Ashura News Update Nigeria

Ashura News Update Nigeria Welcome to Ashura News Update Nigeria your premier source for up-to-date news and captivating news/ photos for Ashura in Nigeria.

Our mission is to keep you informed and engaged with the latest developments and stories. Our team is dedicated to deliveri

Meyasa muke yin tattaki?? Amsa zuwa ga masu Hankali.Bayan an kashe Imam Hussain a karbala, sojojin yazidu sun daddaure r...
12/08/2025

Meyasa muke yin tattaki?? Amsa zuwa ga masu Hankali.

Bayan an kashe Imam Hussain a karbala, sojojin yazidu sun daddaure ragowar iyalan wadanda s**a kashe a karbala babu takalma a kafafun su suna dukan su da bulala ana jansu a kafa tun daga karbala wadda take kasar Iraki a yanzu har zuwa fadar yazid bin Muawiya a Damascus wadda take Siriya a yanzu.

Sannan bayan sun isa an gama abinda za'a yi musu, sun taka da kafafun su ne tun daga fadar yazidu har zuwa karbala domin ziyarar wanda aka kashe ranar da s**a iso shine kuma ranar da suke cika kwana 40 da kashe wa "Yaumu Arbaen" Maulana Imam Ali bin Hussain(as) shiya jagoranta kuma muma sunnar su muke rayawa.

Sahabin manzon Allah(S) Jabir bin Abdullahi Al-ansari shima yayi wannan tattakin a karbala kuma ya ziyarci Imam Hussain(as) sannan Imamai da dama da manyan bayin Allah na gari sun cigaba da raya wannan Al'amari. Misali kamar Shehu Ibraheem Inyass yayi tattakin Imam Hussain a Karbala shi ya fada ma da kansa a rubuce.

Allah ya tashe mu tare da Imam Hussain ranar kiyama ya sanya mu a cikin wadanda Manzon Rahama zai musu Masauki.

• Auwal Salisu

Zuwa yanzu haka an fara gabatar da Tattakin Arba'een Na Yankin Pambeguwa, da amsa ta haɗa da Jos, Lafia, Bauchi, Taraba,...
11/08/2025

Zuwa yanzu haka an fara gabatar da Tattakin Arba'een Na Yankin Pambeguwa, da amsa ta haɗa da Jos, Lafia, Bauchi, Taraba, Adamawa, Gombe da sauransu



Kallin wasu hotunan yadda Tattakin Arba'een ke gudana na yankin Kano.
10/08/2025

Kallin wasu hotunan yadda Tattakin Arba'een ke gudana na yankin Kano.


Rahoton Gaggawa.Tattakin Yankin Kano ya ɗaga da sunan Allah!A yau, al’ummar yankin Kano sun fara  gudanar da tattaki mai...
10/08/2025

Rahoton Gaggawa.

Tattakin Yankin Kano ya ɗaga da sunan Allah!

A yau, al’ummar yankin Kano sun fara gudanar da tattaki mai cike da nufin alheri da haɗin kai. Tattakin, wanda aka fara da ambaton sunan Allah, ya ja hankalin mutane daga sassa daban-daban na birnin.



-16 Safar, 1447
-10 August, 2025.
-Sani Hamisu.

Zallar Hotinan: Tattakin Ashura na Yankin birnin kudu (birnin zone) Jigawa state  Yanda ya gudana a yau Asabar 9/8/2025 ...
09/08/2025

Zallar Hotinan: Tattakin Ashura na Yankin birnin kudu (birnin zone) Jigawa state Yanda ya gudana a yau Asabar 9/8/2025 Wanda miqatin farko s**a. Fara daga garin babaldu zuwa cikin garin birnin kudu miqati na biyu sun fatane da garin tsamiya zuwa garin birnin kudu alhamdulillah anyi lpy an tashi lpy

RAHOTO.Ana ci gaba da gudanar da hidima ga mahalarta Tattakin Arba’in a Maukibin Ofishin Jagora (H) dake Amudi na 1117, ...
05/08/2025

RAHOTO.

Ana ci gaba da gudanar da hidima ga mahalarta Tattakin Arba’in a Maukibin Ofishin Jagora (H) dake Amudi na 1117, kan hanyar Najaf zuwa Karbala. Wannan hidima na gudana ne domin taimakawa masu tattaki wajen sauƙaƙa musu tafiya da gudanar da ayyukan ibada cikin sauƙi da jin daɗi.

Za a ci gaba da hidimar har zuwa ƙarshen lokacin tattaki domin tabbatar da cewa duk mahalarta sun amfana da cikakken kulawa da hidima daga Maukibin.

-Sani Hamisu.
-11 Safar, 1447.
-5 Aug, 2025.

SANARWAR TATTAKI NA BANA 1447/2025 NIGERIYA.Ana sanar da al’ummar mumineen cewa Tattakin Yaumul Ar’ba-een na yankin Kano...
05/08/2025

SANARWAR TATTAKI NA BANA 1447/2025 NIGERIYA.

Ana sanar da al’ummar mumineen cewa Tattakin Yaumul Ar’ba-een na yankin Kano, Potiskum, Azare da Maiduguri zai fara ne a Ranar Litinin 17 Safar kuma zai kare a Ranar Laraba 19 Safar, 1447AH.

Wannan tattaki alama ce ta biyayya da ƙauna ga Sayyidina Imam Hussain (AS), don tuna shahadar sa da juriya akan gaskiya a filin Karbala.

Ku zo mu haɗa hannu mu amsa da Labbaika Ya Hussain tare da sauran ‘yan uwa a cikin wannan tafiya mai albarka.





Ashura News Update Nigeria

Yunwa da kishin ruwa na kashe mutane a Falastinu😭
23/07/2025

Yunwa da kishin ruwa na kashe mutane a Falastinu😭

RAHOTO| YADDA AKA GABATAR DA MAJLISIN JUYAYIN ASHURA WANDA SHURAFA'U S**A SHIRYA A DA'IRAR Cikin alhini da juyayi aka ga...
19/07/2025

RAHOTO| YADDA AKA GABATAR DA MAJLISIN JUYAYIN ASHURA WANDA SHURAFA'U S**A SHIRYA A DA'IRAR

Cikin alhini da juyayi aka gabatar da zaman juyayin Ashura wanda sharifai s**a shirya a babban ɗakin taro na Univasal Basic Of Education (U.B.E) dake garin jimeta babban fadar jihar Adamawa

An fara da bude taro da addu'a wanda sidi Nuhu Loko ya gabatar sai karatun Alkur'ani daga Sayyida Ruƙayya Umar Hamza, sannan Ziyarar Aba Abdullah Hussain (as) Ya Biyo Baya, Daga nan aka baiwa Sha'irul Hussain Shamsu Fudiyyah Tare da Malam Abdullahi Lushi S**a gabatar da waken juyayi tare da ma'atam.

Sidi Umar Hamza Hussainiyya shine ya gabatar da Babban Baƙo Sheikh Sidi Abdullahi Ashura (Bauchi) domin ya gabatar da jawabi kan al'amarin ashura, yayin gabatar da jawabin nashi Sidi Abdullahi yayi jawabai masu sosai rai da sanya zubar kwalla (Hawaye).

Kuna iya kallo cikin hotuna yadda yan'uwa s**a ruɗe da koke-koke suna kiran "YA HUSSAIN" yayin da Sidi Abdullahi yake gabatar da jawabi, Sannan Malam Nasiru (Mai Shayi) ya gabatar da nashi waken juyayin Sidi Umar Hamza ya rufe taron da addu'a.

ٱلسَّلَامُ عَلَيْكَ يَا أَبَا عَبْدِ اللَّهِ ٱلْحُسَيْنِ، قَدْ خَلَعْنَا قُلُوبَنَا عَلَى قَاتِلِيكَ يَا أَبَا عَبْدِ اللَّهِ ٱلْحُسَيْنِ

20 MUHARRAM 1447 - 19 July 2025
Media Forum Yola

Alhamdulillah
07/07/2025

Alhamdulillah

Address

Hussainiya Bakiyyatullah Zaria
Abuja
900001

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ashura News Update Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share