Abdallah Amdaz

Abdallah Amdaz 𝐄𝐱𝐜𝐞𝐥𝐥𝐞𝐧𝐜𝐲 🌍🕊️💰 Singer • Actor • Writer • Brand Ambassador • Crypto analyst
(9)

07/10/2025

Duk wani abu da muke tak**a da samunsa a wannan rayuwar, musani ba namu bane mu kadai, duk inda kakai ga samun wani abu na jin dadi ko alfarma, wani ya fika wannan abu ko kafi wani shi, kuma duk sonka da shi lokaci yanayi zaku rabu.

“Imani da aiki nagari sune kasonka a duniya”

Yi kokari ya kiyaye su, idan kabarsu suma anan duniya baka tafi dasu lahira ba, hmmmmm 🙃

07/10/2025

Watarana k**ar haka bama wannan duniyar, duk abinda muka samu a wannan duniyar mun tafi mun barshi, idan ba aikin alkairin da mukai, ko wanda muka sana’antawa wasu ba.

“Muyiwa kanmu hisabi kafin lokacin da za’ayi mana hisabi.”

Allah yasa mutuwar mu, ta zama mafi so yiwa daga rayuwar da mukeyi.

07/10/2025

Nayi matukar nishadantuwa da wannan video shi yasa nace bari nayi wannan abin arziki da ku. #

Kayi iya ƙoƙarinka har saika samu gamsuwa!
06/10/2025

Kayi iya ƙoƙarinka har saika samu gamsuwa!

عَنْ مُعَاذِ بْنِ جَبَلٍ رضي الله عنه قَالَكُنْتُ رِدْفَ النَّبِيِّ ﷺ عَلَى حِمَارٍ، فَقَالَ لِي:يَا مُعَاذُ، أَتَدْرِي ...
06/10/2025

عَنْ مُعَاذِ بْنِ جَبَلٍ رضي الله عنه قَالَ
كُنْتُ رِدْفَ النَّبِيِّ ﷺ عَلَى حِمَارٍ، فَقَالَ لِي:

يَا مُعَاذُ، أَتَدْرِي مَا حَقُّ اللَّهِ عَلَى الْعِبَادِ، وَمَا حَقُّ الْعِبَادِ عَلَى اللَّهِ؟

قُلْتُ: اللَّهُ وَرَسُولُهُ أَعْلَمُ

قَالَ: فَإِنَّ حَقَّ اللَّهِ عَلَى الْعِبَادِ أَنْ يَعْبُدُوهُ وَلَا يُشْرِكُوا بِهِ شَيْئًا،
وَحَقُّ الْعِبَادِ عَلَى اللَّهِ أَنْ لَا يُعَذِّبَ مَنْ لَا يُشْرِكُ بِهِ شَيْئًا

قُلْتُ: يَا رَسُولَ اللَّهِ، أَفَلَا أُبَشِّرُ النَّاسَ؟

قَالَ: لَا تُبَشِّرْهُمْ فَيَتَّكِلُو

Abinda wannan Hadisi ya ƙunsa da Hausa:

Mu‘az bin Jabal (Allah ya yarda da shi) ya ce:
Na kasance ina bin Annabi ﷺ a bayan jaki (yana goye da shi), sai Annabi ya ce mini:

“Ya Mu‘az! Ka san menene haƙƙin Allah a kan bayinsa, da kuma haƙƙin bayin Allah a kansa?” Na ce: “Allah da ManzonSa sun fi sani.” Sai Annabi ﷺ ya ce:

“Haƙƙin Allah a kan bayinsa shi ne, su bauta masa kada su yi masa shirka da komai .
Kuma haƙƙin bayin Allah a kanSa shi ne, ba zai azabtar da wanda bai yi masa shirka ba.”

Sai na ce: “Ya Manzon Allah, shin ba zan sanar da mutane wannan bushara ba?” Sai ya ce: “Kada ka sanar musu, kar su dogara (su daina aiki suna tsammanin za a gafarta musu kawai).”

Darussa biyar a takaice daga wannan Hadisi:

Tauhidi shi ne haƙƙin farko da Allah yake da shi akan bayinsa, kuma wajibi ne su kawo wannan haƙƙi.

Yin shirka shi ne, mafi girman zunubi a gurin Allah, wanda akan rasa rahma saboda wannan laifi.

Yana nuna cewa Allah yana da rahama sosai ga wanda yake bauta masa shi kaɗai, batare dayi masa kishiya ba.

Manzon Allah ﷺ yana da hikima, wadda har bai yarda a yaɗa labarin rahama kawai ba, domin mutane kada su daina aiki, shi ke kara nuna maka cewa ana addini ne, Bayna’l khawf wa Raja, hadisin na nuna cewa Ilimi da hikima su ne ginshikin isar da saƙon addini.

Fassarar wasu kalmomi da Sharhin Hadisin, don ƙara fito da ma’ana.

Kalmar Mu‘az ta farko wadda yake cewa: “Na kasance ina bayan Annabi ﷺ akan jaki, sai ya ce mini: ‘Ya Mu‘az, ka san menene haƙƙin Allah akan bayinsa da haƙƙin bayinsa akan Allah?..

Kalmar tana nuna yadda Annabi ﷺ yake nuna ƙauna da kulawa ga sahabbansa. Ta yanda har yana iya ɗaukar Mu‘az a bayansa, kaga kenan ashe duk shugaba, yana da kyau ya fahimci cewa, rashin girman kai da kyautatawa na ƙasa shi ne nagarta, tunda ga wanda yafi kowa ﷺ yana hawa abin hawa daya da sahabinsa, har yana tambayarsa don koyar da shi wasu darussa da bai sani ba.

Malam Ibn Hajar al-‘Asqalani (a Fath al-Bari) ya ce: Annabi ﷺ yana yin hakan ne domin ya sa Mu‘az ya fahimci darasi sosai, ma’ana cikin hikma ta Annabi ﷺ zaka fahimci kenan ana jan mutum ne a jiki, batare da kyara ko tsangwama ba, idan ana son a fahimtar da shi wani ilmi.

Abu na gaba shi ne Tambayar: “Ka san menene haƙƙin Allah a kan bayinsa da haƙƙin bayinsa a kan Allah?”

Tana nuna hikima ta yanda Annabi ﷺ ya fara da tambaya domin ya jawo hankalin Mu’az, Wannan hanya ce ta malamai masu hikima, a tambayi ɗalibi kafin a faɗa masa amsa, domin ya natsu ya kuma bayar da hankalinsa wajen sararo, ta nan zaka ƙara fahimtar irin fasaha da hikimar Allah ya yiwa Manzon Allah ﷺ.

Sannan amsar Annabi ﷺ ya bayar cewa,“Haƙƙin Allah akan bayinsa shi ne su bauta masa, kada su haɗa shi da wani wajen bauta, tare da faɗinsa.“Haƙƙin bayin Allah a kansa shi ne, ba zai azabtar da wanda bai yi masa shirka ba.

Wannan yana nufin cewa, haƙƙin Allah akan bayinsa, kai tsaye wannan yana nufin tauhidi, kenan yin ibada ko bauta ga Allah yake shi kaɗai, ba tare da yin shirka, kuma wannan shi ne tushen dukkan wata bauta a musulunci, k**ar yadda Allah ya ce:

وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ

“Ban halicci aljannu da mutane ba sai domin su bauta mini.” (Surat adh-Dhariyat: 56)

Faɗin Haƙƙin bayi akan Allah kuwa, wannan ba yana nufin Allah yana da wajibi a kansa saboda wani iko na bayi ba, amma saboda karamci da rahama ta Allah, ya alƙawarta rahama da gafara ga wanda bai yi masa shirka ba, ma’ana wanda baya haɗa Allah da kowa a cikin bautarsa.

Imam An-Nawawi ya ce a Sharh Sahih Muslim:

Wannan hadisi yana nuna cewa Allah yana da rahama da alƙawari na adalci, amma wannan haƙƙi ya tabbata ne saboda alƙawarin da Allah Ya yi, ba domin wani ya tilasta masa ba, ko kuma yana da ikon yasa Allah yayi hakan.

Faɗin maganar Mu‘az ta cewa, “Ya Rasulallah, shin ba zan sanar da mutane wannan bushara ba?.

Wannan kai tsaye yana nuna ƙaunar Mu‘az ga mutane, yana so mutane su san wannan ni’ima, saboda sahabban Annabi basa taɓa jin wani ilimi su ɓoye shi don amfanin kansu, Amma kuma Annabi ﷺ ya nuna hikima a amsar daya bawa Mu’az.

“Kada ka sanar da su, kar su dogara.”

Kai tsaye wannan na nuna maka irin yanda Annabi ﷺ ya san halin mutane, ta yanda idan sun ji cewa wanda bai yi shirka ba, ba zai shiga wuta ba, wasu zasu iya kasala wajen bautar Allah, su daina aiki, su dogara kaɗai kan cewa in basuyi shirka ba, bazasu shiga wuta ba.

Don haka Annabi ﷺ ya hana yaɗa wannan bayani a lokacin, har sai mutane sun karɓi tauhidi sosai, sannan sai a sanar dasu wannan ni’ima.

Anan gurin yakai mai karanta wannan dogon rubutu zaka fahimci cewa, Tauhidi shi ne ginshiƙin addinin Musulunci, sannan shirka ita ce babban zunubin da Allah baya gafartawa idan mutum bai tuba ba, sannan zaka ƙara fahimtar Rahamar Allah tana da girma da faɗi sosai, amma kuma aikin ibada yana da muhimmanci, sannan zaka ƙara fahimtar cewa, Ilimi yana da daraja Annabi ﷺ yana koyar da sahabbai ta hanya mai taushi da hikima, batare da kyara ko ɗaga murya ba, kuma zai ƙara nuna maka cewa, ba’a yaɗa ilimi ba tare da hikima ba, k**ar yanda Annabi ﷺ ya hana Mu‘az ya rarraba labarin kafin lokacin da ya dace mutane su sani.

Abun nufi dai wannan hadisin yana nuna cewa, dukkan wata bauta da ibada ga Allah ne shi kaɗai, saboda shike karɓa ya bada sak**ako, matuƙar dai babu shirka, wannan ita ce hanyar tsira da rahama.

Sannan wannan hadisi yana jaddada ma’anar Kalimatut Tauhid ta “Lā ilāha illallāh”

Allah yasa mu dace duniya da lakhira, mu kwana lafiya…

Abdallah Amdaz

Wannan shi ne Allah yasa mu dace…
06/10/2025

Wannan shi ne Allah yasa mu dace…

Lokuta da dama idan nayi rubutu ina ganin yanda mutane suke sharhi, ciki harda gidajen jaridun social media, wasu su rub...
06/10/2025

Lokuta da dama idan nayi rubutu ina ganin yanda mutane suke sharhi, ciki harda gidajen jaridun social media, wasu su rubuta karya s**e nace abinda bance ba, wasu suyi rashin adalci, wasu kuma bama su fahimci abinda nake nufi ba, wasu kuma su dauka wata kungiya ko wani nakeson karewa ko naci mutuncin wasu, ko tallata tawa akidar duk dai suna neman jan hankali i understand that.

Wannan duk idan nagani Kawai murmushi nakeyi na wuce, illa kadan da s**a cancanci na bada masa, sai nayi rubutu don fito da abun a a fili.

Yauma k**ar kullum wani comments na gani na daya daga cikin mabiya hanyoyi da kungiyoyi, yace wai bansan dadin tasu hanyar bane, daya yace naje nayi ilimi a cikinta, ba nazo ina rubuta shirme ba.

Akan kawai nace adaina munana kalami ga Annabi Muhammad Allah ya yarda da shi, kuma nace duk wanda yayi hakan yana da kyau a hukuntashi, bayan ya tuba gami da karyata kansa akan abinda baida ilimi daga alqur’ani da koyarwar Manzon Allah صلى الله عليه وسلم

To a matsayin na mai neman shiryar Allah da son ganin nayi ilimi, tunda yace naje nayi karatu, kuma a media ya wallafa tare da sauran cin mutunci, wanda ni ba hakan nayi ba, to na amshi maganarsa kuma zanje nayi wannan karatu, na hanyar da yake bi wadda yace itace gaba.

To amma ta ina zan fara karatun ga tambayata k**ar haka: 1. ilimin Shari’a 2. ilimin Tariqa 3. ilimin Hakika 4. kona ma’arifa 5. ko kawai na koyi Adabi da Tarbiyya. Sun isheni zama cikakken musulmi?.

Ya banbanta min wanda zan fara da shi, nayi masa alkawarin in sha Allah, wallahil azeem zan koya, kuma zanzo nayi bayani dalla dalla a media din dai in yana da bukatar nayi haka.

Tare da sauran masu goya masa baya wajen zagina.

Har yanzu zan sake maimaitawa, Duk abinda malami zai koya maka, Indai ba alqur’ani bane da hadisan Manzon Allah ingantattu, ka ajiye masa abinsa domin Allah bazai tambayeka su ba a lahira.

Annabi Muhammad صلى الله عليه وسلم shi kadai nasani, shi akai aiko min, kuma shi akace nabi, don haka shi zanbi don nasan cewa shi kadai ne Allah ya bawa tabbacin inka bishi ka tsira. صلى الله عليه وسلم

Ban zagin Akidar kowa donta saba da tawa cewa nakeyi kawai aje ayi karatu, duk abinda kaga na rushe karatu ne ya rushe shi ba son zuciya ta.

Musulmi dan uwan musulmi ne, don haka ku daidaita tsakaninku sai Allah ya daidaita muku zukata.

Idan kana son kaci ribar rayuwa, dole saika koyi abubuwa guda biyu.Abu na farko shi ne “SAURARE” a lokacin da ake sanar ...
05/10/2025

Idan kana son kaci ribar rayuwa, dole saika koyi abubuwa guda biyu.

Abu na farko shi ne “SAURARE” a lokacin da ake sanar dakai wani abu, wannan zai baka damar fahimtar kowanne irin abu, kuma zai hanaka yin reaction akan abinda baka fahimta ba.

Abu na biyu shi ne “NAZARI” wannan zai baka damar gane abu, koda rubutu ne yana da kyau kayi nazarinsa, kafin kace zakayi sharhinsa, ballanta maganar da akeyi da kai koda waninka…

Allah yasa mu dace duniya da lahira!

Bayan anbaka ilimi kayi karatu gun wanda ya dace, to daga nan kuma ya rage ya naka, kayi abinda zai sadaka da Allah lafi...
04/10/2025

Bayan anbaka ilimi kayi karatu gun wanda ya dace, to daga nan kuma ya rage ya naka, kayi abinda zai sadaka da Allah lafiya, ko ka tsaya biyewa labarin shaci faɗi.

Addini shi ne abinda Allah yace ayi da manzonsa ﷺ saɓanin wannan duk wata koyarwa da za’a kawo maka, zato ne da shaci faɗi.

Mu raba kanmu da wane yaji ga wane, ko mun gada daga wane, ko haka mukaga anayi, iyaye da kakanni, duk abinda ba daga Allah da manzonsa ﷺ yake ba, abar musu kayansu kawai!

Karka taɓa ɓata lokacinka akan wata soyayya da bata Allah da manzonsa ﷺ babu wani daɗi na duniya kowanne iri mai ɗorewa, kaɗai abinda za’a tambayeka a lahira shi ne wannan aƙida.

Karka yarda wani yace maka, kayi duk abinda zakai a duniya zai ceceka a lahira, mai ceton da Allah ya bawa lasisi da ikon yin ceto, shi kaɗai ne Muhammad rasulallah ﷺ Jagoran halittun Allah baki ɗaya ﷺ

Mu kwana lafiya ‘yan uwa masu daraja.

Juma’at babbar rana…
03/10/2025

Juma’at babbar rana…

In banda toshewar kwakwalwa da rashin hankali, zaka iya kwaikwayon dokar haraji ta turai, amma bazaka iya kwaikwaiyon ay...
03/10/2025

In banda toshewar kwakwalwa da rashin hankali, zaka iya kwaikwayon dokar haraji ta turai, amma bazaka iya kwaikwaiyon ayyukan hidimtawa kasar da suke ba, tare da kawo ci gaba.

Kaida baka da tsaro, baka da wuta, baka da tsayyayen ruwa, asibitoci nagartattu, ma’aikata a wahale, Jami’an tsaro a wahale, yan siyasa barayi da maciya amana, ko ina rashawa rashawa.

Talakan kasa na cikin ukubu da fatara, a’a kaine mai kawo dokar haraji kuma, su kuma tawagar barayi da ‘yan dumama kujera sun biye maka, kana ganin wata tsiyar kuke aikatawa.

Wacce tsiyar kuka tsinana, banda kara jefa talakan kasa cikin fatara da talauci, amma hakan bai isa ba sai an kakabawa mutane wata sabuwar dokar hmm.

Bakomi akwai Allah.

Allah ya sayani mutum mai son karanta comments, saboda wasu lokutan ana matukar karuwa da abubuwan da baka sani ba, k**a...
02/10/2025

Allah ya sayani mutum mai son karanta comments, saboda wasu lokutan ana matukar karuwa da abubuwan da baka sani ba, k**ar kullum yau ma wani comments ne na wani bawan Allah yasani murmushi.

Abinda yace shi ne, nace bana bin kowacce kungiya ko wata darika game da addini, ni kawai Al-kitabwassunah (QUR’AN & HADITH) nakeyi, sai yace saboda bansan dadin su bane, kuma tayaya zanje gun Allah babu wanda ya k**a hannuna?…

Ina ganin comments din murmushi kawai nayi, nace Allah sarki Abdallah Amdaz ya sani ko Excellency, amma daya san Abdullahi da bai fadi wannan maganar ba.

Amma wallahi shiru na, batare da tankawa masu irin waccan maganganun ba shi ne alkairi, saboda kalmar daya fada, amsoshin bazasu yiwa wasu dadi ba, ni kuma banson tattauna abunda zai haifar da cacar baki, kasancewar kowa da fahimtarsa, amma da ace irin dane sanda nake koyarwa saina bashi amsa..

Any way Allah ya sada kowa da alkairi, rayuwa ce kowa da yanda Allah yake tsara masa tasa.

Address

Abuja
900211

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abdallah Amdaz posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abdallah Amdaz:

Share