Mizani-360

Mizani-360 This Page Is Tv Channel Page t at Will Bring You News and documentary.

DA DUMI-DUMI: Yan Daba Sun Farfa$a Motocin Tawagar Abubakar Malami, Tsohon Ministan Shari’a A Jihar Kebbi.
01/09/2025

DA DUMI-DUMI: Yan Daba Sun Farfa$a Motocin Tawagar Abubakar Malami, Tsohon Ministan Shari’a A Jihar Kebbi.

DA DUMI DUMIJami’an ‘Yan sanda sun k**a mak**ai masu yawa da ke kan hanya daga Jigawa zuwa Safana, tare da gurneti mai ƙ...
01/09/2025

DA DUMI DUMI

Jami’an ‘Yan sanda sun k**a mak**ai masu yawa da ke kan hanya daga Jigawa zuwa Safana, tare da gurneti mai ƙarfi (GPMG) da alburusai 1,295.

An cafke mutum biyu Abdulsalam Muhammad (25) da Aminu Mamman (23), mazauna Baure, Safana LGA yayin da suke ɗauke da mak**an cikin motar Golf mai launin shuɗi.

Mak**ai da aka samu sun haɗa da:

GPMG guda ɗaya

Alburusai 1,063 na AK-47

Alburusai 232 na PKT
An gano mak**an sun fito daga Hadejia (Jigawa) ana kai su Safana LGA.

Gwamnatin Jihar Katsina ta yaba da ƙoƙarin ‘Yan sanda, tana kuma tabbatar da ƙara tallafawa jami’an tsaro wajen kawar da miyagu.

Dr. Nasir Mu’azu
Kwamishinan Tsaro da Harkokin ciki
Na Jihar Katsina
01 Satumba, 2025

Aurenta Saura 5 month amma shawara take nema 🤐
31/08/2025

Aurenta Saura 5 month amma shawara take nema 🤐

Da Dumi Dumi:: Waɗansu Mutane Da Muggan mak**ai Sun Farwa Tawagar Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasiru El Rufa i da ...
30/08/2025

Da Dumi Dumi:: Waɗansu Mutane Da Muggan mak**ai Sun Farwa Tawagar Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasiru El Rufa i da Sara Da jifa Harda Fasa Motoci A Lokacin Da Suke Gudanar Da Babban Taron Bude Office Din Jam Iyyar ADC Yau A Jihar Kaduna, Waɗanda S**a ga Abinda Ya Faru Sun Tabbatar Mana Dacewa Maharan Sun zo da Ihu da jifa Tareda Ambaton Karyane Karyane, Sai Sara Da Jifa kawai sukeyi, Sun Jikkata Mutane Maza Da Mata Tareda Barnata Motocin Mahalarta Taron, Tuni Jami an Tsaro S**a Kawo Dauki Domin Magance Lamarin"

Izuwa Yanzu Dai Ba A Tabbatar Ko suwaye S**a Turo Waɗan nan Matasa Domin Hargitsa Wannan Taro ba, Abin Farinciki Dai Taron Ya Kammalu Cikin Nasara k**ar yadda Tsohon Gwamnan jihar Kaduna yayi jawabi bayan Taron, Malam Nasiru El Rufa'i yace babu wani Abin Mamaki Don anyi musu Haka, malam yace Kowa yasan su waye S**a sanya Ayi musu wannan aika aikan, amma wannan bazai Sa Jam Iyyar ADC Ta Kasa Samun Nasara ba Insha Allah"

Jarumar Finafìñan Hausà, Farida Abdullahi Kenan, Wadda Mahaifiyarta Ta Rabu Da Mìjìnta Saboda Ta Samu Damar Ba Ta Tarbìý...
29/08/2025

Jarumar Finafìñan Hausà, Farida Abdullahi Kenan, Wadda Mahaifiyarta Ta Rabu Da Mìjìnta Saboda Ta Samu Damar Ba Ta Tarbìýýa

Ji wani abin mamaki akan gawurtaccen dan dabar daya addabi Kaduna wanda ya rigamu gidan gaskiya, Watau Habu dan Damusa.R...
29/08/2025

Ji wani abin mamaki akan gawurtaccen dan dabar daya addabi Kaduna wanda ya rigamu gidan gaskiya, Watau Habu dan Damusa.

Rahotanni sunce, haka mahaifinsa ya rasu a ranar da aka haifeshi, wanda shima a wancan lokacin ya fitini al'umma da ayyukan daba.

Shima kuma gashi ya rasu kwana daya bayan da matarsa ta haihu.

Ku karan ta har Karshe.Sun kashe kasar. Sun sace dukiyar kasar. Sun talauta ku. Sun azurta kansu da yayansu. Sun kashe h...
23/08/2025

Ku karan ta har Karshe.

Sun kashe kasar.
Sun sace dukiyar kasar.
Sun talauta ku.
Sun azurta kansu da yayansu.
Sun kashe harkar ilimi
Sun kashe harkar Lafiya.
Sun kashe harkar Tsaro
Sun haɗa ku faɗa da juna.
Sun barku da Yunwa.
Makarantin ku daban da na yayansu.
Asibititocin ku da ban da nasu.

Idan zasuyi Jinya Kasar waje su ke zuwa sabi da sun kashe harkar da gangan.

Sannan don kai Dakiki ne akan su ne kake tada jijiyar wuya don Wani ya zage su ko ya Zagi iyalansu don kawai ana baka abinda baikai yakawo ba cikin hakkin ka da aka sata.

Mutanen da su damuwar ka ba tasu ba ce muddin bazasu Karu ba to babu ruwan su. Dukiyar nan da kuke ganin suke Wadaka da ita da iyalansu naku ne hakkin ku ne.

Malaman ku na addini da kuke ganin girman su, yanzu suma sun zama nasu, da su ake damawa, shiyasa wa’azin su yakare akan ka, kai Talaka, kai ne zaka shiga Wuta shi kuma Shugaba Aljanna zashi domin ya gina masallaci da kudin sata.

Daga Karshe Talaka ka ta shi ka nemi yancin ka.

A taron FEC na jiya, Shugaba Tinubu ya sake bada approvals din aiki a Lagos na gyaran gadoji guda biyu, Third Mainland B...
14/08/2025

A taron FEC na jiya, Shugaba Tinubu ya sake bada approvals din aiki a Lagos na gyaran gadoji guda biyu, Third Mainland Bridge akan kudi N3.6Trillion, da kuma gyaran gadar Carter ita kuma akan kudi N360Billion, idan ka hada su jimilla ya k**a kusan N4Trillion. Idan ka tara wannan tiriliyoyin akan lissafin N7Trillion da nai a baya na aiyukan da aka kai jihar Lagos, kenan a cikin shekaru biyun gwamnatin Tinubu an tura kudi a kalla N11Trillion. Wato TIRILIYAN GOMA SHA DAYA KENAN!

A sanda nai rubutin farko, an samu yan arewa da suke cikin gwamnatin Tinubu sun min raddi kala kala, cewa Tinubu na aiki a Arewa. Sun lissafo min aiyukan da kusan karashen na gwamnatin Buhari ne, a matsayin aiyukan Tinubu a Arewa, ciki harda titin Kano zuwa Hadejia, wanda ni hanyar gida na ce, kuma na san kiris ne ya rage, a karasa shi lokacin Gwamnati Buhari, amma dan rinto, an hada a cikin jeran aiyukan arewa da Tinubu yayi.

Tambaya ta ga yan Arewa dake cikin gwamnatin Tinubu shine, da karashen aikin Buhari da ake rinto da shi, da kuma aiyukan da ake daure mu da igiyar zato cewa za ayi su nan gaba, shin jimmillar su gaba daya a jihohin Arewa 19, kudin su ya kai N11Trillion? Idan kun ce ya kai, toh dan Allah ku lissafo min su.

Wato dan kana cikin gwamnati ba lasisi bane na ka kyale a cuci al'ummar ka. Idan ka ga ba daidai ba, toh ko ba za ka iya magana ba, ya k**ata ka kauda kai, ka kyale wanda za su iya su yi domin a gyara, wani zubin gwamnati sai da s**a.

Ba na mantawa lokacin Obasanjo, da sahalewar yan Arewan da ke cikin mulki, aka saka hannu a dokar 13% derivation, wanda hakan ta sa har yau, ake kwashe kaso sha uku, na ribar arzikin man kasa, ana bawa jihohin da suke da arzikin mai. Ban ce kar a basu ba, amma kowa ya san duk duniya ba inda ake bada kaso 13% sai a Najeriya.

Idan ba muyi wa tufkar hanci ba tun yanzu, ban san ya zata kasance ba Idan Tinubu ya zarce har tsahon shekara 8 yana mulki. Ba mamaki idan dan Arewa zai je Lagos sai yayi Visa! Ko mu hadu mu taka musu birki, ko su take mu har illa masha Allah!

Salihu Tanko Yakasai
Dawisun Kanawa
August 14, 2025.

SULHU:Zan fara da tunawa mutane Waye Bello Turji da kuma Shekh Musa Assadus Sunnah, ba wai don mutane ba su San su bane,...
08/08/2025

SULHU:

Zan fara da tunawa mutane Waye Bello Turji da kuma Shekh Musa Assadus Sunnah, ba wai don mutane ba su San su bane, a a Sai don mutane suyi adalci wajen fadin ra’ayin su ga abinda zan rubuta.

Bello Turji Kasurgumin dan Ta’adda ne a kasar nan, wanda ayyukan ta’addancin sa s**a addabi kasar nan musamman yankin Arewa Maso Yamma da kuma Arewa ta tsakiya. Turji Yayi Kaurin suna wajen kashe mutane, sace mutane da kuma kisan kare dangi, wanda gwamnatin baya ta Ayyana shi a matsayin dan Ta’adda mai hatsarin gaske. Bello Turji babu ruwan sa da kai Musaulmi ne ko ba Musaulmi ba, Bafulatani kake ko Bahaushe, muddin kashiga Hannun sa to taka ta kare.
A yau babu wanda ya Isa ya lissafa irin mutanen da Turji yakashe ya kuma kwashewa dukiya a kasar nan. Wannan kadan ne daga cikin tarihin Turji wanda kowa yasani.

Asheikh Musa Assasudus sunnah, sannanen Matashin Malami mai ikirarin sunnah, wanda ya shahara wajen bayyana ra’ayinsa ga Gwamnati da sauran mutane a kasar nan, musamman abun da ya shafi al’ummah yana kokari matuka sosai.

Bayan Rasuwar Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ansamu cece kuce sosai, Inda mutane s**a rabu gida biyu, wasu ke cewa bazasu yafe masa ba, wasu kuma ke cewa sun yafe masa, a wannan lokaci ne dai shi Sheikh Musa ya kawo wata Fatawa Inda yake cewa “Allah yana yafewa mutum ko da kuwa ya cuci wani kuma wanin yaki yafewa” to mutane da dama musamman manyan Malamai a kasar nan Sunyi masa raddi kan wannan domin Maganar gaksiya Allah shi ba azzalumi bane, domin duk wanda ya zalunci wani to lallai Sai Allah Yayi musu hisabi muddin wanda aka zaluntan bai yafe ba.

To a nan shi Musa Assadus sunnah yana kokari ya yi amfani da wannan muguwar Fatawar tasa da bata da asali, ya wanke Bello Turji daga manyan laifukan da Yayi wa kasar nan.
A ganina babu yadda za’ayi ace mutum k**ar Turji anyafe masa ko kuma Anyi sulhu da shi, lokacin yin hakan a ganina ya wuce.

Irin su Musa Assadus Sunnah wadanda ke amfani da rigar addini wajen batar da mutane domin ra’ayin kansu, ba karamar barazana ba ce ga addinin musulunci da kuma yankin mu na Arewa.

Tsakanin mu da Turji saidai Allah ya isa kuma bazamu yafe masa ba da duk wanda s**a kawo masa tashin hankali a kasar nan.

Muna da yakinin Gwannati ta kusa gamawa da Turji da mukarrabansa in sha Allah.

Daga Ardo Saddam H. Dogo

Shin Idan Jonathan ya sake tsayawa Zabe, zaku Zabe shi ko kuwa??Ku rubuta mana a comment section. 😆
05/08/2025

Shin Idan Jonathan ya sake tsayawa Zabe, zaku Zabe shi ko kuwa??

Ku rubuta mana a comment section. 😆

Allah ya wulaqanta wannan mutumin…Shine Kachalla Bello (Dan Sadiya)  Wanda yayiwa ‘yan uwanmu kisan Gilla ta hanyar yank...
31/07/2025

Allah ya wulaqanta wannan mutumin…

Shine Kachalla Bello (Dan Sadiya) Wanda yayiwa ‘yan uwanmu kisan Gilla ta hanyar yankan Rago😭 tare da tilasta dan uwa yama dan uwansa yankan Rago a gundumar Banga dake karamar Hukumar Kaura Namoda a jihar Zamfara.

Innanillahi wa’inna ilaihirraji’un 💔😥😭

Address

Zenco Estate Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mizani-360 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share