
02/06/2025
INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJ'UN 😭
Mijin ya shiga dakin matarsa a asibiti,
ya kalli fuskarta wacce ta canza kala sbd cutar da take fama da ita
Sai ya tambayeta cikin hargowa:
“Kin karanta rahoton?”
Ta ce: “Eh.”
Sai ya sake tambaya:
“Kin san kina da cutar kanjamau (AIDS)?”
Ta gyada kai kawai,
sannan ta cigaba da kwanciya cikin wahala,
ta janyo bargo ta rufe kanta.
Ya aje wata wasiƙa a ƙarƙashin matashinta,
sannan ya juya zai fita daga ɗakin yana cewa:
“Wata wasiƙa ce a ƙarƙashin matashin ki idan kin ga dama ki duba.”
Bayan ya fita kadan,
ta janyo wasiƙar, ta fara karanta ta.
Sai ta gani a rubuce
“na sakeki saki daya 1.2.3
Ta jefar da wasiƙar, ta lulluɓe kanta da bargo.
Yayin da yakusa barin asibitin,
likitan da ke kula da matarsa ya gan shi,
ya kira shi:
“Alhaji...”
Sai mijin ya juya yana tambaya cikin rashin damuwa:
“Kana da wani magana ne akan matar da ta riga ta zama tsohuwar mata ta,?
Domin na sake ta.
Zuwa yanzu iyayenta za su kula da ita b ni ba.”
Likitan ya kalle shi sosai sannan ya ce:
“Ba haka abin yake ba.
Kai kanka kana bukatar a duba jininka.”
Ransa ya baci, sosai Amma beyi gardama.
Bayan an kammala gwaje-gwajen,
likitan ya dawo da sak**ako.
“Alhaji,” ya ce cikin takaici,
“Da bakin ciki nake fada maka cewa kai ma kana ɗauke da cutar da tsohuwar matarka ke da ita…”😳
Sai mijin ya katse shi cikin mamaki:
“Shin ta shigar min da cutar?”
Likitan ya ce:
“A’a, kai ne ka sa mata cutar.
Domin Kwanan cutar a jinin ka ya fi tsawon lokacin da cutar ta fara bayyana a gareta.
Dan haka Kai ne ka shigar mata da cutar.”
“Bayan ’yan kwanakii kai ma zaka fara ganin alamomin cutar.”
Mijin ya yaga rahoton, ya fice da gudu daga asibitin,
ya hau motarsa, ya tafi da gudu har kura tana tashi a bayan sa.
A daren nan mai sanyi gashi ana ruwa,
matar tana kwance a gadon asibiti,
iyayenta da ’yan uwanta suna gefenta.
Ta kalli fuskokinsu da farin jikin mutuwa yana bayyana a jikinta.
Da ƙyar ta iya magana:
Tana cewa “Ya Allah, Ka sani ban taɓa saba maka ba ta wan