Fim Magazine

Fim Magazine The best place for authentic stories about Hausa movies, culture, writing, and music

Jarumar Kannywood, Jamila Gwarzo, matar Ɗantani Mai Shayi a ‘Daɗin Kowa’, ta rasu
06/09/2026

Jarumar Kannywood, Jamila Gwarzo, matar Ɗantani Mai Shayi a ‘Daɗin Kowa’, ta rasu

CIKIN alhini da jimami ne aka samu labarin rasuwar tsohuwar jarumar Kannywood, Hajiya Jamila Gwarzo, wadda ta shahara musamman da

Farha, ‘yar tsohuwar jaruma Halima Atete, ta cika shekara ɗaya
05/09/2026

Farha, ‘yar tsohuwar jaruma Halima Atete, ta cika shekara ɗaya

TSOHUWAR jarumar Kannywood, Hajiya Halima Yusuf Atete, tare da mijin ta sun gudanar da bikin zagayowar ranar haihuwar 'yar su,

04/09/2026

Rasuwar Sarkin Gumel babban rashi ne ga masarautun gargajiya da Nijeriya – Shettima
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana rasuwar Sarkin Gumel, Mai Martaba Alhaji Dakta Ahmed Muhammad Sani II, a matsayin babban rashi ga Jihar Jigawa da Nijeriya baki ɗaya.

Shettima ya ce marigayin yana daga cikin sarakunan gargajiya da s**a sadaukar da shekaru masu yawa wajen tabbatar da zaman lafiya, bunƙasa ilimi, cigaban al’umma da ƙarfafa haɗin kan 'yan ƙasa.

Mataimakin Shugaban Ƙasan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a Jihar Jigawa, lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayin da Masarautar Gumel, inda ya isar da saƙon ta’aziyyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Gwamnatin Tarayya.

Marigayi Sarkin Gumel na 16 ya rasu a birnin Alƙahira na ƙasar Masar a ranar 3 ga Satumba, 2026, bayan shafe kusan shekaru 46 yana mulkin masarautar. Ya hau karagar mulki ne a ranar 16 ga Disamba, 1980.

Mataimakin Shugaban Ƙasan ya ce za a tuna da marigayi Sarkin ne saboda tsawon mulkin sa, tare da hikima, zaman lafiya da kishin al’ummar da ya nuna wajen gudanar da shugabancin sa.

Ya bayyana shi a matsayin uba, mai haɗa kan jama’a, kuma mai bayar da shawarwari, wanda hikimar sa ta taimaka wajen hidimta wa al’umma da ƙasa tsawon kusan rabin ƙarni.

Shettima ya ce duk da cewa mulkin marigayin ya gudana a lokacin da Nijeriya ta fuskanci sauye-sauyen siyasa da zamantakewa da dama, ya ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, ilimi, karatun addinin Musulunci da zaman tare cikin lumana.

Ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu yana matuƙar girmama marigayin, musamman bisa gudunmawar da ya bayar wajen samar da zaman lafiya da cigaban al’umma.

Shettima ya yi addu’ar Allah ya gafarta wa marigayin kurakuran sa, ya karɓi kyawawan ayyukan sa, ya sanya shi cikin Aljannar Firdausi, tare da ba iyalan sa, Masarautar Gumel da al’ummar Jihar Jigawa haƙurin jure wannan babban rashi.

04/09/2026
Tinubu ya yi alhinin rasuwar Sarkin Gumel, ya jinjina wa shekaru 46 na mulkin saShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayya...
03/09/2026

Tinubu ya yi alhinin rasuwar Sarkin Gumel, ya jinjina wa shekaru 46 na mulkin sa
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhinin sa bisa rasuwar Sarkin Gumel, Mai Martaba Alhaji Dakta Ahmed Muhammad Sani II, CON, wanda ya rasu yau Alhamis, 3 ga Satumba, 2026, a birnin Alƙahira na ƙasar Masar.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabarun Sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar a yau Alhamis, Shugaba Tinubu ya miƙa ta’aziyyar sa ga iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Gumel, gwamnatin da al’ummar Jihar Jigawa, tare da sauran masarautun gargajiya a faɗin Nijeriya.

Shugaban Ƙasar ya bayyana rasuwar Sarkin Gumel a matsayin babban rashi da kuma ƙarshen wani muhimmin babi na tarihi, yana mai tuna cewa marigayin ya hau gadon sarautar Gumel a ranar 16 ga Disamba, 1980.

Marigayin ya shafe kusan shekaru 46 a kan karagar mulki a matsayin Sarkin Gumel na 16, lamarin da ya sanya shi cikin sarakunan gargajiya da s**a fi daɗewa kan karagar mulki kuma s**a samu girmamawa a Nijeriya.

Shugaba Tinubu ya bayyana marigayin a matsayin ƙwararren malami, gogaggen ma’aikacin gwamnati kuma ɗan kishin ƙasa, yana mai cewa gudunmawar da ya bayar ga cigaban al’umma ta zarce iyakokin masarautar sa.

Kafin hawan sa karagar sarautar Gumel, Alhaji Ahmed Muhammad Sani II ya yi aiki a hukumar Native Authority ta Gumel da Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya, sannan ya kasance babban jami’i a Ofishin Gundumar Kazaure.

Tsakanin shekarun 1978 zuwa 1980, marigayin ya riƙe muƙamin Kwamishinan Yaɗa Labarai, Harkokin Cikin Gida da Al’adu na tsohuwar Jihar Kano.

A lokacin da yake riƙe da wannan muƙami ne aka kafa jaridar Triumph, da tashar talbijin ta CTV 67, wadda daga baya ta zama ARTV, tare da faɗaɗa ayyukan gidan Rediyon Kano.

Waɗannan kafafen yaɗa labarai, a cewar sanarwar, sun kasance daga cikin muhimman cibiyoyin yaɗa bayanai a Arewacin Nijeriya.

Shugaba Tinubu ya ce bayan hawan sa karagar sarautar Gumel, Alhaji Ahmed Muhammad Sani II ya jagoranci masarautar cikin hikima, tare da mayar da ita abin koyi wajen samar da zaman lafiya da cigaba.

Ya bayyana marigayin a matsayin uba ga kowa, mai hikima kuma mai kishin al’adu, wanda ya sadaukar da tsawon rayuwar sa da mulkin sa wajen bunƙasa ilimi, ƙarfafa karatun addinin Musulunci, inganta haɗin kan al’umma da kuma kare kyawawan al’adun Masarautar Gumel.

Shugaban Ƙasar ya kuma ce salon jagorancin marigayin mai natsuwa, taka-tsantsan da haɗa kan jama’a ya taimaka matuƙa wajen tabbatar da kwanciyar hankali a Jihar Jigawa, musamman a lokutan sauye-sauyen siyasa da ƙalubalen tsaro.

A cewar sa, Sarkin Gumel ya kasance abokin hulɗa nagari ga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da zaman lafiya da cigaban al’umma, tare da fifita jin daɗin jama’ar sa.

Shugaba Tinubu ya ce Nijeriya ta yi babban rashi na wani fitaccen shugaban gargajiya, wanda za a yi kewar shawarwarin sa masu hikima da kuma gudunmawar da yake bayarwa wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa.

Ya ce rasuwar Sarkin Gumel babban giɓi ne, musamman a wannan lokaci da Nijeriya ke ci gaba da dogaro da tasiri da gudunmawar sarakunan gargajiya wajen tabbatar da haɗin kai, zaman lafiya da cigaban ƙasa.

Shugaban Ƙasar ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki ya gafarta wa marigayin kurakuran sa, ya karɓi kyawawan ayyukan sa tare da ba shi Aljannar Firdausi.

Haka kuma, ya roƙi Allah ya bai wa iyalan marigayin, Masarautar Gumel da ɗaukacin al’ummar Jihar Jigawa ƙarfin jure wannan babban rashi.

Sha’iri Aminu Ala ya gudanar da taron Mauludi a Kano
02/09/2026

Sha’iri Aminu Ala ya gudanar da taron Mauludi a Kano

FITACCEN mawaƙi kuma Sarkin Adabin Ƙasar Hausa, Alhaji Aminu Ladan Abubakar (Ala), ya gudanar da taron Mauludin da ya saba

Address

19 Chelsea Chibuzor Street Off NICON Junction Maitama
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fim Magazine posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fim Magazine:

Shortcuts

Share