14/12/2025
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ce taɓarɓarewar rashin tsaro a Najeriya na nuna gazawar shugabanci.
Ya yi kira da a gudanar da bincike mai zurfi cikin gaggawa kan zargin wasu jami’an gwamnati da taimaka wa ’yan ta’adda.
Obi, ya bayyana hakan ne bayan wani bidiyo da aka yaɗa a kafafen sada zumunta, inda wasu da ake zargin ’yan ta’adda ne s**a ce jami’an gwamnati ne ke taimaka musu da mak**ai.
Ya ce wannan zargi abu ne mai matuƙar muhimmanci da bai k**ata a yi watsi da shi ba.