Shirin "MATA Iyayen GIDA"

Shirin "MATA Iyayen GIDA" Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Shirin "MATA Iyayen GIDA", Digital creator, Niger state television, Abuja.

An tsinci wata jaririya a bakin hanya tare da wani rubuta a takarda.An wayi gari da wannan abin mamaki da ya karaɗe ungu...
19/12/2025

An tsinci wata jaririya a bakin hanya tare da wani rubuta a takarda.

An wayi gari da wannan abin mamaki da ya karaɗe unguwa a Nasarawa, inda aka ga wata kyakkyawar jaririya a yashe gefen hanya da sanyi safiya.

Sai dai Babban abinda ya ba mutane mamaki shi ne, takardar da a ka samu tare da jaririyar. Takardar na dauke da bayani mai matuƙar tausayi sosai. Inda aka rubuta " Ban so rabuwa da ke ba, ban so mu rabu ta wannan sigar ba. Amma babu yacce na iya sai dai hakan ta faru. Na kasance bana iya daukar nauyin kaina saboda talauci, kuma na yi bakin kokarina domin domin neman taimako daga babanki ko dangin shi, amma abin ya gagara. Bani da wani zaɓi wanda ya fi wannan. Ina miki fatan alkhairi kuma Allah ya sa wadanda za su dauke ki su zamanto iyaye nagari a gareki, su kuma baki tarbiyya yacce ake ba kowanne yaro mai cikakken ƴanci.

20/11/2025
ALLAHU AKBAR: An ɗauko gawar Jarumin Kannywood Malam Nata'ala daga babbar Asibitin Maiduguri zuwa garin Potiskum jihar Y...
03/11/2025

ALLAHU AKBAR: An ɗauko gawar Jarumin Kannywood Malam Nata'ala daga babbar Asibitin Maiduguri zuwa garin Potiskum jihar Yobe, domin yi masa jana'iza.

Tawagar hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA), ta isa babban asibitin Maiduguri domin ɗaukar gawar marigayi Malam Nata’ala Potiskum.

Ismail Danmallam Buniyadi, mai taimaka wa Gwamnan Yobe kan yaɗa labarai ne, ya tabbatar da hakan a shafinsa na Facebook ya ce, an ɗauki gawar ne zuwa garin Potiskum domin gudanar da jana’izarsa da misalin ƙarfe 2:30 na rana, a fadar Mai Martaba Sarkin Fika.

Jarumin fina-finan Hausan ya rasu ne a ranar Lahadi bayan fama da jinya a asibitin Maiduguri.

Yanzu haka ana cikin shirye-shiryen kaddamar da bikin bada tallafin jari na ₦50,000 ga mata 5,200 a fadin Jihar Kano kar...
28/10/2025

Yanzu haka ana cikin shirye-shiryen kaddamar da bikin bada tallafin jari na ₦50,000 ga mata 5,200 a fadin Jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba K Yusuf

An samu Wani Mara imani ya yiwa wannan yarinyar yar Shekara 3  fyde Sai da y bata giya tasha ta bugu kafin yazo yayi lal...
22/10/2025

An samu Wani Mara imani ya yiwa wannan yarinyar yar Shekara 3 fyde
Sai da y bata giya tasha ta bugu kafin yazo yayi lalata da ita inda yaji mata

Munanan Raunuka a Farjinta kawo yanzu an k**a Wanda yayi mata wannan Danyen Aikin amma har yanzu Hukuma Ta Kasa yin komai a kasa

Kasa cewar shi Dan wani ne ita kuma wannan yarinyar iyayen ta bama su karfi bane Tabbas An Cutar da Shukura Rashin Gata yana neman hana shukura samun Adalci dan Allah

Jama,a kuyi mana Share Har Allah yasa wannan Sakon Yaje wajan Wadan da Zasu iya Karbawa Shukura Hakkinta a wajan Daman iskan

Tabbas fyde mumunar Dabi,a ce da take Ruguza Rayuwar yaya mata Allah ya kawo mana Karshen wannan iftila,in na fyde

Matan Tsofaffin ‘Yan Sanda Sun Koka: “Ana Neman Mu Da Lalata Kafin A Biya Mu Kudin Fansho”Matan tsofaffin ‘yan sanda a N...
08/10/2025

Matan Tsofaffin ‘Yan Sanda Sun Koka: “Ana Neman Mu Da Lalata Kafin A Biya Mu Kudin Fansho”

Matan tsofaffin ‘yan sanda a Najeriya sun shiga zanga-zanga tare da mazajensu a majalisar dokoki ta ƙasa a ranar talata, suna korafi kan rashin kula da walwalar iyalansu.

Sun bayyana cewa a lokacin da mazajensu ke cikin aikin tsaro, ba a ba su kayan kariya na asali k**ar rigar hana harsashi ba, kuma su ne kan fara fuskantar harbi yayin ayyukan sintiri.

Sun kuma koka cewa wasu daga cikinsu ana cin zarafi da neman su da yin lalata kafin a biya su hakkokinsu na fansho da tallafin mazajensu.

ko kun gane mai jan kayan?
03/10/2025

ko kun gane mai jan kayan?

SANARWA DA GARGADI !Cikin Alhini Dakuma Bakinciki Muke Sanarda Yan Uwa Musulmi Kowane Lokaci Daga Yanzu Hukumar Rima ( S...
23/09/2025

SANARWA DA GARGADI !

Cikin Alhini Dakuma Bakinciki Muke Sanarda Yan Uwa Musulmi Kowane Lokaci Daga Yanzu Hukumar Rima ( Sokoto Rima River Basin Development Authority ) Sun Sanarda Kara Bude Ruwa Daga Goronyo Dam A Yau.

Wannan Karin Za'ayishi Sanadiyar Bakin Ruwa Da Zasu Shigo Dam Daga Dam Din Jibiya Daya Karye Kamar Yadda S**a Fada.

Bisaga Haka Ana Sanarda Yan Uwa Cewa Su Zama Cikin Shiri Haka Wadanda Suke Zaune Kan Tsofaffin Hanyyoyin Ruwa Dasu Kiyaye !

Ubangiji Allah Ya Saukaka Muna Wannan Lamarin

Amin

ALLAH YA KARBI IBADA ZAKI DAN YAYA
12/09/2025

ALLAH YA KARBI IBADA ZAKI DAN YAYA

Hilda Baci ta fara aikin wanke ƙatuwar tukunya da aka ƙera mata don dafa dafadukar shinkafa buhu 80 a yunƙurinta na kafa...
12/09/2025

Hilda Baci ta fara aikin wanke ƙatuwar tukunya da aka ƙera mata don dafa dafadukar shinkafa buhu 80 a yunƙurinta na kafa sabon tarihin girki a Kundin Duniya na World Guinness Record.

Aminiya.

28/08/2025

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ya Jaddada Fifikon Gwamnatinsa Kan Gina Ababen More Rayuwa da Walwalar Ma’aikata

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen gina ababen more rayuwa da inganta walwalar ma’aikata a fannoni masu muhimmanci, ciki har da bangaren shari’a, majalisar dokoki da kuma ma’aikatar gwamnati, domin karfafa inganci da kuma samar da jin daɗin aiki.

Gwamnan ya yi wannan bayani ne lokacin da ya duba aikin gyaran da ake gudanarwa a Kotun Al’ada da kuma Babbar Kotun Yola.

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ta kuduri aniyar samar da ingantattun kayan aiki da muhallin aiki domin bai wa ma’aikata damar gudanar da ayyukansu cikin nagarta da kwarewa.

Gwamna Fintiri ya ce, kasancewar bangaren shari’a daya daga cikin muhimman rassan gwamnati uku, ya sami kulawa ta musamman ta hanyar samar da ofisoshin zamani masu inganci da jin daɗi.

Haka kuma, Gwamnan ya yaba da ingancin aikin da kamfanin da ke gudanar da aikin gyaran kotunan ke yi, inda ya bayyana cewa kayan daki da yanayin wurin sun nuna nagarta da kwarewa. Ya tabbatar da cewa gine-ginen za a kammala su nan gaba kadan sannan a mika su ga bangaren shari’a don fara amfani da su.

Bugu da kari, Gwamna Fintiri ya bayyana cewa ginin Majalisar Dokokin Jihar Adamawa yana cikin cikakken gyara, yayin da Gidan Gwamnati ya samu sabon kyan gani tare da ofisoshi na zamani ga Gwamna da ma’aikata.

Ya ce kuma tsofaffin gine-ginen ma’aikata da hukumomi, wadanda wasu tun daga zamanin Gongola aka gina su, an rusa su domin gina sabbin gine-ginen da s**a dace da bukatun zamani da jin daɗin aiki.

A bangaren walwala kuwa, Gwamna Fintiri ya bayyana cewa ma’aikatan gwamnati tuni s**a fara amfana da karin girma da alawus-alawus na kudi, har ma daga matakin makarantar firamare. Ya bayyana wannan ci gaba a matsayin abin tarihi da bai taba faruwa ba, wanda ma’aikata s**a karɓa da matukar farin ciki.

Address

Niger State Television
Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Shirin "MATA Iyayen GIDA" posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share