Fim Magazine

Fim Magazine The best place for authentic stories about Hausa movies, culture, writing, and music

Tattaunawa da fitacciyar marubuciya, Jamila Abdullahi Rijiyar Lemo
17/10/2025

Tattaunawa da fitacciyar marubuciya, Jamila Abdullahi Rijiyar Lemo

HAJIIYA Jamila Abdullahi Rijiyar Lemo tana ɗaya daga cikin manyan marubuta mata waɗanda s**a daɗe suna bayar da gudunmawa a fagen rubutun littattafan Hausa. Ta rubuta littattafan hikaya, waƙoƙi da dirama da dama. Ta samu kyaututtukan karramawa a harkar rubutu a lokuta daban-daban, ciki har da g...

Sauye-sauyen Da Tinubu Ya Kawo Suna Haifar da Gagarumin Cigaba Ga Jama’a — MinistaMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai,...
16/10/2025

Sauye-sauyen Da Tinubu Ya Kawo Suna Haifar da Gagarumin Cigaba Ga Jama’a — Minista
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa tsarin sauye-sauyen da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu yake aiwatarwa yana haifar da sakamako mai kyau, wanda ke bai wa gwamnatocin jihohi damar gudanar da ayyuka masu amfani kai-tsaye ga jama’a.

Idris ya bayyana hakan ne a Maiduguri, Jihar Borno, a ranar Laraba, yayin da ya jagoranci kwamishinonin yaɗa labarai daga jihohin da jam’iyyar APC ke mulki a wani zagayen duba muhimman ayyukan Gwamnatin Tarayya da na jihohi, wanda wani sashe ne na taron musamman wata hurhuɗu da suke yi a jihohi.

Ministan ya ce sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ta aiwatar sun ƙara yawan kuɗaɗen da ake tura wa jihohi, wanda ya ba su damar aiwatar da manyan ayyuka masu tasiri ga rayuwar talakawa.

Ya ce: “Ina tabbatar muku da cewa ajandar sauye-sauyen Shugaban Ƙasa na aiki yadda ya kamata. Yana ƙara wa jihohi kuɗaɗe domin su yi amfani da su wajen yi wa jama’a aiki.”

Tawagar ta ziyarci sabuwar cibiyar bada lantarki ta hasken rana mai ƙarfin 12MW a Jami’ar Maiduguri, wadda Hukumar Samar Da Wutar Lantarki a Karkara (REA) tare da goyon bayan Bankin Duniya ta gina.

Shugaban Jami’ar, Farfesa Mohammed Mele, ya bayyana cewa wannan cibiya tana wadatar da jami’ar da asibitin koyarwa da wutar lantarki, tare da rage musu kashe kuɗin wuta da kusan naira miliyan 170 a duk wata.

Haka kuma, tawagar ta duba tashar samar da wuta ta gaggawa ta Maiduguri mai ƙarfin 50MW, wadda gwamnatin Buhari ta ƙaddamar, kuma gwamnatin Tinubu ta ƙara inganta ta, tana samar da wuta ko da yaushe ga gidaje da masana’antu a cikin birnin da kewaye.

Yayin da yake jaddada nasarorin da Gwamnatin Jihar Borno ta samu, Idris ya yaba wa Gwamna Babagana Umara Zulum bisa gina manyan makarantun zamani guda 104 da ya yi a dukkan mazaɓun sanata uku na jihar cikin shekara guda, yayin da aka kusa kammala guda 35.

Yayin da s**a kai ziyara a ɗaya daga cikin makarantun da aka sanya wa sunan Shugaban Ƙasa Tinubu, Idris ya ce wannan shiri yana nuna yadda gyare-gyaren da Gwamnatin Tarayya take aiwatarwa suke ba jihohi damar zuba jari a fannin ilimi da makomar yaran Nijeriya.

Sauran ayyukan da aka ziyarta sun haɗa da gadar sama ta Borno Express Terminus, wadda za ta zama gada ta huɗu da gwamnatin jihar ta gina, inda aikin ya fara tun a farkon wannan shekara.

Idris ya ce wannan nasara alama ce ta haɗin gwiwa mai kyau tsakanin Gwamnatin Tarayya da na jihohi.

“Wannan shi ne abin da haɗin kai tsakanin Gwamnatin Tarayya da na jihohi zai iya haifarwa,” inji shi.

Tawagar ta kuma ziyarci tashar cajin motocin lantarki ta Herwa EV Station — ɗaya daga cikin tashoshi bakwai da gwamnatin Jihar Borno ta kafa tare da goyon bayan Hukumar Cigaban Arewa Maso Gabas (NEDC).

Idris ya ce wannan shiri ya yi daidai da manufar Gwamnatin Tarayya ta ƙaura zuwa tsaftataccen makamashi da sababbin hanyoyin samar da wuta.

A ƙarshe, aikin gina sabon sashen ƙasa da ƙasa na Babban Filin Jirgin Sama na Muhammadu Buhari, Maiduguri, yana ci gaba da tafiya.

Shugaba Tinubu ya amince da haɓaka filin zuwa na ƙasa da ƙasa a watan Maris 2025, wanda hakan ya sanya shi zama shi kaɗai irin sa a yankin Arewa-maso-gabas.

Borno Ta Fi Kowace Jiha Juriya a Nijeriya – MinistaMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayy...
16/10/2025

Borno Ta Fi Kowace Jiha Juriya a Nijeriya – Minista
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana Borno a matsayin jihar da ta fi kowace jiha juriya a Nijeriya, domin mutanen ta sun ƙware wajen shawo kan duk wani ƙalubale.

Idris ya bayyana hakan ne a Maiduguri a ranar Laraba, yayin da ya kai ziyarar ban-girma ga Mataimakin Gwamnan Jihar Borno, Alhaji Umar Isa Kadafur, a cikin jerin ayyukan da ke gudana a Taron Kwamishinonin Yaɗa Labarai na APC.

Ya ce: “Jihar Borno ita ce jihar da ta fi kowace jiha juriya a Nijeriya, idan aka yi la’akari da ƙalubalen da ta fuskanta a cikin shekaru goma da s**a gabata.”

Ministan ya ƙara da cewa ya kamata duk ‘yan Nijeriya su yaba wa mutanen Borno bisa jajircewar su da kuma yadda suke farfaɗowa duk lokacin da s**a shiga mawuyacin hali.

“Mutanen Jihar Borno suna nuna ƙarfin hali da juriyar da ‘yan Nijeriya ke da shi gabaɗaya, kuma ya dace sauran ‘yan ƙasa su yaba musu ba kawai da kalmomi ba, har ma da alfahari da yadda suke iya shawo kan ƙalubale,” inji shi.

13/10/2025

Hukumar Gudanarwa ta gidan talbijin na Hijrah ta tabbatar da naɗin Ghali El-Abdallah DZ a matsayin sabon Manajan Darakta na tashar. Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da hukumar gidan talbijin ɗin ta raba wa manema labarai, inda ta ce sun yi naɗin ne saboda irin gwagwarmayar da Ghali ya yi a ...

Abin da ya sa na fi shaƙuwa da marigayiya Hauwa Lawan Maiturare a duk aminai na - Bilkisu Yusuf Ali
13/10/2025

Abin da ya sa na fi shaƙuwa da marigayiya Hauwa Lawan Maiturare a duk aminai na - Bilkisu Yusuf Ali

Dakta Bilkisu Yusuf Ali aminiya ce ta kurkusa ga marigayiya Hauwa Lawan Maiturare, wadda Allah ya yi wa rasuwa a ranar 1 ga Oktoba, 2025. Tun da aka yi rasuwar, mujallar Fim ta so jin ta bakin ta a game da wannan babban rashi da irin alaƙar marubutan biyu, amma yanayin da ta samu kan...

Iyalan Bilyaminu Ahmed Bello, wanda matar sa Maryam Sanda ta yi wa kisan gilla a cikin 2017, sun ce ba su aminta da yafe...
13/10/2025

Iyalan Bilyaminu Ahmed Bello, wanda matar sa Maryam Sanda ta yi wa kisan gilla a cikin 2017, sun ce ba su aminta da yafewar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa Maryam ɗin ba.

  Iyalan Bilyaminu Ahmed Bello, wanda matar sa Maryam Sanda ta yi wa kisan gillar a cikin 2017, sun ce

Minista Ya Taya Ɗanlami Nmodu Murnar Zama Shugaban Ƙungiyar Mawallafan OnlayinMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alh...
13/10/2025

Minista Ya Taya Ɗanlami Nmodu Murnar Zama Shugaban Ƙungiyar Mawallafan Onlayin
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya taya Alhaji Ɗanlami Nmodu murna kan zaɓen sa a matsayin Shugaban Ƙungiyar Mawallafan Jaridun Yanar Gizo (GOCOP) a zaɓen da aka gudanar a Legas.

Idris ya ce: “Malam Nmodu, mawallafin Newsdiary Online, wanda nake da alaƙa ta abota da ta aiki da shi tsawon shekaru da dama, ɗan jarida ne nagari wanda ya tabbatar da cancantar sa a aikin jarida, kuma ya dace da wannan matsayi mai daraja.”

Ministan ya kuma yaba wa tsohuwar Shugabar GOCOP, Hajiya Maureen Chigbo, mawallafiyar RealNews Online, kan jagorancin ta na mawallafan onlayin su sama da ɗari da kuma barin “gado mai cike da daraja, ƙima, gaskiya, da cigaba mai ban-sha'awa ga ƙungiyar.”

Idris ya yi kira ga sabon Shugaban na GOCOP da abokan aikin sa na gudanarwa da su bai wa haɗin kan ƙungiyar muhimmanci, inda ya jaddada muhimmancin ƙulla kyakkyawar dangantaka a ƙungiya wadda za ta dauwama tsawon lokaci.

Ya ce: “Yayin da nake taya Nmodu murna, yana da kyau in yi kira a gare shi da ya jagoranci ƙungiyar ta hanyar haɗa kai, wanda ke tabbatar da cewa dukkan membobin GOCOP sun haɗa hannu da hannu wajen ci gaba da cimma burin ƙungiyar."

Haka kuma, ya jaddada muhimmancin lura da “mummunan tasirin labaran ƙarya, bayanan da ba daidai ba da kuma labaran ɓarna da ke barazana ga sahihancin aikin jarida.”

Saboda haka, Idris ya yi kira ga sabon shugabannin GOCOP da su yi aiki kafaɗa da kafaɗa da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, wadda ke jagorantar wayar da kan jama’a kan ilimin kafofin yaɗa labarai a faɗin ƙasar nan.

“Na yarda da Malam Nmodu, wanda ya gina sana’ar aikin jarida bisa gaskiya, jajircewa, ƙarfin hali, da juriyar aiki, ya kuma kawo wannan irin ƙwarewa wajen haɗin gwiwa da gwamnati domin tabbatar da aminci da ilimin kafofin watsa labarai, musamman a cikin harkar kafofin watsa labarai na gidan gizo,” inji shi.

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaryata Zargin Ana Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci Da Wani Sanatan Amurka Ya YiGwamnatin Tarayya ta s...
08/10/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaryata Zargin Ana Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci Da Wani Sanatan Amurka Ya Yi
Gwamnatin Tarayya ta sake ƙaryata zargin da wani Sanatan ƙasar Amurka wai shi Ted Cruz ya yi cewa wai ana yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Nijeriya.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya ƙaryata zargin a cikin wata hira ta musamman da Fox News Digital da ke Amurka ta wallafa a ranar Talata.

Ministan ya ce: “Gwamnatin Nijeriya ta ƙi amincewa da wannan zargi. Wannan ba gaskiya ba ne kwata-kwata.”

Yayin da yake mayar da martani kan alƙaluman da Sanata Cruz ya bayar, Idris ya ce: “Ba gaskiya ba ne. Wannan ba shi ne abin da ke faruwa ba. Ina nufin ba gaskiya ba ne a ce an ƙone fiye da coci 20,000. Kuma ƙarya ce a ce an kashe Kiristoci 52,000. Daga ina ya samo waɗannan alƙaluma? Ba shi da wata hujja ko shaidar da ya dogara da ita. Gwamnatin Nijeriya ta ƙi amincewa da wannan zargi.”

Ya kuma jaddada cewa babu wani jami’in gwamnati ko wata hukuma a Nijeriya da ke mara wa ‘yan ta’adda baya ko yin aiki tare da su don kai hari ga mabiya wani addini.

A cewar sa: “Babu wani jami’in gwamnati a Nijeriya da zai goyi bayan masu tayar da ƙayar baya don su kai hari ga mabiyan wani addini. Wannan zargi ƙarya ne ɗari bisa ɗari.”

Ministan ya sake tabbatar da cewa Nijeriya ƙasa ce mai yawan addinai da kuma zaman lafiya da juna, inda ya ce: “Nijeriya ƙasa ce da ke da mabiya addinai daban-daban. Muna da Kiristoci, muna da Musulmai, har da waɗanda ba sa bin waɗannan addinai biyu. Nijeriya ƙasa ce mai yarda da bambancin addinai. Gwamnatin Nijeriya ta ƙudiri aniyar tabbatar da cewa ana da ‘yancin yin addini a ƙasar nan.”

Ya ƙara da cewa matsalar ta’addanci ta shafi kowa, ba tare da la’akari da addini ba. Ya ce: “Abin baƙin ciki ne cewa waɗannan ‘yan ta’adda suna kashe Kiristoci da Musulmai a wurare daban-daban da suke samun goyon baya. Don haka, ba gaskiya ba ne. Gaba ɗaya ƙarya ce a ce wai ana da wani shiri ko ƙudiri na gangan don hallaka wata ƙungiyar addini; wannan ba daidai ba ne, abin takaici ne ƙwarai.”

Idris ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya tana da cikakken ƙudirin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa, inda ya jaddada cewa hukumomin tsaro na ƙasar nan ba su yi ƙasa a gwiwa ba a yaƙi da ta’addanci da fashi da makami a kowane salo.

Gwamnatin Kano ta horas da ‘yan Kannywood 100, ta ba su kayan aiki
07/10/2025

Gwamnatin Kano ta horas da ‘yan Kannywood 100, ta ba su kayan aiki

Gwamnatin Jihar Kano ta ɗauki nauyin horas da 'yan fim 100 a Makarantar Koyon Harkar fim ta Kano (Kano Film Institute) tare da ba su tallafin kayan aiki domin su je su gudanar da aikin su a kan abubuwan da s**a koya. A wani taron bayar da kayan tallafi ga matasa da aka gudanar a...

Masha Allah.
06/10/2025

Masha Allah.

Addu'ar uku: Marubuta sun yi dandazo wajen ta'aziyyar Hauwa Lawan Maiturare* Mutuwar Hauwa ta girgiza mu sosai, inji Sad...
05/10/2025

Addu'ar uku: Marubuta sun yi dandazo wajen ta'aziyyar Hauwa Lawan Maiturare

* Mutuwar Hauwa ta girgiza mu sosai, inji Sadiya Garba Yakasai

ƊIMBIN marubutan Hausa sun taru a gidan su marigayiya Hauwa Lawan Maiturare a ranar addu'ar uku a Kano a jiya Asabar. Malama Hauwa ta rasu ne a asibiti a Kano a ranar Laraba, 1 ga Oktoba, 2025 bayan gajeren rashin lafiya. A jiya, wato ranar addu'ar uku, ƙungiyoyin marubuta a ƙarƙashin ƙungiyar ...

Address

19 Chelsea Chibuzor Street Off NICON Junction Maitama
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fim Magazine posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fim Magazine:

Share