10/06/2026
Hukumar Daidaiton Jinsi ta Jihar Filato (PLASGEOC), ta bayyana cewa wasu ’yan mata, ciki har da ɗaliban manyan makarantu, na sayar da ƙwayoyin haihuwarsu domin samun kuɗi.
Shugabar Sashen Yaɗa Labarai ta hukumar, Nene Dung ce, ta bayyana hakan a wani shirin rediyo na Hausa da aka gudanar a Jos, inda ta ce hukumar ta gano wata cibiyar kula da matsalolin haihuwa da ke karɓar ƙwayoyin haihuwa daga matasa mata.
A cewarta, wasu mata na karɓar kuɗi tsakanin Naira 120,000 zuwa Naira 150,000 bayan an cire musu ƙwayoyin haihuwar.
Ta ce wasu daga cikinsu na amfani da kuɗin wajen sayen wayoyi masu tsada ko biyan wasu buƙatun rayuwa.
Dung ta bayyana wannan lamari a matsayin cin zarafi da kuma take haƙƙin mata.
Ta ce hukumar na ƙoƙarin wayar da kai a cikin al’umma da makarantu kan illolin wannan ɗabi’a.
Ta ƙara da cewa hukumar ta gana da shugabannin wasu manyan makarantu a jihar, ciki har da Jami’ar Jos, domin faɗakar da ɗalibai game da hatsarin sayar da ƙwayoyin haihuwa.
A ƙarshe, ta yi kira ga iyaye da sauran masu ruwa da tsaki da su riƙa kula da tarbiyyar ’ya’yansu mata, tana mai cewa rashin kulawa na daga cikin abubuwan da ke haifar da irin wannan matsala.