10/09/2026
Adadin mutanen da aka ruwaito sun mutu bayan da ake zargin sun sha wasu magungunan gargajiya a Jihar Ondo ya karu zuwa 30, yayin da wasu 50 ke kwance a asibiti. Lamarin ya shafi garuruwan Odigbo da Newtown da Orita da Araromi-Obu.
Gwamnatin jihar ta dakatar da sayarwa da shan barasa da ake sarrafawa a gida da wasu hadadden magungunan gargajiya a yankunan da lamarin ya shafa.