Premium Times Hausa

Premium Times Hausa Jaridar PREMIUM TIMES HAUSA ta shahara wajen kawo muku sahihan labarai daga kwararru bayan an tabbatar da gaskiyar labari. Ku ci gaba da bin mu.

Rajistar Hajjin 2027: NAHCON ta sake jaddada wa’adin 26 ga Satumba ga mahajjataWa’adin na ranar 26 ga Satumba yana da mu...
07/09/2026

Rajistar Hajjin 2027: NAHCON ta sake jaddada wa’adin 26 ga Satumba ga mahajjata

Wa’adin na ranar 26 ga Satumba yana da muhimmanci musamman saboda sauye-sauyen da Saudiyya ke yi a tsarin shirya da gudanar da aikin Hajji, inda ake ƙara bai wa gabatar da bayanan mahajjata tun da wuri da kuma amfani da tsarin zamani na zamani wajen gudanar da aikin muhimmanci.

https://hausa.premiumtimesng.com/manyan-labarai/88921-rajistar-hajjin-2027-nahcon-ta-sake-jaddada-waadin-26-ga-satumba-ga-mahajjata.html

Iyalan El-Rufai sun kalubalanci Ministan Tsaro kan zargin kisan 'yan Kudancin Kaduna lokacin yana mulkin jiharIyalin El-...
07/09/2026

Iyalan El-Rufai sun kalubalanci Ministan Tsaro kan zargin kisan 'yan Kudancin Kaduna lokacin yana mulkin jihar

Iyalin El-Rufai sun ce ba sa adawa da s**ar tsohon gwamnan ko yadda ya gudanar da mulkinsa.
Sun ce abin da s**a ki amincewa da shi shi ne zargin cewa El-Rufai da gangan ya shirya kashe-kashen da aka yi a Kudancin Kaduna.

https://hausa.premiumtimesng.com/labarai/88928-iyalan-el-rufai-sun-kalubalanci-ministan-tsaro-kan-zargin-kisan-yan-kudancin-kaduna-lokacin-yana-mulkin-jihar.html

Wani mazaunin Kaduna da ke auren wata ‘yar Morocco ya zargi Sheikh Gumi da ƙwace masa mata, Gumi ya maka shi a Kotu“Mata...
07/09/2026

Wani mazaunin Kaduna da ke auren wata ‘yar Morocco ya zargi Sheikh Gumi da ƙwace masa mata, Gumi ya maka shi a Kotu

“Matata ‘yar Morocco ba ta san kowa a Najeriya ba, kuma babu wanda ya san ta sai saboda ni. Na je Morocco domin neman aurenta, kuma an ɗaura mana aure bisa ƙa’ida tare da amincewar iyayenta da ofishin jakadancin Najeriya.”

https://hausa.premiumtimesng.com/labarai/88926-wani-mazaunin-kaduna-da-ke-auren-wata-yar-morocco-ya-zargi-sheik-gumi-da-%c6%99wace-masa-mata-gumi-ya-maka-shi-a-kotu.html

07/09/2026

Kanun labaran PREMIUM TIMES HAUSA na ƙarshen mako:

Sanatan Kano ɗaya tilo a NDC, Rufa'i Hanga da Kabiru Gaya sun koma APC a yayin da wasu jiga-jigan APC a Bauchi ke barazanar ficewa daga jam'iyyar.

Peter Obi ya ce s shirye yake ya sadaukar da rayuwarsa saboda ci gaban Najeriya a 2027.

Wike ya ce zai shiga cakwalkwalin cakwakiya matuƙar Tinubu ya faɗi zaɓe a 2027

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo ya bayyana yadda ɗakinsa ta gamu da wani irin ciwon kai bayan shan matsattsen ruwan lemo

Ga cigaban kanun labaran...

Ku biyo mu ta - Facebook, X, TikTok, WhatsApp - 08026352700 da Whatsapp Channel.

Premium Times Hausa

Address

Abuja
900281

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Premium Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Premium Times Hausa:

Shortcuts

Share