11/09/2026
Kungiyar malaman jami’o’in Najeriya (ASUU) ta yi barazanar shiga yajin aikin gama-gari saboda zargin rashin tura wasu kudaden da ake cirewa daga albashin mambobinta da kuma gazawar gwamnati wajen cikakken aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma a 2025.
Shugaban ASUU na ƙasa, Farfesa Chris Piwuna, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, bayan taron gaggawa na Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) ta ƙungiyar da aka gudanar a Jami’ar Abuja.
Piwuna ya zargi gwamnatin tarayya da na jihohi da rashin cikakken aiwatar da yarjejeniyar FGN-ASUU ta Disamba 2025.
Ya ce malamai na fuskantar rashin tabbas kan lokacin da za a biya albashinsu da kuma adadin abin da za a biya a kowane wata.
Ya yi gargadin cewa idan ba a ɗauki matakan gaggawa da za su magance matsalolin jin daɗin malaman jami’o’i ba, ASUU ba za ta ɗauki alhakin matakin kiran mambobinta zuwa yajin aikin ƙasa baki ɗaya cikin kankanin lokaci ba.
A cewar Piwuna, wasu jihohi da s**a haɗa da Abia, Bauchi, Ekiti, Ogun, Benue, Yobe, Adamawa, Kebbi, Katsina da Borno sun fara aiwatar da yarjejeniyar 2025, yayin da wasu s**a yi alkawarin fara aiwatar da ita a watan Satumba ko Oktoba.
Shugaban ASUU ya kuma bayyana damuwa kan albashin watanni uku da rabi da har yanzu ba a biya malaman jami’o’i ba, daga cikin watanni bakwai da rabi da aka riƙe a lokacin gwamnatin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari.
Ya ce gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta biya albashin watanni huɗu daga cikin bashin, amma rashin biyan sauran kuɗin na ci gaba da jefa malaman cikin matsalar kuɗi da taɓarɓarewar tunani.
ASUU ta kuma nuna damuwa kan kudaden fansho, ƙungiyoyin haɗin gwiwar ma’aikata da kuma kuɗaɗen rajistar ƙungiyar da ake cirewa daga albashin mambobinta, waɗanda ta ce ba a tura su yadda ya kamata tsawon watanni.
Piwuna ya ce ƙungiyar ba za ta ci gaba da kallon yadda tsaiko na ofisoshin gwamnati ke raunana harkar ilimi da jami’o’in ƙasar ba.