Fim Magazine

Fim Magazine The best place for authentic stories about Hausa movies, culture, writing, and music

15/01/2026

1966: KISAN ALHAJI SA ABUBAKAR TAFAWA-ƁALEWA

15 ga Janairu, 1966

“Waye a nan?” wata murya ta tambaya daga ciki. Amma Manjo Ifeajuna bai amsa ba; sai kawai ya shuri ƙofar da takalmin sa na soja, ya kutsa kai ciki.

“Mun k**a ka, ran ka ya daɗe,” inji Ifeajuna, yana nuna bindigar sa ga Firayim Ministan, wanda ya firgita. “Tashi, ran ka ya daɗe, ba mu da isasshen lokaci.”

Firayim Ministan ya amsa a hankali, ya ce, “To. Ka ba ni dama in saka kaya.”

Ya tashi ya sanya farar babbar riga da farin wando, ya sa takalmi silifas, sannan ya ɗauki carbin sa. Ba tare da wani tsoro ba, fuskar sa cike da k**ala da natsuwa, ya fita daga ɗakin sannan daga gidan a hankali, yayin da Ifeajuna da sojojin sa suna bin shi a sukwane riƙe da bindigogi.

S**a isa inda motocin su suke tsaitsaye a ƙofar gidan.

Da ma Ezedigbo ya riga ya kamo Ministan Kuɗi, Cif Okotie-Eboh, ya jefa shi k**ar buhun gyaɗa a bayan motar sa ta ɗaukar kaya mai nauyin tan uku.

Da aka zo da Firayim Minista, aka taimaka masa ya shiga bayan motar alfarma ta Ifeajuna, wata jar Marsandi. Ifeajuna ya shiga gaba ya raɗa motar, Sa Abubakar yana baya tare da Manjo Okafor.

Aka buga motoci, ayarin ya k**a hanyar inda s**a yi niyyar zuwa.

Bayan sun yi tafiyar kilomita kaɗan a bayan garin Legas, sai Firayim Ministan ya fara mutsu-mutsu, yana jan ayoyi a hankali yayin da yake jujjuya tasbahar sa. Okafor da ke zaune tare da shi a gidan baya ya sanar da Ifeajuna halin da ake ciki, shi kuma nan take ya taka birki ya fito daga motar.

“Lafiya kake kuwa, ran ka ya daɗe?” Ifeajuna ya tambayi Firayim Ministan yayin da ya buɗe ƙofar gefe. “Ko kana son ka sha iska kaɗan ne?”

A ganin Tafawa-Balewa, wannan tambayar ba ta buƙatar amsa kai-tsaye; zaɓin amsawa ko a’a ya rage nasa na ƙashin kan sa. Ba tare da ya amsa tambayar Manjo ɗin ba, sai kawai ya fice daga motar a hankali, ya shiga tafiya cikin duhun daren, yayin da Ifeajuna yake kallon sa cike da fargaba, domin bai san abin da Firayim Ministan yake nufi ba.

Sai tafiyar Sa Abubakar ta sauya daga taku a hankali zuwa sassarfa, daga nan ya ɓalle da gudu, ya ruga cikin duhu.

Ifeajuna bai yi ƙoƙarin bin shi ba. Sai kawai ya yi wuf ya jawo bindigar sa daga cikin mota, ya saita ta, ya auna Firayim Ministan da ke ƙoƙarin tserewa—ana hangen fararen kayan sa raɗau a duhun dare, suna bayyana shi sarai.

Da ma “Juyin juya halin” da Inyamiran s**a so yi ya ci tura, kuma a ganin su Firayim Ministan ya zama wani nauyi maras amfani a gare su. Don haka Manjo ɗin ya buɗe wa mutumin da ke tserewa wuta ba ƙaƙƙautawa, ya rikita duhun daren da ƙarar harbi tamkar ƙarar busassun ganyayyaki masu ƙonewa.

Tafawa-Ɓalewa ya faɗi rica, yayin da Ifeajuna yake kallon duhun a cikin razana, yana tunanin ko ya cimma nasarar nufin sa.

An kashe bawan Allah Mai Muryar Zinari na Afrika!

Nan take Manjo Ifeajuna ya taka zuwa inda gawar Firayim Ministan take kwance, ya juya ta. Da ya tabbatar lallai ya mutu, sai ya ja gawar a ƙasa zuwa jikin wata bishiya ya jingina ta a yanayin zama. Tufafin Sa Abubakar sun jiƙe sharkaf da jini.

Daga nan Ifeajuna da Okafor s**a fitar da gawar Largema daga but ɗin motar, s**a kwantar da ita a gefen gawar Tafawa-Ɓalewa.

Sun dai fahimci lallai juyin mulkin da s**a so yi ya gaza a ɓangaren su, don haka ba abin da ya rage sai gudu. S**a shiga motocin su s**a hau hanyar Abekuta zuwa Shagamu, s**a doshi Inugu a Gabashin Nijeriya, tafiyar kusan kilomita 450 daga nan inda suke. S**a tsere daga Legas.

* Ibrahim Sheme. Fassara da gyara daga rubutun Aniekpeno Ekong (2023)

Gwamnatin Tarayya da ASUU sun ƙulla yarjejeniya ta farko a tarihi domin kawo ƙarshen yawan yajin aiki a jami’o’iGwamnati...
15/01/2026

Gwamnatin Tarayya da ASUU sun ƙulla yarjejeniya ta farko a tarihi domin kawo ƙarshen yawan yajin aiki a jami’o’i
Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) sun ƙulla wata babbar yarjejeniya da nufin inganta jin daɗin malamai, tabbatar da zaman lafiyar aiki da kuma kawo ƙarshen yawan yajin aikin da ya shafe shekaru yana durƙusar da jami’o’in ƙasar nan.

An bayyana yarjejeniyar ta shekarar 2025 tsakanin Gwamnatin Tarayya da ASUU a ranar Laraba a Abuja, inda Ministan Ilimi, Dakta Maruf Tunji Alausa, ya bayyana ta a matsayin wani sabon shafi a tarihin ilimin gaba da sakandare a Nijeriya.

A cewar sa, yarjejeniyar ba rubutun takarda ba ne kawai, illa alamar dawo da amana, girmamawa da ƙwarin gwiwa ga tsarin jami’o’in ƙasar nan bayan shekaru na rashin tabbas da yajin aiki.

Ministan ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa ɗaukar mataki na musamman wajen fuskantar matsalar da ta daɗe tana addabar jami’o’i, tana lalata jadawalin karatu tare da rusa makomar miliyoyin ɗalibai.

“Wannan ne karon farko da Shugaban Ƙasa mai ci ya tsaya tsayin daka wajen fuskantar wannan ƙalubale kai-tsaye, ya ba matsalar kulawar shugabancin da ta dace,” inji Alausa.

Ya ce gwamnatin ta zaɓi tattaunawa maimakon rikici, gyara maimakon jinkiri, da warware matsala maimakon surutu.

Ɗaya daga cikin manyan abubuwan da yarjejeniyar ta ƙunsa shi ne ƙarin albashin malaman jami’a da kashi 40 cikin 100, wanda Hukumar Albashi, Kuɗaɗen Shiga da Albashi ta Ƙasa (NSIWC) ta amince da shi.

Sabon tsarin albashin zai fara aiki daga ranar 1 ga Janairu, 2026.

A ƙarƙashin sabon tsarin, albashin malamai zai haɗa da CONUASS da kuma ingantaccen alawus na kayan aikin koyarwa da bincike (CATA).

An ƙarfafa CATA domin tallafa wa wallafa mujallu, halartar tarurruka, amfani da intanet, rajistar ƙungiyoyin ƙwararru da rubuce-rubucen littattafai, domin ƙara gogayya da rage guduwar ƙwararru zuwa ƙasashen waje.

Ministan Ilimi, Dakta Maruf Tunji Alausa

Haka kuma yarjejeniyar ta sake tsara alawus-alawus guda tara na Earned Academic Allowances, inda aka fayyace su sarai tare da danganta su kai-tsaye da ayyukan da ake yi k**ar kula da ɗaliban digirin digirgir, aikin asibiti, jarrabawa da shugabancin harkokin ilimi.

A wani sabon salo da ba a taɓa gani ba a tsarin jami’o’in Nijeriya, Gwamnatin Tarayya ta amince da wani alawus na musamman ga manyan malaman jami’a, wato Farfesoshi da Ƙananan Farfesoshi (Readers).

A ƙarƙashin wannan tsari, Farfesoshi za su riƙa karɓar naira miliyan 1.74 a shekara (naira 140,000 a wata), yayin da Readers za su karɓi naira 840,000 a shekara (naira 70,000 a wata).

Ministan ya ce an samar da wannan alawus ne domin ƙarfafa bincike, tsara takardu da inganta gudanarwa, ta yadda manyan malamai za su fi mayar da hankali kan koyarwa, renon matasa da ƙirƙire-ƙirƙire.

Ya kuma tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa gwamnatin Shugaba Tinubu za ta aiwatar da yarjejeniyar yadda ya k**ata a ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata, tare da ci gaba da tattaunawa da gyare-gyare a fannin ilimi.

Masu ruwa da tsaki na ganin yarjejeniyar za ta kawo sabon zamani na kwanciyar hankali da inganci a jami’o’i, tare da dawo da daidaito a jadawalin karatu da kuma sabunta fata ga ɗalibai da iyaye.

Ministan ya yaba wa tawagogin tattaunawar ɓangarori biyu, ƙarƙashin jagorancin Alhaji Yayale Ahmed daga ɓangaren Gwamnatin Tarayya da Farfesa Pius Piwuna daga ASUU, tare da tsohon shugabancin ASUU na Farfesa Emmanuel Osodeke, bisa rawar da s**a taka wajen samar da wannan nasara.

A ƙarshe, Alausa ya ce tarihi ba zai tuna wannan rana a matsayin ranar ƙaddamar da yarjejeniya kawai ba, har ma ranar da Nijeriya ta zaɓi tattaunawa, gaskiya da jajircewar shugabanci a matsayin hanyar warware matsalolin da s**a daɗe suna addabar ƙasa.

Da yarjejeniyar ta kammala, al’ummar Nijeriya na fatan cewa zamanin rufe jami’o’i na dogon lokaci zai zama tarihi, yayin da ake sa ran samun kwanciyar hankali, ƙwarewa da gogayya da jami’o’in duniya a fannin ilimi.

Rawar da Babban Bankin Nijeriya ke takawa a tallafin kuɗin nomaDaga Ashafa Murnai BarkiyaNoma a Nijeriya na cike da babb...
13/01/2026

Rawar da Babban Bankin Nijeriya ke takawa a tallafin kuɗin noma

Daga Ashafa Murnai Barkiya

Noma a Nijeriya na cike da babban tasiri da kuma ƙalubale. Manoma na buƙatar irin shuka masu inganci, kayan aiki na zamani, da samun kasuwanni, amma a mafi yawan lokuta babban cikas shi ne kuɗi. Ba tare da kuɗin jari ko mafi kyawun ƙasar noma ba, to ba za a iya samun biyan buƙatar noma yadda ya k**ata ba. A nan ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ke taka muhimmiyar rawa.

Tsawon lokaci, CBN bai tsaya kawai wajen sa ido da kula da bankuna ba, har ma ya na shiga tsakani domin tabbatar da cewa kuɗaɗe sun isa hannun manoma da masu zuba jari a harkar noma. Duk wanda ke da sha’awa a fannin noma ko kasuwancin noma, yana da muhimmanci ya fahimci yadda CBN ke tallafa wa ɓangaren noma, shirye-shiryen da ake da su, da yadda za a iya amfana da su.

CBN ba bankin kasuwanci ba ne, kuma yawanci ba ya bai wa manoma rance kai tsaye. Maimakon haka, yana tsara shirye-shirye, yana samar da kuɗaɗen tallafi ga bankuna da sauran cibiyoyi, sannan yana kafa manufofi da ke sauƙaƙa isar da rance zuwa ɓangaren noma.

Yawancin bankunan kasuwanci a Nijeriya na kallon noma a matsayin harkar da ke da haɗari. Sauyin yanayi, ƙwari, cututtuka da sauyin farashin kasuwa na iya shafar manoma har su fuskanci ƙalubalen iya biyan bashi. Ba tare da tallafin CBN ba, bankuna da dama ba sa son bai wa manoma rance. Amma da tallafin CBN, ana rage haɗari, ana sauƙaƙa riba, kuma kuɗi na shiga fannin noma da yawa.

A taƙaice, rawar CBN a fannin tallafin kuɗin noma ta haɗa da samar da kuɗaɗen shiga tsakani, rage haɗarin bankuna, kafa ƙa’idoji, da kuma ƙarfafa ci gaban muhimman ɓangarorin noma.

Ɗaya daga cikin manyan hanyoyin da CBN ke tallafa wa noma shi ne ta hanyar kuɗaɗen shiga tsakani. Waɗannan kuɗaɗe ne da aka ware domin manoma da ‘yan kasuwar noma. Ana ɗora kuɗin ruwa da ba su kai ksshi tare da riba mai kashi 10 bisa 100, idan aka kwatanta da rancen banki na yau da kullum. Yayin da rancen banki na kasuwanci zai iya kaiwa kashi 20 cikin 100 ko fiye, rancen da CBN ke tallafawa yawanci yana zuwa da kuɗin ruwan da ba a tsauwala ba.

CBN kuma na taimaka wa bankuna wajen rage haɗurran da ke tattare da harkokin noma.

Ta hanyar shirye-shirye irin su 'Nigeria Incentive-Based Risk Sharing System for Agricultural Lending' (NIRSAL), ana kare bankuna daga asara mai yawa idan manoma s**a fuskanci matsaloli na gaske. Wannan yana ƙara wa bankuna ƙwarin gwiwar bai wa manoma rance.

Haka kuma, CBN na kafa manufofi da ke tilasta ko ƙarfafa bankuna su bai wa noma kaso mai ma’ana na rancen da suke bayarwa. Ba tare da irin waɗannan manufofi ba, bankuna za su fi karkata zuwa ɓangarorin da ke da riba cikin sauri k**ar man fetur da kasuwanci.

CBN kuma na zuba kuɗaɗe zuwa amfanin gona da kiwon dabbobi da ke da muhimmanci ga ƙoƙarin wadata ƙasa da abinci. Waɗannan sun haɗa da shinkafa, masara, rogo, kiwon kaji, kifi, da auduga. Ta hanyar fifita waɗannan ɓangarori, CBN na tabbatar da cewa kuɗaɗe sun tafi inda aka fi buƙata.

Shirye-shirye da Tsare-tsaren da Ya Kamata Manoma Su Sani

A tsawon lokaci, CBN ya ƙaddamar da shirye-shirye da dama da ke haɗa kuɗin noma kai tsaye da manoma da masu kasuwancin noma. Fahimtar waɗannan tsare-tsare na taimaka wa masu ruwa da tsaki su samu dama.

Shirin Anchor Borrowers’ Programme (ABP):

An ƙaddamar da wannan shiri a shekarar 2015, kuma yana haɗa ƙananan manoma da manyan masu sayen amfanin gona, da ake kira 'anchors'. Misali, injinan casar shinkafa ko kamfanonin abincin kaji na iya zama anchors. Manoma na samun iri, taki, da tallafin horaswa, yayin da 'anchor' ke tabbatar da sayen amfanin gona bayan girbi. Rancen yana zuwa da kuɗin ruwan da ba a tsauwala wa mai karɓar rancen, kuma biyan bashin yana da alaƙa da amfanin da aka kai.

Tallafin 'Commercial Agriculture Credit Scheme' (CACS):

Wannan tsari ya shafi matsakaita da manyan manoma da kuma kamfanonin noma. Rancen na iya kaiwa biliyoyin naira, kuma yana tafe da biyan kuɗin ruwa ƙanƙane. Ana tallafa wa manyan gonaki, masana’antar sarrafa amfanin gona da sauran harkokin noma.

Tallafin Asusun 'Agricultural Credit Guarantee Scheme Fund' (ACGSF):

Wannan asusu wanda CBN da Gwamnatin Tarayya ke tallafawa, yana bayar da tabbaci ga bankunan da s**a bai wa manoma rance. Idan manomi ya kasa biya saboda dalilai da ba laifin sa ba, asusun zai biya wani kaso na bashin ga banki. Wannan yana rage haɗarin da bankuna ke fuskanta kuma yana ƙarfafa bayar da rance.

NIRSAL (Nigeria Incentive-Based Risk Sharing System for Agricultural Lending):

Ko da yake tana aiki a matsayin hukuma mai zaman kanta, an kafa NIRSAL da ƙarfi tare da tallafin CBN. Tana bayar da inshora, kawar da shakku da taimakon fasaha, tare da taimaka wa bankuna su tsara rancen da ya dace da halin manoma.

Waɗannan shirye-shirye sun zuba biliyoyin naira a harkar noma, amma samun damar amfana da su na buƙatar sani, takardu, da kuma shiga ƙungiyoyin manoma a wasu lokuta.

Abin da Masu Ruwa da Tsaki Ya Kamata Su Lura da Shi:

Akwai muhimman darussa da manoma, ƙungiyoyi, da masu zuba jari a noma ya k**ata su sani.

Na farko, haɗin kai yana da muhimmanci. Yawancin shirye-shiryen CBN sun fi aiki idan manoma suna cikin ƙungiyoyi ko haɗin gwiwa. Bankuna da 'anchors' sun fi son mu’amala da ƙungiyoyi fiye da mutum ɗaya.

Na biyu, rubuta bayanai yana da matuƙar muhimmanci. Manomi da ba shi da tarihin masaniyar girbi, mallakar ƙasa, ko cinikayya zai iya fuskantar ƙalubale wajen samun rance. Amma bayanai masu sauƙi na iya gina amincewa.

Na uku, yawanci rancen na da alaƙa da tak**aiman amfanin gona. Neman rance a wajen ɓangarorin da ba su cikin fifiko na iya zama da wahala. Ya dace manomi ya san amfanin gona da ake fifitawa a jihar sa.

Na huɗu, biyan bashi wajibi ne. Rancen noma ba kyauta ba ne. Rashin biya na raunana tsarin kuma yana hana shirye-shirye na gaba. Manoma masu kishin aiki ya k**ata su ɗauki rancen a matsayin jarin kasuwanci.

A ƙarshe, ya zama dole a riƙa bin sauye-sauyen manufofi. CBN na sabunta tsare-tsaren sa lokaci zuwa lokaci. Bibiyar jami’an noma, ƙungiyoyi, da sanarwar hukuma na taimakawa wajen samun bayanai.

Tasirin Hakan Ga Bunƙasa Abinci:

Ta hanyar rawar da yake takawa, CBN ya taimaka wajen ƙara yawan amfanin gona a wasu muhimman fannoni. Shinkafa na daga cikin misalai. Tun bayan fara Shirin :Anchor Borrowers', noman shinkafa a gida ya ƙaru, kuma an samu ƙarin injinan casar shinkafa. Haka kuma masara da rogo sun samu bunƙasa sosai.

Sai dai har yanzu akwai giɓi. Samun rance a yankunan karkara na iya ɗaukar lokaci. Wasu manoma na kokawa da masu shiga tsakani da jinkiri, yayin da wasu ke fuskantar matsalolin biyan bashi sak**akon sauyin yanayi. Wannan na nuna cewa kuɗi kaɗai ba ya wadatarwa, dole ne a haɗa shi da ababen more rayuwa, aikin jami’an noma, da kasuwanni masu kyau.

Domin Nijeriya ta ciyar da al’ummar ta da rage shigo da abinci daga waje, dole ne kuɗin noma su ci gaba da gudana. CBN za ta ci gaba da zama jigo, amma nasara na buƙatar haɗin gwiwa. Bankuna su bayar da rance cikin gaskiya, manoma su biya bashi, ƙungiyoyi su tsara kan su da kyau, yayin da gwamnatoci su gina hanyoyi, rumbunan ajiya, da tsarin ban ruwa.

Tallafin kuɗin noma ba kuɗi kaɗai ba ne. Ya shafi amincewa, gaskiya, da amfani da albarkatu yadda ya k**ata.

Rawar CBN ita ce ta ci gaba da aiwatar da waɗannan tsare-tsare. Amma manoma da masu zuba jari a noma dole su ɗauki kuɗaɗen a matsayin kayan aikin kasuwanci, ba sadaka ba.

13/01/2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu lokacin da yake isa ɗakin gabatar da babban taron kyautata muhalli na "Abu Dhabi Sustainability Summit" a birnin Abu Dhabi a ƙasar Haɗɗaɗiyar Daular Larabawa (UAE) a yau.

13/01/2026

Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), Mista Ola Olukoyede, ya ƙaryata zargin cewa gurfanar da tsohon Babban

12/01/2026
Tinubu ya sauka Abu Dhabi don halartar taron ADSW 2026Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na ƙasar H...
11/01/2026

Tinubu ya sauka Abu Dhabi don halartar taron ADSW 2026
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a daren yau Lahadi domin halartar taron Abu Dhabi Sustainability Week (ADSW) na 2026, wanda zai fara gobe.

Jirgin Shugaban Ƙasar ya sauka a Sashen Shugaban Ƙasa na Filin Jirgin Sama na Zayed da misalin ƙarfe 11:30 na dare agogon Dubai.

Ministan Harkokin Wajen UAE, Sheikh Shakhboot Nahyan Al Nahyan, tare da Jakaden UAE a Nijeriya, Salem Saeed Al-Shamsi, da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Jakada Yusuf Maitama Tuggar, da kuma jami’an ofishin jakadancin Nijeriya a Abu Dhabi su ne s**a tarbe shi.

Haka kuma, wasu ministoci da s**a haɗa da Ministan Kasafi da Tsare-tsare, Atiku Bagudu; Ministan Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, Dakta Jumoke Oduwole, da Darakta-Janar na Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa (NIA), Jakada Muhammed Muhammed, sun tarbi Shugaban Ƙasar a otal ɗin sa.

Shugaba Tinubu tare da jami'an UAE bayan saukar sa a ƙasar

Kafin isar sa Abu Dhabi, Tinubu ya shafe wani ɓangare na hutun ƙarshen shekara a Turai, inda ya yi muhimman tattaunawa da Shugaban Ruwanda, Paul Kagame, da Shugaban Faransa, Emmanuel Macron.

Taron ADSW 2026, mai taken “The Nexus of Next, All Systems Go”, dandali ne na duniya da ke haɗa shugabanni, masu tsara manufofi, masu zuba jari da ƙwararru domin tattaunawa da ɗaukar matakai kan cigaba mai ɗorewa, yaƙi da sauyin yanayi, sauya tsarin mak**ashi da bunƙasa tattalin arziki da ya haɗa kowa da kowa.

Ziyarar ta ƙara jaddada kyakkyawar alaƙar diflomasiyya da tattalin arziki da ke tsakanin Nijeriya da UAE, tare da nuna matsayar Nijeriya a matsayin ƙasa mai taka rawa a tattaunawar duniya kan cigaba mai ɗorewa.

Manyan Nasarorin Da CBN Ya Samu Cikin 2025Ashafa Murnai Barkiya1. Kare darajar Naira a kasuwar hadahadar musayar kuɗaɗen...
10/01/2026

Manyan Nasarorin Da CBN Ya Samu Cikin 2025

Ashafa Murnai Barkiya

1. Kare darajar Naira a kasuwar hadahadar musayar kuɗaɗen waje.

2. Sa-ido kan bankuna domin tabbatar da suna bin ƙa'idoji da sharuɗɗan da CBN ya gindaya masu.
3. Rangadin wayar da kan jama'a kan illar wulaƙanta Naira.
4. Kawar da wahalhalun hadahadar kuɗaɗe a ƙarshen shekara.
5. Soke lasin bankuna biyu - A*o Savings and Loans Plc da Unions Homes Saving Loans Plc.
6. Bijiro wa cibiyoyin hadahadar POS hanyoyin magance yawan tangarɗar tura kuɗaɗe.
7. Kaddamar da Kwamitin Asusun Bada Bashi ga Manoma (ACGSF)
8. Sabunta wa BDC 82 rajistar iznin sana'ar canjin kuɗaɗen waje.
9. Matsa-lamba kan dokar ƙarfafa yawan jarin bankuna.
10. Ƙara adadin kuɗaɗen da za a iya cira da ATM.
11. Umartar bankuna su mayar wa waɗanda aka zambace ta 'APPs' kuɗaɗen su cikin sa'o'i 48.
12. Ceto tattalin arzikin Nijeriya
13. Dokar bankuna su janye talloli masu ɗauke da salo da sigar yaudarar kwastomomi.
14. Dokar hukunta masu rubuta cakin kuɗi na bogi.
15. Hana tashin farashin kayan abinci.
16. Gindaya sabbin ƙa'idojin amfani da POS.
17. Gargaɗin a yi kaffa-kaffa da 'Zuldar Microfinance Bank' .
18. Ƙaddamar da Shirin Daƙile Tsadar Rayuwa (DGAS).
19. Tallabar tattalin arzikin Nijeriya a lokacin da farashin ɗanye mai ke faɗuwar-'yan-bori.
20. Wanzar da daidaiton farashin kayan abinci daidai da aljihun talaka.

Cika shekaru 2: Ali Nuhu ya hango kyakkyawar makoma ga industirin ƙirƙira cikin 2026
10/01/2026

Cika shekaru 2: Ali Nuhu ya hango kyakkyawar makoma ga industirin ƙirƙira cikin 2026

MANAJAN Daraktan Hukumar Finafinai ta Nijeriya (NFC), Alhaji Ali Nuhu, ya hango cewa masana’antar finafinan Nijeriya za ta samu kyakkyawar makoma a shekarar 2026. Ali, wanda a ranar 12 ga Janairu, 2026 zai cika shekaru biyu da zama shugaban NFC, ya yi hasashen cewa a wannan shekarar za a samu ƙar...

Ranar Marubuta Hausa ta Duniya: Sanarwar Bayan Taro
10/01/2026

Ranar Marubuta Hausa ta Duniya: Sanarwar Bayan Taro

Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya ya gudana cikin nasara a ranar 31/12/2025 a garin Dutse, Jihar Jigawa, inda ya haɗa marubuta, manazarta, malamai, ɗalibai, da wakilan gwamnatoci daga sassa daban-daban na Nijeriya da maƙwabtan ta. Taron ya ƙara jaddada muhimmancin rubutun Hausa a ƙarni na 21...

09/01/2026

Shugaban Amurka Donald Trump ya amince cewa ana kashe Musulmi ma a Nijeriya, amma ya jaddada cewa Kiristoci ne ke

Address

19 Chelsea Chibuzor Street Off NICON Junction Maitama
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fim Magazine posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fim Magazine:

Share