12/06/2026
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a jawabinsa na Ranar Dimokuraɗiyya ta 12 ga Yuni, ya amince cewa Najeriya na fuskantar ƙalubalen tsaro, yana mai cewa:
“Dimokuraɗiyya ba za ta yiwu ba idan babu tsaro.”
Shugaban ya ambaci hare-hare da sace-sacen mutane da s**a faru a sassa daban-daban na ƙasar nan, ciki har da sace ɗalibai a jihohin Oyo da Borno, tare da alƙawarin ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ta’addanci, ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da sauran barazanar tsaro.
Ya ce gwamnatinsa ta ɗauki sama da jami’an ’yan sanda 50,000 aiki tare da ƙarfafa ayyukan rundunonin tsaro domin inganta tsaro a faɗin ƙasar.
Dangane da tattalin arziki kuwa, Tinubu ya kare sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatinsa ke aiwatarwa duk da wahalhalun da ’yan Najeriya ke fuskanta.
Ya ce waɗannan matakai suna da muhimmanci wajen farfaɗo da tattalin arziki, ƙarfafa kuɗaɗen gwamnati, jawo masu zuba jari da kuma shimfiɗa tubalin ci gaba mai ɗorewa.
Shugaban ya jaddada cewa sauye-sauyen sun fara haifar da sak**ako mai kyau, tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da su yayin da take neman hanyoyin rage raɗaɗin da jama’a ke ciki.
Tinubu ya yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da nuna haƙuri da haɗin kai, yana mai cewa ingantaccen tsaro da ci gaba da gyaran tattalin arziki su ne ginshiƙan ci gaban ƙasa da dorewar dimokuraɗiyya.