
22/08/2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin K**a Dukkan Masu Hannu a Kisan Masu Ibada a Malumfashi
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta bi diddigin masu hannu a mummunan kisan da aka yi wa masu ibada a karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina, tare da tabbatar da cewa an gurfanar da su a gaban shari’a.
A cikin wata sanarwa, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce wannan ta’addancin da aka aikata kan mutanen da s**a taru domin bauta wa Allah ba zai taɓa wucewa babu hukunci ba.
Ya bayyana cewa jami’an tsaro sun soma ƙoƙarin farauto waɗanda s**a aikata wannan mummunan aiki, tare da tabbatar da cewa an kamo su da hukunta su.
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan waɗanda s**a rasu, al’ummar Malumfashi da gwamnatin Katsina, yana addu’ar Allah ya jikansu ya kuma ba iyalan juriyar wannan rashi.
Sanarwar ta kuma bayyana nasarorin da aka samu a yaƙin da ake yi da ta’addanci, inda kwanan nan cibiyar yaki da ta’addanci NCTC ta k**a manyan shugabannin ’yan ta’adda ciki har da Mahmud al-Nigeri, da kuma Mahmud Muhammad Usman (Abu Baraa) na ƙungiyar Ansaru.
Gwamnati ta jaddada cewa duk mai zubar da jinin al’ummabba zai sami mafaka a Najeriya ba, tare da tabbatar da cewa ƙarshen ayyukan ta’addanci a ƙasar ya kusa.