15/10/2025
PDP Ta Rasa Gwamnoni 2 a Rana Daya; Gwamna Diri da Kakakin Majalisa Sun Fice
Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP. Ya ce ya yanke wannan shawara ne bayan ya yi dogon shawarwari da shugabannin jihar.
Ya bayyana hakan ne a wani taro da aka yi a gidan gwamnati, inda Kakakin Majalisa Abraham Ingobere, mataimakinsa, da wasu ‘yan majalisa guda takwas s**a halarta.
Gwamnan ya ce: “Na fice daga PDP. Ina tare da Kakakin Majalisa, mataimakinsa da sauran ‘yan majalisar da ke tare da mu.”
Kakakin Majalisa Ingobere ya ce su ma sun goyi bayan ficewar gwamnan, kuma mafi yawan ‘yan majalisar jihar sun yarda da wannan mataki.