Sgobeer Empire

Sgobeer Empire Well Come To Sgobeer Empire Gaisawa Online Newspaper

EFCC ta bankado wasu makudan kudade da s**a kai biliyan 37 da ake zargin an wawure a ma’aikatar jin kai a karkashin tsoh...
25/12/2023

EFCC ta bankado wasu makudan kudade da s**a kai biliyan 37 da ake zargin an wawure a ma’aikatar jin kai a karkashin tsohuwar Minista Sadiya Umar-Farouk.

Sadiya Umar-Farouk tana cikin majalisar ministocin gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari

A shekarar 2020, hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta (ICPC) karkashin jagorancin Farfesa Bolaji Owasanoye, ya bayyana cewa hukumar ta bankado Naira biliyan 2.67 na asusun sirri, wanda ake biyan wasu kwalejojin gwamnatin tarayya don ciyar da makarantu yayin da jama'a suke gida saboda COVID-19

Tsohon shugaban ICPC ya ci gaba da cewa an biya kudin ne lokacin da yara ba sa makaranta.

Sai dai duk da bukatar da kungiyar kare hakkin al’umma da tattalin arzikin kasa ta bukaci Sadiya Umar-Farouq da ta buga bayanai da sunayen wadanda ake zargin, amman tsohuwar ministar ta kasa bayyana sunayensu.

WATA SABUWA: Saudi Arebiya ta shiga jerin ƙawayen Amurka wurin kaiwa Dakarun Musulunci tsagin Yaman hari, wadda aka san ...
24/12/2023

WATA SABUWA: Saudi Arebiya ta shiga jerin ƙawayen Amurka wurin kaiwa Dakarun Musulunci tsagin Yaman hari, wadda aka san su da ƴan Hou*thi da s**a datse Ruwan Maliya.

Wannan ƙawancen, Amurka ne ta naima daga sashin ƴan uwanta turawa da wasu rukunin larabawa da take juya akalar su, akan suzo ai gamayyar murkushe Dakarun Musulunci na Yaman ɗin daga farmakin da suke kaiwa kan Jiragen ruwa na Kasuwan Isra**ila, da kuma wadda zasu kaiwa Isra**ila kaya ko daga wace ƙasa ne.

Dakarun Musuluncin na Yaman sunce wannan matakin, sun dauke shine don dakile hare-haren da Isr**la take kaiwa kan yara da mata a Gaza tare da rubde gidajen su, wuraren cin Abinci da kuma Makarantu zuwa Masallatai da Cocina.

Sunce zasu cigaba da wannan Hare-haren har sai komi ya lafa a Gaza dake Falas*dinu, sannan su janye kudiri da Mak**an su, ko kuma su kansu Falasdinawa a Hukumance s**e basa bukatar abinda Yaman take na tallafa musu, sai su janye kai hare-haren.

Wannan shine dalilin da yasa Amurka ta naimi hadakar ƙasashen dake Iyaka da Yaman akan su basu goyon baya wurin murkushe Dakarun na Musulunci, yanzu haka Saudi Arebiya ta shiga jerin ƙasashen da zasu farmaki Dakarun na Musuluncin, saboda hare-haren da suke kaiwa ƙasar ta Isr**la da kuma duk wani jirgin kasuwanci na ruwa da zai kai musu kaya zuwa ƙasar.

Yau Asabar 02 Dec 2023 Mataimakin shugaban Kasar Nigeria H.E Kaishim Shattima ya halacci daurin Auren Dan Gidan tsohon s...
23/12/2023

Yau Asabar 02 Dec 2023 Mataimakin shugaban Kasar Nigeria H.E Kaishim Shattima ya halacci daurin Auren Dan Gidan tsohon shugaban Kasar Nigeria Gen. Sani Abacha wanda aka daura a Jihar Barno.

Cikin yan tawagar daya diba domin su rakashi akwai gwamnan Kano Engineer Abba Kabir Yusuf tare da Gwamnan Zamfara Alh Dauda Lawan Radda.

Muna addu'ar Allah ya sanya dukkanin alkairai Allah ya basu zaman lafiya tare da zuri'a tagari.

Zamani ya nuna, duk kirkinka, mutuncinka... suna biyo bayan idan kana da kuɗi ne, musamman a hidimar zamantakewa ko mu'a...
23/12/2023

Zamani ya nuna, duk kirkinka, mutuncinka... suna biyo bayan idan kana da kuɗi ne, musamman a hidimar zamantakewa ko mu'amala da mata, soyayya, aure...

Mu kuma matasa da rashin iya lissafi, matasa na ƙoƙarin neman kuɗi, amma maimakon a tattala, ko a juya kuɗin ya ruɓanya, sai matashi ya ɓuge da son ya nunawa duniya ai shi yana kuɗi, don ya zama relevant a cikin al'umma, musamman a wurin 'yan mata.

Sai matashi ya fara ɗinka sutura ta kece raini, ya bi yayi a siyan wayar hannu, ya riƙa kashewa 'yan matan kuɗi don ya nuna yana da su, alhali a wani yanayi matsa kansa yake, last coins yake sadaukarwa. Duk da wannan sadaukarwa, da gayu... da za a ce a ya kawo sadaki a ɗaura masa aure ba, ba fa wani abu da ya ajiye, saboda kuɗin na shigo, an sayi shadda, ko hula, ko an canja waya, ko an kashewa yarinya kuɗin anko.

Don Allah muna amfani da hankali,
Mu riƙan rayuwa da nazari.

Sabiu Tunde ne Ya Sanya Hannu A Takaddun Sake fasalin Kuɗin Naira Ba Tsohon Shugaba Buhari ba. Inji Mai Bincike kan Bada...
22/12/2023

Sabiu Tunde ne Ya Sanya Hannu A Takaddun Sake fasalin Kuɗin Naira Ba Tsohon Shugaba Buhari ba. Inji Mai Bincike kan Badakalar CBN

Babban Mai Bincike na musamman kan Babban bankin Najeriya Jim Obazee, ya bayyana cewa sake fasalin kuɗin Naira na baya-bayan nan bai fito Daga hannun Tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ba. Obazee ya tattaro cewa amincewar ta fito ne daga hadimin Buhari, Sabiu Tunde ‘Yusuf’.

Wannan dai na kunshe ne a cikin rahoton karshe na ‘Rahoton Bincike na Musamman kan CBN da Ma’aikatun dake da alaƙa da aka miƙa wa Shugaba Bola Tinubu a Ranar Laraba.

Rahoton ya bayyana Cewa Tsohon Gwamnan Babban Bankin ƙasa CBN, Godwin Emefiele ne tare da Haɗin Gwiwar Sabiu Tunde s**a aiwatar da sake fasalin Naira.

Sabiu Tunde Ɗan uwana ne Tsohon Shugaban ƙasa.

Jaridar KBC Hausa ta ruwaito Cewa Emefiele, Wanda a Yanzu haka yake a Kuje Centre, Ana tuhumarsa da laifin zamba na N1.2bn.bYa kasa cika Ka'idar belin N300m Da Babbar Kotun Birnin Tarayya ta bayar A Ranar 22 ga Nuwamba, 2023.

Sai dai wasu Takardu da Wakilinmu ya samu a Ranar Alhamis din da ta Gabata sun nuna Cewa Tsohon Gwamnan Babban bankin na iya fuskantar Sabon tuhuma kan yadda ake tafiyar da manufofin sake fasalin Kuɗin Naira na CBN.

Buhari Bai Amince da sake fasalin Naira ba
Mai binciken ya Gano Cewa Buhari bai Amince da sake fasalin Naira ba. Sabiu Tunde ne ya fara gaya wa Emefiele a watan Satumba na 2022 ya Duba Batun sake fasalin Naira.

“A Ranar 6 ga Oktoba, 2022, Emefiele ya rubuta wa Buhari Cewa Yana so ya sake fasalin da kuma sake fasalin Kuɗin N1000, N500, da N200.

Tsohon Shugaban yayi tambari amma bai amince da sake fasalin ba k**ar yadda doka ta tanada. Buhari ya Amince a buga Kuɗin Najeriya kawai. A Ranar 15 ga Disamba, 2022 ne kawai aka bayyana sabon tsarin ga Hukumar CBN, bayan da Emefiele ya bayar da kwangilar ga kamfanin buga ma’adanai ta Najeriya a Ranar 31 ga Oktoba, 2022,’’ Takaddun sun Bayyana.

Ance Emefiele ya bai wa De La Rue na ƙasar Birtaniya kwangilar sake fasalin kuɗin.

Mata jamian tsaro na nuna damuwa da yadda galibin mazaje fararen hula ke kin kula su, musamman ma dangantakar da ka iya ...
22/12/2023

Mata jamian tsaro na nuna damuwa da yadda galibin mazaje fararen hula ke kin kula su, musamman ma dangantakar da ka iya kaiwa ga aure.

Ku ba mu matsayinku. Me laifin a rika soyayya da mata sojoji?

Gwamna Uba Sani ya rattaba hannu kan kasafin kudin 2024 yanzu bya zama doka.Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a yau...
22/12/2023

Gwamna Uba Sani ya rattaba hannu kan kasafin kudin 2024 yanzu bya zama doka.

Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a yau, ya sanya hannu a kan kudirin kasafin kudin shekarar 2024 na kimanin Bilyan N458,271,299,477.66.

Gwamnan Ya gudanar da Sanya hannun ne a gidan Gwamnatin Jihar na Sir Kashim Ibrahim dake Kaduna.

22/12/2023

Mutum Dubu Saba'in
70,000 Zasu Shiga Aljannah Ba Tareda Hisabi Ba Inji Manzon (ﷺ)
Allah Yasa Dani Dakai Dake Aciki.

Sau Daya Aka Taba Dandana Mana Kyautar 35,000 An Cutar Damu,Muna shan Wahala – Ma’aikata ga Gwamnatin TarayyaKungiyar ma...
22/12/2023

Sau Daya Aka Taba Dandana Mana Kyautar 35,000 An Cutar Damu,Muna shan Wahala
– Ma’aikata ga Gwamnatin Tarayya

Kungiyar ma’aikata ta tarayya (FWF) ta koka da cewa an dakatar da biyan ƙarin albashin ma’aikata N35,000 da gwamnatin tarayya ke baiwa ma’aikata domin rage radadin tattalin arzikin da ake fama da shi sak**akon cire tallafin man fetur.

Ma’aikatan, a ranar Alhamis din da ta gabata, sun yi zargin cewa Gwamnatin Tarayya ta biya wata daya kacal daga cikin watanni shida da ta yi wa ma’aikata alkawari.

Kodinetan FWF na kasa, Kwamared Andrew Emelieze, a cikin wata sanarwa da aka rabawa DAILY POST ya lura cewa ma’aikatan na cikin mawuyacin hali tun bayan cire tallafin man fetur.

Ya yi nuni da cewa mafi karancin albashi ya rage a kan N30,000 duk wata yayin da farashin ke ci gaba da hauhawa kuma buhun shinkafa yanzu ya haura N60,000.

“Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya a fadin kasar nan suna cikin mawuyacin hali tun bayan cire tallafin man fetur. Kudaden mu na daukar gida sun zama marasa ma’ana sak**akon tsadar rayuwa da kuma faduwar darajar Naira a kodayaushe. Albashi ya kasance iri ɗaya yayin da farashin kaya da ayyuka ya ninka sau uku a cikin wannan lokacin.

“Mun yi mamakin ganin cewa an daina ba ma’aikatan tarayya kason albashin Naira 35,000 da gwamnatin tarayya ta ke ba wa ma’aikatan tarayya don magance matsalar tabarbarewar tattalin arziki da cire tallafin ya haifar. Gwamnatin tarayya ta biya wata daya kacal daga cikin watanni shidan da tayi alkawari.

“Mu ma’aikatan gwamnatin tarayya muna jin cewa gwamnatin tarayya ta ci amanar mu. Mai aikinmu ya yi mana rashin adalci da rashin aminci. Ba a ɗauke mu k**ar muna da komai ba. Mu ’yan kasa ne, ba mabarata ba ne kuma ya k**ata mu cancanci a biya mu albashi mai tsoka. Mu ma’aikatan tarayya muna jin an zamba.

“Ma’aikatan gwamnati sun ji kunyar kudi. Mafi karancin albashi ya rage a kan Naira 30,000 duk wata yayin da farashin komai ke ci gaba da hauhawa kuma buhun shinkafa yanzu ya haura Naira 60,000.

Uwargidan Marigayi Tsohan Shugaban Ƙasa Hajia Turai Umaru Musa Yar'adua Da Abiyar Zamanta Hajia Hauwa Raɗɗa, Yayar Gwamn...
21/12/2023

Uwargidan Marigayi Tsohan Shugaban Ƙasa Hajia Turai Umaru Musa Yar'adua Da Abiyar Zamanta Hajia Hauwa Raɗɗa, Yayar Gwamna Malam Dikko Raɗɗa

INNALILLAHI WA'INNA ILAHIR RJA'UN!!!Anyi Jana'izar Matan Aure Biyu a Yayan Su Bakwai Da S**a Rasa Rayuwar Su Sanadiyar G...
20/12/2023

INNALILLAHI WA'INNA ILAHIR RJA'UN!!!

Anyi Jana'izar Matan Aure Biyu a Yayan Su Bakwai Da S**a Rasa Rayuwar Su Sanadiyar Gobara A Karamar Kudan Dake Jahar Kaduna 🤌

Ubangiji Allah Ya Jikan Su Da Rahama idan Tamu Tazo Ubangiji Allah Yasa Mu Chika Dakyau Da Imani 🤲

Ku gaya min idan har miji zai ce wa matarsa fita ki nema da kanki ki samo muku Abinci ke da Yaranki, Ni nayi iya kokarin...
20/12/2023

Ku gaya min idan har miji zai ce wa matarsa fita ki nema da kanki ki samo muku Abinci ke da Yaranki, Ni nayi iya kokarina ban samo ba, bayan matar bata taɓa yin sana'a ba!

to lasisin me ya bata?

SUBHANALLAH; Yanzu nan aka yi mummunar haɗarin akan hanyar Zaria Road dai-dai Dakatsalle a ƙaramar hukumar Bebej.Ana kir...
20/12/2023

SUBHANALLAH; Yanzu nan aka yi mummunar haɗarin akan hanyar Zaria Road dai-dai Dakatsalle a ƙaramar hukumar Bebej.

Ana kiran mutane da su yaɗa Hoton Motar ko zaa samu Ƴan Uwan masu Motar su biyu. Allah ya Jiƙan rai da gafara.

SUBHANALLA: Motar Mawaki Nagudu Ta K**a Da Wuta, Inda Ta Kone KurmusAllah ya jarrabi shahararren mawakin nan na Jihar Yo...
20/12/2023

SUBHANALLA: Motar Mawaki Nagudu Ta K**a Da Wuta, Inda Ta Kone Kurmus

Allah ya jarrabi shahararren mawakin nan na Jihar Yobe Mohammed Nagudu motarsa ta k**a da wuta yana tsaka da tafiya a hanyarsa ta zuwa mahaifarsa Jakusko dake jihar Yobe, amma cikin hukuncin Allah ya fita lafiya.

Yau Laraba 20 Dec 2023 Gwamnan Kano Engineer Abba Kabir Yusuf zai kaddamar da aikin gadar da zaiyi a Kofar Dan'agundi.Ma...
20/12/2023

Yau Laraba 20 Dec 2023 Gwamnan Kano Engineer Abba Kabir Yusuf zai kaddamar da aikin gadar da zaiyi a Kofar Dan'agundi.

Manufar Aikin Gadar shine rage cunkuso a jihar Kano tare da bunkasa birnin na Kano a matsayin sa na birni mafi Daraja da kyau da yawan mutane Arewacin Nigeria.

Kuma idan baku manta ba za'ayi wadan nan Gadoji ne tare da wasu tituna guda 16 a cikin unguwanin Birnin jihar Kano k**ar na Dabai da Dandinshe da North-northwest tare dana Hotoro layin Cula Dadai sauran su.

YANZU-YANZU: Wannan ita ce, gonar ɗaya daga cikin sahabban manzon Allah (SAW) Salmanul Farisi da ke birnin Madina. |Alla...
20/12/2023

YANZU-YANZU: Wannan ita ce, gonar ɗaya daga cikin sahabban manzon Allah (SAW) Salmanul Farisi da ke birnin Madina. |Allah ya ƙara wa Annabi Daraja.

20/12/2023

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sgobeer Empire posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sgobeer Empire:

Share

Category