Aminiya

Aminiya Sahihin Shafin Jaridar Aminiya. Jaridar Hausa Ta Rukunin Kamfanin Media Trust; Mamallakin Jaridar Daily Trust, Trust TV Da Kuma Trust Radio.
(412)

Burinmu shi ne: Zama wata babbar kafar yada labarai a duniya wadda za ta samu amincewar jama'a. Bayani kan kamfanin da ke wallafa Aminiya:
Kamfanin Media Trust da ke Abuja ne ya ke wallafa jaridar Aminiya da shafukan Aminiya na intanet. Shi ne kuma ya ke buga jaridar Daily Trust, da Daily Trust on Saturday, da Daily Trust on Sunday, da kuma shafukan intanet na Daily Trust. Adireshin Hedikwatar Kamfanin:
Lamba 20, P.O.W. Mafemi Crescent, Gundumar Utako, Abuja.

Tsohuwar ’Yar Majalisar Wakilai, Hajiya Azumi Namadi Babeji, ta nuna damuwa kan yadda ake ci gaba da tauye damar mata a ...
10/06/2026

Tsohuwar ’Yar Majalisar Wakilai, Hajiya Azumi Namadi Babeji, ta nuna damuwa kan yadda ake ci gaba da tauye damar mata a harkokin siyasa, inda ta bayya cewa duk da ana ƙarfafa musu gwiwar shiga siyasa, amma hana su samun damar lashe zaɓe.

Tsohuwar ’Yar Majalisar Wakilai, Hajiya Azumi Namadi Babeji, ta nuna damuwa kan yadda ake ci gaba da tauye damar mata a harkokin siyasa, inda ta bayya cewa duk da ana ƙarfafa musu gwiwar shiga siyasa, amma hana su samun damar lashe zaɓe.

HOTUNA: Yadda ruwan sama ya yi ɓarna tare da yin ajalin wata dattijuwa mai shekara 50 tare da jikarta a garin Bara a yan...
10/06/2026

HOTUNA: Yadda ruwan sama ya yi ɓarna tare da yin ajalin wata dattijuwa mai shekara 50 tare da jikarta a garin Bara a yankin Katsinawa da ke Ƙaramar Hukumar Kirfi a Jihar Bauchi.

10/06/2026
Wata ’yar kasuwa a Jihar Gombe, ta tsallake rijiya da baya, biyo bayan hari da ake zargin saurayinta ya kai mata da gudu...
10/06/2026

Wata ’yar kasuwa a Jihar Gombe, ta tsallake rijiya da baya, biyo bayan hari da ake zargin saurayinta ya kai mata da guduma har cikin gidanta tare da yunƙurin kashe ta.

Wata ’yar kasuwa a Jihar Gombe, ta tsallake rijiya da baya, biyo bayan hari da ake zargin saurayinta ya kai mata da guduma har cikin gidanta tare da yunƙurin kashe ta.

’Yan bindiga sun kai hari makarantar gwamnati da ke Iluke Bunu a Jihar Kogi yayin da ɗalibai ke tsaka da rubuta jarabawa...
10/06/2026

’Yan bindiga sun kai hari makarantar gwamnati da ke Iluke Bunu a Jihar Kogi yayin da ɗalibai ke tsaka da rubuta jarabawar WAEC, inda mutum uku s**a rasa rayukansu.

Daga cikin waɗanda aka kashe akwai mataimakin shugaban makarantar, Ganiyu Anifowose, da wasu mutum biyu.

’Yan sanda sun ce maharan sun mamaye yankin ne a kan babura, amma jami’an tsaro sun yi artabu da su tare da tilasta musu tserewa zuwa cikin daji.

Rundunar ta ƙara da cewa an kashe ɗaya daga cikin maharan, yayin da ake ci gaba da bincike kan rahotannin da ke cewa an yi garkuwa da wasu ɗalibai da mazauna yankin.

Hukumar Daidaiton Jinsi ta Jihar Filato (PLASGEOC), ta bayyana cewa wasu ’yan mata, ciki har da ɗaliban manyan makarantu...
10/06/2026

Hukumar Daidaiton Jinsi ta Jihar Filato (PLASGEOC), ta bayyana cewa wasu ’yan mata, ciki har da ɗaliban manyan makarantu, na sayar da ƙwayoyin haihuwarsu domin samun kuɗi.

Shugabar Sashen Yaɗa Labarai ta hukumar, Nene Dung ce, ta bayyana hakan a wani shirin rediyo na Hausa da aka gudanar a Jos, inda ta ce hukumar ta gano wata cibiyar kula da matsalolin haihuwa da ke karɓar ƙwayoyin haihuwa daga matasa mata.

A cewarta, wasu mata na karɓar kuɗi tsakanin Naira 120,000 zuwa Naira 150,000 bayan an cire musu ƙwayoyin haihuwar.

Ta ce wasu daga cikinsu na amfani da kuɗin wajen sayen wayoyi masu tsada ko biyan wasu buƙatun rayuwa.

Dung ta bayyana wannan lamari a matsayin cin zarafi da kuma take haƙƙin mata.

Ta ce hukumar na ƙoƙarin wayar da kai a cikin al’umma da makarantu kan illolin wannan ɗabi’a.

Ta ƙara da cewa hukumar ta gana da shugabannin wasu manyan makarantu a jihar, ciki har da Jami’ar Jos, domin faɗakar da ɗalibai game da hatsarin sayar da ƙwayoyin haihuwa.

A ƙarshe, ta yi kira ga iyaye da sauran masu ruwa da tsaki da su riƙa kula da tarbiyyar ’ya’yansu mata, tana mai cewa rashin kulawa na daga cikin abubuwan da ke haifar da irin wannan matsala.

’Yan bindiga sun kai hari a wata makarantar sakandare da ke Jihar Kogi da safiyar ranar Laraba, inda s**a kashe mutum uk...
10/06/2026

’Yan bindiga sun kai hari a wata makarantar sakandare da ke Jihar Kogi da safiyar ranar Laraba, inda s**a kashe mutum uku tare da yin awon gaba da wasu ɗalibai.

’Yan bindiga sun kai hari a wata makarantar sakandare da ke Jihar Kogi da safiyar ranar Laraba, inda s**a kashe mutum uku tare da yin awon gaba da wasu ɗalibai.

Rundunar ‘yan sandan Babban Birnin Tarayya Abuja ta bayyana cewa ta jami’anta sun yi nasarar hallaka wasu ‘yan bindiga b...
10/06/2026

Rundunar ‘yan sandan Babban Birnin Tarayya Abuja ta bayyana cewa ta jami’anta sun yi nasarar hallaka wasu ‘yan bindiga biyu tare da ceto mutane biyar da aka sace a ƙauyen Paze da ke unguwar Byazhin a ƙaramar hukumar Bwari.

Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindigar sun sace mutane biyar ciki har da wani fasto, yayin da wani ɗan sa-kai mai suna Shuaibu Yerima ya rasa ransa bayan ‘yan bindiga sun kai hari ƙauyen na Paze a ranar Alhamis.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin kafa wani kwamiti na musamman wanda Shugaban Ma’aikatan Fadar Shuga...
10/06/2026

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin kafa wani kwamiti na musamman wanda Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila zai jagoranta don shirin yaƙi da cutar Ebola da sauran abubuwa masu fitowa da ke barazana ga lafiyar al’umma.

Shugaban ya kuma bayar da umarnin fitar da kuɗi Naira biliyan 10 nan take domin aikin shirin ko-ta-kwana.

Wannan na cikin wata sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga, ya fitar a Abuja ranar Talata.

Alhaji Muhammad Maibarga, malamin JIBWIS da aka sace a Jihar Kebbi, ya rasu a hannun ’yan bindiga bayan shafe lokaci a t...
10/06/2026

Alhaji Muhammad Maibarga, malamin JIBWIS da aka sace a Jihar Kebbi, ya rasu a hannun ’yan bindiga bayan shafe lokaci a tsare a maɓoyarsu.

An sace shi ne tare da wani tsohon shugaban APC na Ƙaramar Hukumar Koko/Besse, yayin da iyalansa ke ƙoƙarin tara kuɗin fansar da masu garkuwar s**a nema.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, ta tabbatar da rasuwar malamin, bayan rahotannin da s**a nuna lafiyarsa ta taɓarɓare kafin mutuwarsa.

Address

20 P. O. W Mafemi Crescent, Utako District
Abuja
900001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aminiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Aminiya:

Share