Fim Magazine

Fim Magazine The best place for authentic stories about Hausa movies, culture, writing, and music

Tinubu yana gina ginshiƙi mai ƙarfi na makomar Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, A...
27/11/2025

Tinubu yana gina ginshiƙi mai ƙarfi na makomar Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu sun fara samar da ribar dimokiraɗiyya ga ‘yan ƙasa.

Ya faɗi haka ne a safiyar yau yayin tattaunawa da ƙungiyoyin goyon bayan jam’iyya mai mulki, wato APC, a ofishin sa da ke Radio House, Abuja.

Idris ya ce: “Mun cika da dama daga cikin alƙawurran kamfen ɗin mu. An kammala batun lamunin ɗalibai, mun kuma kawo ƙarshen almundahanar tallafin man fetur.

"Jihohin mu suna karɓar ƙarin kuɗi, ‘yancin ƙananan hukumomi ya zama na dindindin, kuma kowane yanki yanzu yana da hukumar cigaban sa.

"Tattalin arziƙin mu ya murmure, ajiyar kuɗin waje na ƙaruwa, hauhawar farashi tana raguwa.

"Mun fara manyan ayyukan raya ƙasa a dukkan sassa na tattalin arziki a shiyyoyin ƙasa guda shida.”

Kan batun sababbin umurnin Shugaba Tinubu game da tsaron ƙasa, Ministan ya jaddada cewa Shugaban Ƙasa ya amince da ɗaukar ƙarin jami’ai a sojoji da ‘yan sanda tare da tallafa wa sababbin rundunonin tsaro da gwamnatocin jihohi s**a kafa, yana mai cewa wannan mataki zai zama babban sauyi a yaƙin da Nijeriya ke yi da rashin tsaro.

Ya ce: “Muna fuskantar gaggawar buƙatar kawar da ta’addanci da ‘yan bindiga, mu dawo da zaman lafiya, mu kuma ba ƙasar nan zaman lafiya ga kowa da kowa, ba tare da la’akari da ƙabila ko harshe ko addinin sa ba, k**ar yadda kundin tsarin mulkin mu ya tanada.”

Ministan ya sake tabbatar da ƙudirin Gwamnatin Tarayya na yin duk mai yiwuwa don tabbatar da tsaron ƙasar nan.

A ɓangaren ƙarfafa matasa, Idris ya tabbatar da cewa Tinubu zai ci gaba da kare muradun matasa, ya ƙara da cewa a wannan gwamnati, matasa da ba a taɓa yi ba sun samu muƙamai na jagorantar ma’aikatu da hukumomi.

Idris ya shawarci ƙungiyoyin da su ci gaba da shiga cikin yaɗa shirye-shiryen gwamnati da faɗaɗa haskaka nasarorin ta da tasirin ta.

Ya jaddada cewa wajibi ne a tsaya tsayin daka cikin haɗin kai, tare da bin muradun asali da s**a kafa s**a APC kuma s**a ɗore.

Shugabannin tawagar, Misis Adenike Abubakar da Dakta Abiola Moshood, a madadin ƙungiyoyin, sun sha alwashin ci gaba da bayar da goyon baya ga Ajandar Sabuwar Fata ta Shugaba Tinubu.

Tinubu ya yi matuƙar jimamin rasuwar babban malami, Sheikh Ɗahiru Usman BauchiShugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana matuƙ...
27/11/2025

Tinubu ya yi matuƙar jimamin rasuwar babban malami, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana matuƙar alhini kan rasuwar babban malamin addinin Musulunci, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi, wanda ya rasu a yau Alhamis yana da shekaru 101.

A cikin wata sanarwa da fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, Tinubu ya ce rasuwar Sheikh Ɗahiru babban rashi ne ba kawai ga iyalai da mabiyan sa ba, har ma ga ƙasar nan gaba ɗaya, yana mai jaddada cewa marigayin ya sadaukar da rayuwar sa wajen shiryar da al’umma zuwa ga tafarkin gaskiya.

Shugaban ya bayyana Sheikh Ɗahiru Bauchi a matsayin jagoran Ɗariƙar Tijjaniyya da ya yi fice wajen wa’azi, karantarwa da kuma yaɗa zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Ya ce: “Sheikh Ɗahiru Bauchi malami ne, uba, kuma muryar da ke kira da hikima da natsuwa. A matsayin fitaccen mai tafsirin Alƙur’ani, ya kasance ginshiƙi wajen ƙarfafa zaman lafiya da tsoron Allah. Mutuwar sa ta bar giɓi mai faɗi a wannan fage.”

Shugaban ya kuma tuna da addu’o’i da goyon bayan da Sheikh Ɗahiru ya ba shi a lokacin yaƙin neman zaɓen 2023.

Shugaban ya miƙa ta’aziyyar sa ga iyalan marigayin, mabiyan sa da dukkan al’ummar Musulmi a cikin ƙasar nan da waje.

Ya roƙe su da su ci gaba da ɗaukaka sunan marigayin ta hanyar bin koyarwar sa ta zaman lafiya, kyautata zamantakewa da ƙarfafa kusanci da Allah.

27/11/2025

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya hana Afrika ta Kudu halartar taron ƙolin ƙasashen G20 na shekara mai zuwa da za

26/11/2025

Wani gungun hafsoshin soji a ƙasar Gini-Bissau sun bayyana cewa sun karɓi “cikakken iko” na ƙasar, kwana guda bayan manyan

Tinubu ya bayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro tare da ba da umurni ga hukumomin tsaro da su ɗauki ƙarin ma’aikataShugaba Bol...
26/11/2025

Tinubu ya bayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro tare da ba da umurni ga hukumomin tsaro da su ɗauki ƙarin ma’aikata
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana dokar ta-ɓaci kan harkokin tsaro a faɗin ƙasar nan, tare da bayar da umurnin ɗaukar ƙarin jami’an tsaro da zummar ƙarfafa yaƙi da ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta.

A cikin wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa da aka fitar ranar Laraba, Tinubu ya ce wannan mataki ya zama dole ne sak**akon yadda sabbin hare-hare ke ci gaba da faruwa a wasu jihohin arewacin ƙasar nan.

Shugaban ya ce rundunar ‘yan sanda za ta ɗauki ƙarin ’yan sanda 20,000, lamarin da zai kara yawan waɗanda za su shiga aiki zuwa 50,000 gaba daya.

Ya ƙara da cewa an ba hukumar ‘yan sanda izinin amfani da sansanonin masu bautar ƙasa (NYSC) a matsayin cibiyoyin horaswa na wucin gadi.

Shugaban ya kuma bayar da umurnin cewa jami’an da aka cire daga aikin tsaron fitattun mutane su sake samun horaswa ta musamman kafin a tura su yankunan da ke fama da matsalar tsaro.

A ɓangaren hukumar DSS kuwa, shugaban ƙasar ya ba da izinin tura duka rundunonin forest guards da aka horar domin fatattakar ’yan ta’adda da ’yan bindiga da ke ɓoye a dazukan kasar, tare da umarnin ɗaukar karin ma’aikata domin ƙara mamaye wuraren da ake zargin masu aikata laifuka na fakewa.

Shugaba Ƙasar ya ce wannan mataki yana nuni da cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani yanayi da zai bata tsaron kasa ba, tare da jadadda cewa “ba za a sake samun wani wurin ɓoyewa ga miyagu ba.”

Shugaban ya jinjina wa jami’an tsaro kan ceto ɗalibai 24 da aka sace a Jihar Kebbi da kuma membobin coci 38 da aka ƙubutar a Jihar Kwara, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙoƙarin ceto sauran waɗanda ake tsare da su a Jihar Neja da wasu sassa na ƙasar nan.

Ya kuma buƙaci hafsoshin soji su ci gaba da nuna jajircewa da bin ka’idojin aiki, yana mai cewa babu wani sassauci da za a yi wajen hukunta masana aikata laifi ko wadanda ba su cika ka’ida ba.

A cikin jawabin nasa, shugaban ya buƙaci Majalisar Dokoki ta ƙasa da ta fara nazarin dokokin da za su bai wa jihohin da suke bukata damar kafa rundunar ’yan sanda ta jiha.

Ya kuma gargaɗi jihohi da su yi taka-tsantsan wajen bude makarantu a yankunan da ba su da isasshen tsaro, tare da shawartar masallatai da majami’u a yankunan da ke da matsalar tsaro da su nemi kariyar jami’an tsaro kafin gudanar da ibada.

Tinubu ya jaddada cewa gwamnati ta kafa Ma’aikatar Kiwon Dabbobi ne domin magance rikicin manoma da makiyaya, yana mai kiran ƙungiyoyin makiyaya da su rungumi tsarin kiwo a ruga maimakon yawo da dabbobi a fili, tare da mika duk wasu mak**ai da ba su da lasisi.

Shugaban ya jajanta wa iyalan waɗanda s**a rasa rayukansu a hare-haren da s**a faru kwanan nan a jihohin Kebbi, Borno, Zamfara, Neja, Yobe da Kwara, tare da tunawa da jami’an soji da s**a rasa rayukansu, ciki har da Janar Musa Uba.

Ya kuma yi kira ga ’yan Nijeriya da su kwantar da hankali, su kasance cikin shiri, tare da ba da haɗin kai wajen bayar da bayanai ga jami’an tsaro.

“Wannan lokaci ne da ya buƙaci mu haɗu guri daya domin kare ƙasa. Kada mu faɗa cikin fargaba. Tare za mu iya, tare za mu ci nasara,” inji shi.

CBN ya bar adadin kashi 27% matsayin kuɗin ruwa ga masu ka karɓar rance a bankunaDaga ASHAFA MURNAI A matsayin sa na bab...
26/11/2025

CBN ya bar adadin kashi 27% matsayin kuɗin ruwa ga masu ka karɓar rance a bankuna
Daga ASHAFA MURNAI

A matsayin sa na babban jigon kula da dukkan bankuna a Nijeriya, kuma jagoran bunƙasa tattalin arzikin ƙasa, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bar adadin kashi 27% a matsayin kuɗin ruwa, daga kuɗaɗen da masu karɓar rance za su amsa daga bankuna.

Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso, shi ne ya bayyana haka, bayan tashi daga Taron Kwamitin Tsare-tsaren Kuɗi (MPC) na Babban Bankin Najeriya (CBN), a ranar Talata, a hedikwatar bankin da ke Abuja.

Da yake ganawa da manema labarai, Cardoso ya ce CBN yana ci gaba da dakatar da ƙarin tsauraran matakai, domin bai wa manufofin baya damar fara aiki yadda ya k**ata.

Cardoso ya bayyana haka a Abuja bayan kammala taron MPC na 303, inda ya ce yawancin membobin kwamiti sun jefa ƙuri’a don ci gaba da tsare-tsaren manufofin kuɗi na yanzu, duk da kiraye-kirayen da masana’antu da ‘yan kasuwa s**a riƙa yi kan a sassauta kuɗin ruwan, domin rage tsadar karɓar ramce a bankuna.

Wannan dai shi ne karo na huɗu a 2025 da aka bar adadin kuɗin ruwa a matakin da yake, bayan saukar ɗigo 50 kacal a watan Satumba, wanda shi ne sauƙin da aka yi bayan tsauraran matakai a 2024.

Wannan taro wanda shi ne na 303 a tarihin kafa CBN, kuma na ƙarshe a shekarar 2025.

Taron ya gindaya wa bankuna cewa tilas kowane banki ya riƙa ajiye kashi 45% na kuɗin sa a CBN, wato 'Cash Reserve Ratio' (CCR). Shi wannan adadin kuɗi ne da bankuna ke ajiyewa a CBN, ba tare da suna ɗiba daga ciki suna bayarwa rance ko sayen hannayen jari da su ba.

Sai kuma geji da ƙarfin biyan basuss**a a cikin gajeren lokaci, wato
'Liquidity Ratio', wanda ya tsaya a kashi 30% ɗin sa.

Cardoso ya ce wannan mataki na nufin “ƙarfafa nasarar da aka samu wajen rage hauhawar farashi.”

CBN ya bayyana cewa hauhawar farashi ya ragu a watanni bakwai a jere, ya sauka zuwa 16.05% a Oktoba daga 34% a bara.

Hauhawar farashin abinci ya koma 13.12%, yayin da na cikin gida ya ragu zuwa 18.69%.

An danganta wannan raguwar da tsauraran matakan kuɗi sak**akon daidaiton kasuwar canjin kuɗi, ƙaruwar masu zuba jari daga waje, da daidaiton farashin main fetur.

Ya sanar da cewa Asusun Ajiyar Kuɗaɗen Waje ya ƙaru zuwa $46.7bn, daga $42.77bn a Satumba.

Cardoso ya danganta hakan da ƙaruwa a fitar da kayayyakin da ba na mai ba, ƙaruwar samar da yawan mai, ƙaruwa a kuɗaɗen shiga a Najeriya, sai kuma dawowar masu saka jari daga waje.

Ya kuma ce yanzu matafiya na iya yin amfani da katin naira a ƙasashen waje ba tare da takurawar da aka sani da ta gabata ba.

Alamomin ci gaban tattalin arziki a cikin ƙasa:

Kwamitin MPC ya lura cewa Najeriya ta samu ci gaban tattalin arziki daga kayayyakin da sarrafawa a cikin gida, wato GDP na kashi 4.23% a watannin Afrilu, Mayu da Yuni, daga kashi 3.13% a farkon shekara.
Haka nan PMI ya tashi zuwa 56.4 a Nuwamba, mafi girma cikin shekaru biya, wanda haka yana nuna ƙarfafa harkokin kasuwanci musamman a ɓangaren da ba na mai ba.

Ya ce zuwa yanzu bankuna na ci gaba ƙoƙarin ƙarfafa jarin su. Har ya ce a yanzu haka bankuna 16 sun kammala, yayin da 27 ke cikin matakin ɗaga jari.

Maƙalewar Kuɗaɗen Tallafin Lamuni:

Cardoso ya bayyana cewa binciken cikin gida ya nuna an kashe Naira tiriliyan10.93 a tallafin da aka bayar a baya, inda har yanzu ba a kai ga ƙarni Naira tiriliyan 4.69 ba tukuna, waɗanda ba a biya ba.

Ya ce an amso yanzu ta dawo da Naira tiriliyan 2, amma ragowar ya na takure bankin wajen ɗaukar sabbin tsare-tsare.

Ya ce tsarin tallafin baya ya kawo tangarɗa da cikas a kasuwa, yana jaddada cewa yanzu CBN zai tallafa wa ci gaban tattalin arziki ta hanyoyi marasa samar da cikas a kasuwa.

Ya ƙara da cewa haɗin kai tsakanin hukumomin kuɗi da na gwamnati ya ƙara ƙarfi, wanda ya ce shi ne ginshiƙin da ya haifar da daidaito da ɗorewar tattalin arziki kan miƙaƙƙar turba.

CBN zai haramta wa 'yan gidoga masu rubuta cek na bogi yin hulɗa da banki tsawon shekara biyarDaga ASHAFA MURNAIBabban B...
26/11/2025

CBN zai haramta wa 'yan gidoga masu rubuta cek na bogi yin hulɗa da banki tsawon shekara biyar
Daga ASHAFA MURNAI

Babban Bankin Nijeriya (CBN) zai fito shirin ƙaƙaba wa masu rubuta cek da sunan biyan kuɗi ga wani, alhali ba su da isassun kuɗi a asusun bankin su hukuncin daina hulɗa da su a bankuna har tsawon shekaru biyar. takunkumin haramta cinikayya na shekaru 5 ga masu rubuta takardun bashi (cek) na bogi

Ana wannan shirye-shiryen fara aiki da doka da ƙa'idojin kan masu rubuta cek na bogi, wanda a Turance ake kira 'dud check', a matsayin babban laifi a tsarin hada-hadar kuɗaɗe a bankuna.

CBN dai na shirin kafa wannan sabuwar doka da za ta hana masu maimaita rubuta cek na gidoga ci gaba da yin mu’amalar banki na tsawon shekara biyar.

A ƙarƙashin wannan ƙudirin doka, za a bayyana mutum a matsayin “mai rubuta cekin kuɗi na bogi sau da yawa”, idan ya rubuta takardun bashi sau uku kuma aka ƙi biyan su, saboda rashin isasshen kuɗi a asusun bankin sa.

CBN ta bayyana wannan a cikin daftarin ƙa’idojin da ta fitar cikin wannan mako, dangane da “Shirin Magance Rubuta Cek Na Bogi”, wanda ke bai wa bankuna da sauran cibiyoyin kuɗi ikon sanya sunayen irin waɗannan mutane a jerin waɗanda banki ya yi nuni cewa ba a ba su amana.

Daga cikin abin da dokar za ta tanadar, an rattaba cewa waɗanda s**a karya doka za a hana su karɓar lamuni, sannan a hana su samun lamuni daga kowanne banki.

Kuma za a hana su buɗe asusun 'current account' na tsawon shekaru biyar.

Bankuna kuma za su ƙwace ragowar littafin cekin kuɗaɗen da ke hannun sa da bai a amfani da su ba. Sannan a shigar da sunan sa da bayanan sa, a matsayin mai laifin da gangaci ne ci gaba da yin hulɗar banki da shi, wato 'Credit Risk Management System' (CRMS).

An tanadi takunkumi ga masu maimaita laifin, ta hanyar tsananta hukunci ga masu sake aikata laifi, inda aka tanadi cewa duk wani abokin ciniki da ya sake rubuta takardar bashi ta bogi, wato cek, bayan kammala hukuncin shekara biyar zai sake fuskantar kara wasu shekara biyar a duk lokacin da ya maimaita laifin.

Amma za a cire sunan sa daga wannan takunkumi idan lokacin hukuncin ya ƙare, ko kuma banki ya tabbatar an yi kuskuren shigar da sunan mutum.

Dole ne bankuna su sabunta bayanan mutum a cibiyoyin bayanan masu rubuta cek na gidoga, tare da sanar da shi a rubuce bayan ya ƙare wa’adin hukuncin.

Ƙudirin ya kuma tanadi hukunci kan bankunan da s**a gaza aiwatar da ƙa’idojin, inda za su fuskanci tarar

Naira biliyan 5 idan ba su aiwatar da takunkumin ba.

Sai tarar Naira miliyan 3 idan s**a buɗe 'current account', ba tare da binciken CRMS ba.

Gwamnatin Tarayya da Sarkin Musulmi sun amince wa Rahma Abdulmajid ta shirya fim kan Nana Asma’u ‘yar Shehu Ɗanfodiyo
26/11/2025

Gwamnatin Tarayya da Sarkin Musulmi sun amince wa Rahma Abdulmajid ta shirya fim kan Nana Asma’u ‘yar Shehu Ɗanfodiyo

Ma’aikatar Sana’a, Masana’antu da Zuba Jari ta Tarayya tare da Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, sun amince wa Hajiya Rahma Abdulmajid ta shirya wani fim kan rayuwa da tsatson fitacciyar malama kuma marubuciyar nan, Gimbiya Nana Asma’u 'yar Mujaddadi Shehu Usmanu Ɗanfod...

25/11/2025

’Yan matan da aka sace daga Government Girls Comprehensive Senior Secondary School (GGCSS) ta Maga, a Ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu a

25/11/2025

Sojoji sun k**a riƙaƙƙen shugaban masu garkuwa da mutane a Taraba
Rundunar Sojin Najeriya ta bayyana cewa dakarun ta na Birged ta 6 na Sojan Najeriya/Sashi na 3, Operation Whirl Stroke (OPWS), sun k**a wani fitaccen shugaban masu garkuwa da mutane a kudancin Jihar Taraba.

Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na wucin-gadi, Birged ta 6, Laftanar Umar Muhammad, ya ce a cikin wata sanarwa da ya fitar da yammacin Litinin cewa a yayin wani samame da aka gudanar a ranar 23 ga Nuwamba, 2025, dakarun s**a cafke wanda ake zargi da jagorar masu garkuwa da mutane yayin da yake ƙoƙarin tserewa daga Ƙaramar Hukumar Wukari.

Duba comment section.

Address

19 Chelsea Chibuzor Street Off NICON Junction Maitama
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fim Magazine posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fim Magazine:

Share