Trust Radio Live

Trust Radio Live TRUST RADIO 92.7 - AMINTACCIYAR MURYARKU!!! ABUJA, NIGERIA
08039999277

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ce taɓarɓarewar rashin tsaro a Najeriya na nuna gazawar ...
14/12/2025

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ce taɓarɓarewar rashin tsaro a Najeriya na nuna gazawar shugabanci.

Ya yi kira da a gudanar da bincike mai zurfi cikin gaggawa kan zargin wasu jami’an gwamnati da taimaka wa ’yan ta’adda.

Obi, ya bayyana hakan ne bayan wani bidiyo da aka yaɗa a kafafen sada zumunta, inda wasu da ake zargin ’yan ta’adda ne s**a ce jami’an gwamnati ne ke taimaka musu da mak**ai.

Ya ce wannan zargi abu ne mai matuƙar muhimmanci da bai k**ata a yi watsi da shi ba.

“Ni ne gwamna na farko da na yi rantsuwa da Alkur'ani kan cewa idan ina da hannu kan kisan al'umma kada Allah Ya ba ni l...
14/12/2025

“Ni ne gwamna na farko da na yi rantsuwa da Alkur'ani kan cewa idan ina da hannu kan kisan al'umma kada Allah Ya ba ni lamuni kan wata takarda.” — Bello Matawalle

Jirgin sama ya kusan yin hatsari, ya yi saukar gaggawa a KanoJaridar Solacebase wadda ta ruwaito labarin ta ce an kwashe...
14/12/2025

Jirgin sama ya kusan yin hatsari, ya yi saukar gaggawa a Kano

Jaridar Solacebase wadda ta ruwaito labarin ta ce an kwashe mutane 14 da ke cikin jirgin ba tare da samun rasa rai ba. Jaridar ta ce jirgin ‘yan kasuwa ne wato private jet da kamfanin flybird ke amfani da shi da ya taso daga Abuja zuwa Kano, inda a yayin saukarsa da misalin karfe 9:30am ya samu wannan matsala a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano.

Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta ce ba ta da niyyar ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC, duk da cewa ...
14/12/2025

Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta ce ba ta da niyyar ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC, duk da cewa ana ta yi mata tayin sauya sheka daga wasu mutane da ke da alaka da fadar shugaban kasa da kuma wasu ’yan majalisa.

Ta bayyana hakan ne a wata hira da ta yi a shirin Mic On Podcast, inda ta ce ko da rikicin da ke addabar PDP ya tsananta, ba za ta bi sahun masu sauya jam’iyya ba, tana mai cewa ba ta yarda da barazana ko rarrashi na siyasa.

Sanatar ta kara da cewa an sha tuntubarta a lokuta daban-daban, har da kwanan nan, amma ta fi son ci-gaba da zama a PDP, tana mai cewa har yanzu tana tattaunawa kan makomarta ta siyasa, ciki har da yiwuwar sake tsayawa takara, amma ba a yanke hukunci ba tukuna.

Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Shaibu ya yaba, ya bayyana cewa buɗe cibiyoyin horas da sabbin kura...
14/12/2025

Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Shaibu ya yaba, ya bayyana cewa buɗe cibiyoyin horas da sabbin kuratan sojoji (Depot) a jihohin Kudu zai ƙara ƙarfin rundunar wajen karɓar sabbin ma’aikata a faɗin ƙasa.

Laftanar-Janar Shaibu ya bayyana cewa za a buɗe sabbin cibiyoyin horas da sabbin kuratan sojojin ne a Osogbo da ke Jihar Osun da kuma Abakaliki a Jihar Ebonyi.

Ya bayyana haka ne a yayin bikin yaye sabbin dakarun soji 3,439 da aka yi a Cibiyar Horas da Sabbin Kuratan sojoji (Depot) da ke Zariya, inda ya shawarce su da su zama masu kishin ƙasa da jajircewa.

John Cena na barin “wrestling” a matsayin gwarzo sau 17 na duniya, wanda shi ne mafi yawa a tarihin wasan. Ya fara kokaw...
14/12/2025

John Cena na barin “wrestling” a matsayin gwarzo sau 17 na duniya, wanda shi ne mafi yawa a tarihin wasan. Ya fara kokawa a 2002, ya shahara da taken “You Can’t See Me”, sannan daga baya ya yi fice a fina-finai. Masana da magoya baya na kallonsa a matsayin daya daga cikin mafi girman ‘yan kokawa da WWE ta taba samu.

HOTUNA: Yadda sojoji s**a daƙile wani harin ’yan Boko Haram a sansanin Soja da ke Mairari a Jihar Borno.
14/12/2025

HOTUNA: Yadda sojoji s**a daƙile wani harin ’yan Boko Haram a sansanin Soja da ke Mairari a Jihar Borno.

Yunƙurin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, na kafa wata rundunar tsaro mai k**a da Hisbah ya jawo ce-ce-ku-ce...
14/12/2025

Yunƙurin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, na kafa wata rundunar tsaro mai k**a da Hisbah ya jawo ce-ce-ku-ce a faɗin jihar.

Wannan shiri da ya kira Hisbah mai zaman kanta, an tsara shi ne domin ɗaukar ma’aikata 12,000 waɗanda gwamnatin Kano mai ci ta sallama daga a Hukumar Hisbah.

Sanarwar ta haifar da ra’ayoyi mabambanta, inda wasu ke goyon baya, wasu kuma na adawa, yayin da wasu ke taka-tsantsan.

Kazalika, mutane da dama na tambayar sahihancin kafa rundunar a bisa doka, manufar shirin da kuma tasirinsa ga tsaro da shugabanci a jihar.

'Yan majalisar dokokin Austria sun haramta wa mata 'yan kasa da shekara 14 sanya hijabi a makarantu, a wani mataki da ak...
14/12/2025

'Yan majalisar dokokin Austria sun haramta wa mata 'yan kasa da shekara 14 sanya hijabi a makarantu, a wani mataki da aka bayyana a matsayin nuna kyama ga Musulunci.

Marasa lafiya masu fama da cututtukan da ba sa yaduwa sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta sakin kudin da aka...
14/12/2025

Marasa lafiya masu fama da cututtukan da ba sa yaduwa sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta sakin kudin da aka ware a kasafin kudi na 2025 a kuma aiwatar da shirye-shiryen don cimma kudurinta na samar da lafiya ga kowa.

Kwamitin Cika Aiki kan samar da kudi don magance cututtukan da ba sa yaduwa, wanda ya kunshi masu fama da hawan jini da kungiyoyin farar hula da kungiyoyin kwararru a harkar kiwon lafiya, ya yi wannan kira yayin wani taron manema labarai albarkacin ranar samar da lafiya ga kowa ta duniya ta 2025.

Wakiliyar masu fama da cututtuka a kwamitin, Misis Ijeoma Joseph, ta ce wajibi ne gwamnati ta aiwatar da kudurinta ta hanyar daukar matakan ceton rayuwar mutanen da ke fama da cututtukan mutu-ka-raba.

A cewarta, cututtukan da ba sa yaduwa k**ar hawan jini da ciwon suga (diabetes) da kansa da cututtukan numfashi suna barazana mafi girma ga albarkar da Allah Ya yi wa Najeriya ta yawan jama’a da bunkasar tattalin arzikinta.

Ta kuma ce akalla kashi daya bisa uku na yan Najeriya da s**a haura shekara 18 ne suke fama da akalla daya daga cikin cututtukan da ba sa yaduwa; amma kasa da kashin 20 cikin 100 ne suke samun kulawa.

Misis Ijeoma ta kara da cewa abin da ake gani a zahiri ya ci karo da burace-buracen da ke rubuce a tsarin fadada kula da lafiya ga kashi 80 cikin 100 daga 2019 zuwa 2025 da kuma rage yawan mutanen da ke mutuwa sanadiyyar cututtukan da kashi 25 cikin 100.

A cewarta, kashi shida cikin 100 kacal ne na kudin da aka kasafta don kiwon lafiya ake kashewa a kan cututtukan da ba sa yaduwa.

Kocin Chelsea Enzo Maresca ya ce tun da ya je kungiyar bai taba ganin sa’o’i 48 masu munin wadanda s**a biyo bayan nasar...
14/12/2025

Kocin Chelsea Enzo Maresca ya ce tun da ya je kungiyar bai taba ganin sa’o’i 48 masu munin wadanda s**a biyo bayan nasarar da ta yi jiya Asabar a kan Everton da ci 2-0 ba, saboda rashin goyon baya.

Wannan nasara dai ta haura da kungiyar ta birnin Landan mataki na hudu teburin Gasar Firimiya ta Ingila ta kuma kawo karshen wasanni hudun da ta yi a jere ba ta lashe ko daya ba.

Sai dai Maresca, wanda ya fara horar da yan wasan kungiyar a kakar 2024/2025 ya kuma taimaka musu lashe gasar Europa da Club World Cup, ya ce ba s**a yake yi a kan magoya bayan Chelsea ba.

Da aka tambaye shi ko da magoya bayan kungiyar yake sai Maresca ya ce yana kaunar magoya bayan kuma yana farin ciki da su.

A wata tattaunawa da aka yi da shi shekaranjiya Juma’a, Maresca ya ce nasara ce kawai za ta hana magoya bayan kungiyar yin korafi a soshiya midiya.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ya ce gwamnatin Tinubu ba za ta taba barin Najeriya ta kife a hannunta ba, koma...
14/12/2025

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ya ce gwamnatin Tinubu ba za ta taba barin Najeriya ta kife a hannunta ba, komai rintsi.

Shettima, wanda ya fadi haka yayin da yake jawabi a waje yaye daliban Cibiyar Nazarin Manufofi da Muhimman Bukatu ta Kasa (NIPSS) da ke Kuru, kusa da Jos, ya kuma ce idan Najeriya ta kasa to daukacin al’ummar Bakar Fata ta duniya ta kasa kuma tasirin abin zai shafi kowa a duniya.

Ya ce na fada wa wasu jami’an diflomasiyya na duniya cewa zai fi kyau wa duniya idan Najeriya ta dore. In har Najeriya ta tarwaatse to ’yan kasar masu ji da kansu miliyan 50 za su taka su tsallaka Turai. Saboda haka zai fi zama alheri ga Bakar Fata da ma duniya gaba daya idan Najeriya ta dore.
Mataimakin Shugaban Kasar ya jaddada cewa abin da ya hada yan Najeriya ya fi wanda ya raba su.

Address

20 P. O. W. Mafemi Crescent, Utako
Abuja
900001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Trust Radio Live posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category