White Connect GL

White Connect GL Maraba daku,
Wannan kafar labarai ce Ilimantarwa, Nishadantarwa, fadakarwa gami da tallata hajojinku.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJ'UN 😭Mijin ya shiga dakin matarsa a asibiti,ya kalli fuskarta wacce ta canza kala sbd cuta...
02/06/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJ'UN 😭

Mijin ya shiga dakin matarsa a asibiti,
ya kalli fuskarta wacce ta canza kala sbd cutar da take fama da ita
Sai ya tambayeta cikin hargowa:
“Kin karanta rahoton?”

Ta ce: “Eh.”
Sai ya sake tambaya:
“Kin san kina da cutar kanjamau (AIDS)?”

Ta gyada kai kawai,
sannan ta cigaba da kwanciya cikin wahala,
ta janyo bargo ta rufe kanta.

Ya aje wata wasiƙa a ƙarƙashin matashinta,
sannan ya juya zai fita daga ɗakin yana cewa:
“Wata wasiƙa ce a ƙarƙashin matashin ki idan kin ga dama ki duba.”

Bayan ya fita kadan,
ta janyo wasiƙar, ta fara karanta ta.
Sai ta gani a rubuce

“na sakeki saki daya 1.2.3

Ta jefar da wasiƙar, ta lulluɓe kanta da bargo.

Yayin da yakusa barin asibitin,
likitan da ke kula da matarsa ya gan shi,
ya kira shi:
“Alhaji...”

Sai mijin ya juya yana tambaya cikin rashin damuwa:
“Kana da wani magana ne akan matar da ta riga ta zama tsohuwar mata ta,?

Domin na sake ta.
Zuwa yanzu iyayenta za su kula da ita b ni ba.”

Likitan ya kalle shi sosai sannan ya ce:
“Ba haka abin yake ba.
Kai kanka kana bukatar a duba jininka.”

Ransa ya baci, sosai Amma beyi gardama.

Bayan an kammala gwaje-gwajen,
likitan ya dawo da sak**ako.

“Alhaji,” ya ce cikin takaici,
“Da bakin ciki nake fada maka cewa kai ma kana ɗauke da cutar da tsohuwar matarka ke da ita…”😳

Sai mijin ya katse shi cikin mamaki:
“Shin ta shigar min da cutar?”

Likitan ya ce:
“A’a, kai ne ka sa mata cutar.
Domin Kwanan cutar a jinin ka ya fi tsawon lokacin da cutar ta fara bayyana a gareta.
Dan haka Kai ne ka shigar mata da cutar.”

“Bayan ’yan kwanakii kai ma zaka fara ganin alamomin cutar.”

Mijin ya yaga rahoton, ya fice da gudu daga asibitin,
ya hau motarsa, ya tafi da gudu har kura tana tashi a bayan sa.

A daren nan mai sanyi gashi ana ruwa,
matar tana kwance a gadon asibiti,
iyayenta da ’yan uwanta suna gefenta.
Ta kalli fuskokinsu da farin jikin mutuwa yana bayyana a jikinta.
Da ƙyar ta iya magana:

Tana cewa “Ya Allah, Ka sani ban taɓa saba maka ba ta wan

02/06/2025
Wata kishiyar yinta annoba ce a gida wata kuma Alkhairi ce. Ance kishiyar Uwah ce tayi wannan aikin wayyo hanjinah innal...
02/06/2025

Wata kishiyar yinta annoba ce a gida wata kuma Alkhairi ce. Ance kishiyar Uwah ce tayi wannan aikin wayyo hanjinah innalillahi wa'annah ilaihin raji'un. Dan Allah a kamota itama a buga mata wannan kusar taji. Saboda ba danta bane shine zata kasheshi. Allah ya wulakanta duk wanda yayi wannan aika aikan😭😭😭

Allah yabaka lafiya 🤲🤲😢😢😢

Wata mata ta je gurin Annabi Dauda (AS) cikin fushi, ta ce masa: "Ya Annabin Allah! Ubangijinka yana da adalci kuwa?Sai ...
29/05/2025

Wata mata ta je gurin Annabi Dauda (AS) cikin fushi, ta ce masa: "Ya Annabin Allah! Ubangijinka yana da adalci kuwa?

Sai ya ce: "Kwarai kuwa, mai adalci ne, ba ya zalunci.

Menene labarin ki? Sai ta ce: "Ni bazawara ce, ba ni da mai taimaka min, ga 'ya'ya mata guda 3 marayu. Ina ciyar da su ne da sana'anar saƙa da nake yi.
Jiya na yi sakata mai yawa, na daure a wani jan tsumma, zan tafi kasuwa na sayar, na sami abin da zanciyar da kaina da 'ya'yana, sai wani tsuntsu ya zo ya wafce daga hannuna. Kuma ba ni da komai, ga marayu.😭

Kafin Annabi Dauda (AS) ya ce komai ga wannan mata, sai ga wasu mutane su 10 sun shigo, kowannen su da Dinare 100 a hannunsa, s**a ce:

"Ya Annabin Allah! Muna son za mu yi sadaka da wannan kudi... Sai Annabi Dauda (AS) ya ce da su: "Me ya faru?" Sai s**a ce:
"Muna cikin jirgin ruwa, sai iska mai karfi ta taso, jirgin namu ya bule, sai muka dinga ambaton Allah, kuma muka yi bakancen idan Allah Ya tseratar da mu, za mu yi sadaka da Dinare dari-dari.

Muna cikin wannan hali, sai wani tsuntsu ya jeho mana wani jan tsumma, a cikin tsumman akwai wata saƙa.
Sai muka toshe bular da wannan saƙar, Allah Ya tseratar da mu.

Sai Annabi Dauda (AS) ya yi godiya ga Allah, ya fuskanci wannan mata ya ce mata: "Ubangijinki mai adalci ne... Idan kin yi saƙar nawa k**e siyarwa?"

Sai ta ce: "Dirhami daya".
Sai ya ce: "Ga Dinare 1000, Allah Ya sayi saƙarki, karbi ki je ki ciyar da 'ya'yanki".

ALLAH YA WARWARE MANA MATSALOLINMU, YA KYAUTATA MANA TATTALIN ARZIKINMU.

AKWAI BUKATAN A YAYATA WANNAN KISSAR, KO WASUN MU ZA SUJI KARFIN GUIWA.
*
*Sanna muna rokon ku arzuki kuyi following 💫 wannan account Don Allah ✍️.......

24/05/2025

Shine Maganar Gaskiya

18/05/2025

🫡🧏

Wani mutum ya ce:Na gayyaci ɗaya daga cikin makwabtana zuwa gidana domin mu ci abincin buda-baki tare. A farko ya ƙi zuw...
16/05/2025

Wani mutum ya ce:
Na gayyaci ɗaya daga cikin makwabtana zuwa gidana domin mu ci abincin buda-baki tare. A farko ya ƙi zuwa, amma na dage har ya yarda ya zo.

Da muka isa gidana, na kai shi ɗakin baƙi, na ce masa:
"Ji daɗin kanka, ka ɗauka gidan k**ar naka ne."

Bayan ɗan lokaci kaɗan, lokacin azumin Magariba ya matso. Na fara shirya teburin cin abinci, na jera faranti da abinci iri-iri masu daɗi waɗanda matata ta dafa — abinci masu ƙamshi da ban sha’awa.

Bayan ƴan mintuna, aka yi kiran sallar magariba. Sai muka zauna kan teburin, muka fara buda baki.
Amma na lura makwabcin nan yana cin abinci cikin baƙin ciki, yana ɗan ɗanɗanawa cikin jinkiri sosai.

Sai na kalle shi nace:
"Lafiya dai, ya Abu Abdallah? Me yasa kake cin abinci haka? Kana jin kunya ne? Ko kuwa ba ka jin yunwa?"
Sai ya yi min murmushi kawai, ya ci gaba da cin abincinsa.

Ni kuma na ci har na ƙoshi, cikina ya cika. Kuma abinci da yawa ya rage a tebur. Sai na ce masa:
"Ka ƙara ci, ya Abu Abdallah. Ni zan shiga cikin gida in shirya, mu tafi masallaci tare."

Na shiga ciki don shirya kaina. Amma kafin in fito, na leƙa ta taga mai madubin ɓoye (wanda daga ciki ba za a gan ni ba, amma ni zan iya ganin waje).

Abin da na gani ya karyar min da zuciya, idanuna s**a cika da hawaye ba da niyya ba.
Na gan shi yana tarawa ragowar abinci a cikin wani roba.

Na fito cikin gaggawa nace:
"Me kake yi haka, ya Abu Abdallah? Me yasa kake tara abinci haka?"

Karshen labarin ya na a comments section ko kubi profile Dina don fallow da zaran an ɗaura.....👎

A zamanin da, wata mata ce da mijinta suke zaune a wani qaramin gida. Da ta samu ciki, sai mijinta ya gaya mata da cewa ...
16/05/2025

A zamanin da, wata mata ce da mijinta suke zaune a wani qaramin gida. Da ta samu ciki, sai mijinta ya gaya mata da cewa idan abinda ta haifa mace ce – zai saketa nan take sannan ya kashe yarimyar. Wannan magana ta gigita zuciyar matar – ta shiga baƙin ciki, tana tsoron ranar haihuwar ta.

Kullum tana tambayar kanta:
"Yanzu idan na haifi mace fa? Shin zai iya kashe ta da gaske? Kuma ni ya kore ni?"

Lokaci ya cigaba da tafiya k**ar shekaru. Kowane minti ya fi mata rana tsawo. Zuciyarta cike da fargaba da damuwa. Kafin kwana uku da maganar lokacin haihuwarta yazo, mijinta kuma ya tafi wajen aiki kuma ya ce zai dawo nan kusa.

Haihuwar ta zo cikin dare – kuma abin da ta haifa kuwa? Jaririya! Mace ce!

Ta shiga cikin matsanancin baƙin ciki. Kuma kafin mijinta ya dawo, cikin lokaci kasa da awa goma bayan haihuwa, wata zuciya ta shiga zuciyarta – shaidan ya rinjaye ta ya shawarce ta da cewa ta kawar da jaririyar kafin mijinta ya iso, in ba haka ba – masifa zata biyo baya.

Ta ɗauki jaririyar – wadda bata fi awa goma ba da haihuwarta – tana kuka k**ar tana neman taimako, ta kai ta makabarta! Ta ajiye ta can cikin ƙabari. Ta kalli fuskar yarinyar, ta rungume ta, ta yi mata bankwana da hawaye na ƙarshe... sannan ta tashi ta bar ta, tana jin kuka mai tsanani na jaririyar yana bin bayanta...

"Mamaaamaa... mamaaaa..." – a yadda jariri kan iya kiran uwa da hawaye.

Ta koma gida da zuciya mai ɓaci da rudani. Tana ta tambayar kanta:
"Me zan ce wa mijina? Yaya na aikata haka? Yaushe ya dace in gaya masa?"

Daren farko da ta kwana bayan hakan, ta yi mafarki.
Ta ga jaririyarta tana kuka da ƙarfi, tana buƙatar nono – tana kiran ta da yunwa.
Ta farka tana kuka, tana kiran:
"’Yata! ’Yata!"

Har zuwa safiya bata iya bacci ba. Daren na biyu, mafarkin ya maimaitu.
Ta ga jaririyar tana kuka cikin ƙunci.
Daren na uku kuma haka. Mafarki iri ɗaya – cike da kukan wahala da yunwa.

Sai ta tafi wurin wata abokiyar aminta, ta gaya mata duk abin da ya faru – daga ciki har zuwa mafarkai. Abokiyar ta shiga baƙin ciki sosai. Ta ce mata:

"Kije ki dawo da jaririyarki, Wataƙila har yanzu tana buƙatar ki... kuma zuciyar ki bata samun sukuni sai kin sauke nauyin da ke kanta."

Bayan ta sha wahala da mafarkai, matar ta tafi tare da abokiyarta zuwa wurin wani malami (shehy) a garin. Ta gaya masa duk abin da ya faru. Shehun ya firgita sosai, ya ɗaga murya cikin mamaki yana cewa:

“Me kika aikata, ya mace?! Ki tashi yanzu ki tafi makabarta ki duba jaririyarki!!”

Ba tare da ɓata lokaci ba, ta tafi cikin rudani da tsoro, tana tunani da fatan ta tarar da wata mu’ujiza.

Yayin da take hanyar zuwa makabarta, shehun ya sake tambayarta:

“Menene sunan jaririyarki?”

Ta yi shiru, saboda a gaskiya ba ta taɓa ba mata suna ba. Sai ta ce da karamin murya:

“Faatima... sunanta Faatima.”

Shehun ya ce da ƙarfi:

“Ki je yanzu ki bincika lafiyarta!”

Ta isa makabarta cike da damuwa da fatan samun mafita, ta bude inda ta binne jaririyar — kuma abin mamaki!

Jaririyar tana raye!!!

Ta ɗauke ta da sauri cikin kuka mai ƙarfi, ta rungume ta da ƙarfi, ta ɗora nononta a bakinta don ta sha. Amma yarinyar tana cikin halin wahala sosai. Ta koma gida da gaggawa tana kuka, tana kokarin ceto ’yarta daga mutuwa.

Domin ci gaban labarin kuduba qasan comment, kokuma ka shiga cikin profile dina

14/05/2025
LABARI MAI ƊAUKE DA DARASIYa yi aure, kuma a daren farko na auren (daren farko na zama da matar), sai ya gano cewa ba bu...
13/05/2025

LABARI MAI ƊAUKE DA DARASI

Ya yi aure, kuma a daren farko na auren (daren farko na zama da matar), sai ya gano cewa ba budurwa bace.

A ranar farko ya shiga cikin tashin hankali, ita kuwa tana kuka tana roƙonsa da roƙon Allah Maɗaukaki da ya yafe mata, k**ar yadda ya riga ya shirya ta kafin a ɗaura auren.

Tana kuka sosai tana roƙonsa ya ji tausayinta, ya rufa mata asiri. Ta rantse masa cewa ta tuba domin Allah, ba domin mutane ba. Kuma tana cikin ƙunci, sai dai ta samu nutsuwa ne lokacin da ta k**a hanya ta gaskiya da addini.

Saboda yawan kukanta da roƙonta, sai ya ce mata:

“Zan bar ki tare da ni tsawon watanni 7, sai daga baya na kirkiro wata ‘ƙaramar matsala’ a gidan da za ta kai mu ga saki. Amma ki tabbata cewa ba zan taɓa ki ba, ke kuma ba za ki taɓa ni ba. Za mu zauna k**ar abokai ne kawai.”

Wannan ne mafita da ya yanke bayan duk ƙoƙarin da ta yi na riƙonsa.

Ba ya kusantar ta sam. Duk da haka suna fita tare zuwa wuraren cin abinci, kasuwa, har tafiya suna yi. Amma yana kallonta k**ar abokiyar tafiya ne kawai, ba mata ba.

Bayan da watanni 7 s**a wuce, sai lokacin saki ya yi. Ta shirya kanta, tana kuka, hawaye yana zuba k**ar ruwan sama.

Tana jiran ta ji kalmomin nan:
“Na sake ki… Na sake ki… ke sakakka ce.”

Sai ya ce:
“Ba zan sake ki yanzu ba. Mu je wurin da zan kai ki, in isar da ke gidan iyayenki, sai a can in sake ki kafin ki sauka daga mota.”

S**a tafi, ta ɗauki duk kayanta. Amma sai ya tsaya a gaban wani gidan kwalliya.

Ta ce masa: “Meye wannan?”

Ya ce:
“Ina so ki shiga ki yi gyaran jiki da kwalliya k**ar yadda kika kasance a ranar farko da na aure ki.”

Ta ce:
“Ba daidai bane, iyayena zasu tambayeni, kuma me yasa zan yi kwalliya lokacin da zan dawo gida bayan an sake ni?”

Ya ce:
“Wannan shine sharaɗi na. Idan kin ƙi, zan gaya musu dalilin ainihin sakinki.”

Tayi matuƙar jin tsoro, sai ta amince. Ta shiga wurin kwalliya ta gyara kanta k**ar amarya.

Da ta koma mota, sai ya ce mata ta buɗe drawer a cikin mota. Ta buɗe — sai ta ga takardun tafiy

12/05/2025

Da dumi'dumi: Dan majalisa Hon Abdulmalik Zannan Bungudu Ya Gwangwaje Amaryar Mawaki Dauda Rarara Ayshatul Humairah Da K...
08/05/2025

Da dumi'dumi: Dan majalisa Hon Abdulmalik Zannan Bungudu Ya Gwangwaje Amaryar Mawaki Dauda Rarara Ayshatul Humairah Da Kyautar Sabuwar Mota kirar BMW

Address

Abuja

Telephone

+2348032801782

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when White Connect GL posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to White Connect GL:

Share