03/09/2026
Tinubu ya yi alhinin rasuwar Sarkin Gumel, ya jinjina wa shekaru 46 na mulkin sa
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhinin sa bisa rasuwar Sarkin Gumel, Mai Martaba Alhaji Dakta Ahmed Muhammad Sani II, CON, wanda ya rasu yau Alhamis, 3 ga Satumba, 2026, a birnin Alƙahira na ƙasar Masar.
A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabarun Sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar a yau Alhamis, Shugaba Tinubu ya miƙa ta’aziyyar sa ga iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Gumel, gwamnatin da al’ummar Jihar Jigawa, tare da sauran masarautun gargajiya a faɗin Nijeriya.
Shugaban Ƙasar ya bayyana rasuwar Sarkin Gumel a matsayin babban rashi da kuma ƙarshen wani muhimmin babi na tarihi, yana mai tuna cewa marigayin ya hau gadon sarautar Gumel a ranar 16 ga Disamba, 1980.
Marigayin ya shafe kusan shekaru 46 a kan karagar mulki a matsayin Sarkin Gumel na 16, lamarin da ya sanya shi cikin sarakunan gargajiya da s**a fi daɗewa kan karagar mulki kuma s**a samu girmamawa a Nijeriya.
Shugaba Tinubu ya bayyana marigayin a matsayin ƙwararren malami, gogaggen ma’aikacin gwamnati kuma ɗan kishin ƙasa, yana mai cewa gudunmawar da ya bayar ga cigaban al’umma ta zarce iyakokin masarautar sa.
Kafin hawan sa karagar sarautar Gumel, Alhaji Ahmed Muhammad Sani II ya yi aiki a hukumar Native Authority ta Gumel da Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya, sannan ya kasance babban jami’i a Ofishin Gundumar Kazaure.
Tsakanin shekarun 1978 zuwa 1980, marigayin ya riƙe muƙamin Kwamishinan Yaɗa Labarai, Harkokin Cikin Gida da Al’adu na tsohuwar Jihar Kano.
A lokacin da yake riƙe da wannan muƙami ne aka kafa jaridar Triumph, da tashar talbijin ta CTV 67, wadda daga baya ta zama ARTV, tare da faɗaɗa ayyukan gidan Rediyon Kano.
Waɗannan kafafen yaɗa labarai, a cewar sanarwar, sun kasance daga cikin muhimman cibiyoyin yaɗa bayanai a Arewacin Nijeriya.
Shugaba Tinubu ya ce bayan hawan sa karagar sarautar Gumel, Alhaji Ahmed Muhammad Sani II ya jagoranci masarautar cikin hikima, tare da mayar da ita abin koyi wajen samar da zaman lafiya da cigaba.
Ya bayyana marigayin a matsayin uba ga kowa, mai hikima kuma mai kishin al’adu, wanda ya sadaukar da tsawon rayuwar sa da mulkin sa wajen bunƙasa ilimi, ƙarfafa karatun addinin Musulunci, inganta haɗin kan al’umma da kuma kare kyawawan al’adun Masarautar Gumel.
Shugaban Ƙasar ya kuma ce salon jagorancin marigayin mai natsuwa, taka-tsantsan da haɗa kan jama’a ya taimaka matuƙa wajen tabbatar da kwanciyar hankali a Jihar Jigawa, musamman a lokutan sauye-sauyen siyasa da ƙalubalen tsaro.
A cewar sa, Sarkin Gumel ya kasance abokin hulɗa nagari ga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da zaman lafiya da cigaban al’umma, tare da fifita jin daɗin jama’ar sa.
Shugaba Tinubu ya ce Nijeriya ta yi babban rashi na wani fitaccen shugaban gargajiya, wanda za a yi kewar shawarwarin sa masu hikima da kuma gudunmawar da yake bayarwa wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa.
Ya ce rasuwar Sarkin Gumel babban giɓi ne, musamman a wannan lokaci da Nijeriya ke ci gaba da dogaro da tasiri da gudunmawar sarakunan gargajiya wajen tabbatar da haɗin kai, zaman lafiya da cigaban ƙasa.
Shugaban Ƙasar ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki ya gafarta wa marigayin kurakuran sa, ya karɓi kyawawan ayyukan sa tare da ba shi Aljannar Firdausi.
Haka kuma, ya roƙi Allah ya bai wa iyalan marigayin, Masarautar Gumel da ɗaukacin al’ummar Jihar Jigawa ƙarfin jure wannan babban rashi.