Explorer Hausa

Explorer Hausa 𝐋𝐚𝐛𝐚𝐫𝐚𝐢 | 𝐁𝐢𝐧𝐜𝐢𝐤𝐞 | 𝐒𝐚𝐮𝐲𝐢𝐧 𝐘𝐚𝐧𝐚𝐲𝐢 | 𝐀𝐈 🎤📸

Adadin mutanen da aka ruwaito sun mutu bayan da ake zargin sun sha wasu magungunan gargajiya a Jihar Ondo ya karu zuwa 3...
10/09/2026

Adadin mutanen da aka ruwaito sun mutu bayan da ake zargin sun sha wasu magungunan gargajiya a Jihar Ondo ya karu zuwa 30, yayin da wasu 50 ke kwance a asibiti. Lamarin ya shafi garuruwan Odigbo da Newtown da Orita da Araromi-Obu.

Gwamnatin jihar ta dakatar da sayarwa da shan barasa da ake sarrafawa a gida da wasu hadadden magungunan gargajiya a yankunan da lamarin ya shafa.

10/09/2026

2027: Zan ci gaba da tsarin Tinubu na barin Naira ta samar wa kanta daraja idan aka zaɓe ni – Obi

Ɗan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya ce zai ci gaba da tsarin Shugaba Bola Tinubu a kan Naira na barinta ta samar wa kanta daraja idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban kasa a 2027.

Jam’iyyar APC ta ce tana shirye-shiryen karbar sabbin mambobi sama da 10,000 daga jam’iyyun ADC da PDP da NDC tare da sh...
10/09/2026

Jam’iyyar APC ta ce tana shirye-shiryen karbar sabbin mambobi sama da 10,000 daga jam’iyyun ADC da PDP da NDC tare da shigar da su cikin tsarinta.

Kungiyar Maji Johnson Bello (MJB Movement) ce ke jagorantar shirin sauya shekar, inda ake sa ran gudanar da taron karbar sabbin mambobin bayan kammala tuntuba da shugabannin APC.

Gwamnatin Najeriya ta biya kowacce ’yar wasan tawagar ƙwallon kwando ta mata ta ƙasa, D’Tigress, kuɗin tukuici har dala ...
10/09/2026

Gwamnatin Najeriya ta biya kowacce ’yar wasan tawagar ƙwallon kwando ta mata ta ƙasa, D’Tigress, kuɗin tukuici har dala 100,000, a matsayin cika alkawarin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi musu bayan da s**a lashe gasar FIBA Women’s AfroBasket ta 2025.

Hukumar Wasanni ta Najeriya (NSC) ta bayyana cewa an tura kuɗaɗen zuwa asusun ’yan wasan da jami’an tawagar a ranar 9 ga Satumba 2026. A ƙarƙashin tsarin tukuicin, kowanne jami’in tawagar ya samu kuɗin da ya yi daidai da dala 50,000.

Dan takarar shugaban Najeriya na NDC, Peter Obi, ya ce bai ki amincewa da tayin zama mataimakin dan takarar shugaban kas...
10/09/2026

Dan takarar shugaban Najeriya na NDC, Peter Obi, ya ce bai ki amincewa da tayin zama mataimakin dan takarar shugaban kasa na ADC, Atiku Abubakar, a zaben 2027 ba, domin ba a taba yi masa irin wannan tayin ba.

Obi ya bayyana hakan ne yayin wata hira da Arise TV, lokacin da yake amsa tambayoyi kan yiwuwar jam’iyyun adawa su kulla kawance gabanin zaben.

A 2025, Obi da Atiku da wasu jagororin adawa sun kafa kawance karkashin ADC, amma daga bisani kawancen ya wargaje, inda Obi ya zama dan takarar shugaban kasa na NDC, yayin da Atiku ya zama dan takarar ADC.

Dan takarar shugaban kasa na NDC, Peter Obi, ya ce zai amince da shan kaye a zaben shugaban Najeriya na 2027 muddin aka ...
10/09/2026

Dan takarar shugaban kasa na NDC, Peter Obi, ya ce zai amince da shan kaye a zaben shugaban Najeriya na 2027 muddin aka gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci.

Obi ya bayyana hakan ne a wata hira da Arise TV, inda ya ce zai mutunta zabin ’yan Najeriya idan s**a zabi wani dan takara a matsayin shugaban kasa.

Jam’iyyar NDC ta ce za ta bai wa talakawan ’yan Najeriya damar bayar da gudummawar N1,000 ko N2,000 domin taimakawa waje...
10/09/2026

Jam’iyyar NDC ta ce za ta bai wa talakawan ’yan Najeriya damar bayar da gudummawar N1,000 ko N2,000 domin taimakawa wajen daukar nauyin yakin neman zabenta na 2027.

Jagoran jam’iyyar na kasa, Sanata Seriake Dickson, ya ce NDC na son bullo da tsarin tara kudade daga jama’a kamar yadda ake yi a wasu kasashen duniya, maimakon dogaro da wasu tsirarun masu hannu da shuni.

Tsohon Gwamnan Jihar Delta kuma mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Ifeanyi Okowa, ya ba...
10/09/2026

Tsohon Gwamnan Jihar Delta kuma mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Ifeanyi Okowa, ya bayyana cewa tun kafin gudanar da zaɓen ya san cewa shi da Atiku Abubakar za su fuskanci ƙalubale wajen samun nasara.

Okowa ya bayyana hakan ne yayin da yake magana kan abubuwan da s**a faru a lokacin yaƙin neman zaɓen 2023, inda ya yi nuni da cewa yanayin siyasar ƙasar da kuma wasu abubuwan da s**a dabaibaye jam’iyyar PDP sun sa samun nasara ya kasance mai matuƙar wahala.

Wani jirgin saman rundunar sojin Amurka kirar C-17 zai kai wa rundunar sojin saman Najeriya wasu kayayyaki a karshen wan...
10/09/2026

Wani jirgin saman rundunar sojin Amurka kirar C-17 zai kai wa rundunar sojin saman Najeriya wasu kayayyaki a karshen wannan mako.

Kayayyakin na daga cikin yarjejeniyar sayar da kayan aikin soja tsakanin Amurka da Najeriya.

Amurka ta ce yarjejeniyar za ta kara karfafa hadin gwiwar tsaro tsakanin kasashen biyu.

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA) ta umarci United Nigeria Airlines ta inganta ayyukanta tare da m...
10/09/2026

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA) ta umarci United Nigeria Airlines ta inganta ayyukanta tare da mutunta hakkokin fasinjoji da kuma daina fadada zirga-zirga fiye da karfin jiragen da take da su.

Darakta-Janar na NCAA, Kyaftin Chris Najomo, ne ya bayar da umarnin yayin ganawa da mahukuntan kamfanin a Abuja, yana mai cewa hukumar ba za ta amince da ayyukan da ke jefa fasinjoji cikin wahala ba.

Address

52 ML Wushishi Crescent
Abuja
900108

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Explorer Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share