope Agenda ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma ‘Education Sector Renewal Initiative’ da ke nufin tabbatar da dama ga kowa wajen samun ingantaccen ilimi.

Shugabar sashen ilimi na matakin farko, Dr. (Mrs) Folake Davies Olatunji, ta ce shirin zai mayar da hankali ne wajen koyar da ilimi tun daga tushe, horar da malamai, inganta ilimin zamani ta hanyar fasaha da kuma bayar da damar ilimi ga kowa.

A nata jawabin, wakiliyar EU, Ms. Kate Kanebi, ta tabbatar da jajircewar Tarayyar Turai, inda ta bayyana cewa kuɗin da ya kai Naira biliyan 69.9 za su tallafa wajen samar da tsare-tsaren karatu cikin aminci, koyar da sana’o’in dogaro da kai musamman ga mata da marasa galihu.

Cibiyoyi irin su UBEC, TRCN, UNESCO, UNICEF, Plan International, Save the Children da kuma Bankin Duniya sun halarci taron.

Ƙarshe, taron ya kammala da alkawarin hadin gwiwa wajen tabbatar da ilimi mai inganci da ya shafi kowa a fadin ƙasar.

Sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC na nuna raunin jam’iyyun adawa — ShettimaMataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ce...
14/10/2025

Sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC na nuna raunin jam’iyyun adawa — Shettima

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ce yawaitar sauya sheka daga jam’iyyun adawa zuwa jam’iyyar APC na bayyana raunin da ke cikin jam’iyyun adawa, yayin da APC ke ƙara ƙarfi.

Shettima ya bayyana haka ne a Enugu, inda ya wakilci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a taron maraba da Gwamna Peter Mbah na jihar Enugu, tare da wasu ‘yan majalisar sa da magoya bayansa, da s**a koma APC daga PDP.

A cewarsa, “hanyoyin da APC ta shimfiɗa sun zama gadar haɗin kai, yayin da jam’iyyun adawa ke fuskantar ɓarakar da s**a gina da hannayensu.”

Ya kara da cewa tsarin shugabancin Tinubu, wanda ke da sauraro kowa da ɗaukar kowa babu wariya, shi ya mayar da APC jam’iyya mafi ƙarfi a nahiyar Afirka.

Shettima ya kuma bayyana Gwamna Mbah a matsayin wanda “tun da dadewa yake mai kishin cigaba,” yana mai cewa da alama ya dade da buya da tsintsiya a cikin alamar jam’iyyarsa ta umbrella (PDP).

“Yanzu da ka fito fili, za ka jagoranci gina APC a Jihar Enugu, kuma kana da goyon bayan shugaban ƙasa da jam’iyya baki ɗaya,” in ji shi.

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya ce zuwan Gwamna Mbah da magoya bayansa ya nuna cewa APC ce “gida na gaske ga masu kishin ci gaba.”

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, duka sun yaba da sauya shekar Gwamna Mbah, suna masu cewa hakan ya nuna sabon shafi ga siyasar yankin Kudu maso Gabas.

A nasa jawabin, Gwamna Mbah ya ce matakin da s**a ɗauka na shiga APC ba na shi kaɗai ba ne, illa alƙiblar da dukan jam’iyyarsa da magoya bayansa s**a amince da ita.

Ya ce: “Yau mun yanke shawara tare da haɗin kai, domin mu samu damar shiga sahun gaba a siyasar ƙasa. APC ce babbar jam’iyya a Afirka, kuma yanzu mun dawo gida.”

Gwamna Hope Uzodinma na Imo, wanda ke jagorantar kungiyar gwamnonin APC, ya ce shigar Enugu cikin APC zai ƙara ƙarfafa matsayin shugaban ƙasa a yankin Kudu maso Gabas da siyasar ƙasa baki ɗaya.

Shirin Shugaba Tinubu na rangwamen kuɗin wanke koda ya amfanar marasa lafiya da dama a Jihar KanoGwamnatin Tarayya ta ka...
12/10/2025

Shirin Shugaba Tinubu na rangwamen kuɗin wanke koda ya amfanar marasa lafiya da dama a Jihar Kano

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin rage kuɗin wanke koda daga ₦50,000 zuwa ₦12,000, ragin da ya kai sama da kashi 76 cikin ɗari. Wannan mataki na daga cikin manufofin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Bola Tinubu domin sauƙaƙa wa ‘yan ƙasa samun kiwon lafiya mai ingancin da sauƙi.

Rahotanni daga Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) sun nuna cewa yawan marasa lafiya da ke zuwa neman jinya ya ƙaru sosai tun bayan da aka rage kuɗin. A cewar Tijjani Rahim, Mataimakin Daraktan Sashen Ma’aikatan Jinya (Nas) da ke kula da sashen wanke koda, yanzu ana duba marasa lafiya 22 zuwa 25 a kowace rana.

Wani mara lafiya, Sani Musa, ya ce kafin rangwamen yana biyan kuɗi tsakanin ₦54,000 da ₦60,000 a kowane zama. Ya ce daga baya aka rage shi zuwa ₦20,000 kafin yanzu ya sauka zuwa ₦12,000. Shi ma Mamuda Aliyu ya bayyana cewa ragin ya ba shi damar ci gaba da jinya. Haka zalika, Hafiza Isa ta ce a baya tana biyan ₦60,000, daga baya ₦55,000, sannan ₦45,000, kafin a rage zuwa ₦20,000.

A nasa jawabin, Shugaban Asibitin AKTH, Abdurrahman Sheshe, ya tabbatar da fara shirin rangwamen a Kano, inda aka tura kayan aiki da za su iya ɗaukar zama 1,000 na wanke koda.

Ya yi wannan bayani ne a lokacin ƙaddamar da shirin National Emergency Medical Services and Ambulance Scheme (NEMSAS) a asibitin, wanda zai bai wa mata masu juna biyu, yara, waɗanda s**a samu haɗari da sauran ayyukan gaggawa damar samun awanni 48 na jinya kyauta da sufuri na gaggawa.

Shirin rangwamen wanke koda na cikin tsare-tsaren gyaran kiwon lafiya da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa, ciki har da Basic Health Care Provision Fund (BHCPF) da kuma NEMSAS.

A ranar 21 ga Agusta 2025, gwamnatin tarayya ta amince da shirin a manyan asibitoci 11 na tarayya da ke fadin ƙasar.

Shugaba Tinubu ya tafi Birnin Rome domin halartar taron Shugabannin ƙasashe na ‘Aqaba Process’Shugaba Bola Ahmed Tinubu ...
11/10/2025

Shugaba Tinubu ya tafi Birnin Rome domin halartar taron Shugabannin ƙasashe na ‘Aqaba Process’

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bar Abuja a yau Lahadi domin halartar taron shugabannin ƙasashe na “Aqaba Process” a birnin Rome na ƙasar Italiya.

Taron, wanda zai fara a ranar 14 ga watan Oktoba, zai mayar da hankali kan matsalolin tsaro da s**a addabi yankin Yammacin Afirka.

An kaddamar da Aqaba Process a shekarar 2015 karkashin jagorancin Sarkin Jordan, Abdullah II, tare da haɗin gwiwar gwamnatin Italiya. Manufarsa ita ce ƙarfafa haɗin kai tsakanin ƙasashe da hukumomin tsaro wajen yaki da ta’addanci da sauran manyan barazanar tsaro.

A cewar fadar shugaban ƙasa, tattaunawar za ta mai da hankali kan yadda za a magance yaɗuwar ƙungiyoyin ta’addanci a Sahel, da haɗin gwiwar da masu laifi ke yi da ‘yan ta’adda, da kuma barazanar ta’addanci da fashi a teku da ke ƙara taɓarɓarewa a Tekun Guinea.

Za a kuma tattauna yadda za a yaki yaɗa ra’ayin ƙungiyoyin ta’addanci a intanet da kuma yadda za a katse hanyoyin sadarwar da suke amfani da su wajen yaɗa saƙonni da kuma jan magoya baya.

Shugaba Tinubu zai yi wasu tattaunawa na kashin kai da shugabannin ƙasashe daban-daban domin neman hanyoyin magance kalubalen tsaro da s**a addabi yankin.

Shugaban ya samu rakiya daga wasu manyan jami’an gwamnati ciki har da Ƙaramar Ministan Harkokin Waje, Bianca Odumegwu-Ojukwu, Ministan Tsaro Mohammed Badaru Abubakar, Mai ba shi shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, da kuma Darakta-Janar na Hukumar Sirri ta Kasa (NIA), Mohammed Mohammed.

Hukumar Kwastan ta karyata jita-jitar da ake yadawa na adadin wadanda ta dauka daga Arewa da Kudancin NajeriyaHukumar Kw...
11/10/2025

Hukumar Kwastan ta karyata jita-jitar da ake yadawa na adadin wadanda ta dauka daga Arewa da Kudancin Najeriya

Hukumar Kwastan ta Najeriya (NCS) ta fitar da gargadi kan wani sako da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin nuna yawan wadanda aka tantance daga kowace jiha domin zagayen karshe na daukar ma’aikata a shekarar 2025.

A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a yau, ta ce wannan bayani ba daga gare ta ya fito ba, kuma ba gaskiya bane ba.

A cewar hukumar, tsarin daukar ma’aikata na bana ya fara ne da sanarwar hukuma a ranar 27 ga Disamba, 2024, inda aka samu mutane 573,523 da s**a nemi manyan rukunai guda uku da s**a hada da, Superintendent, Inspectorate da Customs Assistant. Daga ciki, an tantance mutane 286,697 bayan duba takardun su, sannan aka gayyace su zuwa zagaye na farko na jarabawar kwamfuta (CBT).

Hukumar ta ce daga cikin wadanda shiga wannan jarabawa, masu neman rukunin Superintendent ne kadai aka bai wa damar ci gaba zuwa matakin na gaba, wanda za a gudanar da shi a cibiyoyi na musamman a kowace shiyya ta kasar nan.

Hukumar ta kara da cewa wannan tsari ne da zai daidaita da manufar adalci, gaskiya, da bin tsarin kowane yanki ya samu wakilci, tare da tabbatar da cancanta.

NCS ta ja hankalin ‘yan kasa musamman masu neman aikin da su dogara da shafukan hukumar domin samun sahihan bayanai, tare da kauce wa yada bayanan karya da ka iya jefa mutane cikin rudani ko kuma yaudara.

Hukumar ta kuma tunatar da masu nema cewa duk wani sabon bayani kan daukar ma’aikata ana wallafawa kai tsaye a shafin NCS Recruitment Update Portal ta adireshin https://updates.customs.gov.ng.

Jerin sunayen Wadanda Gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi wa Afuwa da Sassauci kan hukuncin da aka zartar musu. Shugaba Bola ...
11/10/2025

Jerin sunayen Wadanda Gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi wa Afuwa da Sassauci kan hukuncin da aka zartar musu.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa manyan fursunoni da tsofaffin fursunoni guda 175 afuwa da sassauci, ciki har da marigayi Major Janar Mamman Jiya Vatsa, marigayi Ken Saro-Wiwa, “Ogoni Nine”, tare da Maryam Sanda da wasu da dama.

Kwamitin bada shawara kan afuwar shugaban ƙasa, ƙarƙashin jagorancin Ministan Shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi ne ya bada shawarar yin afuwa ga tsofaffin fursunoni 15 (11 daga cikinsu sun riga sun rasu), da bayar da sassauci ga fursunoni 82, tare da rage wa’adi ga fursunoni 65. Haka kuma, an mayar da hukuncin kisa ga fursunoni bakwai zuwa daurin rai-da-rai.

Prince Fagbemi ya gabatar da wannan rahoto a taron Council of State ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Cikakken Sunayen Waɗanda S**a Amfana da Afuwa da Sassauci

Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa
1. Nweke Francis Chibueze (44) – daurin rai-da-rai saboda kwayar Co***ne.
2. Dr Nwogu Peters (67) – hukuncin shekara 17 saboda zamba tun 2013.
3. Mrs Anastasia Daniel Nwaoba (63) – ta rigaya ta kammala zaman gidan yari saboda zamba.
4. Barr. Hussaini Alhaji Umar (58) – an yanke masa tara N150M a shari’ar ICPC a 2023.
5. Ayinla Saadu Alanamu (63) – an yanke masa shekara 7 saboda cin hanci a 2019.
6. Hon. Farouk M. Lawan (62) – an yanke masa shekara 5 saboda rashawa a 2021.

Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa Bayan Mutuwarsu

7. Sir Herbert Macaulay – an hana shi muk**an siyasa a 1913 saboda zargin karkatar da kuɗi ta hannun Turawan mulkin mallaka.
8. Major Janar Mamman Jiya Vatsa – an kashe shi a 1986 saboda zargin juyin mulki.

Ogoni Nine
9. Ken Saro-Wiwa
10. Saturday Dobee
11. Nordu Eawa
12. Daniel Gbooko
13. Paul Levera
14. Felix Nuate
15. Baribor Bera
16. Barinem Kiobel
17. John Kpuine

An kuma yi girmamawa ta musamman ga waɗanda aka kashe a wannan rikici:
• Chief Albert Badey
• Chief Edward Kobaru
• Chief Samuel Orage
• Chief Theophilus Orage

Sassauci da Rage Hukunci

Da dama daga cikin waɗanda s**a amfana sun nuna nadama, sun koyi sabbin sana’o’i a gidan yari, ko kuma sun nuna halin kirki. Sun haɗa da:
• Maryam Sanda (37) – an yanke mata hukuncin kisa a 2020 saboda kisan mijinta; yanzu ta amfana daga sassauci bisa nadama da kyakkyawar halinta a gidan yari da kuma bukatar kare yaranta biyu.
• Farfesa Magaji Garba – an yanke masa hukuncin shekara 7 saboda zamba a 2021, an rage shi zuwa shekara 4.
• Major S.A. Akubo – an yanke masa hukuncin rai-da-rai saboda cire mak**ai ba bisa ƙa’ida ba, yanzu an rage zuwa shekara 20.
• Haka kuma fursunoni da dama da aka k**a da laifukan miyagun ƙwayoyi, kisan kai, satar jama’a da cin hanci sun ci gajiyar rage hukunci ko sauyi daga kisa zuwa daurin rai-da-rai.

Waɗanda Aka Sauya daga Hukuncin Kisa Zuwa Rai-Da-Rai

Fursunoni bakwai, ciki har da waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa saboda kisan kai, fashi da makami da miyagun ƙwayoyi, duk sun amfana daga wannan sassauci, an mayar da hukuncinsu zuwa daurin rai-da-rai saboda nuna nadama da ɗabi’a mai kyau.

NELFUND ta sake buɗe damar tantance ɗalibai don samun Lamuni na shekarar karatu ta 2024/2025Hukumar Lamunin Ilimi ta Naj...
11/10/2025

NELFUND ta sake buɗe damar tantance ɗalibai don samun Lamuni na shekarar karatu ta 2024/2025

Hukumar Lamunin Ilimi ta Najeriya (NELFUND) ta amince da sake buɗe rukunin tantance ɗalibai karo na ƙarshe har na tsawon awanni 48, domin jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi ba su kammala tantance dalibai masu nema ba. Wannan zai fara ne daga ƙarfe 12:00 na daren ranar Lahadi, 12 Oktoba, har zuwa ƙarfe 12:00 na daren ranar Talata, 14 Oktoba. 
Daraktar Harkokin Sadarwa ta NELFUND, Mrs. Oseyemi Oluwatuyi ta ce an yi wannan ƙarin lokaci ne don tabbatar da cewa duk ɗalibai da s**a cancanta sun shiga jerin wadanda za a tantance don samun Lamunin.

Tun daga ƙaddamar da shirin a ranar 24 ga Mayu, 2024, NELFUND ta karbi rejistar ɗalibai sama da 835,000 waɗanda s**a nemi lamunin ta shafin hukumar na Intanet. 

Daga cikin waɗanda s**a yi rejista, kimanin dalibai 510,378 ne s**a sami lamunin. Adadin kuɗin da aka raba ya kai kimanin Naira Biliyan 9.5, inda ake biyan kuɗin makaranta (institutional fees) kai tsaye ga jami’o’i da kuma kudin kashewa (upkeep allowance) ga ɗalibai. 

Manufar NELFUND ita ce samar da lamunin ilimi mara ruwa (interest-free), domin ɗalibai su samu damar karatu ba tare da tsaikon rashin kuɗi ba. A farkon matakin aiwatar da shirin, an ƙayyade cewa kimanin ɗalibai miliyan 1.2 ne za su amfana da shirin zuwa shekarar 2025 daga jami’o’i da manyan makarantun gaba da sakandire na gwamnati da ke fadin kasar. 

Oluwatuyi ta yi gargadi ga jami’o’i da cibiyoyin da ba su kammala tantance ɗalibansu ba cewa idan ba su yi hakan ba cikin wannan ƙarin awanni 48, za su rasa damar shiga wannan zagayen lamunin. Ta kuma ce za a fitar da jerin sunayen jami’o’in da s**a gaza tantancewa don a bayyana su a fili saboda dalibai su san inda matsalar take. 

Shugaba Tinubu ya taya tsohon mataimakin shugaban ƙasa Namadi Sambo murna bisa nadin sa a matsayin Sardaunan ZazzauShuga...
10/10/2025

Shugaba Tinubu ya taya tsohon mataimakin shugaban ƙasa Namadi Sambo murna bisa nadin sa a matsayin Sardaunan Zazzau

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Namadi Sambo, murna bisa nadin sa da aka yi a matsayin Sardaunan Zazzau daga Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli.

Nadin ya gudana ne a ranar Asabar, 11 ga Oktoba, a Zariya, Jihar Kaduna.

A cikin wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa, Tinubu ya bayyana wannan mukami da cewa yana da matuƙar daraja a al’adu da tarihi na Arewacin Najeriya, kuma ya nuna yadda masarautar Zazzau ta amince da basira, gaskiya da jajircewar Namadi Sambo wajen ci gaban al’umma.

Shugaban ya ce wannan girmamawa alama ce ta jagoranci nagari da gudummawar Sambo ga cigaban ƙasa tun daga lokacin da ya rike manyan muk**ai a gwamnati.

Ya kuma yabawa Sarkin Zazzau bisa ci gaba da riƙe al’adar girmama mutanen da s**a yi fice wajen jagoranci, kishin ƙasa da kuma ɗorewar zaman lafiya.

Shugaba Tinubu ya yi fatan Allah ya ba tsohon mataimakin shugaban ƙasa nasara a sabuwar rawar da zai taka, tare da kira gare shi da ya ci gaba da zama abin koyi ga matasa da kuma yin aiki kafada da kafada da shugabannin gargajiya domin ci gaban al’umma da ƙasar baki ɗaya.

Shugaba Tinubu ya yafe wa Mamman Vatsa, Herbert Macaulay da wasu mutane 174Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi amfani da ik...
09/10/2025

Shugaba Tinubu ya yafe wa Mamman Vatsa, Herbert Macaulay da wasu mutane 174

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya yi amfani da ikon sa na gafarar shugaban ƙasa wajen yafe wa fitattun mutane da dama ciki har da Herbert Macaulay da Manjo Janar Mamman Jiya Vatsa wanda aka kashe a 1986 bisa tuhumar yunkurin juyin mulki.

Mamman Vatsa, wanda kuma shahararren mawaƙin Zube ne, ya samu wannan gafara ne bayan amincewar Majalisar Ƙasa da ta zauna a Abuja a ranar Alhamis.

Haka kuma, shugaban ƙasa ya yafe wa Herbert Macaulay, ɗaya daga cikin jagororin neman ’yancin Najeriya da ya kafa jam’iyyar NCNC tare da Dr. Nnamdi Azikiwe. Duk da Macaulay ya rasu tun 1946, har yanzu yana ɗauke da tabon kasancewa ɗan gidan yari daga hukuncin da Turawan mulkin mallaka s**a yanke masa.

Tinubu ya kuma yafe wa wasu tsofaffin masu laifi, ciki har da tsohon ɗan majalisa Farouk Lawan, tare da Mrs Anastasia Daniel Nwaobia, Barrister Hussaini Umar, da Ayinla Saadu Alanamu. An bayyana cewa sun nuna nadama kuma ana son ba su damar sake shiga cikin al’umma.

Sauran da s**a ci gajiyar gafarar sun haɗa da Nweke Francis Chibueze, wanda akai wa daurin rai-da-rai kan laifin hodar iblis, da kuma Dr Nwogu Peters wanda ya shafe shekaru 12 cikin hukuncin shekara 17 kan zamba.

Haka zalika, shugaban ƙasa ya bai wa Ogoni Nine cikakkiyar gafara, waɗanda s**a haɗa da Ken Saro-Wiwa, Saturday Dobee, Nordu Eawo, Daniel Gbooko, Paul Levera, Felix Nuate, Baribor Bera, Barinem Kiobel da John Kpuine.
Ya kuma ba da lambar girmamawa ta ƙasa ga Ogoni Four, Chief Albert Badey, Chief Edward Kobani, Chief Samuel Orage da Theophilus Orage.

An bai wa fursunoni 82 cikakkiyar gafara, an rage wa 65 hukunci, sannan an sauya wa 7 girman hukuncin daga hukuncin kisa zuwa daurin rai-da-rai.

Shugaban ya yi wannan ne bisa shawarwarin Kwamitin Taimaka wa Shugaban Ƙasa kan Gafara (PACPM) wanda Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), ke jagoranta. Kwamitin ya kunshi mambobi 12 ciki har da wakilan hukumar ’yan sanda, hukumar gyaran hali, hukumar kare haƙƙin bil’adama, majalisar koli ta musulunci da kuma majalisar kiristoci ta Najeriya.

Rahoton kwamitin ya nuna cewa daga cikin 294 da aka tantance, mutum 175 aka amince su ci gajiyar wannan shirin bisa ƙa’idoji k**ar tsufa, rashin lafiya, ƙarancin shekaru, da kyakkyawan halayya a gidan gyaran hali.

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tura Sabbin Dakarun Tsaron Daji 130,000 Don Fatattakar ‘Yan Bindiga a Dazuzzuka — RibaduMai ba d...
09/10/2025

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tura Sabbin Dakarun Tsaron Daji 130,000 Don Fatattakar ‘Yan Bindiga a Dazuzzuka — Ribadu

Mai ba da shawara kan harkokin tsaro na ƙasa, Mallam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da sabon shiri na tsaro da ake kira “Forest Guards Initiative” domin fatattakar ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane da sauran miyagu daga dazuzzukan Najeriya.

Ribadu ya bayyana haka ne a Abuja a ranar Alhamis yayin taron shugabannin tsaro na tarayya da jihohi (FSSAM) da aka gudanar a Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa. Ya ce wannan shiri da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da shi, na nufin ɗaukar matakin kai tsaye kan wuraren da miyagun ke buya tsawon shekaru. “Za mu kai farmaki inda masu laifi suke buya. Wannan shiri ne na musamman don kare dazuzzukanmu, dawo da zaman lafiya ga kauyuka, da kuma hana ‘yan bindiga da masu garkuwa damar yin tasiri,” in ji shi.

Ya bayyana cewa akwai fiye da jami’ai 130,000 da aka horar tare da mak**ai da za a tura su dazuzzuka 1,129 da ake da su a ƙasar. A matakin farko, za a fara aikin a jihohin Adamawa, Borno, Niger, Kebbi, Kwara, Sokoto da Yobe. Ribadu ya ce wannan mataki wani ɓangare ne na shirin gwamnatin Tinubu na ƙarfafa tsaron ƙasa domin samun zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki.

Taron na tsawon kwanaki uku ya haɗa jami’an tsaro daga jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya domin nazarin tsarin tsaron cikin gida na ƙasa da kuma bayar da shawarwari kan barazanar tsaro da ƙasar ke fuskanta.

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Na Jagorantar Taron Majalisar ‘Yan Sanda ta Ƙasa a AbujaShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na j...
09/10/2025

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Na Jagorantar Taron Majalisar ‘Yan Sanda ta Ƙasa a Abuja

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na jagorantar zaman Majalisar ‘Yan Sanda ta Ƙasa a zauren majalisar da ke fadar shugaban ƙasa, Abuja. Zaman ya fara ne da ƙarfe 2:39 na rana a yau Alhamis, jim kaɗan bayan Shugaban Ƙasa ya kammala taron Majalisar Ƙoli ta Ƙasa inda ya gabatar da sunan wanda zai aka zaba a matsayin sabon shugaban INEC.

Taron ya zo ne makonni biyar bayan da Shugaban Ƙasa ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya tana nazarin batun kafa rundunar ‘yan sanda na jihohi, tare da ƙarfafa sabbin jami’an tsaron daji (forest guards) da aka tura cikin dazuzzuka domin yaki da matsalar tsaro. A ranar 2 ga Satumba, 2025, yayin da ya karɓi tawagar jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dikko Radda, Shugaba Tinubu ya ce: “Ina duba dukkan fannoni na tsaro; dole ne in samar da rundunar ‘yan sanda ta jihohi.”

A yayin zaman na yau, mahalarta sun yi addu’a domin tunawa da tsohon Sufeton ‘Yan Sanda na Ƙasa, Solomon Arase, wanda ya rasu a ranar 31 ga Agusta, 2025. Majalisar ta yi nazari kan kalubalen tsaro na yanzu, cigaban da aka samu a gyaran da akai a hukumar ‘yan sanda, da kuma harkokin jin daɗi da albarkatun jami’ai a fadin ƙasar. Haka kuma, ana sa ran za a tattauna batutuwa da s**a shafi shugabanci da tsarin aiki tsakanin jihohi.

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, Sakataren Gwamnatin Ƙasa George Akume, Mai ba da shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu, da Ministan Harkokin ‘Yan Sanda Ibrahim Gaidam na cikin mahalarta zaman, tare da dukkan gwamnonin jihohi da wakilan su. Majalisar ‘Yan Sanda, wacce kundin tsarin mulki ya kafa ƙarƙashin sashe na 153, tana ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa, kuma tana ba da shawara kan tsari, gudanarwa da kula da rundunar ‘yan sanda, har ma da batun nada ko cire Sufeton ‘Yan Sanda na Ƙasa.

Sabon Shugaban Hukumar INEC: Majalisar Ƙoli ta Ƙasa ta Amince da Farfesa Joash AmupitanMajalisar Ƙoli ta Ƙasa ta amince ...
09/10/2025

Sabon Shugaban Hukumar INEC: Majalisar Ƙoli ta Ƙasa ta Amince da Farfesa Joash Amupitan

Majalisar Ƙoli ta Ƙasa ta amince da nadin Farfesa Joash Ojo Amupitan (SAN) daga jihar Kogi, dake yankin Arewacin Tsakiya, a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC).

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne ya gabatar da sunansa domin maye gurbin Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya kammala wa’adinsa a watan Oktoba 2025 bayan shafe shekaru 10 a kujerar shugabancin hukumar. Shugaba Tinubu ya ce Amupitan shi ne ɗan jihar Kogi na farko da aka gabatar don wannan mukami, kuma mutum ne da aka sheda baya tsangwama irin ta siyasa.

Mambobin majalisar sun amince da wannan nadin ba tare da wani sabani ba, inda gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya bayyana shi a matsayin mutum mai gaskiya da riƙon amana. Bayan wannan mataki, za a tura sunansa gaban Majalisar Dattawa domin tantancewa da amincewa, k**ar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Farfesa Amupitan, mai shekaru 58 daga Ayetoro Gbede, karamar hukumar Ijumu a jihar Kogi, malami ne a fannin shari’a a Jami’ar Jos, inda yake rike da mukamin Mataimakin Shugaban Jami’a (Harkokin Gudanarwa). Ya kware a fannoni da s**a haɗa da Company Law, Law of Evidence, Corporate Governance da Privatisation Law. Ya zama Lauya Babban (SAN) a shekarar 2014.

Ya fara karatunsa a Kwara Polytechnic tsakanin 1982 da 1984 kafin ya ci gaba a Jami’ar Jos daga 1984 zuwa 1987. Ya kammala karatun sa na Shari’a a matakin farko a 1988, sannan ya kammala digirin LLM a 1993 da kuma PhD a 2007 a UNIJOS. Har ila yau, ya yi aikin yi wa ƙasa hidima a gidan jaridar jihar Bauchi tsakanin 1988 da 1989.

Baya ga karantarwa, Amupitan ya riƙe manyan muk**ai a harkar gudanarwa da harkokin ilimi, ciki har da Shugaban Kwamitin Shugabannin Sassa da Daraktoci (2012-2014), Dekan na Faculty of Law (2008-2014), da Shugaban Sashen Public Law (2006-2008). A halin yanzu, shi ne Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Joseph Ayo Babalola da ke Osun.

Ya wallafa littattafai da dama a fannin shari’a, ciki har da Corporate Governance: Models and Principles (2008), Documentary Evidence in Nigeria (2008), Evidence Law: Theory and Practice in Nigeria (2013), da Principles of Company Law (2013).

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sabuwar Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sabuwar Nigeria:

Share

Category