Trust Radio Live

Trust Radio Live TRUST RADIO 92.7 - AMINTACCIYAR MURYARKU!!! ABUJA, NIGERIA
08039999277
(1)

HOTUNA: Yadda gobara ta yi ɓarna a Kasuwar Murtala Muhammad Way da ke Kano.Waɗanda lamarin ya faru a kan idonsu, sun sha...
12/06/2026

HOTUNA: Yadda gobara ta yi ɓarna a Kasuwar Murtala Muhammad Way da ke Kano.

Waɗanda lamarin ya faru a kan idonsu, sun shaida wa Aminiya cewa gobarar ta fara ne tun daga ƙarfe 10:00 na daren ranar Alhamis har zuwa safiyar Juma’a.

📸: Sani Ibrahim P**i

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatinsa na duba yiwuwar kafa jirgin sama mallakin Jihar Kano domin samar da sa...
12/06/2026

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatinsa na duba yiwuwar kafa jirgin sama mallakin Jihar Kano domin samar da sabbin hanyoyin samar da kuɗaɗen shiga.

Freedom Radio ta rawaito cewa gwamnan ya ce idan har shirin ya tabbata, hakan zai inganta sufuri da kuma bunƙasa tattalin arzikin Jihar Kano.

12/06/2026
Sakataren Yaɗa Labaran APC a jihar Gombe, Moses Kyari, ya ce har yanzu tsohon Ministan Sadarwa, Isa Ali Pantami ɗan jam’...
12/06/2026

Sakataren Yaɗa Labaran APC a jihar Gombe, Moses Kyari, ya ce har yanzu tsohon Ministan Sadarwa, Isa Ali Pantami ɗan jam’iyyar APC ne, domin bai miƙa wa jam’iyyar takardar ficewa daga cikinta ba a hukumance.

Duk da shugaban APC na mazaɓar Pantami, Alhaji Bala Galda, ya yi iƙirarin karɓar takardar barin jam’iyyar da Pantamin ya rubuta, Moses ya ce har yanzu a kundin bayanan Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Pantami ɗan APC ne.

Haka kuma ya zargi shugaban jam’iyyar da gaza gabatar da takardar barin jam’iyyar da ya ce Pantamin ya miƙa masa, mai ɗauke da kwanan watsn 19 ga watan Mayu, 2026.

A ƙarasa mana wannan karin maganar
12/06/2026

A ƙarasa mana wannan karin maganar

Wata gobara da ta tashi da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Alhamis zuwa safiyar Juma'a 12 ga watan Yuni, 2026 a hanyar M...
12/06/2026

Wata gobara da ta tashi da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Alhamis zuwa safiyar Juma'a 12 ga watan Yuni, 2026 a hanyar Murtala Muhammad da ke Ƙaramar Hukumar Fagge a Jihar Kano, ta ƙone kamfanoni da shaguna da dama.

A cikin wata sanarwa da Hukumar Kashe Gobara ta Kano ta fitar, ta ce gobarar ta samo asali ne daga tartsatsin wutar lantarki.

Address

20 P. O. W. Mafemi Crescent, Utako
Abuja
900001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Trust Radio Live posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category