Arewa Post

Arewa Post Sahihan labaran ciki da wajen Najeriya.

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN Allah yayiwa Mahaluki Nata'ala Potiskum, (Malam Na Ta'ala) aciki shirin Dadin Kowa N...
02/11/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah yayiwa Mahaluki Nata'ala Potiskum, (Malam Na Ta'ala) aciki shirin Dadin Kowa Na Tashar Arewa 24.

Malam Nata'ala, rãșuwa yanzu a Asibitin Maiduguri

Allah Ya gafarta masa.

Babu Yadda Źà A Yi Na Kaiwa Kasata Harì, Ko Kumà Nà Ķàshè Iyàyèna Kan Wani Zàŕgìn Karyà Na Kisàn Kirìstòcì, Cewar Sojan ...
02/11/2025

Babu Yadda Źà A Yi Na Kaiwa Kasata Harì, Ko Kumà Nà Ķàshè Iyàyèna Kan Wani Zàŕgìn Karyà Na Kisàn Kirìstòcì, Cewar Sojan Amurka Dan Asalin Jihar Kano, Suleiman Isah

KUDIRI EPISODE 6Ku ci gaba da kallon KUDIRI EPISODE 6 yanzu haka a YouTube channel mai suna "Kannwood Exclusive TV"Kudir...
30/10/2025

KUDIRI EPISODE 6

Ku ci gaba da kallon KUDIRI EPISODE 6 yanzu haka
a YouTube channel mai suna "Kannwood Exclusive TV"

Kudiri Labari ne mai dauke da mabambantan darussan rayuwa, wanda idan ka fara kallon shi ba za ka daina ba.

Kar ku bari a baku Labari.

Gaskiyar abunda ya haddasa rikicin masallacin Donga jihar Taraba. ...Ba tsakanin Izala da Dariqa ake fada ba.Wannan masa...
30/10/2025

Gaskiyar abunda ya haddasa rikicin masallacin Donga jihar Taraba.
...Ba tsakanin Izala da Dariqa ake fada ba.

Wannan masallacin da kuke gani a wannan hoton, masallaci ne na JIBWIS NHQ JOS dake garin Donga LGA jihar Taraba.

Masallaci ne da izala ta mallake shi tun 1980s, wanda a yanzu haka aminin sarkin Donga ya sabunta masallacin ma kungiyar Izala NHQ JOS, bayan ya kammala sai ya kira liman zai danka masa keys na masallacin sai yayi tunanin tunda a garin sarki ne kuma kusa da fadarsa shi yak**ata ya dankawa kungiyar Izala duk da kasancewar sarkin ba Musulmi bane amma suna karkashin sa ne.

Bayan sarki ya karbi key na masallaci sai ya nuna shi bazai bawa Yan izalar Jos masallacin ba saidai ya bawa yan darika, sai yan darika s**a ce a'a masallaci kam ae ba nasu bane na izalar Jos ne. Sarki ya sake neman yan izalar Kaduna/Abuja zai basu nan ma s**a ki s**ace masallaci ba nasu bane masallacin.

Magana dai karshe taje kotu aka fara sharia sai ake nemi ayi sulhu a gida sai aka amince aka janye kara daga kotu, wanda karshe bayan janye kara sarki yace sharadin bada keys na masallacin izala dole sai sun amince a canza a limamin masallacin sak**akon shi limamin Dan uwansu ne ma'ana kabilarsu daya da sunan cewa yana zagin su, aka amince masa da hakan don dai a zauna lafiya da sarki ya tashi yace shi limamin masallacin saidai ya kawo daga cikin yan darika ba cikin na'ibai masallacin ba nan ne akace sam bazaiyu ba sbd ba masallacin ba na yan darika bane.

Sanadiyyar haka wanda suke da ikon mallakar masallaci Yan izalar s**a ce zasu bude masallacin su, su fara sallah akaje za,a kwana wajen da niyyar bude wa gobe jiya kenan, a daren wanda ake zaton wanda ba musulmai ba s**a far musu wanda haka yayi sanadiyyar rasa mutum daya tare da jikkata mutum mutum 3.

Gari ya waye anyi janaizar wanda ya rasa ransa za'a Kai shi makabarta aka samu wasu fusatattun matasa s**ayi jifa gidan sarkin Donga s**a fasa glass na gidan wanda hakan ya sake jawo hatsaniya aka sake rasa mutum daya.

Wasu na ganin cewa dogewa da sarki yayi yanada alaqa da wata ziyara da daya daga cikin manyan sarakuna a jahar ya kawo ziyara fadar ranar juma'a inda aka shimafida masa sallaya domin yin sallah a wannan masallacin da yaji masallacin izala ne yace a daga masa sallayarsa baya sallah a masallacin yan izala wanda hakan ake ganin sarkin Donga tsayawa akan wannan maganar, koma dai menene muna kira ga dukkan wanda abun ya shafa da suyi adalci su dankawa kungiyar Izala masallacin ta domin cigaba da ibada k**ar yadda aka saba.

Allah muke roko da ya bamu Lafiya da zaman Lafiya mai dorewa.

Wanda ya rubuta daga jihar Taraba
Daga Abbas Usman

Gwamnan jihar Jigawa ya kaddamar da tallafin Naira 10,000 duk wata ga tsofaffi marasa karfi, masu bukata ta musamman su ...
28/10/2025

Gwamnan jihar Jigawa ya kaddamar da tallafin Naira 10,000 duk wata ga tsofaffi marasa karfi, masu bukata ta musamman su dubu 5,740 a fadin jihar Jigawa.

A kowace karamar hukuma an dauko Dattijai 200, kowace mazaba cikin mazabu 287 na Jigawa, an dauko mutane 20, shine jimilar yawansu ya k**a su dubu 5,740.

TIRKASHI: Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta bayar da Naira biliyan 2.5 ga kasar Najeriya domin su gina filin kwallo...
26/10/2025

TIRKASHI: Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta bayar da Naira biliyan 2.5 ga kasar Najeriya domin su gina filin kwallon kafa a jihar Kebbi da Delta.

Itama Kenya an bata irin wannan kudin domin ta gina.

Ga dai na Najeriya da aka gina a Kebbi an kashe mishi biliyan 1.2😅😂
Ga kuma na Kenya.

KACICI-KACICI: Shin Wace Irin Waya Ce Mutumin Da Ya Fi Kowa Kuɗi A Afrika, Watau Hamshakin Ɗan Kasuwa Alhaji Aliko Dango...
25/10/2025

KACICI-KACICI: Shin Wace Irin Waya Ce Mutumin Da Ya Fi Kowa Kuɗi A Afrika, Watau Hamshakin Ɗan Kasuwa Alhaji Aliko Dangote Ke Riƙe Da Ita?

Gwamnan Bauchi Bala Muhammad Ya naɗa yayansa Adamu Muhammad  Sarkin  Duguri.
24/10/2025

Gwamnan Bauchi Bala Muhammad Ya naɗa yayansa Adamu Muhammad Sarkin Duguri.

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi KanuKungiyar Gamayyar Kungi...
19/10/2025

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi Kanu

Kungiyar Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya (CNG) ta bayyana adawa da s**a mai tsanani kan shirin gudanar da zanga-zangar neman a saki shugaban ƙungiyar IPOB da aka haramta, Nnamdi Kanu.

CNG ta ce wannan yunkuri da wasu shugabannin siyasa da na al’ada na kabilar Igbo, da masu kiran kansu ‘yan gwagwarmaya k**ar Omoyele Sowore, ke jagoranta tare da wasu ‘yan Arewa marasa kishin ƙasa wani makirci ne na yi wa ƙasa karan tsaye da barazana ga zaman lafiya da doka.

Kungiyar ta bayyana cewa Nnamdi Kanu da IPOB sun haifar da mutuwar fiye da mutane 1,200 ciki har da jami’an tsaro sama da 400, sun ƙone ofisoshin ‘yan sanda fiye da 100, kuma sun jawo asarar dukiya da ta haura ₦450 biliyan a Kudu maso Gabas.

CNG ta tunatar da cewa tun daga 2016 Kanu ya kasance mai yada ƙiyayya, tashin hankali da rarrabuwar kai ta hanyar IPOB da rundunarsa ta ESN, inda aka kashe ‘yan Arewa da dama, aka lalata kasuwanci, tare da hana zaman lafiya.

Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da shari’ar Kanu ta tafi yadda doka ta tanada ba tare da matsin lamba na siyasa ba, tare da bukatar jami’an tsaro su hana duk wata zanga-zangar da zata kawo tashin hankali.

CNG ta gargadi ‘yan siyasa da masu daukar nauyin zanga-zangar da cewa za a bincike su, tare da kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya bari a yi masa barazana wajen yin doka bisa ra’ayi ko jin kai.

A ƙarshe, CNG ta jaddada cewa sakin Nnamdi Kanu ba zai kawo zaman lafiya ba, sai dai ya kara dagula ƙasa da karya tsarin shari’a. Ƙasar da ba ta mutunta doka ba, ba za ta samu zaman lafiya ba.

Sa hannu:
Comrade Jamilu Aliyu Charanchi
Koodineta Na Ƙasa, CNG
Abuja, Najeriya

YANZU-YANZU: Tsohon Shugaban Ƙasa, Dr. Goodluck Ebele Jonathan, ya isa garin Zaria domin halartar bikin naɗin sarautar t...
11/10/2025

YANZU-YANZU: Tsohon Shugaban Ƙasa, Dr. Goodluck Ebele Jonathan, ya isa garin Zaria domin halartar bikin naɗin sarautar tsohon mataimakinsa, Arc. Namadi Sambo.

A yau ne ake gudanar da babban bikin naɗa Namadi Sambo a matsayin Sardaunan Zazzau, wanda ke ɗaya daga cikin manyan sarautun gargajiya a masarautar Zazzau, Jihar Kaduna.

Me zaku ce?

KUDIRI EPISODE 4An saki KUDIRI EPISODE 4 yanzu haka a YouTube channel mai suna "Kannwood Exclusive TV"Kudiri Labari ne m...
09/10/2025

KUDIRI EPISODE 4

An saki KUDIRI EPISODE 4 yanzu haka

a YouTube channel mai suna "Kannwood Exclusive TV"

Kudiri Labari ne mai dauke da mabambantan darussan rayuwa, wanda idan ka fara kallon shi ba za ka daina ba.

Kar ku bari a baku Labari.

DA DUMI-DUMI: Mun bada cikakken hadin kai ga hukumar EFCC domin a bincike mu nida sauran ma'aikatan hukumar NAHCON, domi...
08/10/2025

DA DUMI-DUMI: Mun bada cikakken hadin kai ga hukumar EFCC domin a bincike mu nida sauran ma'aikatan hukumar NAHCON, domin tabbatar da gaskiya, tare da jaddada cewa ba za ta kare duk wanda aka samu da laifi ba, inji shugaban hukumar NAHCON Farfesa Sheikh Abdullahi Sale Pakistan.

A yanzu haka EFCC ta k**a wasu manyan jami’an hukumar biyu, su ne Aliu Abdulrazak, kwamishinan kula da ma’aikata da kudi, da Aminu Y. Muhammed, darektan kudi, domin cigaba da bincike.

Rahotanni daga jaridar The Guardian sun bayyana cewa Farfesa Usman ya amsa gayyatar EFCC a babban ofishinta da ke Abuja, inda aka tambaye shi kan yadda aka gudanar da wasu kudaɗe da s**a kai kimanin ₦50 biliyan da s**a shafi shirye-shiryen aikin Hajji na 2025.

Bayan tambayoyi, hukumar ta bashi umurnin komawa gida, amma ta umarce shi da ya rika bayyana kansa a ofishinta kullum yayin da bincike ke cigaba akan hukumar ta su.

Abubuwan da ake bincike a kai sun hada da;

Amfani da ₦25 biliyan wajen biyan kuɗin tantuna a Masha’ir ba tare da cikakken izini ba.

₦7.9 biliyan da aka ce an ware don masaukin gaggawa.

₦1.6 biliyan da aka yi amfani da shi wajen tafiyar matan wasu jami’an gwamnati.

Muna Addu'ar Allah ya bayyana gaskiya.

Address

Nsukka Street Abuja
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Post:

Share