Arewa Bridge Media

Arewa Bridge Media Arewa Bridge Media (ABM): Your leading source for daily news & current affairs in Hausa, Connecting Communities, Amplifying Voices. 🌍

DA ƊUMI-ƊUMI: Sama da Mutum 100,000 Sun Halarci Taron Girmama Takalmin Manzon Allah ﷺ a GombeSama da mutum 100,000 ne s*...
04/09/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Sama da Mutum 100,000 Sun Halarci Taron Girmama Takalmin Manzon Allah ﷺ a Gombe

Sama da mutum 100,000 ne s**a halarci wani gagarumin taron girmama takalmin Manzon Allah ﷺ da aka gudanar a Jihar Gombe, wanda ƙungiyar Sha’irai masu yabon Manzon Allah ﷺ ta shirya.

Taron ya samu halartar malamai da ɗimbin masoya Manzon Allah ﷺ, inda aka gudanar da waƙoƙin yabo da salati cikin yanayi na farin ciki da annashuwa.

An kuma yi kira da a ƙara ƙaunar Manzon Allah ﷺ da koyi da kyawawan ɗabi’unsa, tare da gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Wace fata za ku yi wa mahalarta wannan gagarumin taro?

BABBAR MAGANA: Tinubu Ya Nemi Afuwar ’Yan Najeriya Kan Matakan GwamnatinsaShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nemi afuwar...
04/09/2026

BABBAR MAGANA: Tinubu Ya Nemi Afuwar ’Yan Najeriya Kan Matakan Gwamnatinsa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nemi afuwar ’yan Najeriya idan har wasu daga cikin matakan da gwamnatinsa ta ɗauka sun jawo musu matsala ko kuma s**a yi musu ba daidai ba.

Tinubu ya bayyana cewa gudanar da mulki cikin adalci na iya zuwa da tsauraran matakai, yana mai cewa dole ne kowa ya ji tasirin matakan da ake ɗauka domin tabbatar da daidaito da gyara a ƙasa.

DA ÊUMI-ÊUMI: Sheikh Abdallah Gadon Kaya Ya Gargadi Malamai Kan Maganganun Da Za Su Iya Jawo RikiciSheikh Abdallah Gadon...
04/09/2026

DA ÊUMI-ÊUMI: Sheikh Abdallah Gadon Kaya Ya Gargadi Malamai Kan Maganganun Da Za Su Iya Jawo Rikici

Sheikh Abdallah Gadon Kaya ya yi kira ga malamai da su kiyaye bakinsu da mutuncinsu, musamman wajen magana kan batutuwan da ka iya haifar da rikici tsakanin al’umma.

Sheikh Gadon Kaya ya bayyana cewa matasa na iya ɗaukar mataki kan wasu malamai idan s**a ji an yi musu abin da ya wuce gona da iri, yana mai kawo misalin abin da ya faru a Bodinga, inda wani limami ya fuskanci farmaki.

Ya bukaci malamai da su kasance masu taka-tsantsan wajen furucinsu, domin kauce wa duk wani abu da ka iya haddasa tashin hankali ko rashin zaman lafiya.

— Sheikh Abdallah Gadon Kaya

Ta Mayar Da Sadakin Naira Miliyan Ɗaya Bayan Gwajin Jini Ya Nuna Sun Yi DaidaiMalama Fa’iza Abubakar ta bayyana cewa ta ...
02/09/2026

Ta Mayar Da Sadakin Naira Miliyan Êaya Bayan Gwajin Jini Ya Nuna Sun Yi Daidai

Malama Fa’iza Abubakar ta bayyana cewa ta mayar wa saurayin da za ta aura sadakin Naira miliyan ɗaya da ya ba ta, bayan gwajin jini ya nuna cewa jininsu bai dace da juna ba.

Ta ce ta ɗauki lamarin a matsayin ƙaddara daga Allah, domin ta yi imanin cewa Allah bai ƙaddara saurayin ya zama abokin rayuwarta ba.

Haka kuma, ta gode masa kan kyautar Naira dubu 200 da ya ƙara mata a cikin sadakin.

Zaben 2027: SWMG ta bukaci APC ta ƙarfafa tsarin yaƙin neman zaɓenta a Arewa maso gabashin Najeriya Ƙungiyar South West ...
02/09/2026

Zaben 2027: SWMG ta bukaci APC ta ƙarfafa tsarin yaƙin neman zaɓenta a Arewa maso gabashin Najeriya

Ƙungiyar South West Mandate Group for Asiwaju (SWMG) ta yi kira ga jam’iyyar APC da ta sake duba tare da ƙarfafa tsarin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na 2027, domin ƙara kusantar al’umma da tabbatar da wakilci daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

Ƙungiyar ta kuma jaddada muhimmancin bai wa Arewa maso Gabas dama a tsarin yaƙin neman zaɓen, tare da amfani da ƙwarewa da alaƙar manyan masu ruwa da tsaki a yankin.

Shugaban ƙungiyar, Adebayo Johnson, ya ce nasarar yaƙin neman zaɓen za ta dogara da kyakkyawan tsari, ƙwarewar siyasa, haɗin kai da kuma iya kai saƙon jam’iyyar zuwa ga al’umma.

Ya ce batutuwan da s**a shafi tsaro, aikin yi, ilimi, ababen more rayuwa, wadatar abinci da bunƙasar tattalin arziki ya kamata su kasance cikin manyan abubuwan da za a mayar da hankali a kansu.

“Manufarmu ita ce a ƙarfafa tsarin yaƙin neman zaɓe, tare da amfani da ƙwarewa da hanyoyin sadarwar da ake da su a sassa daban-daban na ƙasar nan,” in ji shi.

Majalisar Shari’ar Musulunci Ta Nuna Damuwa Kan Ci Gaba Da Tsare El-RufaiMajalisar Shari’ar Musulunci ta bayyana damuwar...
02/09/2026

Majalisar Shari’ar Musulunci Ta Nuna Damuwa Kan Ci Gaba Da Tsare El-Rufai

Majalisar Shari’ar Musulunci ta bayyana damuwarta kan ci gaba da tsare tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai.

Majalisar ta jaddada muhimmancin mutunta hakkinsa da kuma tabbatar da cewa ana bin ƙa’idojin shari’a yadda ya kamata a yayin da ake gudanar da shari’ar.

Ku na ganin wannan matsayar za ta iya taimakawa wajen sakin El-Rufai?

KANO: Garin Masoya Manzon Allah (SAW) Kano, birnin da ke cike da masoya Manzon Allah, Annabi Muhammad (SAW), na ci gaba ...
02/09/2026

KANO: Garin Masoya Manzon Allah (SAW)

Kano, birnin da ke cike da masoya Manzon Allah, Annabi Muhammad (SAW), na ci gaba da bayyana ƙauna da girmamawa ga fiyayyen halitta.

Allah Ya ƙara mana soyayyar Ma’aiki (SAW), Ya tabbatar da mu a kan Sunnarsa, Ya kuma azurta mu da samun cetonsa a ranar Lahira. Amin. 🤲

HOTUNA: Yadda Aka Gudanar da Zagayen Takutaha a Birnin GombeAn gudanar da zagayen Takutaha a yau Talata a cikin birnin G...
01/09/2026

HOTUNA: Yadda Aka Gudanar da Zagayen Takutaha a Birnin Gombe

An gudanar da zagayen Takutaha a yau Talata a cikin birnin Gombe, inda aka gudanar da taron a fadar Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar III.

📸 Saifullah Abubakar

Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Duba Tsarin NELFUND, Ya Ce Za A Yi Afuwar Bashin KaratuƊan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar...
01/09/2026

Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Duba Tsarin NELFUND, Ya Ce Za A Yi Afuwar Bashin Karatu

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yi alkawarin sake duba tsarin NELFUND tare da yi wa ɗaliban da s**a cancanta afuwar bashin karatu.

Mai magana da yawunsa, Phrank Shaibu, ya ce Atiku zai mayar da hankali wajen rage tsadar ilimi, domin kada matasa su fara rayuwarsu da nauyin bashin karatu.

Ya kuma soki yadda gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke kallon NELFUND a matsayin mafita ga tsadar ilimi, yana mai cewa lamunin karatu ba ya zama daidai da tallafin karatu ba.

Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Abdulaziz Yari Ya Raba Tallafin Abinci Ga Al’ummaWani matashi mai suna Dan Wanzamai ya wallaf...
01/09/2026

Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Abdulaziz Yari Ya Raba Tallafin Abinci Ga Al’umma

Wani matashi mai suna Dan Wanzamai ya wallafa wani bidiyo a TikTok, inda ya bayyana cewa kwamitin yaƙin neman zaɓen Abdulaziz Yari ne ya ba shi tallafin domin rabawa maza da mata a yankinsa.

Tallafin ya ƙunshi mudun shinkafa da leda guda na taliya, da nufin rage wa al’umma radadin matsin tattalin arziki da suke fuskanta.

Address

Wuse Zone
Abuja
900284

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Bridge Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Bridge Media:

Shortcuts

Share