Ahlul-bayt Radio/TV

Ahlul-bayt Radio/TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Ahlul-bayt Radio/TV, Media/News Company, Abuja.

Motto: "One falls, thousand rises"

Broadcasting/Publishing/Live Streaming

Za mu ke kawo muku labarun Gabas ta Tsakiya gami da Dakarun Muqawama (Gwagwarmayar Musulunci) kai tsaye daga ingantacciyar tushe.

Mutanen Yemen Sun Sake Fitowa Domin Nuna Goyon Baya Ga Falasɗinawa Al’ummar Yemen sun sake mamaye titunan birnin Sana’a ...
17/10/2025

Mutanen Yemen Sun Sake Fitowa Domin Nuna Goyon Baya Ga Falasɗinawa

Al’ummar Yemen sun sake mamaye titunan birnin Sana’a a cikin gangamin mako-mako na miliyoyi, domin nuna goyon baya da haɗin kai da Falasɗinawa, tare da girmama jarumai da shahidan gwagwarmaya.

Sallar Juma'a a MasallacinAl-Aqsa mai girma, bayan cimma yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Ƙasar Mamaya da Dakarun Gwag...
17/10/2025

Sallar Juma'a a MasallacinAl-Aqsa mai girma, bayan cimma yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Ƙasar Mamaya da Dakarun Gwagwarmayar Musulunci.

YANZU-YANZU: Shugaban Sojan Madagascar ya rantsar da kansa a matsayin sabon shugaban ƙasa bayan hambarar da Gwamnatin fa...
17/10/2025

YANZU-YANZU: Shugaban Sojan Madagascar ya rantsar da kansa a matsayin sabon shugaban ƙasa bayan hambarar da Gwamnatin farar hular kasar.

Kanal Michael Randrianirina ya rantse da kansa a matsayin sabon shugaban ƙasar Madagascar kwanaki kaɗan bayan juyin mulkin da sojoji s**a yi a fadin ƙasar da ke gabar tekun Indiya.

Ya sauya daga sanya kayan soji zuwa sutura ta farar hula domin karɓar mulki daga tsohon shugaban ƙasa Andry Rajoelina, wanda ya gudu daga ƙasar kuma daga baya majalisa ta tsige shi, bayan makonni na zanga-zangar matasa da ke neman gwamnati mai gaskiya ta cigaba da jagorantar ƙasar

An gudanar da bikin rantsuwar a gaban Kotun Tsarin Mulki da ke babban birnin ƙasar, Antananarivo, inda taron jama’a da dama s**a hallara don shaida karbar rantsuwar.

—ATP Hausa

Ƙungiyar Red Cross ta mika gawarwakin shahidai da Kasar Mamaya  ta rikeKungiyar Red Cross ta kai gawarwakin shahidai da ...
16/10/2025

Ƙungiyar Red Cross ta mika gawarwakin shahidai da Kasar Mamaya ta rike

Kungiyar Red Cross ta kai gawarwakin shahidai da ƙasar Mamaya Isra’ila ta riƙe zuwa asibitin Nasser da ke Khan Younis, kudu da Gaza, a cewar Hukumar Wafa.

Ƙungiyar Red Cross ta mika gawarwakin shahidai da Kasar Mamaya  ta rikeKungiyar Red Cross ta kai gawarwakin shahidai da ...
16/10/2025

Ƙungiyar Red Cross ta mika gawarwakin shahidai da Kasar Mamaya ta rike

Kungiyar Red Cross ta kai gawarwakin shahidai da ƙasar Mamaya Isra’ila ta riƙe zuwa asibitin Nasser da ke Khan Younis, kudu da Gaza, a cewar Hukumar Wafa.

‘Yan gudun hijira na ci gaba da komawa yankunansu ta hanyar SalahuddinWasu daga cikin ‘yan gudun hijira a Gaza suna ci g...
16/10/2025

‘Yan gudun hijira na ci gaba da komawa yankunansu ta hanyar Salahuddin

Wasu daga cikin ‘yan gudun hijira a Gaza suna ci gaba da dawowa yankunansu na arewacin yankin ta hanyar Salahuddin, bayan da aka samu ɗan sauƙin tashin hankali a wasu wurare.

Rahoton Hukumar Wafa ya nuna cewa mutane da dama suna tafiya a ƙafa ko da ƙananan motocinsu, suna nufin yankunan da s**a bari a lokacin hare-haren da ƙasar mamaya ta kai.

Yawancin waɗanda ke dawowa suna bayyana fargaba da rashin tabbas, saboda lalacewar gine-gine da kuma ci gaba da barazanar farmaki daga sojojin mamaya.

Sai dai mazauna yankin sun ce suna komawa ne domin duba gidajensu da neman abinci, duk da cewa yanayin tsaro da rayuwa har yanzu yana da matuƙar wahala.

Manyan Motoci dauke da kayan tallafi sun shiga GazzaRahoton Hukumar Wafa ya tabbatar da cewa motocin dauke da kayan abin...
16/10/2025

Manyan Motoci dauke da kayan tallafi sun shiga Gazza

Rahoton Hukumar Wafa ya tabbatar da cewa motocin dauke da kayan abinci da man fetur, tare da tawagar Majalisar Dinkin Duniya, sun isa yankin Gaza ta hanyar Karam Abu Salem.

An ce tallafin na nufin taimaka wa dubban mutane da ke fama da karancin abinci da makamashi a yankin bayan dogon lokaci na rikici da kulle.

Wannan na daga cikin ƙoƙarin ƙungiyoyin agaji na kasa da kasa don rage radadin halin da jama’ar Gaza ke ciki.

Sai dai hukumomin agaji sun ce har yanzu adadin kayan tallafin bai wadatar ba, saboda bukatun jama’a sun karu sosai sakamakon lalacewar rayuwa da gine-gine.

Hoto: WAFA News

Shugaban Iran Ya yi Gargadi ga Makircin MaƙiyaShugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya ce maƙiyan ƙasarsu koyaushe suna nema...
16/10/2025

Shugaban Iran Ya yi Gargadi ga Makircin Maƙiya

Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya ce maƙiyan ƙasarsu koyaushe suna neman ɓarkewar rigima a tsakanin ƙasashen Musulmi don raunana su. Kalaman na zuwa ne, ne bayan an dakatar da fada tsakanin Pakistan da Afghanistan.

Pezeshkian ya furta wadannan kalaman a wani zaman daki na ranar Laraba yayin da yake bayyana matsayin Iran game da tashe tashen hankulan da ke tsakanin makwabtan kasashen biyu na Musulmi.

Kazalika, ya ce al'ummomin Musulmi ba sa son rikici da sabani, wanda shi ne sakamakon makircin maƙiyan da na sahyoniya na duniya.

Ya kara da cewa, tashe-tashen hankulan da ya barke tsakanin Afghanistan da Pakistan ya haifar da matukar damuwa a duk ƙasashen yankin, ciki har da Iran, wadda ke da iyaka da ƙasashen biyu.

Al'ummomin Musulmi, musamman waɗanda ke da tushe da al'adu iri ɗaya a yankin, suna da karfin imani da al'adu da ba za a iya karyawa ba, kuma suna da alhakin yin aiki tare a jiki ɗaya don inganta zaman lafiya adalci, da ci gaba, in ji Pezeshkian.

Ya nanata cewa Iran za ta yi amfani da duk wata hanya da za ta iya da kuma yin iya ƙoƙarinta na rage tashin hankali, inganta tattaunawa, da ƙarfafa dangantakar 'yan'uwantaka tsakanin ƙasashen makwabtan biyu. Ya bayyana cewa, tattaunawa da haɓaka alaƙar 'yan'uwa za su taimaka rage tashe tashen hankulan da ke tsakanin Afghanistan da Pakistan.

Yankin yana buƙatar zaman lafiya, haɗin kai, da haɗin gwiwa fiye da kowane lokaci, in ji Pezeshkian, yayin da ya bayyana yakinin cewa gwamnatoci da al'ummomin Afghanistan da Pakistan za su shawo kan matsalolinsu ta hanyar basira.

Noor Al-haq News
16-10-2025.

Indunusiya ta karyata jita-jitar cewa Shugaba Prabowo na shirin ziyartar kai ziyara bani Yahudu Ma’aikatar harkokin waje...
16/10/2025

Indunusiya ta karyata jita-jitar cewa Shugaba Prabowo na shirin ziyartar kai ziyara bani Yahudu

Ma’aikatar harkokin wajen Indonesia ta bayyana cewa babu wani shiri ko niyya daga shugaba Prabowo na kai wa Bani Yahudu ziyara tana mai jaddada cewa ƙasar ba ta da wata dangantaka ta diflomasiyya da bani Yahudu la’akari da matsayinta a kan ƙasar Falasɗinawa.

Venezuela ta sanar da ƙirƙirar sabbin yankunan  a tsaro kan iyakarta da ColombiaKasar Venezuela ta nuna  fargabar baraza...
16/10/2025

Venezuela ta sanar da ƙirƙirar sabbin yankunan a tsaro kan iyakarta da Colombia

Kasar Venezuela ta nuna fargabar barazana daga wadanda Amurka ke marawa baya a yankin,

Shugaba Nicolás Maduro na Venezuela ne ya jaddada haka inda ya ce shi mutuncin ƙasarsa shi ne gaba inda ya ƙaddamar da wani sabon shiri na ƙarfafa tsaron yankin.

Hakan ya zo ne bayan rahotannin da ke nuna cewa Amurka ta sake kai hare-haren sirra a yankin

Noor Al-haq News
16-10-2025.

An samu mummunan faɗa tsakanin dakarun Pakistan da na Afghanistan a daren Talata a yankin Spin Boldak na Afghanistan da ...
15/10/2025

An samu mummunan faɗa tsakanin dakarun Pakistan da na Afghanistan a daren Talata a yankin Spin Boldak na Afghanistan da Chaman na Pakistan, wanda ya yi sanadin mutuwar da raunata mutane da dama.

Ɓangarorin biyu sun ɗora wa juna alhakin tayar da rikicin, wanda ya ƙara ta’azzara rikicin da ke tsakanin ƙasashen da a da s**a kasance abokan hulɗa.

Shin me kuke ganin ke haddasa maimaita irin waɗannan rikice-rikice tsakanin Pakistan da Afghanistan?

—WAT News

An yi jana’izar marigayi Salim Abu Aisheh mai shekaru 57A yau Laraba an yi jana’iza tare da kai Saleem  zuwa makwancinsa...
15/10/2025

An yi jana’izar marigayi Salim Abu Aisheh mai shekaru 57

A yau Laraba an yi jana’iza tare da kai Saleem zuwa makwancinsa na ƙarshe a garin Zababdeh, dake yankin Jenin, kamar yadda rahoton kamfanin labarai na Wafa ya nuna.

(Hoto: Muhammad Mansour / Wafa)

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ahlul-bayt Radio/TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share